https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU YOUNG TALENTED WRITERS ASSOCIATION (YOTA/002) Bright pens 3rd batch. (2025) Bismillahirahmanirrahim. *Labarin BUZU ƙirƙirarren labari ne, duk wani sashi na labarin na iya faruwa a gaske, idan ya yi kamanceceniya da rayuwar wani ko wata arashi ne.* ⚠️ Labarin mallakina ne, ban yarda wani ko wata, su yi amfani da shi ta kowace irin siga ba, sai da izina. AISHA ADAM (Ayshercool) 08081012143 Arewabooks; Ayshercool7724 Watpad: ayshercool7724 Page 1 Dare malafar rana, kowa ya bika ya shirya maka. Danƙareriyar mota ce, ƙirar highlander baƙa, take ta kwarara gudu a saman kwalta, tamkar hanyar domin direban kawai aka yi ta. Gefe da gefen hanyat baki ɗaya babu komai, banda yashin sahara, sai busassun bishiyu jefi jefi. Kasancewar dare ne, wata ya kai kwana goma sha huɗu, ya haska ko ina, ga taurari sun yi wa sararin samaniyar ado. Titin ta tsakiyar sahara ya ratsa, wadda yashin saharar ya bayar da sassanyan yanayi. "Kilomètre nawa ce ta rage mana ne?" Direban ya waiwayo ya kalli mai maganar wandaa fuskarsa a rufe take cikin rawani ya ce "Bai fi 95 kilomètre ba" "Dans  quelques minutes ?? (Nan da wani lokaci?)". "Bai fi awa ɗaya ya rage ba" "Dole fa mu ƙarasa dai-dai lokacin da aka umarce mu, ni ina tsoron ma kar ya farka" Ya yi maganar yana haska fuskar wani matashin mutum, da yake kwance a jikinsa ya haɗa gumi, cikin wani yanayi kamar bacci kamar suma, sai dai  yadda yake gumi ya nuna a wahale yake baccin, babu in da yake motsi a jikinsa, sai ƙirjinsa da yake ɗagawa yana sauka lokaci zuwa lokaci, numfashinsa yana fita da ƙyar. Ya kai hannunsa, ya ɗora a kan ƙirjin matashin, idan zuciyar sa ta buga sau ɗaya, sai ta jima kafin ta sake bugawa. Sai dai duk bugawar da za ta yi, da ƙarfi take bugawa tamkar za ta tsaga ƙirjinsa ta fito dummm!. Cikin damuwa ya ce "Lowalli, sai ka ƙara gudu fa, kar ya mace mana, bugun zuciyarsa raguwa fa yake yi" Lauwalli ya jinjina kai yana ƙara gudun motar. ***** Misalin ƙarfe shida da mintuna goma sha biyar na safiyar ranar asabar, ɗaki ne madaidaici, wanda ya samu kyakkyawan ginin ƙasa ma ƙwarin gaske, duk da kasancewar sa na ƙasa, amma adon da aka yi masa ya bayyanar da darajarsa. Can daga kusurwar ɗakin wata matashiyar mace ce, kwance a kan matsakaiciyar katifa ta yi ɗaiɗai ta na bacci, zaninta ne kawai ya kare bayyanar tsiraicinta, amma idan ta yi kyakyawan yinƙurin za ta yi tsirara. Iya ƙarfinta take ƙoƙarin tashi daga baccin, amma abu ya gagara a sakamakon sleep paralysis, wanda a hausance da kuma fahimta ta mutane suke kira da dannau, a cewar mutane wani aljani ne mai suna dannau, yake danne mutum ya kasa motsi, alhali idanunsa biyu, kamar a zahiri haka ta din ga ganin abubuwan da suke faruwa da ita, amma ta kasa motsawa. Tamkar an cire mata wani abu mai nauyi, haka tayi firgigit ta tashi zaune, ta na mayar da numfashi, a sakamakon fafutukar da ta sha, kafin ta samu ta iya farkawa daga nannauyan baccin da take yi mai kama da na mutuwa. Ware ido tayi, ganin yadda gari ya yi haske, ba tare da ta gabatar da sallar asuba ba. Ta yinƙura za ta sauka daga kan katifar, ta ji duk gaɓoɓinta na yi mata ciwo, jikinta kamar wadda aka yi wa dukan tsiya, zanin jikinta ya yaye. Shiru ta yi ta na ƙoƙarin tuna abin da ya faru a daren jiya, a iya saninta ninkin kaya take yi, ba ta kai ga kwanciya ba, daga nan ba ta san abin da ya faru ba. Ita dai ta san sanye take cikin suturarta, amma yanayin da take ganinta a ciki, yana sanya mata wasi-wasi. A hankali ta tashi ta gyara zaman zanin ta nufi banɗakin da yake cikin ɗakin, domin ta kintsa jikinta ta gabatar da sallar asuba. ***** Sannu a hankali yake buɗe idanunsa, da suke yi masa wani irin zugi saboda hasken da ya cika masa su, sai ya ji tamkar hasken wani baƙon abu ne a cikin idanun nasa. Yanayin ya yi masa kama da farkawa cikin wata duniya ta daban. A hankali ya daina jin zugin da idanun suke yi masa, ya buɗe su tanagrau, ya ƙurawa wurin da yake ido, yana ƙoƙarin gano a ina yake. Wani dogon mutum ne baƙi, fuskarsa ɗauke da jan rawani hannunsa rike da ɗan ƙaramin kofi, ya shigo cikin tantin. Jifa yayi da kofin hannunsa, ya nufi mutumin da yake kwance da matuƙar hanzari. Taimaka masa yayi ya tashi zaune, fari ne amma ba tas ba, irin mai sirkin yellown nan, ya na da ɗan siririn hanci, dai-dai da siririyar fuskarsa, sai gashin baki kaɗan da ya haɗe da ɗan madaidaicin gemunsa, sai kuma manyan idanuwa da yake da su, da su ka kaɗa su ka yi jawur tamkar jini zai kwararo daga cikinsu. Zaman da ya yi, ya bawa gashin kansa damar kwanciya a kafaɗarsa zuwa bayansa, tamakar mace. A hankali ɗayan ya sauke rawanin fuskarsa ya ce "Sannu ya jikin naka?" Maimakon ya bashi amsa, sai ya yi shiru ya na bin sa da kallo. "Akwai abin da yake yi maka ciwo ne?" A hankali ya motsa bakinsa ya ce "Ina ne nan?" Baƙin ya kalli gurin sannan ya mayar da idonsa kan shi ya ce "Mun shigo Nigeria ne yanzu haka" "Nigeria?" Ya maimaita. "Eh Nigeria" ya amsa masa. Ya yi shiru ya na ƙoƙarin tuna a ina ma ya taɓa jin sunan. "Ya na ga ka yi shiru ne? Ka gane ni ma kuwa?" Ya ɗago ya kalle shi a hankali ya girgiza masa kai alamar a'a. "Innalillahi wa innalillahi raji'un, ba ka sanni ba ka ke nufi?" Ya jinjina masa kai. "To ka san sunanka?" Yayi shiru yana ƙoƙarin yin tunani, amma ya gaza tuna komai, sai ma wani irin rugugi da ya ji a cikin kansa tamkar an yi aradu, hakan ya tilasta masa dafe kansa yana rintse idanunsa. "Shi kenan ya isa, ba sai ka tuna ba, amma ka san alwala da salla?" Ya ɗaga masa kai alamar eh, ba tare da ya yi magana ba. "Sallar asuba raka'a nawa ce?" Ya ɗaga masa yatsunsa guda biyu. "Azahar fa?" Ya nuna masa huɗu. "Ka san salla, amma ba za ka iya tuna komai ba bayan haka?" "Eh" ya amsa a taƙaice. "Shikenan, ka zo ka yi alwala sai ka rama sallolin da suke kanka, ka yi ƙasaru, tun da mun yi tafiya mai nisa daga Nijar". Shiru ya yi ya na son tuna a ina kuma ya taɓa jin sunan Nijar, sai kawai ya bar shi a sunan da ya ji ya faɗa ɗazu ne Nigeria. Cif ya jera sallolin kamar yadda wanda suke tare da shi, ya gaya masa waɗanda su ka tsere masa. Ya ɗaukko abinci ya bashi, ya saka hannu ya karɓa ya fara ci. Bayan ya kammala cin abincin, ya tsiyaya masa shayin da ya dafa a cikin ɗan ƙaramin kofi ya miƙa masa. Ya karɓi shayin ya fara sha, hakan ya sanya shi fara ƙoƙarin tuna wani abu, amma abu ya ci tura. Bayan ya gama shan bunun, ɗayan ya fito da wani ƙyalle ya tattare masa dogon gashinsa, ya naɗe masa shi, sannan ya naɗa masa rawani ya kamo hannunsa su ka fito daga cikin tantin. Tsayawa yayi, ya yi wa wurin ƙuri da ido, jeji ne babu kowa a wurin, sai bishiyu sai kuma wani raƙumi da yake gefe a ɗaure ya na ta taune-taune. Ya tafi ya kwanto raƙumin, ya janyo akalarsa zuwa gabansa, ya kalle shi ya ce "Ka san menene wannan?" Ya jinjina kai. "Mene ne shi?" "*Le chameau*" (Camel/ raƙumi ne) Yayi sassanyar ajiyar zuciya ya ce "Hau mu tafi" ya taimaka masa, ya hau kan raƙumin, shi kuma ya ja akalar raƙumin su ka tafi. ***** Tafe take sannu a hankali, ta na ratsa matsakaitan gidajen da su ka haɗu suka samar da rukunin gidajen da suka samar da wani ɓangare na unguwar. Mamakon ruwan saman da aka tafka kamar da bakin ƙwarya awanni kaɗan da suka shuɗe, ya wanko datti da ƙazanta daga mabanbanta wurare, sai dai rashin kyakyawar hanya da magudanan ruwa, ya sanya ruwan shiga gidajen mutane, wani kuma ya kwanta a cikin layuka, ta yadda ba a iya banbance kwata da hanya, duk sun haɗu sun shafe. Gabanta ne yayi mummunar faɗuwa, abin da take tsoro da fargaba ta tarar, tun da hadarin nan ya taso aka fara ruwa, hankalinta ya kasa kwanciya. Daga in da take ta na hango tsakiyar tsakar gidansu, a sakamakon fiye da rabin katangarsu ta zube. Ta lallaɓa ta ƙarasa, duk mutanen gidan su na tsaye sun yi cirko-cirko su na jajanta abin da ya faru. Sai dai abin da ta tarar ya fi wanda ta hanga daga nesa, domin ƙarasawarta gidan ke da wuya, ta tarar rijiyar gidan ta burma, ta haɗe da masai kasancewar daf da juna suke, daga in da aka yi rijiyar babu tazara. Wani babban mutum ne ya fito daga cikin banɗakin, ya dubi matashiyar ya ce "Nana kin dawo?" Jiki a sanyaye ta amsa ta ce "Eh Baba" "Kin ga abin da ya faru ko" Nana ta ce "Eh baba, tun ina makaranta da aka fara ruwan nan, hankalina yake tashe nake a tsorace" "Ai mu na cikin jarrabawa, yanzu lalubawa zaki yi, ɗan abin da aka samu a hannunki, ki kawo a samu ko katangar a fara tayarwa". Saroro Nana ta yi baki buɗe tana bin Baba da kallo, duk da ba abin mamaki bane ba, jin hakan daga bakinsa, cikin ƙarfin hali ta ce "Baba dubu bakwai ne fa albashin nawa, kuma yau goma sha ɗaya ga wata, ko sisi ba ni da ita ka manta dubu biyar ka karɓa ka bani dubu biyu" "Kai Nana, ina ki ke kai kuɗi ne? kullum da an taɓa ki babu, ai shikenan sai ku zauna haka, duk wanda ya ji turotso sai ku bi maƙwabta ko ku tafi jeji ku yi, ni ba ni da yadda zan yi" Wata mata da tun da su ka fara maganar ba ta yi magana ba, sai yanzu, ta kada baki ta ce "Ai kuwa sai ka san yadda za ka yi, haka zamu dauwwama mu na gantalin yawon kashi a maƙwabta kai ko kunya ma ba ka ji, Nana ka tsare ka na ta baka kuɗin da zaka ɗaga katangar gidanka, kai fa take miƙawa albashin nata, dubu bakwan nawa take, ka bi ka kashe zuciyarka, wallahi dole ka nemi yadda za ka yi" Nana dai ba ta sake cewa komai ba, ta nufi hanyar wurin kwananta, ta na jiyo ɗaya daga cikin yaran gidan ya na cewa "Abu mai sauƙi, a samu ƙaton bokiti kawai, kowa ya din ga juyewa a ciki, a tara a sayar zazzafan taki ne fa, tsaf za a samu kuɗin ɗaga katangar gidan nan, gwargwadon ƙwazonmu wurin tarawa da yawa gwargwadon..... "Za ka rufe mini baki, ko sai na daka ka a wurin nan, shashasha mara tunani kawai" Baba kuwa waje ya yi, saboda tijarar da mama ta fara yi masa, maƙwabta duk sun fito waje, ana jajanta ɓarnar da ruwan yayi a layin, tare da jajantawa su Baba abin da ya faru da su. Jiki a sanyaye ta shiga wani ɗan madaidaicin ɗaki, bakinta ɗauke da sallama. 'yan mata biyu ne a kwance su na danna waya, da ƙyar ɗaya ta amsa, ɗayar kuwa ko ɗagowa ba ta yi ba. Nana ta ajiye jakar hannunta tare da faɗin "Jamila, ashe ruwa ne yayi mana gyara haka?" Jamila ta ce "Aikam, ɓarna ma ba ƙarama ba, kin ganni nan lissafi nake yi yadda zan tsallake na bar gidan nan, wannan abin kunya da mai yayi kama, ace in da zaka tsuguna ka juye najasarka babu, sai dai ka bi maƙwabta, wannan gidan Allah kaɗai ya san lokacin da za a gyara shi". Nana ta nemi wuri ta zauna ta ce "Idan kin bar gidan nan, ina za ki je?" Cike da takaici Jamila ta ce "Ko ma ina ne, tun kan jarabar talauci ta kashe mutum, kullum gida babu cigaba ba a ɗauki ɗawainiyarka ba, amma ana nema a wurinka" Nana ta girgiza kai ta ce "To, Allah ya sa mu dace, ya bamu mafita". "Amin, kalli wurin kwanciyar ki ma duk ya jiƙe, nan wurin ma zuba yake yi". Nana ta kalli wurin tare da yin ajiyar zuciya, ba tare da ta ce komai ba. Haka gidan su Nana suka kwana, rabin katanga a zube, kowa ya zo wucewa ya na kallon cikin gidan. Washegari da asuba da 'yan kame-kame su ka kama ruwa, wasu su ka zagaya maƙwabta wasu kuma suka yi a wani wurin, su ka yi alwala su ka gabatar da sallar asuba. Tun daren da abin ya faru maƙwabta suke shigowa yi musu jajen abin da ya faru. Jamila sai masifa take yi tana mita, "Wallahi na san ikon Allah ne kawai zai sanya a gyara katangar nan, haka zamu ci gaba da zama da zubabbiyar katanga, ni matsalar banɗakin nan ba ta dame ni ba sama da katangar nan, duk asirinmu a tone, kodayake wane asiri ne ma da mu, banda damin talauci da tsiya" Nana ta na jin ta ba ta ce uffan ba, ta ɗaukki Alqur'aninta tana dubawa. ***** Tsura masa ido yayi, yana nazarinsa, sannu a hankali yake cin abincin gabansa, ya gama ya wanke hannunsa, ya gyara zaman rawaninsa ya rufe fuskarsa. Habu ya dube shi ya ce "Ka ƙoshi?" Ya jinjina masa kai alamar eh. "Yanzu za ka iya tuna sunanka?" Ya girgiza kai alamar a'a. Habu yayi ajiyar zuciya yana sake jinjina lamarin, ya sake kallonsa ya ce "Babu abin da yake iya zuwa kanka ka tuna?" "Eh" ya faɗa a taƙaice. "Shikenan, kar ka matsawa kanka sai ka tuna wani abu, amma a duk lokacin da ka tuna wani abu ka sanar mini, dole in fara tunanin nema maka magani kafin yin komai, amma sai mun samu wurin masu amana" shi dai yayi shiru bai ce masa komai ba. Ya saka hannu a aljihun babbar rigarsa, ya ɗaukko waya, ya duba wata lamba, ya kara wayar a kunnensa. Mintuna kaɗan ya amsa sallamar sannan ya ɗora da cewa "Mun iso Nigeria tun jiya, yanzu mene ne abu na gaba?" Ya ɗan yi shiru tsawon wasu mintuna sannan ya ce  "Ka tabbatar babu matsala? Ba na son azo a samu matsala, dole ayi taka tsantsan da lamarin nan, kafin mu san ma in da za mu nufa neman maganin" ya sake yin shiru sannan ya ce "Shikenan, ina sauraronka" har ya kammala wayar bin sa yake yi da ido, kamar zai yi magana amma bai ce komai ba. ***** Kwanaki uku suka shuɗe ana tsilla-tsillar makewayi a gidan Malam Isa, wato gidansu Nana, ƙarshe katanga sai buhu aka saka aka rufe ta. Cikin ikon Allah, maƙwabta su ka yi ta kawo masa gudunmuwa, sai dai idan kuɗi ne sai ya karɓa ya saye abin sa, tun da matarsa rabi ta fuskanci haka, ta sanya shi a gaba da tijara, da masifar ya fito da kuɗi a san abin yi. Nana ta na ɗaki tana shafa mai, amma hankalinta yana kan su Baba sa suke ta faɗa. "Amma rabi da kuɗaɗen gudunmuwar nan, nake ta baku kuɗin cefane, kuɗin nan fa ba isa za su yi ba ayi aikin katangar nan" Ta hayyaƙo masa cikin ɗaga murya ta ce "Wane cefanen, ba wata tsiyar ka bamu ba, makewayi ya gagari mutum, kamar mun fi kowa talauci a tsukin nan" Nannauyar ajiyar zuciya Nana ta yi, ta tashi ta ƙarasa shirinta, ko sallama ba ta yi wa su Baba ba ta fice, dan wannan rashin girmamawar da suke yi wa juna ba ƙaramin ƙona mata rai yake yi ba. Kamar yadda ta saba, tana ƙule a gefe guda, tana dudduba cikin Alqur'ani, yayin sa sauran 'yan ajin suke ta tilawarsu daban. A hankali ta fara jin jikinta yana wani irin sanyi, ta fara jin tamkar daga wata duniyar take jiyo karatun 'yan ajin nasu. "Nana" ta ji muryar Amira ƙawarta. Tayi jarumta ta ɗaga kai ta kalleta, Amira ta zauna a kusa da ita ta ce "Na biya miki makaranta, ashe abin da ya faru kenan, Allah ya mayar da alkhairi ya tsare gaba, na tarar da baba yana ta faɗa, wai kowa ya nemi in da zai tafi kafin Allah ya hore masa abin da zai gyara gidan" Sai Nana tayi da gaske take fahimtar me Amira take faɗa, ganin yadda Nana ta ƙura mata idanu ko ƙiftawa ba ta yi, ya sanya ta ɗan matsa baya kaɗan ta ce "Nana lafiya kuwa? Ko baki da lafiya ne?" Ta girgiza mata kai, ba tare da ta ce komai ba. Amira ta koma gefe ta ɗaukko Alqur'aninta, ta koma nesa da Nana. kamar wadda ake zarewa laka, take ji, wani irin sanyi jikinta yayi zuciyarta ta din ga bugawa cikin matsanancin tsoro da fargaba, numfashinta ya dinga sama-sama kamar zai bar gangar jikinta, ji tayi kamar ta kurma ihu, sai dai jikinta babu wannan ƙwarin, ji take kamar ajalinta ne ya risketa. Alqur'anin gabanta take kallo, zuciyarta ta din ga raya mata, ta yi jifa da shi. Ganin yadda yanayinta ya sauya, ya sanya 'yan ajijsu darewa suka koma gefe daga kusa da ita. Malam Auwallu ne ya shigo, 'yan ajin duk suka yi shiru, hankalinsa ne ya sauka a kan Nana, da take ta fizgar numfashi idanunta sun yi jawur. Girgiza kai ya yi ya ce "Nana Asma'u" kamar wadda aka jonawa shocking, haka ta ja da baya a razane, tare da sunkuyar da kanta. Ya janyo kujerarsa zuwa gabanta, ya ce "Yau haddar ki zan fara ji, matso ki karanto mini, kin san ina son ƙira'arki" ba ta yi magana ba ta ci gaba da sunkuyar da kai tana haki. Ya kalli ta kusa da ita ya ce "Amira dawo nan gefe ki fara ke" Cikin damuwa Amira ta tashi, tana kallon Nana cike da tausayawa, hatta 'yan ajin kallon Nana suke yi cike da tsoro, su na jiran kyat su falla da gudu su na iface-iface. Amira na zama a gaban malam Auwal ta fara karatu, a haka ya ci gaba da sauran karatun ɗaliban ɗaya bayan ɗaya. Nana tana gefe a zaune tana ta gursheƙen kukan da ita kanta ba ta san dalilin sa ba, adadin yadda suke karatun ya ingiza bugun zuciyarta, tare da jin jikinta na ci gaba da yin sanyi. Malam Auwal na fita amsa waya, Nana Asma'u ta tashi ta fice ta bar ajin, ba tare da wani ya yi yinƙurin tare ta ba, har ta yi nasarar barin cikin makarantar. Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU YOUNG TALENTED WRITERS ASSOCIATION (YOTA) AISHA ADAM (AYSHERCOOL) Arewabooks Ayshercool7724 P2 Kiraye-kirayen sallar magariba ake yi, Baba ya shigo gida da nufin ya yi alwala ya tafi masallaci. "Nana, Nana" "Baba ba ta dawo ba fa" matashin yaron da bai wuce shekara goma sha biyu ba ya bashi amsa. "Ba ta dawo daga ina ba?" "Makarantar islamiyya" "A yanzun da magaribar nan, ke Jamila, Sa'adatu wai kuna ina ne ina ta magana kun mayar da ni mahaukaci?" Jamila ce ta fito tana yamutsa fuska ta ce "Baba ba ta dawo ba fa" "To tana ina? Ina ta tafi? Ko an aiketa ne?" Rabi ce ta fito ta ce "Wai Nanan yarinyar goye ce ne da ka ke ta wannan haƙilon saboda ita? Idan ta gama yawon nata za ta dawo ai" Guntun tsaki ya yi ya ce "Kai sani da aka tashe ku daga islamiyyar ba ka ganta ba?" Sani ya ce "Ban ganta ba, kuma mu ne ƙarshen tafiya, yau na makara aka sakamu kwashe butocin alwala muka gama aka kulle makarantar" "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Allah ya sa ba bankaɗawa ta yi, tayi wani wurin ba" "Ko kuma yawon watsewa ta tafi ba" "Allah ba zai nuna mini watsewa a kan 'ya'yana ba" yayi maganar yana ficewa daga gidan. Nana kuwa tun da ta fita daga islamiyyar, babu wanda ya ganta, dan haka ta ci gaba da tafiya ba tare da ta san in da take sanya ƙafafuwanta ba, ba ta iya tantance rana ce ko dare ma, sai dai tana jin yadda zafin rana yake ratsa ƙafafuwanta da kuma tafin ƙafarta, da take takawa babu ko takalmi. Ita dai burinta ta yi nesa da in da take, ko ta fita daga halin da take  ciki, ko kuma tserewa abin da take jin tamkar ajalinta ne yake tunkarota. Wani matsakaicin gida ta tunkara, babu sallama babu neman izinin masu gidan, kawai ta afka ciki. Ɗaya daga cikin jerin ɗakunan ta shiga, ta cire hijjabin jikinta na islamiyya, ta cukuikuye shi, ta yi fulo da shi, ta kwanta. Kusan mintuna goma sha biyar, da shigarta babu motsin kowa a gidan. Wani matashi ne yayi sallama, ya ji shiru, ya sake sallama ya ji shiru. Saka kai yayi ya shiga ciki yayi tozali da Nana a kwance tana bacci. Turus yayi yana kallonta, yana tunanin ita kuma wannan daga ina. Shaiɗan ne ya shiga ƙawata masa kyakkyawar baƙar fatarta mai sheƙi, da kuma ilahirin jikinta. A hankali cikin sanɗa ya shiga ɗakin, yana cigaba da ƙare wa ƙirjinta kallo. Ɗan dukan gefen carfet yayi, dan ya tabattar da idonta biyu ko bacci take yi. A hankali yake ƙoƙarin kai hannu jikinta, kwatsam! Ya jiyo muryar matar gidan a ƙofar gida tana gaisawa da maƙwabta. Cikin hanzari yayi baya ya dawo tsakar gida ya tsaya. Sallama tayi tare da yara ƙanana, ya amsa yana mazewa. "Saleh, zuwa babu sanarwa haka?" Ya ɗan sosa kansa ya ce "Wallahi kuwa, ina ta sallama amma gidan shiru babu kowa" Ta kalli gidan ta ce "Ikon Allah, kuma yarinyar maƙwabta na bari a gidan, ta jire mini na je ɗaukko su hafsa daga makaranta shi ne ta bar mini gidan a buɗe haka?" Saleh ya ce "Aikuwa ta yi ganganci da ta bar miki gidan babu kowa haka" "Aikam yaushe ka shigo garin ne?" "Shekaranjiya da daddare na ce yau bari na ɓullo mu gaisa" "Aikuwa ka kyauta" ta yi maganar tana ɗaga labulen ɗakin. Turus tayi, tana maimaita"Innalillahi wa innalillahi raji'un" ganin mutum a kwance. Ya kalleta ya ce "Lafiya kuwa?" Ba ta amsa masa ba, ta ƙarasa tana ƙare mata kallo, ta kai hannu ta taɓa ta ta ce "Nana" sai dai shiru ba ta amsa ba. Ta kalli ƙafafuwan Nanan, futu-futu, har da jini alamar ta taka abubuwa a hanya. "Subhnallah, kar dai da ƙafa ta taho Nana, Nana tashi mana" sai dai ba ta motsa ba. Cikin basarwa Saleh ya ce "Anty lafiya kuwa? Wace wannan ɗin dama da mutum a gidan nake ta sallama ba a amsa ba?" Yayi maganar yana ƙare mata kallo, dan shi gaba ɗaya ma bai lura da raunin da yake ƙafarta ba. Anty ta ce "Ƙanwata ce wallahi, ba ta da cikakkiyar lafiya ne, ga wayata ta lalace balle in kira gida in ce tana nan, kuma ni Wallahi ban haddace lambar kowa ba, balle na kira na gaya musu" Suka ci gaba da jimantawa, Nana kuwa ta ci gaba da baccinta, mai kama da suma. Baba yayi sintiri zuwa islamiyyar su Nana babu adadi, tun yana yawon neman ta har ya gaji. Suwaiba ta ce "Wataƙila mutanenta ne su ka yi wani wurin da ita" "Ba wasu mutanenta, ayi ta fakewa da sheɗanu tana rashin mutunci, ta taɓa yin irin haka ne? Allah ne kaɗai ya san gidan uban wanda ta tafi" Baba ya ce "A'a ba na tunanin za ta je wani wurin ba mu sani ba, tun da ba ta taɓa yin hakan ba, amma ina Jamila ma?" "Ta na gidan uwa ɗakkinta ɗin nan, maman khairat, tun azahar tana can" Baba ya ce "Kuma haryanzu goma saura na dare, ba ta gida uban me take yi a gidan mutane?" Mama ta ce "A'a yau na ga abin tsiya, to malam ba abincin safe babu na rana, ba dole yarinya ta tafi in da za ta samu ta ci ba? Ai gara ita an san in da take, 'yar ka fa? Shi ya yi nasa wuri, ita ma gashi ta kama gabanta" Baba yayi shiru bai sake cewa komai ba. Shirun sa ke da wuya, Jamila ta yi sallama, suka amsa baki ɗaya, Baba ya ɗaga kai zai yi magana, sai yayi shiru ganinta da babbar leda. "Mama na dawo" "Sannu jamila, ya ki ka barota?" "Lafiya kalau Alhamdilillah, baba sannu da gida" Baba ya ce 'Yauwwa Jamila, amma ina ki ka tafi haka ba kya gida?" Jamila ta taɓe baki ta ce "Baba Allah ya gani na gaji da raragefen shiga banɗaki ne, ga yunwa ina ji shi yasa na tafi gidan maman khairat na wuni a can" Baba ya ce "Ku yi ta haƙuri ku na addu'a, in sha Allah za a gyara katangar nan, kuma a gyara masan, mutanen unguwar nan ne ma, babu haɗin kai da zuciyar taimako, amma yadda iftila'in nan ya afko mini, ai kamata yayi ayi gidauniyar da za a tallafa mini" Mama ta ce "Kai wa ka ke tallafawa idan matsalarsa ta tashi?" "Rabi wai babu damar na yi magana, sai ki nemi tozarta ni a gaban yara" Ta girgiza kai ta ce "Ba wani tozarci gaskiya ce" Bai bi ta kanta ba, ya kalli Jamila ya ce "Jamila, Nana fa ba ta dawo gidan nan ba, tun ɗazu ake neman ta ba a ganta ba" Jamila ta tsaya da juye abincin da take yi ta ce "To ina ta tafi?" "Wallahi ban sani ba, an rasa in da ta shiga " Jamila ta ce "Kuma ita ba waya ba, balle a kira ta kuma dai na ga ba ta taɓa yin irin haka ba" "Wallahi kuwa. Kai Sani ɗaukko kwano a zuba mini abincin nan nima na saka a cikina, dan rabona da abinci tun safe, ashe akwai sauran masu zuciyar taimako a unguwar nan, irin wannan abinci haka Jamila" Haka Baba ya karkace aka lamushe abinci da shi, har ya nemi ya manta batun ɓatan 'yar sa Nana. ***** Misalin ƙarfe tara na safe, Nana ce a zaune, tana kurɓar kunun tsamiya, duk da babu sukari a cikinsa, amma ba ƙaramin daɗi yake yi mata ba, ga dankali da aka take mata kwano da shi, wanda rabonta da ta ci ta ƙoshi haka har ta manta. Ummi ta dube ta ta ce "Nana, wai garin yaya aka yi ki ka taho gidan nan a ƙafa haka? Tun jiya kin ƙi magana" Nana ta yi ajiyar zuciya ta ce "Ban san ya aka yi ba, ni dai kawai ina islamiyya na ji duniya ta yi mini zafi, kamar zan mutu shikenan ban san meyafaru ba, na dai ji ina bacci, kawai na farka na ganni a nan" Ummi ta ce "Ohh wannan larura taki Allah ya yaye miki Nana, an gode Allah ma da ki ka yo nan ba wani wurin ki ka yi ba, in ƙara miki dankalin ne?" Nana ta girgiza kai ta ce "A'a na ƙoshi Alhamdilillah" "Nana ina kyautata zaton mutanen nan ne, suka hana miki samun mijin aure har yanzu, ga Habibu, rumi-rumi an fara magana aka fasa, ni a yanzu ma akwai wani a ƙasa kuwa?" Nana ta girgiza kai alamar a'a. "Wallahi Nana ina yi miki fatan ki yi aure, ki bar wannan gidan namu, da ba a iya amfana maka komai, idan ba uwarka ce ta yi maka ba, kin ganni nan duk da yau da daɗi gobe babu, yau mu ci gobe mu yi haƙuri, ga azabar dangin miji, amma ya fiye mini wannan gidan namu, da kamar a cikin sa aka yi wahayin babu, ke kanki a yunwace ki ke, ga Baba ya damu ki yi aure, dan Allah kalli wata breziya a jikinki, dan masifa duk kin ƙuƙƙuleta, wallahi da na shiga banɗaki na tarar da phant ɗinki, na za ta tsumma ne da yarwa zan yi, wannan wace irin rayuwar azaba ce?" Nana ta sunkuyar da kai ta yi shiru, dan duk abin da ummi take faɗa gaskiya ne, amma waye zai aureta da wannan larurar a haka? Malam Auwal na islamiyyar su, na ta nuna mata alamar soyayya amma ta yi burus, dan ta san yau da gobe sai Allah, babban fatanta ta rabu da wannan larurar, duk da tana burin yin auren, dan ita kaɗai ta san masifar da take ciki. "Kin san wani abu Nana, akwai wani mai magani da na ji maƙwabciyata su na magana rannan, zan yi mata magana ta kwatanta mini wurin, anjima mu kama hanya mu je ko Allah ya sanya a dace, daga nan na je na duba idan an gyara mini wayata sai na raka ki gida" To kawai Nana ta iya cewa, ta cigaba da shan kununta a hankali. ***** "Alhajin Allah" "Na'am malam" ya amsa yana tattara nutsuwarsa a kan mutumin da yake zaune, a kan tabarma, gefensa ga carbi mai dubu, ga wani ɗan farantin katako da ƙasa a kai. Yayi shiru ya na nazartar ƙasar da ya yi wa zane-zane a gabansa. "Malam me ka gani ne?" "Eh to, buƙata zata biya Alhaji Zailani, amma gaskiya za a sha gwagwarmaya, ga magauta ko ta ina a tattare da kai, arziki zai ninku fiye da yadda ka ke zato, amma gaskiya zaka sha wahala, ƙila ma ka iya rasa ranka, kuma a gidan huɗu ga wata kujerar siyasa nan ko ta mulki da zaka iya samu, sai dai gidan uku ya nuna shi ma akwai bala'i, da tarin ƙalubale" Alhaji zailani ya yakice gumin da yake tsatsafo masa daga goshinsa ya ce "Yanzu malam menene abin yi, dan ko a yanzu kasuwancina harkokin sun fara ja da baya" Ya sake zazzana ƙasa, ya ɗago ya ce "Eh ga wani ƙulli nan a binne a kusurwa huɗu na mararraba, a kanka, amma warware wannan ba zai yi wahala ba, yanzu mafita ɗaya ce da za a samu mai burujin aƙrabu, ko hutu ko surdanu da zai dace da burujin ka, kuma za su taimaka maka ka kai ga ci, ba tare da ka fuskanci ƙalubale ba" Alhaji Zailani ya tattara hankalinsa, ya gyara zamansa ya ce "Malam Gambo to tayaya zan gane su, kuma a ina za a same su, ko nawa ne zan bayar a samo" "Ba samo su za ayi ba, ka samu mace mai ɗaya daga cikin waɗannan burujan, ka kwanta da ita, zaka samu buɗi ta in da ka zata da in da baka zata ba, taurarinta za su haskaka naka da suke ƙoƙarin disashewa, sannan za ta ɗauke wannan wahalar da zaka sha, kafin ka cimma muradinka" Ya jinjina kai cike da gamsuwa ya ce "In dai mata ne gasu nan kamar jamfa a jos, tayaya zan gane wadda ka ke nufi?" Malam Gambo ya numfasa ya ce  "Wadda namiji bai taɓa kusanta ba ake so, kuma idan aka samo ta sai na duba ranar sa'ar burujanku. Kuma ba a fuska za a gane mai irin tauraron da nake faɗa ba. A samo mai suna Nadiya, ko ɗausiyya, ko badariyya" Alhaji zailani ya ce "Ni yanzu malam ina zan samo waɗannan sunayen?" "Bincikawa za ka saka ayi, ko Asma'u ma zai yi, amma shi ma da sharaɗi, idan aka samo ɗin sai na lissafa adadin sunanta da na mahaifiyarta na tabattar da haɗuwar aikin" "Shikenan malam, in sha Allah zan yi iya ƙoƙarina, zan samo in sha Allah, ga wannan ba yawa" yayi maganar yana ajiye masa kuɗi a kan shimfiɗarsa. ***** Ummi ce ta kalli Nana a ɗan fusace ta ce "Wai nuƙu-nuƙun me ki ke yi ne haka Nana?" "Wallahi Anty ummi ba na son zuwa wurin maganin nan ne, idan ki na da niƙab ki bani na saka, kar na je wanda suka sanni su ganni" Sheƙeƙe ummi ta kalli Nana ta ce "Au to sai me, ba neman lafiya ki ka je ba, duk wanda ya ce ya sanki shi uban me ya kai shi? Ki wuce mu tafi dan Allah" Jiki a sanyaye Nana ta bi Ummi, sai dai gaba ɗaya ranta babu daɗi, sai dai ta wani ɓangaren tana ƙarfafar zuciyarta a kan wataƙila ta dace da maganin. Maƙil suka je suka tarar da gidan mai maganin, tamkar ana rabon gafara, mata ne suke ta shiga suna fita. Suka samu wuri suka zauna, wasu a shigo da su a rirriƙe, wasu kuma da ƙafafuwansu. Ga manyan mata masu shigar alfarma da kuma yaku bayi. Wasu na ta tumamin iskokai, wasu na kwancez Nana dai ta raɓe  ta yi shiru a gefen ummi, kasancewar Ummi ba halinsu ɗaya da Nana ba, tuni ta saki jiki suna hira da matan wurin, wannan ta ce matsalar yara ce ta kawota, wannan ta ce matsalar miji, wasu kishiya wasu larura, wasu su ce mayu ne suka kama su, wasu kuma matsalar rashin mijin aure ne ya kaisu. Nana ta din ga nazarin matsalolin daki-daki, ita a tunaninta matsalar rashin lafiya ce kawai za ta kai mutum wurin mai magani, wadda suke samun saɓani da miji maganin me za a bata, ban da ta kai wa Allah kukanta? Ummi da wayo da dabara, da iya daɗin baki da hira, ta yi wa matan nan wayo, ta ce Nana zata shigar a gani ba ta da lafiya, kwananta uku ba ta magana, kasancewar tun da suka zo ba ta ce uffan ba. A tsanake yake ƙare masa kallo, yadda ya zauna ya tanƙwashe ƙafafuwansa, yake ta wasa da yatsun hannunsa, yaƙi ɗagowa su haɗa ido. Ya mayar da idanunsa kan Habu, da yayi shiru yana jiran bayani daga bakin mutumin. "Wannan ciwon nasa gaskiya ba zan ɓoye maka ba, idan na matsa ni zan shiga matsala, sai dai ku bincika wani wurin" Cikin damuwa Habu ya ce "Yanzu babu yadda za ayi ace ko sunansa ya tuna? Ya san duk wani abu da ya shafi rayuwar yau da kullum, amma ya manta duk wani abu da ya shafe shi" Mutumin da yake zaune a kan sallaya,  "Ka san wa ka kawo mini kuwa? Anya ka san waye?" "Na sani" Habu ya amsa cike da ƙwarin gwiwa, cikin gurɓatacciyar hausar sa" Mutumin yayi murmushi ya ce "Ka san dai abin da ka sani, ka bar shi a haka kawai kar ka matsa sanin abin da yake a ɓoye" jiki a sanyaye habu ya kalle na zaunen ya ce "Tashi mu tafi" ya yinƙura ya tashi, ya tsaya ya  kalli malamin ya saki murmushi ta cikin rawaninsa suka fice. Babu tsammani Nana su na tsaye a ƙofar shiga wurin mai magani, wasu mutane suka fito, ƙafafuwansa kawai ta kalla ta ji jikinta ya saki, zuciyarta ta tsinke ta sulale za ta faɗi a wurin, Ummi ta riƙe ta da sauri tana salallami. A hankali Nana ta bi bayansa da kallo kasancewar ya riga ya wuce, zuciyarta ce ta raya mata ta bishi da gudu ta ga waye, daina ganin kowa ta yi sai itakaɗai a cikin sahara, sai kuma shi wannan mutumin da ba ta ga kowaye ba, yana tafe yana jan akalar raƙumi ya yi nesa da ita, tana hango shi a can nesa sai kuma manyan sawayen raƙumin da nasa. "Nana" ta ji muryar ummi a kunnenta, ta buɗe ido ta kalle ta a hankali ta kalleta. "Sannu Nana kin tashi" ba ta amsa ba ta ɗaga kai ta gansu a gidan Ummi. "Anty yaushe muka dawo?" Ummi ta ce "Hmm tun ɗazu, ai tun kafin mu shiga wurin mai maganin, ki ka sume, ya ce manyan dakarun aljanu ne a kewaye da ke, mu na shiga ya gansu" Cikin mamaki Nana ta ce "Ya ga su wa?" "Aljanun mana" ta bata amsa cike da ƙwarin gwiwa. "Dama mutum yana iya ganin aljani a suffarsa?" "Ban sani ba, tambaya dawanau, yanzu ga magunguna nan da hayaƙi kowane zan nuna miki yadda za ki yi amfani da shi, ki ci abinci muje na raka ki gida" Nana ta jinjina mata kai kawai, amma bakinta akwai tarin tambayoyi. Da yamma Ummi, ta taso Nana a gaba domin ta rako ta gida. Ko da suka je gidan, mamaki ne ya cika Nana, ganin an zube kayan aikin gini  a ƙofar gidansu, a iya tunaninta Baba ba shi da wata hanyar da zai samu kuɗaɗen da za ayi musu wannan gyaran. "Nana, haka gidan ya koma? Ummi ta yi maganar cikin mamaki. "Eh, sai ma kin shiga, rijiya ta haɗe da masai, amma na ga an kawo kayan aiki ban san a ina aka samo su ba" Da haka suka shiga gidan da salallama, Suwaiba da take wanke-wanke ta ɗago ta kalle su, ta ce  "Too yau kuma Allah ya yi miki dawowa daga yawon kenan?" Ummi ce ta ce "Wane irin yawo kuma?" But Mama ta fito daga ɗaki ta ce "To ina ta tafi idan ba yawon ba? Wa ta gaya wa za ta je wani wurin? Kwana biyu babanku ya hana mu sakat, saboda ba a ganta ba, ana ta cigiya a unguwa, dama na gaya masa wani wurin ta yi" Har Ummi ta ɗauki numfashi za ta yi magana, Baba ya yi sallama. Suka amsa masa baki ɗaya, baki sake ya bi Nana da kallo, ya ce "Nana daga ina ki ke? Ina ki ka tafi baki gaya mini ba? Ko wurin uwartaki da ba ta san muhimmancin ki ba ki ka wanke ƙafa ki ka tafi?" Ummi ta girgiza kai ta ce "Haba Baba, dan Allah ka tsaya ka ji mana, ka san halin da take ciki na rashin lafiya, shekaranjiya na je ɗaukko yara daga makaranta, ina komawa gida na tarar da ita, a baje a ɗaki ƙafafuwanta duk jini ko takalmi babu, ba ma ta cikin hayyacinta. Ni kuma wayata ta lalace, babansu kuma ba ya gari, shi yasa ban kira na sanar muku ba. Mama ta yi farat ta ce "Wallahi ƙarya ne, ki na nufin tun daga nan ta tafi gidanki a ƙafa? Ƙarya ki ke yi Ummi, ki faɗi gaskiya idan ma, yawon ta zubar ta tafi ki ke kareta" A fusace Ummi ta ce "Allah ba zai nuna mana mai yawon ta zubar a cikin zuriyarmu ba, baƙin bakinki ya faɗa miki kanki da 'ya'yanki..... "Ke ummi rufe mini baki kafin na kwaɗe ki" Baba ya katse ta cikin fushi. Ya ɗora da cewa "Mara kunya wuce ki tafi gidan ki, Allah ya ba da lada" Nana ji ta yi tamkar ta bi bayan Ummi su koma tare, saboda karɓar da aka yi musu, ko arzikin abin zama ba su samu ba, balle a bawa ko ummin ce ruwa, haka ta kasa magana ta bi bayan ummi da kallo yadda ta fita a fusace. Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU Ayshercool YOUNG TALENTED WRITERS ASSOCIATION (YOTA/002) BRIGHT PENS 3rd BATCH. P3 Nana ta tsaya jiran abin da Baba zai ce, bayan fitar ummi, amma ba ta ji ya ce komai ba. "Wai haka zaka ƙyale yarinyar nan, ba zaka tuhumi ina ta je ta kwana biyu ba?" Mama ta yi maganar tana tsare Baba da ido. "To rabi ya ki ke so na yi, kin san a cikin larura take, ni wannan larurar ta ta ta ishe ni, Allah ya kyauta kawai" Tun da Baba ya faɗi haka, mama ta dasa mita da bala'in baya ganin laifin Nana. Nana kuwa ɗakinsu ta shiga, tana jin yadda maganganun mama ke ratsa zuciyarta, da sanya mata wani irin raɗaɗi da zafi a cikin zuciyarta. Haka ta wuni sukuku, ba wanda ta kula ta ƙule a ɗaki kamar yadda ta saba. Sai dai wunin ɗakin nan, ya ƙara sanya zuciyar Nana a cikin ƙunci, haka kurum kewa da son ganin mahaifiyarta ya bijiro mata. Sai daf da magariba Jamila ta shigo gidan, ta ya da zango a tsakar gida, da abin da ta zo da shi daga gidan uwar ɗakinta. Ƙamshin abinci har cikin ɗaki in da Nana take, ga yunwa tana ta sakaɗar cikinta, kamar ba ta taɓa cin abinci ba, haka take jin cikinta. A lokacin ta tsinkayi hirarsu, wai ashe mijin maman khairat, uwar ɗakin Jamila, shi ne ya ɗauki gabarar gyara musu gidan. Tun tana fahimtar hirar ta su, har ta faɗa duniyar tunani, ba ta iya jin me suke cewa. "Laa Nana yaushe ki ka dawo ke kuwa?" Firgigit Nana ta kalli Jamila, ta yi murmushin ƙarfin hali ta ce "Tun ɗazu, Anty Ummi ce ta rako ni" "Kuma na zo da abinci amma ki na ƙule a ɗaki, kuma na ga alamar yau gidan ba harka, bari Nasiru ya zo ya sayo miki gurasa" Nana ta girgiza kai ta ce "A'a a ƙoshe nake, na ci abinci a gidan ummi" Jamila ta ce "Gidanta ki ka gudu kenan? Kin taimaki kanki, kya rage wata kafar, wannan gida namu da kullum cikin indararon talauci ake, ni ma tun da Allah ya sa na samu wurin fakewa, na riƙe wuta" Murmushin nan na ta da ta saba, shi kawai ta yi wa Jamila. Ta ɗan numfasa ta ce "Dan Allah Jamila idan wayarki da kuɗi, ara mini zan yi kira. Jamila ta miƙa mata wayar ta fice, wata lamba Nana ta danna, ta din ga kira, a ƙalla sau biyar amma ba a ɗaga ba, jiki a sanyaye ta sauke wayar daga kunnenta, tare da zuba wa wayar ido, ko za a biyo amma shiru, har aka fara kiraye-kirayen sallar magariba. Sai da ta fita yin alwala, ta tuna babu damar shiga banɗaki, sai dai ta raɓa ta kama ruwa, haka nan ta shiga banɗakin da dabara, ta kama ruwa ta fito ta yi alwala ta shiga ɗaki ta tayar da salla. Tana jiyo yadda yaran gidan, suka tattara a tsakar gida, tare da mahaifiyarsu, sai ɓaɓɓaka dariya suke yi suna hira, ita kuwa tana ɗakinsu a zaune tsuuruu, 'yar fitilar ma da ta kunna, babu batir ta disashe babu haske, ga uban sauro da yake ta yi mata majalisi a ka. Tana nan zaune aka yi kiran sallar isha'i, ta tashi ta gabatar da sallar, ta idar ta fara tasbihi, ita dai ta san ta fara tasbihi, amma ba ta gane kan lissafin abin da take faɗa, ta tafi wasu tunane-tunanen daban. Wuri ɗaya ta tsurawa ido, yadda inuwar wani ƙwaro, yake ta shawagi a ɗan iya in da hasken fitilar da ta kunna yake. Sai dai sannu a hankali, inuwar ta din ga rikiɗewa zuwa wasu halittun daban. Tsoro ya mamayeta, amma a zahiri ta kasa motsi, duk iya ƙoƙarinta, na tuna wasu daga cikin adduo'in da ta iya domin ta yi, abu ya gagara. "Ke Nana!" Suwaiba ta kira sunanta cikin tsawa. A wahale cikin sauke numfashi, Nana ta amsa tana zare ido. "Dan wulaƙanci ana ta yi miki magana, kin yi wa mutane banza, kuma ki na ji, ki je wai ana sallama da ke a waje" Nana ta waro ido ta ce "Ni ɗin kuma?" "Ban sani ba" Suwaiba ta ba ta amsa, tare da ficewa ta bar ɗakin. Ɗan shiru Nana ta yi, tana mamakin waye wannan ya zo wurinta, dan rabonta da wani ya biyo ta ya ce yana so, kusan shekara ta biyu kenan, tun da aka fasa aurenta da Suleiman. Jin abin take kamar a mafarki, haka ta tashi jiki a sanyaye ta fito. Tana jin maganganun Mama sama-sama, amma ba ta iya fahimtar me take faɗa, dan haka kawai ta saka kai ta fita. Duk da babu haske sosai, amma daga yanayin tsayuwarsa, ta gane waye, cikin azama da ladabi, ta durƙusa har ƙasa ta ce "Ya sayyadi ina wuni?" "Lafiya ƙalau Nana, tashi" yayi maganar yana mata alama da hannunsa, ta miƙe tana sunkuyar da kai cikin jin nauyi. Cikin kulawa ya ce "Nana ina ki ka tafi aka yi ta faman neman ki, ba a san in da ki ka je ba? Hankalin kowa ya tashi, daga fita na bar ku a aji, na dawo aka ce mini wai kin fita, sai ɗazu ƙaninki ya ce mini a gan ki" Gaba ɗaya jikin Nana yayi sanyi, ta san ba kowa za ta gaya wa abin da ya faru, ya yadda ba, amma ba ta sare ba ta ce "Wallahi ya sayyadi ni ban san ya aka yi ba, kawai ganina na yi a gidan yayata Ummi, ita ta riƙe ni a gidanta kwana biyu, amma daga nan ba in da na je wallahi" tayi maganar muryarta na rawa cike da karayar, shi ma babu lallai ya gazgata abin da take gaya masa. Cikin tausayawa malam Auwal ya ce "Ba wani abu, kar ki yi kuka, Ubangiji Allah ya yaye miki Nana, ya kawo miki mafita, amma ki na yin dukkanin azkar ɗin da yakamata?" Ta jinjina kai ta ce "Ina yi" "Yauwwa to ki ci gaba, sannan ki yawaita zama da alawala, kamar yadda nake yawan gaya miki, ki riƙe Alqur'ani Nana, Alqur'ani waraka ne" Cikin sheshsheƙar kuka ta ce "Ko hadda ba na iyawa ko na yi mantawa nake yi" Cikin tausasawa ya ce "Ki yi haƙuri, jarrabawa ce, ki ci gaba da gaya wa Allah, kuma kar ki daina ƙoƙarin yin haddar. Ayatu shifa'a ɗin nan da na gaya miki, ki din ga karanta su a ruwa ki na sha" ta jinjina masa kai tana share hawayenta. Baba ne ya tinkaro gidan, dan haka suka yi shiru, ya ƙaraso, Nana tana yi masa sannu da zuwa, malam Auwal na ƙoƙarin gaishe shi. Baba ya amsa sannan ya ɗora da cewa "Ina fatan ta gaya maka, ni ba a zuwa gidan nan yin dogon zance? In dai da gaske ka ke ka turo magabatanka, ni ba na buƙatar komai da wani ƙaƙale, ku kawo kuɗin aure, a ɗaura aure ba sai ka yi lefe ba, ka yi mata kayan ɗaki dan ni ba ni da halin yi mata kayan ɗaki" Take ran Nana ya ɓaci, wannan soki burutsun da Baba yake yi, duk na mene ne? Idan ma da gaske saurayin nata ne, haka zai yarfata, ta yinƙura za ta yi magana, malam auwal ya riga ta ya ce "To Baba in sha Allah duk ba zai gagara ba, zan yi magana da magabatan nawa in sha Allah" Baba ya ce "Yauwwa Allah ya yi albarka" yayi maganar yana shigewa cikin gida, Nana tamkar ta kasa da gudu ta bi bayan baba saboda matsananciyar kunya. Malam Auwal ya ce "Bari na tafi gida, tun da Baba ya dawo, ki shiga gida ki ci gaba da addu'a " cikin girmamawa ta risuna ta ce "Na gode sosai ya sayyadi". Cikin tausayawa ya ce "Allah yayi miki albarka ya baki lafiya Nana" Ta amsa da "Amin ya Allah" ta nufi hanyar shiga gida. A tsakar gida ta tarar da Baba yana tambayar Mama, dama akwai wanda yake zuwa wurin Nana ba a gaya masa ba. "Babu fa wani wanda yake zuwa wurinta, ni rabon da ace an zo wurinta, tun da aka fasa wancan auren nata, kamar an buga mata hatumin jaɓa, malaminsu ne na islamiyya ba wani ba, kuma Auwwalun gidan  mai koko ne ba wani ba, malaminsu ne na islamiyya" Bab ya ce "Oho ko ma ɗan gidan mai ƙosai ne, na ce ya yi wa iyayensa magana, su zo ayi maganar aure" "To ce maka yayi yana sonta?" Baba ya ce "Koma ba sonta yake yi ba, tun da ya zo wurinta ƙofar gida, ai sonta yake yi, tun da ba karatu yake biya mata ba, in samu in aurar da su na huta da wannan wahalar ta ishe ni, riɗa riɗa da su a zaune a gida, mussaman ita ma, ni duk yarana babu wanda yayi daɗewar su ba su yi aure ba". Mama a zafafe ta ce "A'a itan dai, ta fi uban kowa kwantai, sai an yi magana ace aljani ne ya hanata aure" Baba ya ce "Ko kuma kece aljanar ba, tun da kin taka muhimmiyar rawa wurin fasa wancan auren nata" "A'a ka saka munjaye dai, mun taka muhimmiyar rawa zaka ce, ba wai ka ɗora mini laifin nikaɗai ba" raɓawa Nana tayi, tana bin bango za ta wuce ɗakinsu, dan ba ta son ma wani ya ga wucewar ta, amma haƙarta ba ta cimma ruwa ba, Baba ya hangota. "Yauwwa ke Nana, ki fara shirin ki, dan in dai da gaske yaron nan yake, ko wata guda ba za  ayi ba, ki tattara ki tafi ɗakinki, ki samu nutsuwa nima a rage mini wahala" Nana ba ta iya cewa komai ba, sai tsayawa da ta yi tana wasa da yatsunta a cikin hijjabinta, tana jin yadda zuciyara ke bugawa da matsanancin ɓacin rai da damuwa. Wayar Jamila ce take ringing, Baba ya koma kanta da masifar, ta ɗaga wayar nan ta cika masa kunne. "Hello" Jamila tayi maganar cikin iyayi, ganin baƙuwar lamba ce, a zatonta ko saurayi ne. "Assalamu alaikum" muryar babbar mace ta amsa a wayar. Ta yamutsa fuska ta ce "Wace ke magana?" Matar ta ce "Kira na gani da wannan layin, bana kusa da wayar ne" Jamila ta ce "Anya wannan lambar kuwa? Amma wa ke magana?" "Maijidda ce" Jamila ta ɗan yi jimm ta ce "Maijidda kuma? Auuu Nana ce dai ta yi kira da wayar ta yi maganar tana miƙewa ta nufi Nana domin bata wayar. A hasale, Baba ya fizge wayar cikin ɗaga murya ya ce "Halima babu ke babu 'ya ta, kar ki sake kiran waya ki na neman ta, zan yi ƙarar ki wallahi" Nana ta fashe da kuka ta ce "Baba dan Allah ka yi haƙuri, ni na kira ta" Ya jefar da wayar ya yo kanta, kamar zai rufeta da duka, ya ce "Da ki ka bar gidan nan wurinta ki ka tafi ko Nana?" "A'a Baba ba wurinta na tafi ba" tayi maganar tana kuka. "Wato duk yadda na bi na raba ki da matar nan, ba zaki rabu da ita ba ko? Yadda take mutuniyar banza haka zata lalata miki rayuwa, da tana ƙaunar ki ba za ta tsallake ta bar ku ta tafi ta yi wani auren ba, babu abin da zata tsinana miki, idan kuma ba haka ba sai dai ki zaɓa ko ni ko ita" Sosai Nana take kuka, tamkar ranta zai fita, ta rasa dalilin da ya sanya abin da ya haɗa su, ya shafe ta yake aibata mata uwa a gaban kowa, yana cin mutuncin ta, ita fa uwa uwa ce, mece ce ribarsa idan ya raba alaƙarta da mahaifiyar ta?. Wucewa ɗaki ta yi tana ci gaba da kuka, masifa goma da ashirin, ga yunwa ga yarfata da Baba yayi a gaban ya sayyadi, ga kuma abin da ya fi ci mata tuwo a ƙwarya, cin zarafin mahaifiyar ta. Ko hijjabin jikinta ba ta cire ba, kawai ta kwanta tana kuka, ji take tamkar ta kurma ihu ko za ta ji sanyi a ranta, shiru ta yi hawaye na zuba daga idanunta, tana sheshsheƙar kuka, ga kanta ya fara sara mata da wani irin matsanancin ciwo. Ba ta san iya adadin lokacin da ta shafe a haka ba, ta ji Jamila ta taɓa ta, ta ɗago ta kalli Jamila. "Ungo rabu da shi, kirata ku yi magana" Jiki a sanyaye ta girgiza wa Jamila kai, alamar ba zata karɓa ba. Jamila ta yi ƙasa da murya ta ce "Ya tafi ya kwanta fa, ki kira ta bari na kira miki ita, ai ban san ki na da lambarta ba, ai da kin din ga karɓa ki na kiranta" tayi maganar tana danna lambar, sai dai layin yaƙi shiga. "Ba komai Jamila na gode sosai kar ki damu" ta koma ta kwanta. Ƙoƙarin yin tunani take yi, amma kanta ya ci gaba da sara mata, ba ta san ya aka yi ba, bacci mai nauyin gaske ya ɗauke ta ba. Tana tsaye a wani ɗakin library, amma yanayin wurin kamar a wani zamani ne na daban, litattafan wurin duk sun yi ƙura, wasu litattafan duk yana ta yane su, ga ƙauri wurin yake yi, da ta kasa gane wani irin ƙauri ne. Tari ta fara yi saboda ƙaurin ya fara damunta, babu tsammani ta ɗaga kai ta ga wani zanƙalelen mutum, da tsawonsa ya kusa danganawa da rufin ɗakin. Sai yanzu ta lura, ginin ɗakin ma tsawo ne da shi sosai. A hankali yake tafiya, yana zazzaro litattafai yana duddubawa. Duk iya ƙoƙarin da Nana tayi, domin karanto addu'a, ta kasa ta fara ja da baya tana waige-waige ko za ta samu hanyar guduwa, amma ta kasa samu. Ta sake ɗaga kai a dubi in da yake, amma taga ba ya wurin, ta yinƙura za ta tashi, amma ta ji tamkar an ɗaureta a cikin sarƙa. Ajiyar zuciya ta ji an yi a gefenta, ta waiwaya da sauri, ganinsa ta yi zaune a kusa da ita. Zuciyarta ce take dukan uku-uku, "Kwana da yawa" yayi maganar yana sanya dogayen faratansa a gefen wuyanta, ya tsaga jini ya fara tsatstsafowa. Ta kalle shi, amma ta kasa kallon idanunsa. Yayi gyaran murya ya ce "Yaya maganarmu ne, har yanzu babu abin da ki ka yanke a kai? Kar malaminku ya shiga gonata, saboda shi kashe shi zan yi, ba iya korarsa zan yi ba. Ba na son alaƙar ki da shi" Cikin ƙwarin gwiwa ta ce "Wallahi ba zan yi abin da ka ke so ba, kuma ba ka isa ka hana Ubangiji ikonsa a kaina ba, ko da me ka ke taƙama kuwa" tayi maganar tana jin kamar zuciyarta za ta fito. Ya ɗan ɗage kafaɗarsa ya ce "Ke ko kewata ba ki yi ba ne? Yaushe rabon da na kawo miki ziyara, na je na yi jinyar abin da ki ka yi mini, na dawo da ƙarfina, mu ci gaba da fafatawa" A raunane ta ce "Wai dan Allah me na yi maka, me ka ke nema a wurina ne?" "Kin fi ni sani Nana" "Ni ba zan yi abin da ka ke so ba, ka nemi wani yayi maka, ni ba zan iya ba" "Ke aka bani, dan haka ke za ki yi aikin Nana, idan har ki ka amince, zan daina damun ki, zan ma iya barinki ki yi auren ki, amma idan ki ka ci gaba da gardama, wallahi wataran zaki iya tsintar kanki a gidan mahaukata, sai na haukata ki tuburan na hana kowa ya raɓe ki" Nana tana kuka ta ce "Ba zan yi abin da ka ce ba, ni ba zan yi shirka ba" "Ni ban ce ki yi shirka ba, bayar da magani za ki yi, wannan shi ne gado da sana'ar gidanku. Waɗannan litattafan duk tarihi ne, na waɗanda na yi wa aiki. Kakar mahaifinki 'yar  bori ce, kuma duk wanda aka haifa da irin burujin ki, sai ya yi wannan aikin, ba a samu wanda yake da irin burujin ba wato mai irin tauraronki ba, sai a kanki, abin da baki sani ba, na sadaukar da mahaifina domin kare ki, baban ki yana matuƙar ƙaunarki, a 'yan uwansa waɗanda ba sa shiri, an bayar da jininki a yi masa tsafin kuɗi da ke, muka yi yarjejeniya da aljanin da aka sadaukarwa da jininki, na bashi mahaifina da ya tsufa a matsayin bawa, ya rabu da ke, ke kuma yanzu ki ce ba zaki yi abin da na kare ki saboda shi ba? Ba zai yiwu ba" "Wallahi ƙarya ka ke yi, dama ai ku babu gaskiya a cikin zantukanku" "Na yadda, amma ni ba ƙarya nake yi miki ba, samun kyakyawar rayuwarki, yana hannunki Nana" yayi maganar yana kai hannunsa jikinta. Iya ƙarfinta take kai masa duka, tana son ta yi addu'a amma ta kasa sai gurnani, da surutun"Allah ya fika, ba zaka yi galaba a kaina ba, kuma Allah ya isa tsakanina da wadda ta gada mini wannan masifar ni ba mushrika ba ce ba". A hankali ta buɗe idonta, ta ganta tana ta kaiwa iska naushi tana surutu a fili. Shiru tayi tana waige-waige, ta duba shimfiɗar su Jamila ta ga basa nan, ta ga ƙofar ɗakinsu a rufe, wani irin zafi ta ji a wuyanta, ta kai hannu ta shafa, ta ga jini, a gurin da ya karce ta da farcen sa. Ta nufi ƙofar ɗakin da nufin ta buɗe, amma ta ji a rufe, ta jijjiga amma taƙi buɗuwa. Gari ya yi haske ba ta yi sallar asuba ba. "Suwaiba, suwaiba, mama dan Allah ku buɗe mini ƙofa, waye ya kulle ni, ban yi sallar asuba ba fa" shiru babu wanda ya amsa mata. "Nasiru wai ba kowa a gidan ne, dan Allah ku buɗe mini ƙofa, ban yi salla ba" Nasiru ne ya leƙo daga soro, ta jiyo muryar Mama daga ɗaki tana faɗin "Kai Nasiru ba ka na leƙowa ba, wallahi ka buɗe mata sai na ci ubanka" Nasiru ya ce "Mama wallahi ta dawo daidai, ba ki ji tana maganarta normal ba" "Wallahi ba zaka buɗe ta tana wannan tamɓmelen ba" A raunane Nana ta ce "Dan Allah mama salla zan yi fa" banza ta yi mata, Nana ta gaji ta koma ta nemi wuri ta zauna, ta na tuna mafarkin da ta yi. Sallamar baba ta ji a tsakar gida, da alama shi da wasu ne, saboda ba muryarsa kawai ta ji ba. "Ga ɗakin nan malam, wallahi bamu yi bacci ba, daga mu har maƙwabata, kwana ta yi tana iface-iface, dan kawai na yi mata faɗa kafin ta kwanta, da 'yan shekarun nan, abin nata ya lafa, amma kwanan nan, abin ya dawo tuburan dan kwananta biyu ma, bamu san in da ta tafi ba" "Kar ka damu, in sha Allah koma menene a jikinta, yau sai ya fita" Ita dai Nana ta zubawa ƙofa ido, tana jiran abin da zai faru. Aka buɗe ƙofar, ta ga Baba da wani malamin makarantar allo, da garadan almajirai mutum uku, da wata irin zabgegiyar bulala a hannun malamin, ba shiri ta miƙe tsaye tana zazzare ido ta fara ja da baya. Malamin ya kalli Nana ya ce "Zaka gane kurenka munafuki, yau sai ka fita daga jikinta, ya tunkaro Nana da wannan zabgegiyar bulala. A gigice ta ce "Baba, dan Allah lafiyata ƙalau dan Allah kar ka bari ya dake ni, wallahi ni ba aljani ba ce." Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM (AYSHERCOOL) YOUNG TALENTED WRITERS ASSOCIATION (YOTA 002) BRIGHT PENS 3rd BATCH. P4 Baba ya tsaya daga bakin ƙofa, yana leƙowa. Kuka Nana ta fara yi, tana "Dan Allah kar ka dake ni, wallahi  a hayyacina nake nice" "Ƙarya ka ke yi, babu irin aljanin da ban yi karo da shi ba, duk wani siddabarunku na sani" yayi maganar yana riƙe kan Nana, ya fara tofa mata ayoyin Alkur'ani. Nana ta rasa me yakamata ta yi, ita dai ta san a hayyacinta take, ba ta da zaɓin da ya wuce, ta nutsu ta yi shiru, kar ta yi wani abu, ace aljanin ne. Sai dai jikinta yana ta tsuma, dan tsoron kar malam ya dake ta da bulalar nan. Sai dai ba ta tsira ba, babu tsammani ya zuba mata bulalar nan a jikinta, sai da ta gantsare ta kurma wani irin gigitaccen ihu, ta zube a ƙasa ta gigice. Yana karanta mata Alqur'ani ya ƙara zuba mata bulalar nan tamkar ta dukan doki. Ta yinƙura zata gudu, gardi ɗaya ya danƙo ta yayi ciki da ita, suka kewaye ta su na yi mata karatu, malam yana zuba mata bulala yana cewa "Zaka yi magana ko ba zaka yi ba?" Cikin kuka da ƙaraji ta ce "Ni ba aljani ba ce ba, nice a hayyacina nake, Baba dan Allah ka taimake ni ka ce ya daina duka na" sai jikin Baba yayi sanyi ya ce "Malam ɗayyabu, ba za ayi karatun nan babu duka ba, na ga kamar ita ake duka" Malam ɗayyabu ya ce "A'a kar ka damu, ka yi haƙuri ka je ka jira mu a waje, ai wannan aikina ne, ba ita ake duka ba, ka jira mu mu gama" ganin Baba zai tafi ya bar ta a cikin maza daga ita sai su, ya sanya ta ƙara fashewa da kuka, ga raɗaɗin bulala da fatarta take yi. Tana ji tana gani, malam ya saka almajiransa, suka rirriƙe ta, suna yi mata karatu, malam yana shafa mata man gelo a fuska, yana zuba mata wani ruwa a jikinta, ga kuma bulalar da yake ta zuba mata tana ihu. Babban abin da ya ɗaga mata hankali, bai wuce yadda a wayance ɗaya daga cikin yaran malam, yake goga mata jikinsa yana naniƙar ta ba, kuma yana sane. Tun tana kuka muryar ta na fita, sai da ta yi laƙwas ta kasa motsi gaba ɗaya, kukan ma ta kasa sai ajiyar zuciya da take saukewa, ji take da da makami a kusa da ita, sai ta illata wanda yayi mata rashin ɗa'ar nan, sai ta daina jin zafin bulalar, sai na baƙin cikin tozartar da ta yi. A banza wanda ba muharramanta ba sun daddaneta, babu ladduban ruƙiyya babu komai. Malam Ɗayyabu ya ce "Ina ga aljanin ya tafi, duk na ga gardamamme ne, bai yi magana ba, amma ya kau. Ku tashi muje zan bawa babanta magungunan da zata din ga yi" Nana tana daga kwance tana ji suka fita, hannayenta da suka banƙare suka riƙe kamar ba a jikinta suke ba, ga fatarta kamar an sakata a cikin wuta saboda raɗaɗi. Ta jima a kwance tana numfarfashi, daga baya ta ja jikinta a hankali, ta fita tsakar gida ta yi alwala, ta idar kenan Baba ya shigo da ƙullin baƙar leda a hannunsa, ya ce "Kin farfaɗo kenan?" Ta ɗaga kai ta kalli Baba, ta mayar da kanta ta sunkuyar, wani mugun haushin Baban ya kamata, ba ta ce masa uffan ba, ta shiga ɗakinsu. Tana kallon suwaiba tana raɓe raɓe, za ta shigo ɗakin, ba ta kula ta ba ta tayar da salla. Da ƙyar ta yi sallar, ga yunwa ga zafin duka. Ta zame rigar jikinta, tana haska jikin nata da mudubi, wani wurin har jini ne ya fita, ita kanta ta san ba ƙaramin dakuwa ta yi ba, a take wasu hawayen suka ci gaba da zubo mata. Hankalinta ya kai kan raunin da yake wuyanta, ta shafa wurin ta yi shiru tana tuna mafarkinta da tayi jiya. Jamila ta shigo ɗakin da sallama, Nana ta amsa a hankali. Cikin tausayawa ta ce "Sannu Nana, subhnallah haka duk suka ji miki ciwo?" Tayi maganar cikin tausayawa, ganin yadda fatarta tayi ruɗu-ruɗu. Ga buredi da ƙosai ki samu ki karya. Sai da ta ɗan yi jimm, sannan ta karɓa ta ce "Na gode sosai" Tuni masu aiki suka fara aikin gyaran gidan su Nana. Jamila na shirin fita, mama ta tsare ta a ɗaki ta ce "Ke magana nake son mu yi da ke" "To mama, ina jinki" "Gidan maman khairat ɗin za ki tafi?" Jamila ta jinjina kai ta ce "Eh mana, idan ban je ba me zamu samu mu ci?" Mama ta gyara zamanta ta ce "Zuwa la'asar ki dawo, kin san ba a bori da sanyin jiki, duk da tana yi miki alheri, matar nan tana ƙaunar ki, amma dole mu bi ta wurin malamai, a ƙara yi mana aiki a kanta, yadda zata ƙara sakar mana hannu, ai ni tarewar matar nan alkhairi ne a gare mu" Jamila ta ce "To mama, duk yadda ki ka ce, amma duk da haka ai tana yi mini ƙoƙari sosai fa, kalli abubuwan da take yi mana" "Ke dalla can ba a zama haka, idan ta kama mijinta ma, ba sai a shiga a fita, ayi wadda za ayi ba" Jamila ta ce "Ahh haba mama, banda auren mijinta, butulci kenan ai" "To na ji, ita ɗin dai a ƙara mallake mana ita, ta ƙara sakar mana hannu, daga ita har mijin nata" Jamila ta gyara zaman gyalenta, ta ce "Shikenan, sai na dawo" "To Allah ya tsare yarinyar kirki, duk abin da ki ka ci dai ki tuna da ni, Allah ya yi albarka" "Amin" Jamila ta amsa ta nufi hanyar ficewa. Haka Suwaiba ma ta shirya, tana ta baza ƙamshi, cikin matsatsun kaya ta fice. Nana ta ɗan girgiza kai, su waɗanda suke shigar banza, su wuni jin kaɗe-kaɗe, ba Qur'ani ba azkar, aljanu ba su bi su sun takura musu ba, sai ita da take ƙoƙarin killace jikinta da ƙoƙarin yin addu'oi. Saurin katse tunanin ta yi, ta fara istigfari. Ta lallaɓa jikinta ta fita tsakar gida, ta fara kaye-kaye, ta tattara kwanukan wanke-wanke, ta koma gefe dan ta wanke. Dan bayan da larurar nan ta waiwayota a 'yan kwanakin nan, su na tsoron taɓa ta, da akan wanke-wanke sai a ci mata mutunci, har ma a haɗata da Baba ya yi mata nasa cin zarafin. Kafin yamma tuni an gama da gyaran katangar gidan su Nana, har ma an ci ƙarfin aikin, gyaran masan gidan da na rijiya, mama sai alfahari take tana hura hancin albarkacin 'yarta aka ci, aka yi wannan gyaran, dan da ta malalacin mai gidan ne, sai dai a zauna a haka. ***** "Wata guda kenan, haryanzu shiru babu wani labari, an yi addu'ar, an yi duk abin da yakamata, amma haryanzu babu wani ƙwaƙwƙwaran labari a kan ina ya tafi. Kuma babu wata shaida ko alama, ko saƙo da zai bayar da damar gano in da yake. Amma kai a naka binciken me ka gano?" Mutumin ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ni abin da na gani, ya yi nesa da gida sosai ma, yana kudu da nahiyar nan ma" Matar ta dubi mutumin cikin rashin fahimta ta ce "Me ka ke nufi?" "Ina nufin, koma a ina yake ya riga yayi nesa da gida sosai da sosai" "Innalillahi wa innalillahi raji'un, yanzu mene ne abin yi? Ina mamakin dalilin da zai sanya, ya yi wannan shirmen, kawai ya tafi ya bar gida ba sanarwa ba komai?" Mutumin ya ɗan ɗage kafaɗa ya ce "Allah masani" "To kai yanzu mene ne abin yi, dole dole ana buƙatar sa a gida, a wannan ƙadamin da ake ciki, banda tsabar wulaƙanci da baƙin ciki, kawai sai ya kama ya bar gida? Kawai ayi masa kiranye ko gidan uban wa ya je ya dawo" Da sauri ya ce "A'a, na so na bayar da wannan shawarar, amma na duba na ga akwai matsala idan aka yi masa kiranye za a samu matsala, idan bai dawo ba zai yi hauka tuburan, abin da yafi dai ayi tunanin wata mafitar" Tayi shiru tana tunani, daga bisani ta numfasa ta ce "Shikenan babu laifi, zaka iya tafiya " ya jinjina kai ya tashi ya fice. ***** Tun da Baba ya yarfa Nana, a wurin malam Auwal, take matuƙar jin nauyinsa, shi kuwa har cikin zuciyarsa ya ji ya aminta da abin da baba ya faɗa. Yana zaune a ofishin malamai, yana marking wani assignment da ya bayar, ya hango Nana ta shigo makaranta a makare, ya zuba ido ya ga wani mataki malam Nura zai ɗauka. Ya tattara hankalinsa a kansu, baya son a daki Nana, duk da ya san duk makarantar babu wanda bai san matsalarta ba. Tayi wiƙi wiƙi da ido, tana tsoron kar malam Nura ya daketa. Cikin ikon Allah, sai bai daketa ba, ya sanya ta ɗebo ruwa a rijiya ta zuzzuba a butocin alwala. Yayi ajiyar zuciya, ya ci gaba da makin ɗin sa, kawai zuciyarsa ta raya masa, idan kuma wani abu ya sameta a gaban rijiyar fa? Ba shiri ya tashi da hanzari ya tafi. Tana gaban rijiyar tana jan ruwa, yayi gyaran murya. Tana waiwayawa, ta ganshi, risunawa tayi tana gaishe shi, bai amsa ba, ya ƙarasa ya ce "Bani gugan ki tafi aji" ta zaro ido ta ce "Ya sayyadi Nura ne ya.... "Ni kuma na ce ki kawo ki taf... A ɗan raunane ta ce "Ya sa... Auwal ya ce "Za ki bani, ko sai na jefa ki a rijiyar" murmushi ta yi, tana kallon rijiyar ta ce "To bari na janyo gugan" tayo maganar tana janyo gugan daga rijiya. Ta juye ruwan, ta ajiye zata tafi ya ce "Nana" ta tsaya cak ta ce "Na'am" ya ce "Ya jikinki kuwa?" Take annurin fuskarta ya ɗauke, ta ce "Na ji sauƙi" Auwal ya ce "To Alhamdilillah, Allah ya ɗorar da lafiya, ki ci gaba da addu'a da azkar ɗinki" ta jinjina masa kai ta ce "In sha Allah" "Amm goge wannan abin na bakinki, sai ki tafi aji" kallonsa tayi, man leɓe ne kawai a bakinta, ba jambaki ba, shi aka hana sakawa. Ba tayi musu ba, ta goge. "Maza jeki, anjima zan zo gida in sha Allah" ji ta yi gabanta ya faɗi, amma ta kasa magana, ta ja ƙafafuwanta a hankali ta tafi aji. Auwal su na gaban su Nana sosai, lokacin da take yarinya sosai suka yi sauka, bayan sun yi sauka ya ci gaba da koyarwa, ko da ya tafi karatu ya dawo, ya ɗora da koyarwar a islamiyyar. Tunani take yi, kar dai malam Auwal, da gaske ya yadda da abin da Baba ya gaya masa. Ganin yau tana cikin hayyacinta, ya sanya 'yan ajinsu, suka sake da ita, tare suka zauna da ƙawarta Amira, a wuri ɗaya suka ɗauki karatu. Amira ta so tambayar Nana, ina ta tafi aka yi ta nemanta, amma ta fasa, saboda kar ta tsokanota ta burkice. Duk damuwar da Nana take ciki, da zarar ta fito makaranta, aka yi karatu, ta haɗu da ƙawayenta, sai damuwar ta ragu, sai ta kamo hanyar gida tukuna. Sai dai tana jin babu daɗi yadda wasu lokutan ƙawayen nata, suke gudunta, saboda larurarta. ***** "Yanzu kai Habu yaya zamu yi da wannan mutumin, kana ganin mutum kamar katako, baya gane komai, ni anya ma ba hauka ne yake damunsa ba?" Habu ya ce "Ashsha! Na gaya maka ɗan uwana ne, ba shi da cikakkiyar lafiya ne, magani nake nema masa, da ya warke shikenan" "Ikon Allah, Allah ya bashi lafiya, ga mutum har mutum a haka, amma ba ya gane komai, Allah ya bashi lafiya" Habu ya amsa da Amin, tare da kallon wurin da wanda suke maganar a kansa yake. Yana ta wasa da zobunan hannunsa, manya manyan azurfa, da kuma tagulla. A hankali ya saka hannunsa ya ɗago layar da take wuyansa, wadda ta sauka a cikinsa. Ya zuba mata ido yana jujjuyata. Cikin hanzari Habu ya matsa kusa da shi, ya ce "Ka gane mene ne wannan ɗin?" Ya ɗaga manyan idanunsa ya kalli Habu, amma bai yi magana ba. "To ka tuna wani abu ne? Waye ya baka ita?" Bai yi magana ba, ya tattare ta, ya zura ta a cikin rigarsa, ya kawar da kansa gefe daga kallon in da Habu yake. Habu yayi ajiyar zuciya, ƙasan zuciyar sa, yana fatan Allah ya taƙaita wannan al'amari, kamar kullum ƙara rikicewa yake yi, yanzu ba ya magana sai dole, kuma maganar ma galibi shirme ce kawai. ***** Abin da Baba yayi, tamkar ya share wa Auwal hanya wurin bayyana wa Nana abin da yake zuciyarsa game da ita, sai dai jikinta yayi matuƙar sanyi, da ya ce mata ya daɗe yana tausayinta, hakan ya sanya take tambayar kanta anya so ne? Ko dai tausayin ne kawai, duk da ya daɗe yana nuna mata alamun so. Gefe ga tsoro da fargabar abin da zai biyo baya yana damunta, dan kullum ta kwanta sai ta yi mummunan mafarki a kan malam Auwal, abubuwa na tashin hankali sun faru da shi. Ajiyar zuciya tayi, bayan kwashe dogon lokaci malam Auwal, na ta yi mata bayani, ba tare da ta ce "Uffan ba" "Nana" ya kira sunanta a hankali. "Na'am" ta amsa tana sake sunkuyar da kanta ƙasa. Ya ɗan marairaice ya ce "Ina ta zuba nikaɗai, ki ce wani abu mana" Har yanzun dai ba ta yi magana ba, saboda matsananciyar kunyarsa da take ji, banbarakwai take jin abin, wai yau malaminta ne kuma yake sonta, yake ta tsarata da kalamai na soyayya. Jin taƙi magana, ya sanya ya canza akalar hirar, zuwa ta karatu sai a lokacin ta saki jiki, tana amsa masa. Bai wani daɗe ba, ya ce "Bari na tafi, tun da dai ba za a kula ni ba, amma ki sani duk lokacin da na zo wurinki, a matsayin Muhammad Auwal na zo, ba ya sayyadinki ba" murmushi ta yi, ta cigaba da sunkuyar da kai. "Ungo saka mini lambar wayarki" Ta girgiza kai ta ce "Ai ba ni da waya" "Haba dai? Ke haryanzu baki girma ba kenan, to shikkenan za'a nemo waya in sha Allah, ki gaida Baba, ki sanar masa ina nan tafe, za a zo ayi magana in sha Allah" shiru Nana tayi, ba ta yi murna ba, ba ta ji haushi ba, dan ita ba ma ta tantance tana son sa ko a a ba, ita dai ta san ba dan tana jin tsoron abin da ka iya faruwa ba, da ta so ya aureta, tana matuƙar ƙaunar muryar malam Auwal mussaman idan yana karatun Alqur'ani. "Sai da safe, ki shiga gida, ki yi ta addu'a, idan kin yi azkar ɗin kwanciya bacci, ki yi ta nanata *Wa hifzan min kulli shaɗanin marid*" A hankali ta ce "In sha Allah, na gode sosai" Ya ce "Yauwwa ungo wann, kya sai farar ƙasa, dan naga yadda ki ke shanta a makaranta"  yayi maganar yana miƙa mata kuɗi. Ta ɗan kalle shi ta ce "Ya sayyadi ni ɗin?" "Au ƙarya na yi? Ba kya sha ne?" "Ina sha amma kaɗan" ta faɗa tana mamakin yadda saka mata idon da yake yi, har ya gane tana shan farar ƙasa. "Karɓi mana" yayi maganar yana sake miƙa mata. Ta girgiza kai ta ce "A'a ka bar shi, na gode" Haɗe rai yayi ya ce "Bana son jayayya, karɓi" jikinta na ɗan rawa ta haɗa hannayenta biyu, ta risuna ta karɓa ta ce "Na gode sosai, Allah ya ƙara buɗi" "Amin, shiga gida ina kallon ki" ta juya ta shiga gida, sannan ya juya ya tafi. ta juya a hankali ta shiga cikin gida tana murmushi. Abin har mamaki yake bata, wai ya sayyadi Auwal ne yake sonta, ganin abin take kamar almara. Duk da damuwar, abin da take fargabar faruwarsa, na ci gaba da addabar zuciyarta, amma wani sashin na zuciyarta, na kwantar mata da hankali, saboda a ganinta malam Auwal masanin addini ne, mai riƙo da addini dan haka babu abin da zai faru da shi. Tana sallama Baba ya tsare ta, ya ce "Yauwwa dama ke nake jira, tuntuni" Ta tsaya, tana sauraron abun da Baba zai ce. "Yaya maganar turowar? Ni fa ba na son a tsaya a ɓata lokaci a waje ana shashancin nan, ya kawo abin da Allah ya sa yake da shi, a ɗaura auren nan ki tafi, ko a rage mini wata wahalar" A yanzu dai Nana ba zata iya tuna, rabon da Baba ya mora mata wani abu ba, amma da an motsa sai ya yi ta mitar wahala ta yi masa yawa. Ta numfasa ta ce "Ya ce na ce maka, ka yi haƙuri, yana kan tattaunawa da magabatansa ne, in sha Allah za su zo" "Yauwwa ya dai fi. Na ce babu abin da ya baki ne? ƙanen ki sai kuka suke yi, sun ci abinci amma ba su ƙoshi ba, dama wanda Jamila ta zo da shi ne, suka karɓa suka cinye" Nana ta ce "Gashi ya bani" ta miƙa wa Baba kuɗin da ba ta san ma nawa ne ba. Ya saka hannu ya karɓa, ya duba naira dubu biyu ce. "To shi wannan saurayin naki kuma da haka ya zo, ka zo wurin budurwa ka ɓuge da bata dubu biyu kamar abin tsiya. Wancan saurayin naki Sule ya fi abin arziki. Ungo ga wata naira ɗari nan a aljihuna kya sai awara, wannan kuma ayi 'yan dabaru a ci abincin dare" Nana ta karɓi naira ɗarin ta ce "To Baba na gode sosai" Shigarta ɗaki ke da wuya, Suwaiba ta ja uban tsaki ta ce "Wallahi Nana ba zaki taɓa kan gado a rayuwar ki ba, yanzu kuɗin duk ki ka ɗauka ki ka ba wa Baba, alhalin kin wuni daga ke sai ruwan koko a cikinki, kuma dai duk wannan abin da ki ke yi, dan ya ce kin fimu ƙaunarsa, amma ba tausayinki yake yi ba, haryanzu kallon ki yake yi da laifin babar ku" Tabbas maganganun Suwaiba haka ne, amma har ga Allah tana tausayin mahaifin nasu da gaske, ba ta ƙaunar gori da wulaƙancin da mama take yi masa a kan riƙe gida, amma ita ta lura ko a jikin sa, hakan baya wani damun sa. "Nana, wai da gaske Auwwalun gidan mai koko ne yake zuwa wurinki? Wannan na ajin saukar, lokacin mu na zuwa islamiyya?" Cike da ƙwarin gwiwa Nana ta ce "Eh shi ne, meyafaru?" "Lallai Nana, me na sama ya ci balle ya jefowa na ƙasa? Ban da koyarwar nan fa, ban ce yana da wata sana'ar ba" "Suby arziki ai na Allah ne, kuma ni 'yar waye da zan ɗaga kai na ce sai wani?" Suwaiba ta kwaɓe baki ta ce "Lallai kam" Nana kuwa a zuciyarta, tana addu'a Allah ya tabattar mata da alkhairi, ko a daji malam Auwal yake rayuwa, muddin zai rabata da rayuwar wannan gidan na su, ta samu farin ciki haka take fata. Ta cire hijjabin jikinta, ta saka wani ta fita tsakar gida ta tarar da mama su na ta dambarwa da Baba a kan dubu biyun da ta bayar. Kamar ba ta san abin da yake faruwa ba ta ce "Baba dan Allah zan je bakin layi, idan maimuna tayi waina na sayo" Baba ya ce "To hanzarta, ba na son fitar daren nan, mussaman da ba lafiya ce da ke ba, ki hanzarta" ta nufi hanyar fita cikin takunta mai kama da na ƙasaita. Dai-dai lokacin da yayi sallama yake shigowa, ita kuma ta saka kai za ta fita, suka yi kiciɓis, gabanta ya yanke ya faɗi, ta ja da baya cikin tashin hankali da bugun zuciya mai tsanani. Ayshercool 08081012143 What's app only please. 5 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 Daga tsakar gida Baba ya ce "Muryar wa nake ji haka, kamar Gaddafi?" Kallon kallo Gaddafi suka yi da Nana daga bisani ya ce "Za ki matsa, ko sai na bi ta kan ki?" Jikinta na tsuma, ta ja da baya ta bashi hanya. Sai da ya ja tsaki, sannan ya shiga cikin gidan. "Kai kuwa Gaddafi ya da zuwan dare haka, kamar mara gaskiya?" Ya numfasa ya ce "Na tsaya wani uzuri ne a hanya, fatan na same ku lafiya?" Baba ya ce "Lafiya ƙalau, ya ikkon?" "Lafiya kalau, amma ya na ga gidan duk ya canza?" Baba ya kalli gidan ya e "Damunar nan, ruwan ƙarshe da aka yi ne, ya yi mana gyara, ya zubar mana da katanga, masai ta haɗe da rijiya... Cikin alfahari mama ta karɓe zancen, da bashi labarin cewa mijin uwar ɗakin Jamila ne, ya sanya aka gyara katangar gidan. Ko da Nana ta dawo, duk su na tsakar gida, sun kewaye Gaddafi, ana hira ya ajiye musu ledojin da ya zo da su. Ɗakinsu ta shiga ta zauna, ta cinye wainar fulawan, da bai fi loma huɗu ta yi ba, kuma babu in da ta je mata sam. Ƙasan zuciyarta, tana ta addu'a, Ubangiji Allah kar ya kawo abin da zai haɗata da Gaddafi, saboda karon su ba ya yi mata daɗi. Tana zaune Nasiru ya shigo ya kawo mata abin da aka raba aka bata, ta karɓa tayi godiya, ta ajiye a gefenta ta kwanta, ba tare da ta buɗe, ta ga ko mene ne ba. Sannu a hankali Malam Auwal yake nufo in da da take yana murmushi, ita ma murmushin take yi, tana jiran ƙarasowarsa, sai dai kafin ya ƙaraso in da take, ya bayyana cikin ainihin suffarsa mai tsayin gaske, ya shiga tsakiyarsu. A hankali ya din ga rage tsawonsa ya dawo daidai da tsawonsu. Danƙo wuyan malam Auwal yayi, ya zura dogwayen yatsun hannunsa a cikinsa, yana zaro kayan cikinsa, yana watsarwa a ƙasa, ya ƙarasa har maƙogwaronsa, ya zura faratansa zai zaro maƙogwaronsa. Iya ƙarfinta Nana take ihu, da kururwar neman agaji, tare da magiyar ya ƙyale shi. A fusace Gaddafi ya fito tsakar gida yana bala'i ya ce "Wai wannan 'yar abu kazan uban, ba ta daina wannan iskancin ba dama?" Mama da suka fito tare da Baba daga ɗaki a burkice, suka yi burki a tsakar gida, su Suwaiba tuni sun yo waje daga ɗakin, cikin rige-rige. Nana kuwa na cikin ɗakin, tana ta uban kuka da gurnani, tana ihu iya ƙarfinta. "Gaskiya na fara gajiya da wannan bala'in, kullum sai bawa ya sanya haƙarƙarinsa a ƙasa ya kwanta, ya fara bacci, sannan ta fara ihu, gaskiya na fara gajiya." Mama ta yi maganar a ƙufule. Ɗakin Gaddafi ya nufa a fusace, Baba cewa yake "Gaddafi ka bi ta a hankali dan Allah, ka tofa mata abin da ya sauwwaƙa". Yana shiga ya tarar da ita, tamkar ana girgizata, yatsun ƙafafuwanta duk sun ƙandare, kamar kuturwa. Ƙafa ya saka yayi ball da ita, tamkar abar banza, yana zabga mata ashariya. Sai dai ba ta san yana yi ba, iya ƙarfinta take ƙoƙarin karanta addu'a a cikin baccin, amma ta kasa. Gaddafi ya danƙo ta, ya fito da ita tsakar gida, ya watsar da ita a wurin, ya ce "Ku wuce ku kwanta, idan ta gama iskancin ta tashi, ba wani aljanu iya shege ne kawai, kowa ya koma ɗaki ya yi kwanciyar sa". Jikin Baba ya yi sanyi ganin halin da Nana ke ciki, ya ce "Ba iya shege bane, na kira ma an yi mata karatu fa, kalli yadda jikinta yake yi" yayi maganar yana tsugunawa a kanta, duk da wannan abun na Nana shi kansa ya ishe shi. Wasu lokutan, sai yayi tunanin ko ƙarya take yi, amma idan ya yi la'akari da wasu abubuwan, sai ya ga normally mutum ba zai iya haka ba. Sanyin Asuba, da zafin cizon cinnaku ne, ya sanya Nana farkawa, daga nannauyan baccin da take yi, da babu komai a cikinsa ban da azaba da wahala. Ba ta damu da yadda ta ganta a tsakar gida ba, a tunaninta ita ta fito da kanta ta kwanta a gurin, dan yanzu ba ta mamakin yadda wasu abubuwan suke faruwa da ita. Alwala tayi ta shiga ɗakinsu, ta yi salla, sannan ta tashi su Suwaiba. Cike da farin ciki ta tashi, dan yau ɗin ta kama litinin ce, za a koma hutun makarantar boko. Domin tana koyarwa a wata private school, da Nanny ta nema a makarantar, sai malamar da take koyar da 'yan kindergarten ta koma garinsu, aka bata riƙon ajin, kasancewar tana da kwalin sakandare, sai dai ƙoƙarinta da sabon da tayi da yaran, ya sanya suka ƙyale ta, suke ba ta dubu bakwai a wata. Tana matuƙar jin daɗin, yadda take shiga cikin ƙananan yaran, su yi ta tsalle-tsalle da wasa tana koyar da su. Sai dai ta tsananta addu'a, Allah ya rufa mata asiri, kar ciwonta ya tashi a makarantar, ta cutar da 'yan yaran. Tana ta hanzari, ta gama abin da zata yi, ta shirya ta fita, Gaddafi ya shigo da buta a hannunsa, da alama sai a lokacin zai yi sallar asuba. Yana ganin Nana ya tsaya ya ce "Yauwwa ke Nana, dan abu ta kaza kazanki, idan ki ka kuma tashi cikin dare, ki ka hana mutane bacci kina yi mana ihu, sai na yi miki shegen duka, dan wallahi sai na karya ki na gaya miki. Mahaukaciyar banza maƙaryaciya" Duk da ba wannan ne karon farko, da ake kallon ƙaryar ciwon take yi ba, amma tana mamakin yadda za ace, tana wulaƙanta kanta a gaban mutane, ta hanyar yin wasu abubuwa tamkar mahaukaciya. Ba ta fatan ko maƙiyinta, Allah ya jarrabe shi da irin larurarta, ba dan haka ba da ta roƙi Allah ya jarrabi Gaddafi da jarrabawar da ya daɗe yana ƙaryata ta, a kai. Ba ta ce masa komai ba, ta ci gaba da gudanar da aikinta, ba ta damu da rashin samun abin da za ta karya ba, duk ta ga an yi abin karin kumallon, ta kammala shirinta ta fice. Nana akwai ƙoƙarin sammako, dan haka kusan hatta malaman, duk a makarantar suka tarar da ita, ta ji daɗin ganin yaran sosai, kamar yadda su ma suka ji daɗin ganinta, suke ta murna tamkar sun ga mahaifiyarsu. ***** Ƙurii ta yi masa da idanu, yadda yake ta jujjuya kofin kokon hannunsa, ya kalli yarinyar da take kwance a kan katifa ya ce "Ita wannan ba ta tashi rashin lafiya ba, sai da aka koma makaranta?" Babbar macen da take gefe tana karyawa ta ce "Dama rashin lafiya ana saka masa lokaci ne? Larura ce Allah ya kawo mata" ya jinjina kai ya ci gaba da cakalar abincin. "Wai Auwwalu me yake damunka ne?" Auwal ya numfasa ya ce "A ina?" "Ka ƙi cin abinci, sai jujjuya kofin kawai ka ke yi" ya jinjina kai ya ce "Mama magana na ke son yi, amma ban san yaya za ki kalli abin ba" Ta ajiye kofin hannunta, ta ce "Ko ma a yaya zan kalle shi, gaya mini ina sauraron ka" Ya tattara hankalinsa, cikin nutsuwarsa da kamala ya ce "Mama dama akwai wata yarinya ne, da nake zuwa wurinta, to shi ne mahaifinta ya ce in tura magabatana ayi magana" Tayi masa ƙuri da ido, sai da ya kammala, sannan ta ce "Me ka taka haka ne Auwwal, da zaka ɗaukko maganar aure? Fili ne fa kawai da kai a ƙasa, babu muhalli ba wata uwar da ka ke yi tun da ka kammala makaranta, bayan koyarwar nan sai 'yan kame-kame, abin da ka ke samu mu kanmu bai ishe mu ba, balle ka yayimo mana wata a bar maganar nan, kar ka sake tayar da ita yanzu maganar aure, ba nan ba ce" Auwwal yayi shiru, ya rasa abin da yake yi masa daɗi, ba ya son mutuncinsa ya zube a idon Nana, da mahaifinta. Har cikin ransa yake son ya taimaketa, mussaman da ya fuskanci ita sam ba ta da buri, kamar na sauran 'yan matan zamani. **** A wannan karon ma, Alhaji zailani ne a zaune a gaban Malam, fuskarsa ɗauke da damuwa ya ce "Wanda aka samu ka ce duk ba su yi ba, abin ba zai yiwu da su ba, na rasa abin yi gaba ɗaya" "Alhajin Allah, ai ci gaba da duddubawa za ayi, za a samu dai ba za a sare ba, sai kuma ɗaya aikin da na baka, yaya ake ciki yau kwana ashirin da huɗu da fara shi ko?" Alhaji zailani ya ce "Eh, na kusa kammala shi wannan, kuma na fara ganin alamun nasara" Mutumin yayi dariya ya ce "In dai zaka yi biyayya, to za ka samu duniya yadda ka ke so, shi wanda ka ke maganar a kansa, shi ma ba a zaune yake bane ba, wani shu'umin aljani nake so ya yi mana aikin nan, zai iya dan yana da juriya da baƙin naci, amma fafur yaƙi" Alhaji zailani ya tattare babbar rigarsa ya ce "Dan Allah ka tambaye shi, ko me yake so zan yi masa, ba ni da burin da ya wuce, na ga bayan fatuhu, gaba ɗaya shi ya hana arzikina haɓaka, ba a faɗar sunan kowa sai nasa" "Ai duk wani tayi, da mu kan yi wa aljani, domin mu saka shi aiki yayi, na yi masa ya ce ba zai yi ba, akwai aikin da yake yi. Makirin aljani ne, idan na matsa masa zai iya ɓata mini wasu ayyukan, amma ka ci gaba da waɗanda na baka, sallar asuba da la'asar sai kwanakin da na ɗibar maka sun cika, sannan za ka ci gaba. Zan so ace kafin lokacin a samo yarinyar nan, aikin zai fi tafiya dai-dai " "In sha Allah, zan ci gaba da ƙoƙarin hakan, za a samo yarinyar duk in da take" "To shikkenan, kai nake sauraro" yayi maganar yana ci gaba da zazzana ƙasar gabansa. ***** Shigar Nana gida babu daɗewa, Baba ya ce mata, taje gidan da Jamila take zuwa, ta kira masa ita. Nana ta ji daɗin hakan, domin a zatonta Baba zai tsawatar wa Jamila ne, saboda yadda take zuwa ta shantake a gidan, ta wuni kamar a gidan ubanta. A ƙalla Nana tayi sallama ya kai sau huɗu, sannan aka amsa aka ce ta shiga. Jamila ta tarar a zaune a falo, tare da matar gidan maman khairat, sai kuma wata hamshaƙiyar mata a gefe, su na ta hira. Rashin dacewar hakan Nana ta gani, bai kamata ace Jamila tana tsakiyar su, su na ta uwar hira har tana sallama ba sa jin ta ba. Nana ta kalli maman khairat ta ce "Ina wuni?" Cikin sakin fuska ta ce "Lafiya ƙalau Nana, ke ba kya zuwa gidana, Jamila ce kawai 'yar ɗakina" Nana tayi murmushi, ta kalli matar da tun da ta shigo, ta ƙure ta da ido. Haka kurum gaban Nana ya faɗi, amma ta dake ta gaishe ta. Cikin ƙasaita ta amsa mata "Lafiya ƙalau 'yan mata ya ki ke?" Nana ba ta iya amsawa ba, jikinta ya hau rawa har bakinta ya nuna ta ce "Ja.jam..jamila Baba yana kiranki" tana faɗar haka kawai ta juya ta fice. Maman khairat ta ce "Jamsy, meya samu yayarki ne?" Cikin ko in kula ta ce "Wallahi ban sani ba, kin san tana da aljanu ba wuya ta burkice, kamar sun taɓa mata ƙwaƙwalwa ma" Maman khairat ta ce "Subhnallah, ƙwaƙwalwa kuma?" Jamila da ta tashi tana ɗaukar mayafinta ta ce "Wallahi Anty, to sai ta tashi cikin dare tana kurma ihu, ranan fa kwananta biyu ba ta gida, babu ma wanda ya san in da take ba, kullum cikin ciwo take" Matar da take gefe ta ce "Allah sarki, har ta bani tausayi, amma ta burge ni a nutse take masha Allah. Masu irin larurarta na buƙatar tausayawa da ja a jiki, kar ku ƙyamace ta, abin zai yi mata yawa" Jamila ta ce "Ai ko ba ka ƙyamace ta, ka yi gudun ceton ranka, duk da ba ta duka, amma idan ta fara ihu cikin dare da gurnani, layin nan ba wanda zai rintsa. Yanzu hatta ƙawayenta sun daina zuwa wurinta, saboda tsoron kar su kwasa" Jamila ta daɗe tana ba su labarin Nana, sannan ta tafi gida. Nana kuwa tun da ta baro gidan, jikinta yake wata irin tsuma, zuciyarta take bugawa, haka kurum jikinta ya din ga bata akwai wani abu na ba daidai ba, a tattare da gidan, ko kuma matar da ta tarar a gidan. "Hasbunallah wa ni'imal wakil. Wa hifzan min kulli shaɗanin marid " ta din ga maimaitawa cike da fatan Allah ya daidaita mata nutsuwarta. Gaza cigaba da addu'a ta yi, bayan da ta jiyo Baba yana tambayar Jamila, wai gidan uwar ɗakin nata, ba su gama abinci ba, yunwa yake ji, Gaddafi ya bayar da kuɗin cefane, amma an yi girki an hana shi. Wani malulun takaici, ya turnuƙe Nana, duk wani salo na zubar da kai, Baba ya iya shi, kuma hakan shi sam baya damunsa ko kaɗan. Tun da Gaddafi ya dawo, Nana take iya ƙoƙarinta, wurin ta kaucewa yin duk wani abu da zai haɗa su, amma hakan ba ya sanya wa, ta tsira daga zagi da cin mutuncinsa. Wannan bai dame ta ba, kamar yadda malam Auwal ya rage shiga harkar ta, zuwan ma ya daina yi gaba ɗaya, sosai abin yake damunta, zuciyarta na ta son gazgata cewar Aljanin da yake bibiyarta ne, ya shiga tsakaninsu amma wata zuciyar ta hana ta yadda da hakan, domin malam Auwal mutum ne mai addini, kuma ta yadda duk abin da ya samu bawa muƙaddari ne daga Allah, Aljani bai isa ya hana Ubangiji ikonsa ba. Duk da ya hanata yin kwalliya a lokacin zuwa makaranta, ko da kuwa man leɓe ne, dan haka yau ta saka jam baki, ko zata samu ya kula ta. Ta riga kowa zuwa a ajinsu,  ta ɗauki tsintsiya, ta fara share ajin, ta shimfiɗa musu tabarma, ta fito harabar makarantar ta share iya in da za ta iya. Tana shirin komawa ajinsu, Auwal ya shigo makarantar, jinkirta tafiya aji tayi, ta tsaya ya zo zai gifta ta, ta ce "Yaya Auwal ina wuni" wani zirr ya ji a jikinsa, yanayin yadda ta gaishe shin, ya ce "Lafiya ƙalau" ya wuce ta zuciyarsa cike da damuwa, kamar ya waiwayo ya kalleta, sai jikinsa ya ba shi: shi take kallo, dan haka ya fasa waiwayowa. Tana ɗan jima a wurin a tsaye, daga bisani ta nufi ajinsu, gwiwa a sanyaye tana tunanin meyafaru Auwwal ya canza lokaci guda. Tana ta kallon Alqur'aninta, tana son ta yi tilawa, amma zuciyarta na ta gargaɗinta, da tunatar da ita, halin da za ta iya shiga, muddin ta ce za ta karanta. Tana nan zaune, 'yan ajinsu, suka taru suka fara tilawa. Malam Auwal ne ya shigo yayi musu ƙarin Alqur'ani, sai dai da ta ɗaga kai, sai su yi ido huɗu da shi yana kallonta. Sai dai kafin ya kammala ƙarin, ƙafafuwanta sun riƙe gam, su na yi mata wani irin zugi kamar ana karyata. Gwargwadon ɗaga muryarsu a karatun, gwargwadon raɗaɗi da zugin da ƙafafun nata suke yi mata. Ba a tashi ba, ta ɗauki jakarta ta bar makarantar, da ƙyar ta nufi gida, tana taka ƙafafuwan nata da kyar. Ummi ta tarar a gidan, tare da Baba a tsakar gida. Amsa sallamar Nana suka yi, suka tattara hankalinsu a kanta. Ummi ta ce "Ummi ya dai na ga kina bin bango, kina tafiya a hankali?" Ummi ta kalli ƙafafuwanta ta ce "Ƙafafuwana ne suke yi mini ciwo, ba a tashi ba ma na taho gida" Baba yayi caraf ya ce "Haka dai, kullum cikin ciwo ki ke Nana, yau ƙafa in anjima ciwon kai, gobe kuma ciwon ciki, idan ki ka ƙoshi kuma sai ihu da kururuwa, ni wannan lamarin ciwon naki ya ishe ni wallahi. Can a dangin babarki ki ka kwaso wannan jarabar, ni dangina babu irin wannan" Ummi ta ce "Baba aka ce mahaifiyar Inna 'yar bori ce " "In ji uban wa? Ƙarya ne bayar da magani kawai tayi" Ummi ta yi murmushi, ta ce "Nana ƙaraso magana zamu yi" Nana ta so wucewa ɗaki, ta kwanta, duk da ta yi murnar zuwan Ummi gidan, amma soki burutsun da Baba ya fara ya sanya duk ta ji komai yayi mata zafi. To idan ubanta mahaifi ya gaza da larurarta ina ga miji, da za su haɗu rana tsaka su yi aure?" Ta zauna a hankali, tana jin yadda ƙafafuwan nata suke yi mata zugi. "Yaya magungunan da muka karɓo a wurin mutumin nan, kin yi su kuwa?" Nana ta jinjina kai alamar eh. "To yaya ki ka ji, akwai sauƙi?" Da ƙyar Nana ta ce "Eh akwai" Baba ya ce "Ina fa wani sauƙi, babu sauƙi ko kaɗan sai wurin Allah. Nan na ɗaukko malamin nan na almajiran gangare, yayi mata ruƙiyya wai aljanun suka ƙi magana, ba ki ga dukan da ta ci ba, sai da ta ba ni tausayi amma jiya i yau. Shiyasa duk na damu na aurar da ita, ko na huta. Ai ni wannan zancen da ki ka zo mini da shi, ba ƙaramin daɗi yayi mini ba, Allah ya tabattar da alkhairi tun da shi wancan yaƙi cewa komai". Cikin mamaki da rashin fahimta, Nana ta ce "Wane zancen ne?" Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM (Ayshercool) Arewabooks Ayshercool7724 Watpad Ayshercool7724 YOTA 002 BRIGHT PENS 3rd batch P6 Ummi ta yi murmushi, ta tura wa Nana wata leda gabanta. Nana ta kalli ledar, daga saman ledar take iya hango sabulun wanka da man shafawa. "Saleh ne ya aiko ni, tun ranar da ki ka je gidana, yake bibiyata shi fa son ki yake yi, auren ki zai yi" take Nana gabanta ya faɗi, damuwa ta bayyana ƙarara a fuskarta ta ce "Anty Ummi, Saleh kuma?" Baba ya ce "Shi fa, ƙanin mijin Ummi ba yaron kirki" Jiki a sanyaye Nana ta ce "To Baba Auwwal ɗin fa, da ka ce masa ya turo?" Sai Baba ya hau faɗa ya ce "To ina na ganshi? Tun da na ce ya fito ɗin ya fito? Da a bawa bare ke, ba gara shi ba, tun da ya san larurar ki, idan aka yi auren ba ruwanmu da kayan ɗaki, ya ɗauke ki ya tafi da ke can Ikkon, wurin neman kuɗinsa ba, ɗaki ɗaya ya ishe ku kafin Allah ya yassare masa ku tara zuriya ba. Nana wannan iskokan duk aure ki ke buƙata da kin yi shikenan za su daina damun ki". Har Nana za ta yi shiru, amma ta kasa ta ce "Baba to idan iyayen malam Auwal ɗin suka turo fa?" Ummi ta ce "Nana wai ƙanin mijin nawa ne ba kya so ko kuwa?" Gaddafi da yake gefe, tun da ake maganar bai ce uffan ba, ya na ta faman gyara wata radio ya ce "Ai dama ke Ummi ke ce ki ke tausayin yarinyar nan, ita ba tausayin kanta take yi ba" Nana ta yi shiru ta rasa abin da yake yi mata daɗi, ya ma za ayi Ummi ta yi mata haka, ta ce zata haɗa ta da wani Saleh, mutumin da ba nutsuwa ce da shi ba, ga shaye-shaye da yake yi, askin da yake kansa kaɗai ya isa ya bayyana maka, abin da yake aikatawa a Lagos ɗin. Ummi ta taɓa ta ta ce "Nana kin yi shiru" "To me zan ce, Allah ya zaɓa mana abin da ya fi alkhairi" Baba ya amsa da Amin. Nana ta miƙe ta nufi ɗakinsu, zuciyarta babu daɗi, addu'a take yi da fatan, Ubangiji Allah ya sa Auwal ya fito, amma Saleh kam, ba ta tunanin ko me za ayi mata, zata iya aurensa. Dan ko Suleiman da aka fasa aurensu ya fi dama dama a kan Saleh. Ji tayi jiri yana ɗibar ta, dan haka ta samu wuri ta kwanta, ta din ga yi wa Allah kirari, tana magiyar Allah ya daidaita ta da Auwwal ya fito ya turo iyayensa. Ummi ta leƙo tayi mata sallama, amma ta ganta a kwance, ta ce "Nana bacci da yammacin nan, ni dai na tafi, in sha Allah zai zo ku gaisa". Nana na jin Ummi, amma tayi banza da ita. Shikenan dan ana so ka yi aure, sai a ace ka auri mutumin banza. Ranar dai haka ta ƙarasa wunin ranar sukuku, dare ma yayi bacci ya ƙaurace wa idanunta, sai wani azababben ciwon kai da ya kama ta. A hankali ta din ga juyi a kan shimfiɗarta, amma babu bacci babu alamarsa, sai wannan ciwon kan, da take jin tamkar ana sara mata kan da gatari. A hankali kuma ta din ga jin, tamkar ana ɗaɗɗaureta da sarƙa, ambaton Allah take ƙoƙarin yi, amma ta kasa sai a zuciyarta. Ta saka hannun tana laluben hularta, domin ta saka a bakinta ta toshe, kar ta yi ihu cikin dare, ta hana mutane bacci. Ji ta yi an kira sunanta a tsakar gida, duk da ba ta san muryar ba, amma ta amsa a wahale. Jin an ci gaba da kiran sunanta, ya sanya ta yinƙura da ƙyar ta tashi, kanta babu ɗankwali, ta fito tsakar gida neman mai kiranta. Kallon tsakar gidan tayi, taga duhun ya ninka na dare, ba ta iya gane komai a tsakar gidan. Ta juya don ta koma cikin ɗaki, amma ta rasa hanya, saboda duhu ba ta ganin komai. Ji ta yi an ci gaba da kiran sunan ta, kawai ta hau tinkarar wurin da take jin ana kiranta. Gaddafi yana shagonsa a ƙofar gida, ya ji an buɗe gida, ya duba agogon wayarsa, ƙarfe biyu saura mintuna tara na dare. Tashi yayi ya leƙo, ya ga Nana ta fito, daga ita sai zani da vest kanta ko ɗan kwali babu. Sai da ya bari ta yi nisa, sannan ya fito ya bi bayanta, a zaton sa ko wani yawon banzan take, sai dai ga mamakinsa kawai tafiya take yi. Ganin tafiyar ta ƙi ƙarewa ya sanya ya ce "Ke dan ubanki ina za ki je a tsohon daren nan?" can kamar a wata duniyar, haka take jiyo muryarsa. Ba ta tsaya ba, kuma ba ta yi magana ba, ta cigaba da tafiya. Danƙo hannunta yayi, ya din ga  jan ta har zuwa gida, sai dai ba ta yi masa musu ba, bin sa kawai take yi, dan ta kasa tantance bacci take yi, ko kuma a zahiri ne. A tsakar gida ya hankaɗa ta, ta faɗi ƙasa, cikin ɗaga murya, yake tambayarta gidan uban wa za ta a wannan daren. Shiru tayi, ta ci gaba da laluben hanya tana ƙoƙarin tashi. Ya saka ƙafa ya hankaɗa ta ta sake bajewa a wurin. Wata 'yar ƙaramar ƙara ta saki, ta sake yinƙurawa za ta fita, wannan karon da azama ta yinƙura, sai dai tamkar ya samu namiji ɗan uwansa ya sake janyota yayi jifa da ita. A wannan karon, ba ta ji muryar komai, sai dai zafin buguwar da take yi. Baba ne ya fito daga ɗaki, yana tambayar Gaddafi ko lafiya. "Wannan mahaukaciyar yarinyar ce, ta buɗe gida ta fita a haka, na bi bayanta na kamo ta". Baba ya ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, ni Wallahi lamarin nan na Nana ya ishe ni, kula Gaddafi za ta sake fita". Baba yayi maganar yana nuna masa Nana, da ta kwaso da gudu za ta nufi hanyar fita. Ƙafa Gaddafi ya saka mata, ta faɗi a wurin, amma cikin ƙarfin hali, ta sake tashi. Fizgo ta ya sake yi, ya wanka mata mari har sau biyu. Amma ko gezau ba ta yi ba. Baba ya ce "Gaddafi daina dukanta, ba fa ta hayyacinta, ba ta san me ka ke yi ba" "Wallahi ƙarya take yi, iskanci ne kawai, buɗe idonki ki kalle ni" dan sai a lokacin ya lura duk abin nan idanunta a rufe suke. "Gaddafi tofa mata abin da ya sauwwaƙa, ni tsorona kar ta fita tayi wani wurin ba a sani ba" "Ni me na iya da zan tofa mata?" Baba ya ce "Jeka kawai, bari na zauna na ga jikinta ya saki, kar ta sake fita. Dan Allah ko da bacci zai ɗauke ni, idan ka ji motsinta ta buɗe gidan, ka riƙota" "A'a wallahi ban yi alkawari ba, bacci zan yi" Baba ya ciro zanin mama da yake kan igiya, ya rufawa Nana da take baje a wurin kamar abin banza. ***** Washegari da safe, Nana sai haƙura ta yi da zuwa makaranta, saboda yadda jikinta yake yi mata ciwo, dan har targaɗe ta yi a hannu. Da safe Jamila take gaya mata abin da ya faru. Shiru Nana tayi ba ta iya cewa komai ba, ita kanta dan babu yadda za ta yi da ƙaddararta ne. Ƙugin da cikinta yake yi na yunwa bai dameta ba, ta nemi wuri kawai ta kwanta tana goge hawaye a ɓoye. ***** Fuskarta babu annuri take kallon mutumin, kamar ta fasa ihu ta ce "Wai kana nufin babu abin da ya sauya kenan?" "Ƙwarai kuwa, komai yana nan yadda yake" Ta sake tsuke fuska ta ce "Kuma kai babu wani abu da zaka iya yi a kai, gaskiya ba zan iya zuba ido, duk aikin da na yi tuƙuru, kuma ace ba zan mori wahalata ba, ba fa zai yiwu na zama a ƙarƙashin maƙiyana ba" Yayi murmushi ya ce "Bar ganin mu na kauce hanya, akwai abin da bamu isa mu yi wani abu a kai ba, ko kuma mu canza ba, ke za ki yi duk iya ƙoƙarin da za ki yi, sai mu ga ta ɓangarenmu me za mu iya yi. Amma taurarinta su na da haske sosai, duk wanda ya raɓe ta, za ta iya haska na su tauraron" Guntun tsaki matar ta ja, ta ce "Ka ga duba mini wani abun, ka bar maganar nan kawai" Can gida babu wanda ya matsa Nana ta fito ta yi aikin gida, ita ma kuma ba ta yi ba. Sai dai abin da ya ɗaga mata hankali, bai wuce yadda ta ji Baba su na magana da Mama da Gaddafi ba, wai akwai wani mai magani a tsanyawa, idan aljanu suka gagara, har kwantar da mutane yake yi, a tafi a bar shi, sai ya warke ya sallame shi. Babu tunanin komai ta ji Baba ya amince, za a kaita. Rasa abin yi ya sanyata fashewa da kuka. Sallamar Jamila ce ta sanya ta goge hawayenta. "Nana ya jikin?" "Da sauƙi" ta amsa a hankali. "Ungo wannan naki ne" tayi maganar tana miƙa mata leda. Ba ta karɓa ba ta ce "Mene ne wannan?" Jamila ta gyara zama ta ce "Kin tuna ranar da ki ka je kira na, a gidan maman khairat" Nana ta jinjina kai, ba tare da ta yi magana ba. "Kin tuna matar nan da ki ka gaisar a falo" "Na tuna" "To ita ce ta ce a baki, atamfa ce da turaruka, kin san 'yar kasuwa ce" "Meyasa za ta bani, ta sanni ne?" Jamila ta ce "A'a ranar da ki ka je ne, ta ga duk kin rikice da kuka gaisa, bayan kin tafi ta tambaye ni ko ta yi miki wani abin ne; na ce mata a'a baki da lafiya ne, shi ne ki ka bata tausayi". Ita dai Nana ta yi ƙuri da ido, tana kallon Jamila. "Nana ki karɓa mana, ba a mayar da hannun kyauta baya" ta saka hannu ta karɓa ta ce "To na gode sosai" ba dan ta so ta karɓa ɗin ba, ita abubuwan da suka dame ta a yanzu, sun hanata jin daɗin komai na duniya yanzu. Ji take yi tamkar ta kashe kanta ta huta kawai. Kullum cikin addu'a take, babu dare, babu rana, akan Ubangiji Allah ya bata lafiya, sai dai haryanzu Allah bai karɓa mata ba. Wasu lokutan har shagala take da roƙo lahirarta, saboda yadda take fatan lafiya ido rufe, sai dai idan ta tuna ta yi ta istigfari. ***** Ranar laraba, ta shirya ta tafi makarantar da take koyarwa, sai dai zuwanta ke da wuya, aka sanar mata da director yana son ganinta. Ta san a rina, dan haka ta tsananta addu'a, ta nufi ofishin nasa. Ta tarar da shi tare da wani babban mutum, zaune kirim a kan kujera. Ta gaida mutumin ba tare da ta kalle shi ba, ba kuma ta jira ya amsa ba, ta gaida director. Ɗan ƙaramin yaron da yake zaune a jikin mutumin, ya saukko daga jikinsa, cikin gwarancin yara, ya nufo Nana yana faɗin "Anti Nana" ɗagowa ta yi tana murmushi, dan gaba ɗaya da ta shigo, hankalinta ba a jikinta yake ba, dan haka ba ta lura da yaron ba ma. Ta buɗe hannayenta ta rungume shi. Director ya ce "Kin ga wannan shaƙuwar taki, da yaran nan ne, ya sanya haryanzu ban sallame ki ba daga makarantar nan. Babu wadda take iya ɗaukar rigimarsu kamar ki, amma ki na ta wasa da damarki. Kwata-kwata yaushe aka dawo makarantar da har za ki yi fashin kwana biyu, ba tare da kin sanar da hukumar makaranta ba?" Cikin nutsuwarta da kamala ta ce "Dan Allah sir ka yi haƙuri, ba ni da lafiya ne, ba a son raina na yi fashi ba" A ƙule ya ce "Wai wace irin rashin lafiya ce haka, da kullum ba ki da lafiya, idan ba zaki iya ba, ki ajiye aikin mana dole ne?" Mutumin da yake zaune ya ce "A'a ba za ayi haka ba, ayi mata uzuri musamman duba da yaranmu suke ƙaunarta. Ka ga ba zuwa makarantar nan nake yi ba, na fi shekara rabon da na zo, amma na san Anty Nana a bakin Muhsin, duk abin da yake yi, idan aka ce za a gaya mata sai ya daina. Ina nema mata afuwa dan Allah" Director ya ce "Alhaji ba zaka gane ciwon kan da yarinyar nan take bamu ba. She's very hardworking lady, yarinya ce mai ƙoƙari da juriya, amma wannan fashin nata, kullum cikin ciwo shi ne yake ɓata mini rai wallahi" Mutumin ya kalli Nana ya ce "Anty mene ne rashin lafiyar taki ne?" Nana tayi shiru ta rasa abin cewa. Bai damu ya sake tambayarta ba ya ce "Kuma ki na zuwa asibiti?" Ta jinjina kai alamar eh. "Allah ya sarki, to Allah ya baki lafiya yanzu dai ki tashi ki je, na roƙa miki afuwa " Nana ta sake risunawa cikin girmamawa ta ce "Na gode sosai, Allah ya saka da alkhairi" Director ya ce "Tashi ki tafi" ta tashi jiki a sanyaye, hannunta riƙw da na Muhsin, da bakinsa yaƙi rufuwa yana ɗagawa babansa hannu. Duk da ranta ba ya son faɗan da ake yi mata, yanzun ma ba ta ji daɗin faɗan ba, amma da tuna laifinta ne, haka nan ta haƙura, ta danne damuwarta ta shiga cikin ɗalibanta, tare da ƙoƙarin samarwa kanta nishaɗi da nutsuwa tare da yaran. Amma sai ya zamana yaƙe kawai take yi, ƙasan zuciyarta tamkar ta fasa ihu, ga batun kaita gidan mai magani, duk da ba a kuma zancen ba, ga kuma maganar Saleh, ga malam Auwal ya juya mata baya baki ɗaya. Da ta dawo daga makaranta, ta yi sa'a, ta tarar da wata guntuwar shinkafa, an ajiye mata, sai dai ko maggi babu, ta barbaɗa gishiri, ta ci ta tafi islamiyya. Duk da ta san tayi sammako da yawa, hakan bai dame ta ba, saboda zaman gidan na su ne ba ta so, bata ƙaunar duk wani abu da zai ƙara dagula mata lissafi. Kamar yadda ta saba, ta share duk wuraren da taga zata iya sharewa, ta shiga wurin ajiye tabarmi, ta hangi Auwal a cikin ofishin malamai, yana duba wasu litattafai. Ɗauke kanta ta yi, kamar ba ta ganshi ba, ta shiga ta ɗaukko tabarmar 'yan ajinsu, ta fito. Ba ta sanya ran zai kula ta ba, dan sati guda kenan, ko gaishe shi ta yi, sama-sama yake amsawa. "Nana" ya kira sunanta ba tare da tayi tsammanin haka ba, ta waiwaya tare da tunanin ko ba shi ba ne ya kirata. Amma ta ga yana kallonta, tabbacin shi ne yake kiranta. Sharewa tayi, ta fice ta tafi ajinsu. Tana tsaka da shimfiɗar tabarmin ya shigo ajin, ya ce "Nana, ki na ji ina kiran ki ki ka yi share ni, Yaushe ki ka zama haka?" Ta miƙe sosai tana kallonsa, ta haɗiye wani abu mai ɗaci da ya tsaya mata a maƙogwaronta. "Me yasa ba ka yi wa baba bayani ba, kuma ka hanani na yi masa; cewar kai malamina ne ba wanda yake so na da aure ba? Dama ka ce tausayina ka ke ji, ni kuma kasancewar wanda yake ruwa, ko takobi aka miƙa masa kamawa zai yi, na kawar da tunanin komai, na fara sonka ina tunanin ko yaya zan samu afuwa. Amma sai halayenka suka sha banban da abin da ka ke koya mana. Ina ma baka ce ana so na ba, na ci gaba da kallonka a matsayin malamina mai tausayina. Jiki a sanyaye cike da borin kunya ya ce "Ki yi haƙuri Nana, na san ban kyauta miki ba, babu yadda zan yi ne, matsala aka samu, na rasa ta yadda zan yi miki bayani. Ina ta ƙoƙarin shawo kan matsalar ne, amma ban ce ina sonki dan na yaudareki ba, ko na yi wa mahaifinki wasa da hankali ba". Shiru ta yi masa, ta ci gaba da gyara tabarmin, dan ba ta ma san meyakamata ta sake ce masa ba. "Nana, ki ɗan bani lokaci kaɗan, ina daf da shawo kan matsalar" "Tom" ta faɗa a taƙaice, ba tare da ta ko kalle shi ba. Bai taɓa zaton Nana tana fushi har haka ba. Ya kalli yadda take ta jan tabarmin, ba tare da wani dalili ba, ya durƙusa a kusa da ita ya ce "Kalli ki ga" ta ɗaga kai ta kalle shi. "Tabarmar ta shimfiɗu haka, ba ita ta yi miki laifin ba, ni ne amma ki yi haƙuri" Ta kalle shi da idanunta, masu kama da za ta yi kuka, har za ta yi magana, sai kuma ta haɗiye ta fasa. "Kin haƙura?" Yayi maganar yana tsareta da idanunsa shi ma. Murmushi ta yi, ba tare da ta shiryawa hakan ba. Shi ma murmushin yayi mata ya ce "Barakallahu fik, ki ci gaba da yi mana addu'a, in sha Allah komai zai daidaita amaryata". Sunkuyar da kai ta yi, bakinta ya kasa rufuwa saboda murmushi. "Ya jikinki, ina fatan ki na kula da duk adduo'in da nake baki" Ta jinjina kai ta ce "Eh, ina yi" "Yauwwa ki ci gaba da kula, Ubangiji Allah ya baki ingantacciyar lafiya" "Amin na gode sosai" ya fice bar ajin. A hankali ta ji zuciyarta ta yi sanyi, daga zunzurutun damuwar da take ciki. Aka yi karatun Alqur'ani da ita lafiya ƙalau, sai da lokacin fita salla yayi, ta tashi abu ya gagara ta ji gaba ɗaya tamkar an saka sarƙoƙi, an nannaɗe mata ƙafafuwanta. Duk wani ƙoƙari da za ta yi domin ta tashi abu ya gagara, kawai ta fashe da kuka. Amira ta dubeta ta ce "Nana, menene ki tashi an tafi salla". Cikin kuka ta ce "Amira na kasa tashi ƙafata ciwo take yi mini, kamar ana karya ni" Ganin yadda Nana take kuka, sai jikin Amira yayi sanyi, a baya da yawa ana zaton Nana ƙarya take abubuwan da take yi, amma yanayin da take ciki yanzu dole mutum ya tausaya mata. Amira ta fita ta kirawo malam Auwal, suka dawo tare, ko da suka dawo suka tarar ta mimmiƙe tamkar gawar da ta jima da rasuwa. Cike da tausayawa shi ma ya tsuguna a kanta, ya kalli bakinta na ta fitar da kumfa, yatsunta daga na hannu har na ƙafa, sun lanƙwashe. Ayoyin suratul jinn, ya fara karantawa yana tofa mata, ya idar ya koma ayoyi biyar ɗin farko na suratul baƙara, ya ɗan jima yana yi mata karatu kafin jikinta yayi saki, sai dai ba ta tashi ba. Sosai tausayin Nana yake ratsa Auwal, Nana tana buƙatar kulawa ta musamman daga namiji mai addini, da haƙurin gaske, idan Allah ya taimake ta tayi aure, tasirin larurarta zai ragu idsn aka dagewa addu'a da kulawa sosai. Kwanakin nan jikinta ya tsananta, kusan kullum ba ta da lafiya. Ganin ta yi bacci, ya sanya ya cewa Amira ta tafi wurin salla, su ƙyaleta ta huta. Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM (AYSHERCOOL) YOTA(002 7 Wunin yau Nana, a ɗaki tayi shi, ta ɗauki azumi tana tawasalli da azumin da fatan Ubangiji Allah yaye mata larurar da take damunta ya ba ta lafiya. Saboda ita kanta yanzu lamarin yana matuƙar ba ta tsoro. A tsakar gida take ji yo radion mama, wani likita yana ta bayani, a kan cutar depression cutar damuwa, anxiety disorder cutar fargaba, shaye-shaye da farfaɗiya. Shiru tayi, tana nazarin alamomin cututtukan baki ɗaya, cike da fatan ta gano wanne ne yake damun ta a ciki. Sai ta ji tana da wasu daga cikin alamomin anxiety disorder, wato cutar fargaba, sai kuma ta ga wasu alamomin na ciwon damuwa ne yake damunta. Tabbas akwai abubuwa da dama na ƙaluble daa suke binne a cikin zuciyarta, wanda galibi marasa daɗi ne. Ba ta tunanin akwai wani abu na farinciki da ya faru da ita, da za ta ce ba zata manta ba, gaba ɗaya rayuwarta a kan siraɗin ƙaddara take. Sai dai ta na godewa Ubangiji, da ya bar ta da imaninta. Haka kurum sai ta ɗan ji salama a ranta, ta fara saka ran larurarta ta asibiti ce, idan ta je za ta samu mafita. Tayi ajiyar zuciya, ta lumshe idsnaunta, kawai ta ji an bushe da dariya. Ta buɗe idonta da sauri, ta waiwaya ba ta ga kowa ba. A take ta tuna da ire-iren mafarke-mafareken da take yi, da yadda mutumin nan yake tilasta  mata yarda da sharaɗinsa na sai ta bayar da magani. Ta tuna ire-iren gane-ganen da take yi, a zahiri kuma ba ta ji likitan ya yi bayanin makamantan wannan alamomin a cikin bayanin cututtukan da ya yi ba, a take ta karaya ciwon dai da ba ta son ace shi ne da ita ya tabbata shi ɗin ne dai, ko ta na so ko ba ta so aljanu ne  suke damunta. Ko ta yi yinƙurin kawar da tunanin, sai ta tuna yadda take ganin mutumin nan a mafarki, da irin maganganun da suke yi da shi. Kawai ta fashe  da kuka, babu wanda zai iya gane halin da take ciki, sai wanda ya tsinci kansa a halin da take ciki, dan wasu sun gaza yadda ciwo ne Allah ya jarrabe ta, kawai ta ɗorawa kanta ne, dan samun attention ɗin mutane wato hysteria a turance. Ta tashi ta ɗaukko bagcon kayanta, ta din ga ciro magungunaa, kala-kala da ake ba ta, da sunan maganin aljanu, leda-leda ta din ga fito da su. Ta gama tattare su wuri guda, ta fita tsakar gida ta din ga tura su a murhu ɗaya bayan ɗaya. A take gidan ya kaure da ƙauri da hayaƙi mara daɗin shaƙa. Mama ce ta fito tana faɗa "Ƙaurin meye haka mara daɗi kamar gidan 'yan bori?" Ta tarar da Nana a bakin murhun ta na ci gaba da ƙona kayan. "Ke meye haka? Uban me ki ke tura mini a murhu?" Nana ta ɗago ta kalleta, ta yi shiru ta ci gaba da abin da take yi. Tari mama ta hau yi, ta ce "Idan ma uwarki ce ta aiko miki da wata tsiyar ki ke babbaka mini, to baƙar aniyarku ta koma kanku, dan na fi ƙarfin ku daga ke har ita" gaba ɗaya hankalin Nana ba ya kan Mama, zancen zuci kawai take yi, tana kallon yadda kayan ke babbakewa a cikin murhu. Ganin Nana ta mayar da ita mahaukaciyar ƙarfi da yaji, ya sanya ta koma gefe ta zauna, ta na cigaba da ƙananan maganganu. Ko da Nana ta yi buɗa baki, kunun tsamiya kawai ta samu ta sha, hakan bai dame ta ba, ta mayar da hankali sosai wurin roƙon Allah samun lafiya, da miji na gari. Yaro ne yayi sallama, ya ce ana kiran Nana a waje. Jamila ce ta ce masa ya ce tana zuwa. Nana ta fito ƙasan zuciyar ta cike da murnar, malam Auwal ya dawo, akwai yiwuwar ya fito ayi auren, tun da ya dawo. Sai dai tayi turus, da hasken fitilar wutar lantarki ya haske mata fuskar Saleh, ƙanin mijin Ummi. Wani takaici ne ya kama ta, amma ta dake ta ƙarasa fuskarta babu yabo babu fallasa. "Hajiya Nana, barka da fitowa ya ki ke ya gida?" "Lafiya ƙalau, ya su Anty Ummi?" Saleh ya ce "Duk su na nan lafiya" ya ɗan yi shiru, sannan ya numfasa ya ce "Na san dai Ummi, ta yi miki bayanin komai ko?" Nana ta kalle shi ta ce "Wane bayanin kenan?" Ya gyara tsayuwarsa ya ce "Ba ta kawo miki kaya ba, ta ce in ji ni?" "Ohh na tuna, na gode sosai da sosai" Yayi murmushi ya ce "Ai ba wani abu, ta ce Baba ya ce ba sai na wahalar da kaina ba ma, na yi miki kayan ɗaki kawai ba sai an yi lefe ba. Kin ga faɗuwa ta zo daidai da zama, sai mu tafi can lagos tare wurin sana'ata, akwai ɗakin da nake haya komai akwai a ciki na buƙata" Nana ta sake kallonsa ta ce "Baban bai gaya maka ba ni da cikakkiyar lafiya ba?" Ya gyara tsayuwarsa ya matsa kusa da ita ya ce "Ai duk wannan ba wani abu ba ne ba, muddin za a samu fahimtar juna da ni da ke. Wallahi a matse nake ne Nana, ni ko wannan juma'ar ta jibi, a ɗaura ki tare a gidanmu kan na gama shirin tafiyarmu ikko" yayi maganar cikin numfarfashin rashin gaskiya, yana ƙoƙarin ya kai hannunsa jikinta. Ja da baya ta yi, cike da takaici sai dai kafin ta yi magana, ta hango Auwal a tsaye, hannunsa riƙe da leda ya tsaya sak yana kallonsu. Ta kalli Saleh da yake ƙoƙarin kuma matsowa, ta kalli in da Auwal yake, kawai ta juya ta shiga gida, gabanta yana faɗuwa, ba ta san ma me yakamata ta yi ba. Kawai ta shiga ɗaki ta kwanta. A waje kuwa Gaddafi ne ya tarar da Saleh, suka gaisa Gaddafi ya ce "Mutumina yau kai ne a gidan namu?" Saleh ya ce "Wallahi kuwa, na zo wurin Nana, kuma mu na cikin magana ta shige gida, ba ta ce mini komai ba" "Ita Nanan?" "Eh wallahi, ina so mu fahimci juna da ni da ita, ayi a wuce wurin kawai" "Ka kwantar da hankalinka, kamar ka aureta ka gama ne, har wani zaɓi take da shi, kai da zaka taimaka mata. Ka manta da ita kawai ka turo a kawo kuɗi" Saleh ya washe baki ya ce "Allah mutumina" "To me za a jira, kawai ayi abin da ya dace" Nan ya tsaya suka ci gaba da hira, saboda Gaddafi ma a Lagos yake neman kuɗi, kuma su na haɗuwa da Saleh sosai. Sai da suka gama hirar, sannan suka yi sallama, Gaddafi ya shiga cikin gidan, ya dira wa Nana bala'i da cin mutunci a tsakar gida. " 'yar gidan uban waye ke, da za ki hurawa mutane hanci, ke da da za a taimakawa, mahaukaciyar banza da ta wofi. Ki na yawo a kwararo ki na wannan tamɓelen ki hana jama'a bacci, kowa ya san mahaukaciya ce ke a unguwar nan, kin samu ana sonki, amma ki bujire. To wallahi ba ki isa ba dole ki auri Saleh, ki fita ki bar gidan nan ƙila ma rashin aure ne ya sanya ki ke wannan haukan " Nana ta toshe kunnneta, saboda zafi da tururin da zuciyarta take yi, ji take tamkar ta ɗura masa ashariya, ta rama cin mutuncin da yake yi mata, amma ta din ga maimaita Innalillahi wa innalillahi raji'un. Baba ne yayi sallama, ya tarar da Gaddafi yana bala'i, da ya tambaye shi ba'asi, ya ji da Nana yake, sai ya karɓa ya ɗora shi ma. Nana ta rasa wannan jaraba, babu wanda aka tsangwama yayi aure a gidan sai ita, saboda su ga babarsu a gidan, ita kuma ga rashin uwa, ga larura ga shi duk wata hanya da za ta samu mahaifiyarta ko a waya, Baba ya datseta, har yana nema ya yi mat baki. 'meye na damuwa ma, matar da ko in da ku ke ba ta zuwa, ta ga halin da ku ke ciki, balle ki gaya mata halin da ki ke ciki, ta saka ki a addu'a, ko kuma t nema miki magani' wata zuciyar tayi mata tunin, abin da ba ta so, domin in dai tana ire-iren waɗannan tunanin, ta na jin zafin mahaifiyarta a ranta. "Ke Nana, zo ga waya Atine za ta yi magana dake" maganar Baba ta dawo da ita daga duniyar tunani da ta lula. Gabanta ne ya faɗi, wata sabuwa in ji 'yan caca, ba ta ƙaunar duk abin da zai haɗata da matar nan a rayuwarta. Ba tare da ta amsa ba, ta tashi ta fita. Baba ya miƙa mata waya, ta karɓa hannunta na rawa ta saka a kunneta, ta yi shiru. "Ke ma'u ki na ji na?" "Eh" ta amsa a cunkushe. "Dan ubanki sai ki yi mini shiru, ko gaishe ni ba za ki yi ba, har kya yi wa mutane ƙaryar iskancin aljanu, mu da a ka yi gadon bori a gidanmu. Nana ta yi shiru, tana mamkin yadda jahilci, ya sanya yaya Atine alfahari da harkar shirka, da shi ne musababbin gadar mata da bala'i, kamar yadda mutumin da take mafarki da shi, yake iƙrari. "Ki buɗe kunnenki da kyau ki saurare ni, ranar asabar ki yi kuɗin mota, ki taho gidana, akwai gidan wani mai magani da zan kai ki. A baki maganin aljanu da na farin jini, aure dole ki yi shi babu fashi, ko shi wanda ba kya so ɗin ko wani daban. Ke wannan baƙin jinin kamar an jiƙa hatimin jaɓa an baki, daga nonon babarki ki ka shawo shi. Mu zuriyarmu farin jini ne da su wallahi, babu mai nauyin jini" "Yaya atine, idan ni a nonon uwata na sha, su suwaiba a naki nonon suka sha? Tun da Uwar tawa ba ta nan, menene na sakota a zancen ki, koma wani bala'in ne ya same ni, ba duk a dalilin shirka da iyayenku suka yi ba ne, da har ki ke alfahari da ita" ita kanta Nana ba ta san yaya aka yi, suke fita daga bakinta ba, saboda yadda ranta ya ɓaci zuciyarta take tafasa fiye da kima. "Ma'u ni ki ke gaya wa haka?" Gaddafi ne ya yi kan Nana, amma Baba ya tare shi, ya ce "Rabu da ita, ka na taɓa ta babu lallai, mu yi bacci mai daɗi a gidan nan, wataƙila ma ba ita ba ce ba, ƙyale ta" Ta ajiye wa Baba wayarsa, ta koma ɗaki. **** Cike da damuwa Auwwal ya koma gida, 'yar tsarabar da ya yi wa Nana, ya bawa ƙannensa, wani irin kishi ya addabi zuciyarsa, sai dai kuma yanayin kallon da ya ga tana yi wa wanda suke tsayen ne, bai gama gane kansa ba. "Auwwalu" Umma da ta gama kasa gurasa da naman gabanta. Ya kalleta ya amsa da "Na'am Umma" "Magana nake son mu yi da kai ta fahimtar juna. A matsayina na mahaifiyarka". Ya tattara mata hankalinsa baki ɗaya cike da ladabi. "Ka zo mini da maganar aure, na ce maka ka dakata, ba yanzu ba tukuna. Karo na farko abin da ba ka taɓa yi mini ba, ka kai ƙarata wurin kawunka ƙanin mahaifinku. Ya zo har gidan nan baka nan, mun yi magana ta fahimta da shi sosai na kuma fahimce shi, har ya gaya mini ka gaya masa sunan yarinyar da gidan mahaifinta. Na ce masa to ya ɗan saurare ni. Na zo da kaina na saka ayi mini bincike, shi ma kawun naka na saka yayi ta nasa ɓangaren. To magana ta domin Allah ba zan yadda ka auri wannan yarinyar ba, ashe ita ce wadda ka ke bani labari mara lafiyar nan. 'yan unguwarsu sun tabattar da ba ta da wata matsala sai wannan iskokai, kuma ana kyautata zaton kakaninta 'yan bori ne, ni kuma gaskiya ba zan yadda a ɓatawa tsatsonmu suna ba, a sa a gada wa zuriya masifa ba. Dan haka mun gama magana da shi, shi ma zai neme ka ya kuma yi maka magana. Ya ce mini ya saka wani abokinsa ya yi naka hanyar tafiya Qatar ko Allah ya sa a dace da kyakyawar sana'a. Idan Allah ya sa ka tsaya da ƙafarka ka samu wata yarinyar mai kyakyawar nasaba da lafiya ka aura. Ba cin mutunci ba amma an ce yaran gidan ma galibi su ne suke ciyar da kansu, uban ba ya sana'ar komai, yarinya budurwa kuwa duk in da aka bari ta ciyar da kanta, ai an samu matsala. Dan haka ka cire ta daga zuciyarka" da ƙyar Auwwal ya haɗiye wani abu mai zafi da ya tsaya masa. Mama tana da gaskiya amma idan aka ce waɗannan abubuwan kacokan za a duba a ɗora mata laifi shikenan ba za a aure ta ba kenan? Nan aka zo neman auren ƙamwarsa aka ce ba za a aureta ba, 'yar mace ce, aka yi ta ɗauki ba daɗi kafin auren ya yiwu, amma Umma ta manta da wannan, ita ma tana hango aibun da ba ya cikin jerin abin da zai iya hana aure a shari'a a yanzu". "Auwalu ka yi shiru, ko baka yarda ba zaka bujire ne?" "A'a subhnallah, na amince Allah ya zaɓa abin da ya fi alkhairi, amma Umma, da a bar maganar Qatar ɗin nan, idan Nana ce na haƙura amma.. Ta tari numfashinsa ta ce "Ai mun gama yanke hukunci, biyayya ce kawai taka Auwal" Ya risuna ya ce "Shikenan Allah ya wuce mana gaba" ya tashi jikinsa a sanyaye ya bar ɗakin Umma, ya koma shagonsa. Washegari da safe, ta je gaida Baba, bayan ta shirya za ta tafi wurin aiki, amma ya ƙi amsawa, ya ma tashi ya bar wurin. Cikin damuwa ta koma ɗakinsu, ta ɗauki jakarta, ta kalli Jamila, da ke ta danna waya ta ce "Jamila, dan Allah ko kin san laifin da na yi wa Baba, ya ƙi amsa gaisuwata?" Jamila ta ɗago ta ce "Lallai Nana, jiya da ki ka gaggaya masa magana, da shi da yaya Atine, ko har kin manta?" Shiru Nana ta yi, ta fara jin wata ƙara a cikin kanta, ta jingina da bango ta dafe kanta ta ce  "Subhnallah" Jamila ta tashi zumbur, ta ja da baya ta ce "Ya dai?" "Wallahi Jamila, ban san ya aka yi hakan ta faru ba, da na tashi daga bacci, tunanin abin nake yi kamar mafarki ba a gaske ya faru ba, gaba ɗaya na kasa gane kan rayuwata, amma shikenan" kawai ta fita daga ɗakin, ta saka takalmanta ta fice. A ƙofar makarantar, danƙareriyar motar ta yi parking, gilasanta baƙaƙe ne ƙirin, ba a ganin wanda yake cikin motar. Yaro ne ɗan shekaru uku, ya fito daga cikin motar, ya zura hannunsa ya ɗaukko akwatin abincinsa, bai tsaya rufe motar ba ya nufo wurin da Nana take tsaye, yana washe baki cike da murna. Sakin fuska ta yi, ta ƙarasa ta ɗauke shi, ta ɗaga shi tana murmushi. Sai dai yayi shiru yana kallonta, ganin alamun damuwa a fuskarta. Ta shiga da shi cikin makarantar, ta fara tafiya da shi aji, in da take ajiyewa ɗaliban nata, kwanukan abincinsu, ta juyo za ta kama hannunsa su fita, amma ya ƙura mata ido. Cikin harshen turanci ta ce "Muhsin let's go" (Muhsin mu tafi) "Anty sorry" (Anty ki yi haƙuri) ya furta cikin damuwa. Kallon sa tayi ta ce "Meyasa ka ke bani haƙuri?" "Anty waye ya dake ki, ki ka yi kuka?" Ya faɗa cike da yarinta. Haɗiye hawayen da ke ƙoƙarin zubo mata tayi, ta ce "Atishawa na yi, mu tafi assembly ground" Ko da suka je wurin assembly, an yi tsit ana addu'a, amma ɗalibanta na ganinta, suka fara tsalle, su na kiran sunanta. "Anty, ko ki saka 'ya'yanki su yi mana shiru, ko ki ja su ku tafi" vice principal ya gargaɗeta. Cikin hikima ta sanya yaran yin shiru, yaran da take jin ƙaunarsu, har cikin zuciyarta. Lokacin tashin yaran, duk an zo an ɗauke su, saura muhsin da ta biyewa, take yi masa lilo, kafin a zo ɗaukarsa. Daga ita sai shi a harabar wurin nishaɗin yara, ta ɗora shi a wannan lilon ta sauke shi a wancan. "Laa Anty kin ga Daddy" yayi maganar yana nuna bayanta. Ko da ta waiwaya, mutumin nan ne da suka haɗu a ofishin director, ta sauke muhsin, ya nufi wurin babansa da gudu, ita kuma ta ɗaukko masa jakarsa da lunch box ɗin sa. Har ƙasa ta risuna ta gaida shi, ya amsa cikin sakin fuska ya ce "Ya yaran naki, ya ƙoƙari?" Ta amsa da "Alhamdilillah" "Madalla mu na ta goɗiya, mun yaba da ƙoƙarin da ki ke yi wa yara, Allah ya saka da alkhairi" "Amin na gode sosai" Har zai juya su tafi ya ce "Amma yaran naki, sun tashi gaba ɗaya ko?" Ta ce "Eh, sun tafi dama Muhsin ne ya rage, zan tafi nima" "To mu je, sai mu sauke ki a hanya mana" Nana ta ɗan yi turus ta ce "Bakomai na gode, ai babu nisa sosai" "A'a bakomai, ai ni na ce muje sai mu ajiye ki a hanya" sai ta ji mutumin yayi mata kwarjini, ta ci gaba da jayayya da shi, amma har cikin zuciyarta ba ta so hakan ba sam. Su na tafe a hanya, yana yi mata tambayoyi, kan matakin karatunta, da makamantansu. Ta din ga bashi amsa sama-sama a tsorace, dan haka kurum ta ji ya takura mata da yawa. Sai dai ya din ga yaba mata, da ƙoƙarin da take yi da yara. A bakin titi ta ce za ta sauka, ya ɗauki kuɗi dubu biyar ya ba ta, ta ce masa ba zata karɓa ya ce ba zata sauka daga motar ba, sai da ta karɓa, sannan ya buɗe, ta yi masa godiya ta nufi hanyar gida. A ƙofar gida ta hangi Baba, yana zaune a ƙasan bishiya, sai hamma yake yi, idanunsa jawur. Ta nufi inda yake, ta je ta durƙusa tana gaishe shi. Da ƙyar ya amsa mata yana kawar da kai gefe. Ta ɗaukko dubu uku a kuɗin nan ta miƙa masa ta ce "Baba ga wannan, yaran da nake kula da su ne, baban wani ya bani" sai ya waiwayo da sauri ya saka hannu ya karɓa. "Masha Allah, ai yakamata dai dama iyayen yaran nan, su din ga yi miki ihsani, tun da dai yaran nan na su da ki ke yi musu wahala, ba wani biyanki ake yi da kyau ba. Ko suturar jikinki suka kalla ai sun san mabuƙaciya ce ke, ba sai an ce su baki ba" Nana ta basar da zancen, dan ba ta son ire-iren waɗannan zantukan na Baba, masu cike da son zuciya ta ce "Bari na shiga na shirya, na tafi Islamiyya" "Zauna nan mu yi magana kafin ki shiga gidan" Nana ta zauna sosai tana sauraren Baba. "Nana duk abin da ki ka ga ina yi, ƙoƙari nake yi a kanki. Ki daure ranar talata ki je gidan yaya Atinen, a jarraba mai maganin wurinta ko za a dace. Idan bai yi ba sai fa mun dangana da mai maganin da Gaddafi ya bani labari, idan ba haka ba babu lallai ki iya zaman aure ki yi haƙuri  shi wancan malamin naku dama ba sonki yake ba, tun da ya gudu bai turo iyayensa ba. Tun daga wannan ba sai ki haƙura ayi da shi ba, nima a rage mini ɗawainiya ba. Yanzu ba a auren soyayya, ko wani zurfafa bincike duk bayi ake ba. Ki tashi ki shiga kar ki makara" Ba ta ce uffan ba, ta tashi jikinta a sanyaye ta shiga gida, gaba ɗaya kalaman Baba babu na ƙwarara gwiwa sai na kashe jiki da cire wa mutum tsammani. ***** Gaba ɗaya Auwal ya daina shiga makaranta, wanda hakan ya ɗagawa Nana hankali, ta na ta son su haɗu da shi, ta yi masa bayanin abin da ya gani ranar da ya je gidansu, amma ba ta samu ganinsa ba. Ita ba waya ba balle ta kira shi, abin duniya duk ya dameta. Ranar asabar da sassafe, Baba da kansa ya tashi Nana, ya sanyata shiryawa, ta tafi gidan yaya Atine. Babu yadda ta iya Baba, zuciyarta ta din ga raya mata, kar ta je, amma ta tabattar idan ba ta je ba, fushi zai yi da ita. Tun da Allah ya sa ta je gidan, bayan sun gaisa yaya Atine take masifa, wai ta ƙi tsayawa a nema mata magani ta wahalar mata da ɗan uwa. Nana dai ba ta ce uffan ba, Yaya atine ta yi ta faɗanta. Ta shirya ta saka Nana a gaba, suka tafi wurin mai magani. Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU Ayshercool YOUNG TALENTED WRITERS ASSOCIATION (YOTA 002) P8 Kallon farko da Nana ta yi wa mai maganin, takaici ya kama ta duƙun-duƙun da shi kamar wakilin sarkin dauɗa. Yana zaune a cikin wasu tarin shirgi da ta rasa ko na uban mene ne. Ɗakin sai azabar ƙauri yake yi, da tsamin wasu abubuwa da ta kasa tantance ko na mene ne. Jikin bangon ɗakin, an zana wasu irin hatimai, kuma an saƙale ƙahunhuna da layoyi. A take zuciyar Nana ta bata wannan mutumin boka ne, ba malami ba, ko kuma malun malun. Ya ƙare wa Nana kallo, ta kawar da kai ta ƙi kallonsa, Yaya Atine ta gyara zama za ta fara yi masa bayani, ya dakatar da ita, ya ce "Ɗan saurara tukuna Hajiya. Ba ki ga ta kasa haɗa idanu da ni ba? Ai sun zo shegun sun ƙaraso, tare ku ka shigo da su ai, ku na tafe su na biye da ita runduna guda, manya da yara tsofaffi da matasa, yanzu haka kusa da ke ma duk su ne a zazzaune makaran nata, sun cika gurin nan" Yaya Atine ta zabura ta tattare ƙafafuwanta ta ce "Innalillahi. A nan ɗin malam?" "Eh fa, yi a hankali kar ki hau kan wani" Nana kuwa waiwaya ta yi, domin ƙara tabattar da a kan wa yake maganar ne?. Ya gyara zama, ya juya ya ɗaukko wani ruwa, a wata tasa ruwan duk yayi gansa kuka, baƙi ƙirin da shi, ya ɗebo a hannunsa ya watsowa Nana. Take Nana ta ɗan ja da baya, saboda idan wannan ruwan dauɗar ya zuba a hijjabinta jirwaye zai yi. Ya ce "Kin gani ko, ga su nan za su yi magana, sun ji ruwan azaba, wane su dan uban su. Waye ya zo kanta za ka yi magana ko kuwa?" Nana ta ɗago kai baki buɗe tana kallon ikon Allah, tana tsoron ta yi wani abin, ya ce Aljanun ne suka zo, kar ta je ya zane ta. Sai dai ta ga idan ba ta yi da gaske ba, sai ya yi mata wanka da ruwan dattin nan, aikuwa ta tashi tsaye ta ja da baya. Yaya Atine ta miƙe da sauri, ta yi baya cike da tsoro da fargaba. "Ba za ku yi magana ba?" Yayi maganar yana zare mata ido, tare da miƙewa. Nana ta ce "Wai suwaye za su yi maganar ni ce fa" Ya ce "Da alama wannan makaran nata, su na da azabar taurin kai, sai an yi aiki tuƙuru a kansu. Yanzu zan yi mata wani ƙaramin aiki, somin taɓi idan kuma da kuɗi a hannunki ki bayar da dubu goma sha biyar, za a sayo turarukan da za ayi mata aikin da su. Ranar Litinin kafin hudowar alfijir, ake yin aikin, za ki kawo mana namijin goro guda bakwai, da zuma farar saƙa, kuma da wuya idan ba sai an yi yanka ba, kin ga sun ƙi magana". Yayi maganar yana ƙarasa sheƙa wa Nana ruwan hannunsa, hakan ya sanya hijjabin Nana, kwanciya a jikinta ya fito da surar da Allah yayi mata. Takaici ya isheta, tun da suka zo, mutumin nan bai ambaci Allah ba, ko ayar Alqur'ani sai shirme da soki burutsu. Warin ruwan da ya zuba mata duk ya cika mata hanci. Kawai ta nufi hanyar fita ta bar ɗakin. Yayi wuf ya riƙo hijjabinta. A fusace Nana ta juyo ta ce "Meye haka, ka sakar mini hijjabina ba na son haka" Mutumin ya dubi Yaya Atine da ke zare ido ya ce "Hajiya za su yi magana yanzu, ba ita ba ce ba" Nana ta saka ƙarfinta za ta fizge hijjabinta, ya saka ƙarfinsa ya hankaɗata take ta faɗa kan shirgin da ke cikin ɗakin, wani azababben wari, kamar na ruɓewar wani abu, ya daki hancin Nana, ga ƙume ƙeya da ta yi, wanda gudun kar ta yi ihu, ya sake fakewa da haka ya yi mata wani abun, ya tilasta ta yin shiru. Tana ƙoƙarin ɗagowa, ya shaƙa mata wani abu a hancinta, ta kawar da kanta ba ta sheƙa da yawa ba, amma ta ji wata irin gigitacciyar azaba ta ratsa hancinta zuwa kanta. Ba ta san lokacin da ta kurma ihu ba, jin azabar ta danne mata hanyar fitar numfashi. Ya kalli Yaya Atine ya ce "Hajiya jeki waje zan yi aikina" Yaya Atine ta ce "Ka na ganin ba wani abu na je?" "Eh mana, idan ma kin tsaya babu abin da za ki iya yi, idan ba haka ba idan suka zo fita su shige jikinki" ai cikin azama ta bar ɗakin. Sai da ya leƙa ya tabattar ta bar wurin, sannan ya dawo kan Nana, da take ta layi a ƙasa. Kan Nana ya yi, yana ƙoƙarin kai hannayensa ƙirjinta duk biyun, ta yinƙura ta juya tana takaicin yadda Yaya Atine ta iya tafiya ta bar ta, daga ita sai wannan zindiƙin mara tsoron Allah. Ƙoƙarin juyo da ita yayi, yana laluben yadda zai saka hannu a cikin jikinta, tayi wani kyakyawan yinƙuri, ta fizgo wani ƙaho da ke rataye daf da ita, ta raɗa masa a daidai tsakiyar kansa. Afujajan ya tashi tsaye, yana zazzaro ido, ya gigice saboda yadda ta yi masa dukan a bazata, dan a zatonsa hankalinta ya gushe. Ya kasa tsayuwa, ya nemi wuri ya zauna, saboda azabar raɗaɗi. Ta tashi da ƙyar, tana tangaɗi, ya yinƙura ya yi kanta domin hanata fita, kar ta tona masa asiri. Amma ta sake ɗaukan wata ƙwarya wadda take cike da ruwa, yayi baƙi ƙirin saboda tarkacen da yake ciki, ta sheƙa masa a fuska, sannan ta tattara ɗan kuzarin jikinta, ta yi masa ɓarin makauniya da ƙwaryar a fuska sai da ƙwaryar ta ragargaje. Ganin Nana ta fito tana tangaɗi, ya sanya Yaya Atine tashi ta nufe ta, mutanen wurin na ta yi mata sannu. "Ke Nana lafiya, ke ce ko aljanun naki ne? Wani mugun kallo ta yi wa Yaya Atine, ta ɗauki takalmanta a hannu ta riƙe. Yaya Atine ta koma ɗakin mai maganin, ta tarar da shi hanci na zubar da jini. Cikin tashin hankali ta ce "Malam lafiya kuwa?" "Artabu muka yi da aljanun nata, ba aljanu ne a kanta ba, baƙaƙen iblisai ne, shaiɗan ne da zuriyar sa" ya yi maganar yana shafo jinin da yake fita daga hancinsa. Sai hankalinta ya rabu biyu, tana ƙoƙarin ta tambaye shi, abin yi, kuma ga hankalinta a kan Nana. Ta koma in da ta bar Nana a tsaye, wanda suke zaune suka ce mata ai ta fita. Ta fita da sauri, amma ko alamar Nana ba ta gani ba, ta bi hanya tana salati da fatan ba wani wurin ta yi ba. Sai da ta ƙarasa titi, ta hangota zaune a gefen hanya, takalmanta a hanunta tana ta layi. Su na yin ido huɗu, kafin Atine ta tsallaka, Nana ta tashi ta shige wani adaidaita sahu, ya ja sun tafi. Salallami da salati, Atine ta hau yi, ta tari wani adaidaita sahun, ta tafi gidansu Nana. Baba na ganinta a rikice ya ce "Atine yaya dai? Lafiya kuwa?" "Ina fa lafiya Isa, mu na wurin mai magani, sun yi karambatta da aljanun nata, kawai ta fita ta haye adaidaita sahu, ai na za ta nan ta yo" Gaddafi da yake wanki, ya ja tsaki ya ce "Wallahi lamarin yarinyar nan har da iskanci, kuma da gangan take ƙin yin auren nan, a kaita gidan mutumin nan da na gaya maka Baba, idan ba gaske ne, idan ma ƙarya take yi duk zai faɗa babu wani aljani da ya gagare shi" "To yanzu a ina za a ganota?" Baba ya ce "To wa ya sani, kwanaki fa kwananta biyu ba ta nan, sai daga baya suka zo da Ummi, wai kawai ganinta ta yi a gidanta, idan ma da gaske take, idan ma ƙarya suke yi oho musu. Ni wallahi na gaji da sabgar yarinyar nan shi yasa nake Alla-Alla a samu mai so ya aura na huta. Kuma ga wannan ƙanin mijin Ummi ta tsaya tana iyayi" Babu tsammani, sai ga Nana ta shigo, Jamila ta riƙota tana ta tangaɗi, da takalmanta a hannu. Gaba ɗaya suka yi kan Jamila da tambaya "A ina ki ka ganta?" "Gidan maman khairat zan je, kawai na hangota tana ta tangaɗi kamar ma ta kasa gane hanyar gida ne" Mama da take ɗaki, tana jin su, sai yanzu ta yi but ta fito ta ce "Jamila, ban hana ki naniƙar yarinyar nan ba, sai kin kwashi masifa da bala'i" Atine ta ce "To 'yar nema, da ki na jin duk abin da ake yi, ki ka ƙule a ɗaki?" Mama ta ce "Ya shafe ni ne da zan fito, ba zaki cikata ba?" "Mama faɗuwa za ta yi fa idan na cikata" "Dan ubanki ki rabu da ita aka ce, duk ranar da ta ji miki rauni, ta sabauta ki ai kya shiga hankalinki" Gaddafi ya yi maganar cikin ɗaga murya. Duk da abin da mai maganin nan, ya shaƙa wa Nana, bai gama sakinta ba, amma tana jin duk abin da suke faɗa. Ta zame hannunta daga jikin Jamila, ta dafa bango ta nufi ɗakinsu. Tana jin Baba yana tambayar ta, dan me ta baro wurin mai magani, tayi masa shiru dan ko buɗe baki, wahala yake yi mata balle doguwar magana. Tana jin yadda Yaya Atine ta cafe, take yi masa bayanin, bataliyar aljanun da ke kan Nana, har da ƙara abin da ba a yi ba, kamar yadda mai maganin yayi mata bayani. Tun tana jin su sama, har wani abu mai kama da bacci ya ɗauketa. Kamar a zahiri ta daina jin komai a duniyar da take ciki, ya zauna a gabanta yana kallonta, kafin ya ƙyaƙyace da dariya wani irin baƙin hayaƙi yana fita daga bakinsa. Sam dariyar babu daɗin ji, ta saka hannu ta toshe kunnuwanta, amma ba ta fasa jin dariyar ba. "Igiyar ƙaddara, ta ɗaure ki ta ko ina, kuma kina da damar kwanceta, amma azabar baƙin taurin kanki, ya hana ki saduda ki karɓi ƙaddararki" Nana ta numfasa ta ce "Shirka ba ta cikin ƙaddarata, komai za ka yi mini, ba zan karɓi abin da ka ke buƙata na yi ba" Ya ɗago dogwayen yatsunsa, ya kai fuskarta ya lakuto gumin da take ta yi, ya kalli gumin a hannunsa ya ce "Ki daina cika baki, lokaci zai fayyace komai" Daga haka ya ɓacewa ganin Nana. Bayan farkawar Nana, ta tashi da wata azababbiyar yunwa, ga sallolin da ake bin ta. Ta tarar da Ummi ta zo, ta gaisheta amma ta amsa mata sama-sama. Ba a damu ba, ta yi sallolinta ta koma tsakar gida ta ce "Mama akwai abinci kuwa?" "Babu" ta bata amsa kai tsaye. Ummi ta ce "Mhmm Nana kenan, ai in dai irin wannan abubuwan ne, yanzu ki ka fara gani, tun da zaman gidan bai ishe ki ba, shi wancan na farkon Allah bai ƙaddara an yi da shi ba. Shi malamin naku an ce ya fito yaƙi, amma duk da larurarki, Saleh ya ce yana sonki amma sai wulaƙanci ki ke yi masa. Ya je ai ya gaya mini duk abin da ki ka yi masa" Nana ta yi kunnen uwar shegu da Ummi, kamar ba da ita take ba. "Mun yi magana da Baba, aure babu fashi, ya ce a gaya masa iyayensa su turo" Nana ta kalli Ummi ta ce "Yanzu za ki so hafsa ta auri mutum irin Saleh? Kin san fa ɗan shaye-shaye ne, kuma a Lagos ɗin kin san ina ne wurin sana'arsa da suwa yake tare? Duk ba kwa duba mini wannan?" "Nana ke ma fa kina da aibun nan, amma ya runtse ido ya ce ya ji ya gani, ita fa rayuwa yanzu idan ki ka samu mai sonki, duk wani tone-tone ba naki ba ne ba" ba ta sake kula Ummi ba, har ta gama abin da za ta yi ta bar gidan. Tunanin yadda Allah ya ƙwaceta daga hannun mai maganin ɗazu take yi, da tuni ya cuceta ya cuci rayuwarta, ita kanta ta san Allah ne kawai ya ƙwaceta, amma ya riga ya bugar da ita. 'wataƙila ga in da addu'oinki suke yi miki amfani, amma ki ke garaje da ɓacin rai' wata zuciyar ta tunatar da ita, a take ta yi ta istigfari. Sosai Baba ya ɗauki maganar Saleh da muhimmanci, Nana kuma ta na ta kai kukanta ga Allah, duk da neman lafiya da take roƙa ya rinjayi duk sauran adduo'in da take yi. Gashi duk da shirun da take yi wa Saleh idan ya zo, ba ya zuciya sai ya kuma dawowa, dan babban abin da yake saka shi zuwa ba yau ba gobe, bai wuce tozali da ƙirar jikin Nana ba, da yake jin kamar zai ɗimauce, idan bai kai hannunsa jikinta ba. Ta kan ƙare masa kallo, tana mamakin yadda Baba ya rintse ido, daga ganin aibun Saleh, kama daga kan askin banzar da yake kansa, zuwa suturar da yake sakawa da sunan gayu. Kodayake dama gayu idan ya haɗu da jahilci hauka ne tuburan, duk soki burutsun da zai yi mata babu maganar Allah a ciki sai shirmensa. Gefe guda ga kewar malam Auwal da ta dameta, tabbas ba dan mutunci da kamewarta, na ɗiya mace ba da babu abin da zai hanata zuwa gidansu ta tuntuɓi ko lafiyarsa ƙalau. Sai dai duk da haka sai da ta tambayi abokinsa malam Nura, ya tabbatar mata da lafiyarsa ƙalau ayyuka ne su ka yi masa yawa kawai. Kimanin makwanni biyu kenan, ba ta ga malam Auwal ba, zuciyarta na raya mata, karɓar lambarsa a wurin malam Nura, ta ari waya ta kira shi, amma ta kasa. Kwatsam su na cikin karatu a aji, ta jiyo muryarsa a waje. Ta kasa riƙe kanta, ta tashi ta fita. Kafin ta isa, har ya shiga cikin ofishinsa, yana cikin tattara litattafansa, kawai ya waiwayo ya ga Nana. "Yaya Auwal meyasa ka ke guduna? Ina ta son mu haɗu na yi maka bayani, amma ka daina zuwa ma gaba ɗaya" "Babu malami a ajinku ne?" "Eh, tilawa muke yi" "Ki koma aji" ya bata amsa ba tare da ya kalle ta ba. Ta marairaice ta ce "Amma Yaya Auwal, magana nake son mu yi, dan Allah ka fahimce ni ba abin da ka gani, ba abin da ka ke tunani ba ne... "Ki tafi aji na ce Nana, ba sai kin yi mini bayanin komai ba" yayi maganar cikin tsawa. Tsayawa ta yi tana kallonsa, bayan tayi nasara sun haɗa ido. A hankali ta sauke ajiyar zuciya, ba ta tafi ba kuma ba ta ce komai ba, sai dai idonta ya cika da hawaye. Sai ya tausasa murya ya ce "Ki je aji Nana, ba na son gardama" Ta girgiza kai ta ce "Koma me ka ke ɓoye mini ka gaya mini. Kai malamina ne, kuma abin koyi na, ka karantar da ni nagartattun halayen fiyayyen halitta Manzon Allah Sallallahu alaihi Wasallam. Wanda ya haɗa da gaskiya, da kuma haƙuri. Ka gaya mini ko ma mene ne a ranka dan Allah" Jiki a sanyaye ya ɗan sunkuyar da kansa, sannan ya kalle ta ya ce "Nana kin san komai nufi ne na Allah, maganar aure tsakanina da ke, ba zai yiwu ba yanzu haka Qatar zan tafi da wani ɗan ƙanƙanin lokaci" Murmushi ta yi, duk da hawayen da ya cika mata ido, ta ce "Ko kai fa, ka ga yanzu da ka gaya mini gaskiya zan fi samun nutsuwa sosai da sosai. Ina yi maka fatan alkhairi amma dan Allah ka ci gaba da yi mini addu'a, na san larurata ce ta saka ka fasa aurena, ka yi mini addu'a Allah ya bani wanda zai iya aurena da larurata a haka" "A'a Nana, idan baki manta ba, tausayinki da halin da ki ke ciki, ya sanya na ce zan aure ki, ban ƙi auren ki saboda larurar ki ba" Ta share hawayenta ta ce "Eh, da fari tausayina, daga baya ka koma so na, dama na san zaka rabu da ni, dama na fi so na ji daga bakin ka ne, tun lokacin da aka ce ba zaka iya riƙe aure ba, na ga komai a bacci, har rabuwar nan tamu na yi mafarki na gani, ba zaka aure ni ba. Hakan ba ya nufin zan manta tarin alkhairin ka a gare ni, Ubangiji Allah ya baka mace ta gari lafiyayyiya" Zai yi magana ta girgiza kai, ta fice daga ofishin, zuciyarta na zafi hawayen da take ƙoƙarin dannewa, su ka ƙi dannuwa. Auwal bai taɓa tunanin yana son Nana har haka ba, sai da Umma ta hana shi aurenta, kuma abin bai tsaya a nan ba, sai da Umma suka tura shi Qatar. Nana ta tafi rijiya, ta ɗebi ruwa ta wanke fuskarta, sannan ta koma ajinsu aka ci gaba da tilawa da ita. Sosai rabuwa da Auwal ya shigi Nana, duk da ta yi mafarkin hakan, amma ba ta bari ta gasgata hakan ba. Har aka tashi daga makaranta, hankalinta ba ya kan abin da aka ƙara musu sam. Da daddare, bacci ya gagari idanun Nana, sai tunani da zancen zuci, ya din ga ziyartar zuciyarta, har ta rasa wane tunani ya kamata ta yi. Jamila ce ta zo da abinci daga gidan maman khairat, ta cewa Nana ta tashi ta ci, amma ta ƙi. Sai da ta takura mata, sannan ta ci kaɗan, ta sha lemon ta kwanta, sai dai abincin ya tsaya mata yaƙi wucewa. Tana daga kwance, tiryan-tiryan, yadda aka fasa aurenta na farko ya dawo mata, yadda take samari, su na tafiya, duk da galibi mutanen banza ne suke bibiyarta. Amma Suleiman ya zo da gaske zai aure ta. Sai dai Baba ya din ga zubar mata da mutunci a idonsa, ta hanyar roƙe-roƙen kuɗi, kuma wani abin mama ce take ziga shi yake yi, har ita ma wasu lokutan sai ta tura ta ce ya bata kuɗi, sun wuni ba su ci abinci ba. Tun yana bayarwa da marmari, har ya gaji ya fara mita. Ya san da Nana ba ta da cikakkiyar lafiya, duk da a lokacin abin ya lafa, amma mama ta zaunar da shi, ta din ga karanta masa Nana aljanu har sun fara haukata ta. Matarsa ta zo har gida ta ci mutuncin Nana, har da an gaya musu babarta ce take biye-biyen bokaye, abin ya koma kanta take fama da aljanu. Duk da dama Mama ta saba faɗar wannan maganar, idan ta so cin mutuncinta, amma abin yayi mata zafi ya mata ciwo. Wuni ta yi tana kuka, Suleiman da kansa ya je gida ya ba wa Nana haƙuri, bayan ya samu labarin abin da matarsa ta zo ta yi mata, sai dai tun da matar ta koma gida, ya aka rasa gane kanta, ta kwanta rashin lafiya. Ta din ga fama da matsanancin ciwon kai, idan ta fara sai ta fita hayyacinta ko gani ba ta iya yi, suka je asibiti ba a ga komai ba. Ya koma gidansu Nana, ya ce idan ta san wani abu ta yi wa matarsa, ta bari uwar 'ya'yansa ce, ba zai so lafiyarta ta taɓu ba, tun da ai ya zo ya bata haƙuri. Nana ta din ga rantse-rantsen ita babu abin da ta yi mata, ƙarshe dai matar kamar za ta haukace, ya zo ya ce a dawo masa da kayan aurensa, tun a waje Nana ta cutar da iyalinsa, ina ga idan ya aureta, dama kuma an ce masa mahaifiyarta na biye-biye. Duk yadda Nana take son ta yi aure, ko dan saboda tarin ƙalubalen da take fuskanta, amma fasa aurenta da Suleiman bai wani dame ta ba, domin tana fargaba mussaman yadda aka gama zubar mata da mutunci a wurinsa. Ajiyar zuciya ta sauke da ta zo nan a tunaninta, sai da kanta ya sara, ta sauke ajiyar zuciya. Ga abubuwa da dama su na cin zuciyarta, tana buƙatar abokin shawara da tattaunawa, amma rashin yardarta bai sanya ta bawa wani damar, hakan a rayuwarta ba. Mutanen da suka cancanci hakan a rayuwarta duk ba ta ita suke yi ba. Babbar damuwarta a yanzu, bai wuce yadda ta san ko ba ta so, Baba sai ya ƙaƙaba mata Saleh ba, dan ta fuskanci zamanta ne kawai ba a so cikin gidan, duk ga su Suwaiba da Jamila, su babu wanda yake takura musu a kan aure sai ita. Sosai take jin zafin rashin Auwal, ko ba komai mutum ne ma'abocin Alqur'ani da kuma riƙo da addini, ta san abu ne mawuyaci a iya cutar da shi, ta sanya ran idan tana tare da shi, za ta samu sauƙin wasu abubuwan. "Ke baiwar Allah" ta ji an kirata. Ta ɗaga kai, ta hangi wata mata bararoji a tsaye, ta yi kwalliya da tarin tsummokara, da wasu irin tarin sarƙoƙi na zare a wuyanta, da ƙullin kaya a hannunta, ta burtso da gashin ta gaban goshin ta. Nana ta ɗaga kai ta ganta a wani wuri, da ba ta san ina ne ba. Matar ta ce "Zo na baki magani" Nana ta ce "magani kuma, na me?" Matar ta sauke mayafin da ta rufe fuskarta, ko ina tsagu ne a fuskarta, har baka iya tantance kamaninta, saboda azabar billayen da ke fuskarta. Matar ta ciro wani magani a cikin, ƙullin kayanta ta ce "Ki zuba a tafin hannunki, ki lashe" Nana ta ce "To ai ba ki gaya mini na mene ne ba?" "Idan ka sha, ba zaki ganin Ƙaisar ba, zai daina bibiyar ki yana takura wa rayuwarki, zai rabu da ke har gaban abada. Dukkanin damuwar ki za ta kau, babu wanda zai sake zuwa auren ki, yayi nasarar korarsa ko ya saka miki wani ciwo. Dan yan daf da fara kashe mutane, domin wata ƙungiyar asiri ce suke nemansa ido rufe yayi musu aiki. Idan suka sadaukar masa da jini, zai fara kisan mutane ne, kuma zai fara da mutane mafi soyuwa a gare ki" Jiki na rawa Nana ta miƙa mata hannu, domin karɓar maganin. Matar ta yi murmushi, haƙoranta suka bayyana baƙaƙe ƙirin da su, ta kama tafin hannun Nana, ta zuba mata maganin, da yawa. Tana kama hannunta, Nana, ta ji tamkar an zare mata lakar jikinta, jikinta yayi wani irin sanyi, da ta kasa ko ƙwaƙwƙwaran motsi. Ta kai garin maganin bakinta ta fara sha... Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM AYSHERCOOL YOTA/002 P9 Ko da Nana ta sake lasar maganin, sai ta ga fuskar matar tana komawa baƙa ƙirin, tana ta fito da dogon harshe, tamkar na macijiya, wani abu mara kyan gani na futa daga bakin nata. Iya ƙarfinta Nana take son ta yi addu'a, idan mafarki take ta farka, amma ta ji tamkar an saka dutse an tokare maƙogwaronta zuwa huhunta. Babu tsammani, ta ga wata irin guguwa ta haɗu, Ƙaisar ya bayyana a tsakaninsu yayi wani irin mugun cilli da matar a gefe. Yayo kan Nana, ya zubar da sauran maganin hannunta, ya shaƙe mata wuya. Wani irin kakari ta din ga yi, ta na amai dunƙunlen jini yana fitowa ta hancinta da bakinta. Ji ta yi numfashinta na neman ɗaukewa. Ita ma Nanan, ya yi jifa da ita gefe, ta riƙe wuyanta tana numfashi da ƙyar. Ya kalle ta a zafafe ya ce "Idan ki ka ci gaba da irin wannan gangancin, za a kashe ki a haka, babu wani mahaluki da zai iya raba ni da ke. Guba ta baki za ta kai jininki ayi tsafi da ke saboda tasirin taurarinki. babu wanda zai iya baki wani magani ya raba ki da ni, idan ki ka ci gaba da yinƙurin rabuwa da ni, za ki kashe kan ki da kan ki" yana maganar tartsatsin wuta na fitowa daga jikinsa, yana ƙona Nana. A hankali ta buɗe idonta, ta ganta a kan shimfiɗarta, ta takure jikinta yana ta rawa, numfashinta yana fita da kyar. Wuyanta sai raɗaɗi yake yi mata, haka ma jikinta. Ta kai hannu ta ɗauki fitilarta ta kunna, tana haska ɗakin, ba kowa a ɗakin sai ita kaɗai. Jikinta ya ba ta wani abin tayi, su Jamila suka gudu suka bar ta a ɗakin. Ta yinƙura da azama ta tashi tsaye, amma jikinta sai raɗaɗi yake mata, kafaɗunta kamar ba a jikinta suke ba. Ayatul kursiyyu ta din ga karantawa, ta fita ta ɗauki buta, ta shiga banɗaki. Tana fara fitsari ta ji ƙarnin jini, tana dubawa ta ga fitsarin jawur, jini a maimakon fitsari. Gashi ko kwana bakwai ba ta yi da gama al'ada ba. Ta wanke jikinta tayi alwala, ta koma ɗaki, gaba ɗaya ta kasa yadda har yanzu ba a cikin mafarki take ba. Da safe ta fito ta yi aikace-aikace da za ta yi, Jamila ta ce "Nana me ya same ki haka?" "A ina?" "Jiya da daddare ki na ta kakarin amai, ki na kuka a bacci, yanzu kuma kalli jikinki, kamar an zane ki da bulala" Baba da ya fito daga banɗaki, shi ma ya kalli Nana. Jikinta duk kwanciyar bulala, gashi ta ɗashe ta yi haske, kamar mara jini a jiki. Nana ta kalli jikinta, ta ɗan taɓe baki ba ta ce komai ba, ta ɗebi ruwa ta shiga banɗaki domin yin wanka. Sai dai wannan karon ma, fitsarinta jini ne kawai yake zuba. Kawai ta jingina da jikin banɗakin, ta fashe da kuka, sai da ta yi mai isarta sannan ta ta fara yin wankan. Sai dai tana zuba ruwan a jikinta, ta ji kamar fatarta za ta zazzago, jikinta ya hau kyarma. Duk da a cikin banɗaki ta yi, haka ta furta a'uzubillah, ta cigaba da zuba ruwan a jikinta tana wanka, har ta kammala ta fito. Ta yi alwala, ta shiga ɗaki ta shirya, tana kallon Baba yana kallonta, amma ba ta gaishe shi ba, haka kurum ta tashi da matsanancin ɓacin rai, ko ganin Baban ba ta son yi. Ba ta kula kowa ba, ta fice ta tafi makaranta. Gaba ɗaya jikinta ciwo yake yi mata, ga jiri tana fama, dan haka a cikin aji ta yi zamanta, ta kifa kanta a kan tebur, tana ta kewar rashin Auwal. ***** "Safiyya" "Na'am Hajjaju" "Yaya kin yi magana da Jamila kuwa?" "A'a yanzu dai nake saka ran zuwanta" "Dan Allah, ki ɗan bugi cikinta ki ji, yarinyar nan ta sha lemon kuwa?" Maman khairat ta ce "In sha Allah, zan bugi cikinta zamu yi magana da ita" "Amma ina fatan, ba ki gaya mata ko na mene ne ba" "A'a haba Hajiya, ya ma za ayi na gaya mata, ai kin ce ko wani ma ya ci ba komai, ita ɗin dai ake so ta ci, zan tambaye ta idan ta zo" "To shikenan, na gode sai na ji ki" ***** Ƙamshin turare ne ya cika wa Nana hanci, sai dai ba ta motsa ba ko ta buɗe idanunta ba. Teburin da take kai, ya ɗan bubbuga, sai a lokacin ta buɗe idonta a hankali. Dishi-dishi ta fara gani. A hankali idonta ya washe, ta ɗaga kai ta kalle shi. Yayi murmushi ya ce "Anty ya dai ki ke bacci, ko babu lafiya ne?" A hankali ta tashi zaune, ta kalli agogon ajin nata ƙarfe biyu. Tunani ta hau yi, tun da ta shigo da safe take wannan baccin, ko kuwa? Maganar Muhsin ce ta dawo da ita hankalinta ya ce "Anty kin ga na gama" yayi maganar yana nuna mata littafin sa, da ya cika page guda da A. "Afuwan Anty Nana, direbansu ya yi tafiya ne, mahaifiyarsa babu lafiya, ni kuma ba ni da isasshen lokaci, na shiga wani meeting ne, shi yasa na daɗe ban zo ɗaukarsa ba, ki yi haƙuri na ɓata miki lokaci". Jinjina kai kawai ta yi ta tashi, ya ce "Mu je sai mu sauke ki a hanya" sai dai haryanzu ba ta yi magana ba, ta bi shi su ka tafi. Jamila na zaune, tana ta zaman kashe wando a gidan maman khairat, kamar yadda ta mayar da hakan ibada, tana tayata aiki su na hira. "Ni kuwa jiya kin ci abincin jiya Jamcy?" Jamila ta ce "Lallai ma Anty Safiyya, me zai hana ni ci, na yi abincin kuma na kasa ci?" "Wallahi ni gaba ɗaya kasa cin abincin na yi, na ce da na sani, na ce ki tafi da shi duka" Jamila ta ce "Subhnallah, ko dai Khairat za a yi wa ƙani" Tayi murmushi ta ce "Rufa mini asiri, wallahi sai da ki ka tafi na ga kamar abincin ba zai ishe ku ba, kuma har su Nana duk sun samu sun ci?" Sai da Jamila ta yi mamakin tambayar, amma ta ce "Eh mana, Nana ce ma babu lafiya, ba wani ci ta yi ba, kin san 'yar ƙi faɗi ce, sai na je da abu sau shurin masaƙi amma babu lallai ta ci" "Eyya, to ai ba komai, mun riga mun zama ɗaya Allah ya ba ta lafiya, ta sha lemon ma?" "Eh amma ba da yawa ba" Safiyya ta jinjina kai ta ce "Dan Allah ki yi mata sannu" Jamila ta ɗan taɓe baki ta ce "To, za ta ji, kin san ita kullum cikin ciwo take ne, abin nata ba na ƙare bane ba" Suka ci gaba da hira, ƙasan zuciyar Safiyya, cike da farin ciki ***** Ƙarfe huɗu da rabi na yammaci, sannu a hankali yake ƙarewa garin kallo, duk ya kwana biyu baya garin, amma ba wani abu ne ya canza ba, amma har cikin zuciyarsa yake jin kewar Kanon dabon. Tun daga can babban titi ya sauka, ya saɓo hanya, domin ya samu isashshiyar damar ƙarewa garin kallo, yadda yake so. Dandazon mutane ya hango a wani wuri, mutane na ta surutu da hayaniya. Har ya yi gaba, kawai ya dawo da baya domin ganewa idanunsa abin da ya tara wannan cincirindon al'ummar. Ya din ga kutsawa, yana ture mutane. Kawai ya tarar da wata matashiyar budurwa a kwance a wurin, sai dai ta juyar da fuskarta ba a iya ganin fuskarta. Ya taɓa wani mutum ya ce "Malam lafiya, me ya faru don Allah?" Mutumin ya ce "Wallahi tun azahar, muka ganta a kwance a wurin nan, an zata ma ko ba ta da hankali, ko kuma ba ta da lafiya, amma jikinta fes babu datti ba alamar hauka a tare da ita. An yi anyi ta tashi ko motsi ba ta yi, kuma tana da rai. An duba jakarta babu waya sai maka da kuɗi, yanzu ma dai an kirawo 'yan sanda". Bai ce uffan ba, cikin azama ya nufi kanta, mutane na ƙoƙarin hana shi, amma bai saurari kowa ya je kanta ya ɗago ta. Idanunta a rufe, sai dai hawaye da yake ta fita ta gefen idonta, ga jikinta zafi tamkar wuta. A sanyaye ya ce "Nana" shiru ba ta amsa ba. Miƙewa yayi yana ƙoƙarin ɗaukarta, wani ya ce "Malam lafiya, ina zaka kaita?" "Ƙanwata ce" ya faɗa a taƙaice, ya fita ya taro adaidaita sahu. Bai sake tsayawa yi wa kowa bayani ba, ya saɓa Nana ya shiga adaidaita sahu, ya tafi da ita. Mama na tsakar gida tana tankaɗen tuwo, sai ganinsa tayi a tsakiyar tsakar gida. Suwaiba da take jan ruwa ya kalla ya ce, "Shimfiɗa mini tabarma a tsakar gida" Ta ajiye gugan, ta ɗaukko tabarma, ya kwantar da Nana a kai. Ya ɗebo ruwa a kofi, ya zo ya zauna a kusa da ita, yana ƙare mata kallo, gaba ɗaya ta rame sosai da sosai. Cirko-cirko mutanen gidan suka yi, su na bin sa da kallo, kowa da magana a bakinsa, amma babu damar furtawa. Ya tofa ayatul kursiyyu, da falaqi da nasi, kowacce da bismillah, ya shafa mata ruwan a fuskarta, da tafukan hannayenta. A hankali yake bin jikint da kallo, yana mamakin shaidar duka ce, ko ta ƙonuwa a jikinta. "Nana" ya kira sunanta. Cikin sa'a sai ta buɗe idonta a hankali, ta sauke a kan fuskarsa. Shiru ta yi tana kallon sa, kamar ba ta taɓa ganin sa ba, zuciyarta na raya mata kawai tarkacen mafarkin da take yi ne. Ta yi shiru, ta tuna ta shiga motar baban Muhsin, su na tafe a hanya, a kunnenta ta ji ana ce mata, ga Auwal can a marrraba, nan da mintuna goma tirela za ta taka shi. Babu shiri ta tsayar da baban Muhsin, bai gama parking ba, ta buɗe motar ta fita daga nan kuma, sai ta ɗimauce ta rasa gane gaba da baya. Mayar da idanunta tayi ta sake lunshewa. "Ma'u" ya kuma kiranta yana matsa hannunta. Ta sake kallonsa a hankali ta ce "Wai da gaske kai ne?" "To da waye? Dama haryanzu ba ki warke ba, ki na wannan ciwon Nana? Kuma uban waye ya dake ki duk jikin ki ya tashi haka?" Ta yinƙura ta tashi zaune, kawai ta fashe da kuka. "To kukan uban me ki ke yi kuma? Na ce uban wa ya dake ki?" "Ba dukana aka yi ba" ta bashi amsa tana share hawayenta. "To me ya kai ki yin bacci a titi, maza sun baibaye ki, kamar ƙudaje sun ga mangwaron Binta suga" Ba ta bashi amsa ba, ta ci gaba da kuka. Ya tsuke fuska ya ce "Dalla yi mini shiru, ina yi miki magana ki na wani kukan banza" "Me yasa ka tafi ka bar ni?" Ta yi magana cikin kuka. Guntun tsaki yayi, ya ce "To dai ba ga ni na dawo ba? Uban me ake tsinana mini a gidan idan na zauna, yanzun ma tunaninki ne ya addabe ni, nake ta mafarkinki shiyasa na taho, kuma ina zuwa na tarar da dandazon mutane, ina dubawa na ga ke ce. Allah dai ya tsinewa wannan matsiyatan aljanun naki banzaye marasa imani" Za ta yi magana, Baba yayi sallama suka amsa, sai dai ya ja tunga ya tsaya, ganin wanda bai taɓa zato ba a gidan. "Kai imrana, uban me ka ke yi mini a gida? Me ya kawo ka gidana?" Tsuke fuska ya yi ya ce "Kamar yaya? Ya ka ke magana kamar wani shege ba kai ka haife ni ba? Gidan ubana na zo, kuma wurin 'yar uwata na zo" "Ban yi maka iyaka da gidana ba? Ki na me ki ka bari ya shigo mini gida?" Yayi maganar yana kallon mama. A ƙufule ta ce "Au to kokawa ka ke so na yi da shi? Ko saɓa shi zan yi na jefa waje, tun da kai ka dawo sai ka fita da shi ai" Ya sake kallon imrana ya ce "Ba magana nake yi maka ba? Ban hanaka zuwar mini gida ba?" Cikin rashin ɗa'a Imaran ya ce "Sai ka ce wani gidan kirki, to ka mayar da ni in da na fito, cikin uwata ta mayar maka da ni" Nana ta ce "Imarana Baba ne fa" "Shi ɗin, shekaru uku ba ka ga ɗanka ba, da haka yakamata ya karɓe ni komai girman laifin da na yi masa? Ba azabtarwa da ake yi mana ne ya tilasta mini barin gidan nan ba" Gaddafi ne ya shigo, bayan dawowarsa ya jiyo hayaniya daga cikin gidan ya shigo, domin duba abin da yake faruwa. Shi kansa mamaki ne ya kama shi, ganin Imran a gidan. Baba kamar ya fashe da kuka ya ce "Imrana ni ka ke gaya wa haka? Ka tashi ka fita ka bar mini gida na ce maka" "Idan na bar gidan shege nake, wallahi sai na gama kwanakin da zan yi. Ke Nana ga jakata nan zan je na dawo. Nana ta tashi ta ɗauki jakar, ta nufi ɗakinsu da ita, Baba ya daka mata tsawa ya ce "Bashi jakarsa ya bar mini gida" Cikin kuka Nana ta marairaice ta ce "Dan Allah Baba ka yi haƙuri, tun da ya ce idan ya gama kwanakinsa tafiya zai yi. Shekara uku ban ganshi ba, dan Allah ka yi haƙuri" "Au Nana kin fi son ɗan uwanki da ni ko? Amma yana sane da mu, ya kama gabansa ya tafi gantalinsa har shekaru uku, yana gararamba bai waiwayo gida ba, sai yanzu saboda ya mayar da ni ɗan iska zai dawo mini gida?" Imaran ya nufi Nana, ya karɓi jakarsa, ya kaita wani ɗan lungu ya ajiye, ya fice ya bar gidan. Shi kansa Gaddafi kasa magana ya yi, saboda tsagwaron zunzurutun tsageranci kawai yake iya ganowa a cikin idon Imran ɗin. ***** "Hajiya Sa'a aiki ya lalace fa" "Ban gane ba, kamar yaya?" "Akwai wani hatsabibin shaiɗani a tattare da yarinyar nan, ya lalata mana aiki gaba ɗaya. Ba a samu adadin jinin da ake buƙata a jikinta ba" Dafe kai Hajiya Sa'a tayi, ta ce "Yanzu mene ne abin yi, ka ce akwai sa'a a tattare da yarinyar yanzu babu wata dabarar kuma? Yarinyar ce wata irin majanuniya, har kaya na bayar a kai mata, babu yadda ban yi a sake kawo mini ita gidan yarinyat Safiyya ba, dama a can na ganta wai ta ƙi yarda. Ni kuma na abin na je gidansu ba, ba na son zargi da saka ido" "Aikuwa neman mafita ya ganki, domin wani baƙin sheɗani ne a tattare da ita, babu lallai ya bari wani ya raɓe ta, saboda wasu dalilansa, 'yar aiken tamu ma ya ƙona ta. Yanzu dole ki san yadda za ki yi, a sake ba ta maganin zamu sake tura wani ɗan aiken" Hajiya Sa'a ta jinjina kai ta ce "Amma, ba yadda za ayi a samo jininta nata, dole sai an bata wani abin ta ci?" "Eh dole ne, idan ba haka ba babu ta yadda za a samu jininta, ba zai bari a tunkare ta ba. Kuma ko ba haka ba, idan ba ta hanyar abincin da za a bata ba, ba kowane aljani zai iya raɓarta ba, saboda tana zama da alwala, kuma tana adduo'i shi kansa aljanin jikin nata, ba ƙaramar azaba yake sha ba. Dan haka yanzu ko dai a samu jininta ta wannan hanyar ko kuma ki janyo ta ƙungiya" Hajiya sa'a ta ce "Ba abu ne mai sauƙi ba hakan, muguwar miskila ce, ba kamar 'yar uwatta ba, da ɗayar ce ko nan ka ce na kawo maka ita, zan kawo ta, amma babu komai zan san abin yi, dole haƙata ta cimma ruwa" "Babu laifi" **** A hankali jikin Nana ya ci gaba da yi mata raɗaɗi, tamkar ana kunna mata wuta, ta daure ta din ga nanata suratul jinn, tun daga farko har ƙarshe a zuciyarta. Imaran ne ya dawo bayan sallar isha'i, hannunsa riƙe da ledoji. "Nanawo, sannu ya jikin?" Yayi maganar bayan ya ja kujera ya zauna. "Jiki Alhamdilillah" "Kai Nasiru ɗaukko faranti" yayi maganar yana kallon Nasir. Ya je ya ɗaukko faranti, ya zazzage musu gurasa da nama fal a kai. Ya kalli Nana ya ce "Ina Jamila ne? Tun da na dawo Suwaiba kawai na gani, ko an yi mata aure ne?" Nana ta ce "A'a tana maƙwabta" Ya tsuke fuska ya ce "Har bayan sallar isha'i, kamar gidan ubanta?" Yana rufe baki ta yi sallama. Sai dai ta tsaya da ta ga Imaran, ta ce "Imran dan Allah kai ne ko gizo idona yake yi mini?" "Ban sani ba, tun la'asar ba kya gida kina can kina gantali a gidajen mutane" "Haba ai ka bari mu gaisa, ina ka tafi shekara uku ba wanda ya san inda ka ke?" "In da ki ka aike ni. ware ki wanko hannu ku zo mu ci abinci" Ta ce "Yanzu ma kuwa" Cikinsu ya shiga, suka rufarwa gurasar, yana kallon Nana, da ƙyar take ci. A haka Gaddafi ya shigo ɗaukar abincin dare ya tarar da su. Imran ya kalli Nana ya ce "Wai ba za ki ci ba ne?" "Imrana ba a ɗebarwa Baba ba, Mama ba a bata ba" Haushi ne ya kama shi ya ce "Wallahi ba zai ci ba, da na zo ko ruwan gidansa ya bani, ba kora ta ma ya yi ba? Kar Allah ya sa ki mayar da hankali ki ci" Abinka da 'yan uwa, haka suka kewaye Imran. Jamila ta ce "Wai dan Allah tsawon wannan lokacin, ina ka tafi?" "Duniya na shiga mana, tun da an kore ni an ce ba a buƙata ta a gidan" Baba yayi sallama, suka amsa masa gaba ɗaya. "Imarana ban ce ka bar mini gida ba wai?" "Wallahi Baba ba zan bar gidan nan ba, sai na gama abin da nake yi" A fusace Gaddafi ya ce "Wai kai baban  ka ke yi wa magana a haka?" Imran ya kalle shi ya ce "Kai kuma ina ruwanka da ni? Kai a yaya ne baka yi masa magana, ya taɓa korarka ne? Ka ga tun da na zo ban kula ba kar ka shiga harkata ehee" A fusace Gaddafi ya yo kan Imran, Imaran ya miƙe tsaye ya ce "Wallahi yanzu ba da ba ce, wallahi ka taɓa ni sai na soka maka ƙarfe". Baba ya tare Gaddafi ya ce "Rabu da shi, kar ya yi maka rauni, alamu sun nuna haryanzu yana shaye-shaye" "Wallahi Baba ko uban me yake sha, dai-dai nake da shi, ka bari na sauke masa tsagerancin da yake kansa" "A'a gara dai ya riƙeka, dan wallahi ka taɓa ni sai na buga ka da ƙasa ba abin da ya dame ni" ya kaɗe rigarsa ya fice. Nana ta dafe kanta, ta rasa abin da yake yi mata daɗi, tun tsaowar su Baba ba sa shiri da Imran ko kaɗan, tabbas a baya babu wanda suke tsoro sama da Gaddafi sun daku a hannunsa, saboda ya ce babar su ce ta yi sanadin da aka saki babarsa, kuma har ta mutu Baba bai dawo da ita ba. Ta yi alwala ta yi sallar isha'i ta kwanta, ba dan tana jin bacci ba. Kwanciyarta ke da wuya, ta lumshe idanaunta, ta lula duniyar tunani, ta buɗe idonta domin juyi ta gyara kwanciyarta, kawai ta ganta a bakin wani ruwa a zaune. Ta ɗaga kai ta waiwaya, ba kowa a wurin, sai dogwayen bashiyu koraye shar, ruwan gabanta kuma sai tambal-tambal yake yi tamkar zai yi ambaliya. Ta kalli jikinta, ta ga babu kaya a jikinta, sai wani ɗan mayafi da aka rufe mata ƙirjinta, zuwa al'aurarta. Jikinta duk ya ɗuri ruwa, ya kwaile saboda ƙuna. Ta yinƙura za ta ja ƙafafuwanta, ta tashi ta gansu ɗaure a jikin sarƙa. Free pages na daf da ƙarewa. Contact me to subscribe yours. Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU YOTA/002 AYSHERCOOL P10 Ta waiwaya jin maganganun su Suwaiba, a kusa da ita, har su na faɗa a kan charger, amma ba ta ganinsu sai ita ƙwal a wurin. Ta rintse idanunta, tana faɗin "La haula wala ƙuwwata illa billah" Ji ta yi an taɓa ta, ta buɗe idonta tana tsammanin ganinta a ɗakinsu, amma ta ganta dai a wurin a zaune. Ya durƙusa ya kwance sarƙar ƙafarta, sannan ya kalleta, ba ta iya kallonsa, duk da a suffar mutum ya bayyanar mata, duk da dogwayen yatsunsa masu ɗauke da zaƙo zaƙon farata sun fallasa bambancin da yake da shi da bil adama. "Kalli jikin ki, kalli irin raunukan da suke jikin ki, saboda azabar taurin kan ki da dan halin ki zan bi, da sai dai ciwon nan yayi ajalinki" Nana ta ɗan kalle shi, ta kawar da kanta ta ce "kai ne fa ka yi mini raunin, da tartsatsin wutar da ya din ga fitowa daga bakinka" Ya dube ta ya ce "Ba zan yi miki irin wannan illar ina sane ba, kafofin da za a din ga zuƙar jininki ake so. Ina sake jaddada miki ki karɓi abin da ƙaddara ta zana miki. Ni hadiminki ne zan zama mai biyayya a gare ki, idan kuma ki ci gaba da bujirewa zan ci gaba da azabtar da ke, dan rayuwata ba za ta salwanta a banza a kan ƙoƙarin kare ki da baiwarki ba, ba wannan aikin na karɓi yi daga wurin kakaninki ba". Ta ɗan ɗago ta ce "Wani irin aiki ka karɓa a kaina, kuma meyasa ka dage lallai ni zan yi harkar bori? Kai ba ka ga ilimin addini ya yawaita ba yanzu? Su ma na yi imani da Allah, rashin ilimi ne ya sanya su ka yi wannan harkar. Kuma duk sauran mutanen dangin babu wanda za ka matsawa ya yi harkar shirka sai ni?" "Ba ni da lokacin da zan tsaya yi miki wani dogon bayani, amma ina mai tabbatar miki tashin hankali da masifun rayuwa yanzu a ka fara, ko ƙafa ba ki saka ba domin ba ayi komai ba". Nana ta ce "Abin da Allah ya ƙaddara ya zai same ni ne kawai zai faru da ni, na zan taɓa yadda da duk wata tatsuniya da za ka karanta mini ba" "Shikenan, ba na buƙatar dama ki yarda, zan cire hannuna na ja da baya na zura miki ido, da kan ki za ki neme ni". "Da ni da kai duk bayin Allah ne, dan haka babu yadda za ayi na nemi taimakon ka. Ko da ka tare mini wani abu, Allah ne ya tare mini kai sila kawai za ka zama" Ta yi maganar cike da ƙwarin gwiwa. Yayi mata shiru, ya juya ya kalli ruwan nan, ya fara fito da wata baƙar iska daga bakinsa yana hurawa ruwan. A take iskar ta dinga tafasa ruwan har da tururi. Ya kwantar da Nana, ita kuwa ta zuba wa sarautar Allah ido. Ya ce "Maganin da matar nan ta baki ki ka sha, ta samu damar tsinka wata jijiya a mararki, shi ne ki ke wannan fitsarin jinin kuma sun samu sun tara, duk da bai ishe su ba. Wannan ciwon na jikinki, ba ƙonuwa ba ce ramuka suka yi miki, jininki na zubowa ta ramukan sai dai ba za su iya amfani da shi ba, saboda yana jikin fatarki ne kuma ba za su iya raɓarki a haka ba" Nana jin sa kawai take yi, ba wai dan tana yadda da maganganun na sa ba. Ya din ga ɗebo ruwan tekun nan, yana zuba wa Nana a jikinta. Ta rintse idanunta tana jin yadda wani irin zafi yake ratsata har cikin ƙashinta. Ya zira hannunsa a cikin bakinsa, ya zaro wata doguwar allura, ya shammaci Nana ya caka mata a mararta. Ta kurma ihu sai da gaba ɗaya dajin ya ɗauka. A zahiri kuwa, tun da ta lumshe idonta, jikinta yake rawa haƙoranka suna karo da juna, idanunta suka kakkafe. Su Jamila suka fito suka bar mata ɗakin,  zuba mata ruwan nan da ƙaisar yake yi, a zahiri ihu take yi. Gaddafi ya je ƙofar ɗakin ya tsaya yana bala'i. "Wallahi ko ki rufe mana baki, ko na yi miki mugun duka, dan abin naki zunzurutun iskanci ne na za ki hana mutane bacci ba". Amma a banza dan ba ta san ma yana yi ba, sai wani irin gurnani da take yi kamar an yanka sa. Ya nufi wurin da aka sayo ice aka ajiye, ya samo wata sanda dai-dai lokacin ta fito daga ɗakin za ta fita waje. Babu tausayi babu imani, ya fara shirga mata icen nan a jikinta. Nasiru tun da Nana ta fara wannan gurnanin, ya fita majalissar da ya ga Imarana, ya ce masa ya zo ya ga abin da Nana take yi, zuwansu yayi daidai da dukan da Gaddafi yake yi wa Nana. Imran ya hankaɗe shi ya ce "Kar ka sake dukanta, wani irin azzalumi ne kai, da wanne za ta ji? Dama abin da ku ke yi mata kenan" hankaɗe shi Gaddafi ya yi yana ƙoƙarin sake dukan Nana, Imran ya ɗaukko ƙaton itace a murhu yana wuta yayi kan Gaddafi zai jirga masa gadan-gadan. Da ƙyar Baba ya raba faɗan ya ce "Gaddafi na ce ka daina dukan yarinyar nan, tun da ka ga nima na saduda ba ciwon ƙarya take yi ba, ba ta da lafiya da gaske. Kuɗin auren da na ce yaron nan Saleh ya kawo, su nake jira mu kaita can in da ka ke ba ni labarin nan, amma tun da abin ya kai haka ma dole ko rance ayo a kaita wannan jaraba ta ishe ni. Kai kuma jarababbe ɗan nema, kai ba aljan ba amma ka fi sheɗan shaiɗanci,  wallahi aljanun Nana sun fiye mini hatsabibancin ka nesa ba kusa ba Imrana." Imran bai kula Baba ba, ya durƙusa ya ɗago Nana, matsanancin tausayinta ya mamaye zuciyarsa. Suka ci gaba da hayaniyarsu, shi kuma ya mayar da hankali kan tofa wa Nana ayatul kursiyyu, a fuskarta. Miƙa ta yi a hankali, sai kuma ta riƙe hannunsa tana ajiyar zuciya. "Nana" "Na'am Imran, ka tsaya a kusa da ni, tsoro nake ji" "Na sha gaya miki, ki daina jin tsoro, kar wani abu ya din ga ba ki tsoro. Babu wani abu da ya isa ya cutar da ke sai abin da Allah ya ƙaddara zai same ki" Ta jinjina masa kai, tare da ƙara jin ƙwarin gwiwa. Ya ɗaukko ruwa pure water ya bata ya ce "Yi bismillah ki sha ruwa" ta karɓa ta yi bismillah ta fara sha. Ta kammala sha, ta ce "Alhamdilillah" "Amma Nana ki na addu'a kuwa?" Ta jinjina masa kai ta ce "Eh" "Lamarin nan yana damuna Nana, da kafin na tafi kamar abin ya lafa miki" "Eh, tun da aka saka mini rana ta farko abin ya dawo, har zuwa yanzu" Imran ya ce "Ba komai akwai Allah" "Imran" ta kira sunansa a hankali. Ya amsa da "Na'am" "Tun da ka tafi, ka je wurin babarmu ne?" Tsuke fuska ya yi ya ce "Ai ni da sake zuwa in da take har abada" Cike da damuwa Nana ta ce "Saboda me? Mahaifiyarmu ce fa, ni ko a waya ba na samunta, ga Baba ya hana duk wata hanya da za ta sada ni da ita" "Nana, ki yi focusing a kan rayuwarki. Duk duniya babu wanda dan ya cire hannunsa daga rayuwarki za ki kasa rayuwa. Uwa na haifar jariri ma, ta mutu a take ya girma ya rayu, balle ke da wayon ki da girman ki, ki ci gaba rayuwarki kawai. Ta fi son mijinta da yaran da ta haifa yanzu a kanmu, ban da haka ai ya kamata ta waiwayo mu, ta ji halin da muke ciki, amma tana can tana rayuwarta cikin kwanciyar hankali" Hawaye na bin idon Nana ta ce "Ba haka ba ne Imran, babarmu tana sonmu, Mijin da take aure ne ba ya son mu je in da take, nan ma idan ta zo ka san Baba wulaƙanci zai yi mata". "Kin ga mu bar wannan maganar, ki je ki yi alwala ki nemi wuri ki kwanta kawai" fafur Imran ya ƙi yarda su ci gaba da maganar. ***** Buzaye ne su uku, zaune a cikin jeji, mai ɗauke da manyan bishiyu, iska sai kaɗawa take yi. Dukkaninsu sanye da rawani. Shikaɗai ne a gefe, ya zuba shayi a kofi , yana sha yana lumshe idanunsa, alamar yanayin yana yi masa daɗi. Cikin damuwa Habu ya ce "Souley, na rasa abin yi, kaina ya kulle fa" Souley ya ce "Nima hakan take Habou, anya ba za ka mayar da shi Nijar ba, tun da an kasa samun magani?" Da sauri Habu ya girgiza kai ya ce "A'a, ba zan mayar da shi Nijar ba yanzu, akwai wani mai magani da na ji labari, har kwantar da mutane yake yi, ina jiran cikakken adireshin gurin ne, shi ma za mu jarraba" "To ai ni tsoro nake ji ne Habou, kar a garin yawon neman maganin nan a samu mushikila, ka na kallo kullum abin nasa babu wani ci gaba, duk in da aka je sai dai ace mana babu mafita. Kawai ka tsinci mutum ka yi ta wahala da shi, ka je in da ka tsinto shi ka mayar da shi kawai mu huta" Habu ya kalli Sule cike da takaici, kawai ya tashi, ba tare da ya sake tanka masa ba ya nufi in da ɗayan yake. "Taso mu tafi" yayi maganar yana kallonsa. Sai dai bai motsa ba, ya ci gaba da tsiyayo shayin da yake cikin buta yana sha. Habu ya miƙa masa hannu, ya sake cewa "Taso mu tafi" sai a lokacin ya ɗaga kai ya kalli Habu, ya ƙarasa shanye shayin, ya tashi tsaye. Sule ya ce "Habou kalli fa ko magana a 'yan kwanakin nan ba ya yi, sai a shafe kwana da kwanaki bai ce komai ba, haka zamu ci gaba da wannan aiki haka?" Habu bai tanka masa ba, ya riƙe hannunsa suka yi gaba. ***** Dawowar Imran gidan malam Isa, ya sanya kullum cikin rigima ake da shi, kullum sai sun yi faɗa da Baba ko Gaddafi. Ba ya kwana a gidan, amma garin Allah na wayewa zai zo. Nana ta samu afuwa sosai da dawowar Imran. Saboda ba ta taɓa zama da yunwa, sau ukun nan sai ta ci abinci a rana. Sai dai ta kasa tunanin Auwwal, tun ranar da suka rabu, ba ta sake ganinsa ba. Ga Baba ya fara addaba mata da maganar Saleh, wanda ko sunansa ba ta ƙaunar ji. A can makaranta da take koyarwa, mahaifin ɗalibinta Muhsin, ya fara damunta, kullum ya zo ɗaukar Muhsin, sai ya ce zai rage mata hanya. Ga shi ba ta da damar tafiya, sai an gama zuwa ɗaukar yaran gaba ɗaya, kuma kullum Muhsin ne ƙarshen zuwa ɗauka. Yau bayan ta dawo daga islamiyya, Yamma liƙis, Baba ya shigo fuskarsa ɗauke da fara'a ya ce "Ke Nana, ki je ga Saleh can a waje yana jiranki" gaban Nana ya faɗi. Imran ya tashi ya nufi hanyar fita, Baba ya ce "Kai malam ba kai fa kai na ce ba" Ya waiwayo ya kalli Baba ya ce "Ni akwai gurin da zan je" ya fice. "Ke kuma Nana ba magana nake yi miki ba?" Jiki a sanyaye ta ce "Ina zuwa, kaya zan canza" Imran kuwa yana fita ya tsaya ya ƙarewa Saleh kallo, ya ce "Kai ai kamar na sanka a gidan Ummi" Saleh yayi murmushi ya ce "Ba kama ba ce ba ni ne ai" Imran ya ce "Bala'i ashe idan na je neman aure nima za a bani, duk da ana ganin ba ni da saiti. Kai yanzu saboda ka raina wa kanka hankali gurin ƙanwata za ka zo neman aure a haka? Kalli wani shegen wando a jikinka ba ka san saukakkiyar Alqur'ani ba ce, kuma mahaddaciya ba?" Saleh yayi saroro yana kallon Imran. "Eh kalle ni da kyau, wallahi sai na je har gida na kasa wa Ummi warning, mai ku ka mayar da Nanan, wallahi ta fi ƙarfinka me za ta yi da ɗan jagaliya kamar ka?" "Saboda na zo ƙofar gidanku neman aure, ka ke gaya mini abin da ka ga dama?" Imaran ya ce "Malam gaskiya nake gaya maka, ba ka cikin irin mutanen da Nana za ta so da aure, a tsarinta tana son mutum mai kamala da sanya manyan kaya kuma... Shiru ya yi, ganin Nana ta fito fuskar nan babu walwala. Maimakon ya tafi sai ya ja ya tsaya, takaici ya hana Saleh magana, a girme ya girmi Imran amma ya tsaya yana gaya masa magana dan ya zo wurin ƙanwarsa. Ya maze ya kalli Nana ya ce "Gimbiyata barka da fitowa" Imran ya kwaɓe baki yana jiran me Nana za ta ce. Ta ɗago suka haɗa ido. "Amma ko za ka bamu wuri mu yi magana" Saleh yayi maganar yana kallon Imran. "In ba ku guri na je ina? Ka zo wurin ƙanwata zance da crazy jeans, meye banbanci na da kai, da ake cewa ba ni da hankali?. Kai wallahi ba za ayi zancen nan ba, ke koma gida ranar da ya shirya neman aure, yayi shigar mutunci ya zo" Babu musu Nana ta shige gida, dama haka take so. Baba na ganin ta dawo ya tambayi ko lafiya?. "Imaran ne ya ce na dawo gida" "Ki dawo ki yi masa uban me? Idan ba ki yi aure ba zai aure ki ne?" Ya nufi waje yana faɗa, ya tarar da Imran ya tare ƙofar gida yana cewa Saleh idan gidan ubansa ne, ya ture shi ya shiga da wannan shigar tsiyar. "Imrana wai ba ka da hankali ne? Meye haka?" "Baba, wai ya za a ɗauki aure a ba wa mutumin da zai zo neman aure, yayi ido huɗu da sirikinsa da yagaggen wando, da tarin suma kamar shekararren zakara. Kuma a gaya masa gaskiya Nanan nan fa ba son sa take yi ba" Baba ya ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Imrana yaushe ka yi hankalin da ka fi ni sanin dai-dai? Shigar mutum ake dubawa ko halin iya riƙe auren? Ita Nanan ba taimaka mata zai yi ba, tun da ba lafiya ce da ita ba" Imran ya ce "Baba neman kan da ka ke yi da Nana ba daidai ba ne ba, Allah ya ɗora mata larura alhakinka ne nema mata magani, ba neman kai da ita ba, amma shikenan 'yar ka ce, duk matakin da ka ɗauka a kanta daidai ne" yayi maganar yana barin gurin. Baba ya kalli Saleh ya ce "Dan Allah malam Saleh ka yi haƙuri, yaron nan ba cikakken saiti ne da shi ba, ka san idan mutum yana shaye-shaye sai a hankali ka yi haƙuri. Nana 'ya ta ce kuma na isa da ita, ka je ka turo magabatanka kawai kar ka ɓata lokaci kamar yadda wancan yayi" Saleh ya ce "In sha Allah Baba na gode sosai" "Yauwwa yi tafiyarka, kar ya zo ya yi maka wani haukan a ka" Saleh ya so keɓewa da Nana, amma Imran ya wargaza komai. An fara kiraye-kirayen sallar magariba, Jamila ta shigo Nana ta fara  nema, Nana ta ce "Wannan kiran fa ta samu ne?" "Wai dan Allah ina kayan da Hajiya ta bani na kawo miki, ko sau ɗaya ba ki saka ba, balle na yi miki hoto na tura mata, tun da na san ba za ki je ta gani ba" Nana ta ce "Zan saka ne, kawai ni ban san dalilin da ya sanya ta bani kayan ba ne, amma zan saka in sha Allah" Jamila ta ce 'Ai mace ce mai kyauta, babbar 'yar kasuwa ce fa, kwanan za ta fara bani kaya ina ɗora nawa nima, kin ga turare ta bani na kawo miki " ta yi maganar tana miƙa wa Nana wani turare. Nana ta karɓa tana murmushi, kasancewar tana son ƙamshi sosai. Ta sunsuna turaren ta kalli Jamila cikin murmushi ta ce "Amma ƙamshin turaren nan yayi daɗi sosai, ki ce mata na gode sosai" Nana ta fara ƙoƙarin fesa turaren a hannunta, amma idan ta fesa babu abin da yake fitowa, ga kuma turaren tana gani cikin kwalba. Tayi tayi amma abu ya gagara. Suwaiba da ta fito daga banɗki ta ce "Wai ke Jamila ba ki gaya wa hajiyar, ki na da 'yar uwa da ku ke uwa ɗaya uba ɗaya ba, ni ba zata bayar da komai a kawo mini ba sai wata Nana da uba kawai ku ka haɗa?" Suwaiba ta ƙaraso, ta karɓi turaren hannun Nana, ta fesa a hannunta ta sunsuna. Wurin da ta fesa turaren Nana ta ga duk ya ɓuɓɓule, kamar an caccaka allura jini ya fara fitowa. Sai dai ta ga Suwaiba normal, ba ta nuna wata alama na ta ga abin da ya faru ba, hakan ya tabattar wa Nana, ita kaɗai take gani. Suwaiba cike da mugunta, ta feshe rigar material ɗin jikinta milk. Nana ta ɗan ja da baya ganin jini, ya ɓata rigar maimakon ruwan turare. Suwaiba kuma ta ce "Amma turaren yayi ƙamshi" tana sake feshe jikinta da shi. Sai dai duk in da turaren ya taɓa a fatarta ɓulewa yake jini ya fara zubowa. Ta gama fesawa, ta bawa Nana turaren ta ci gaba da sabgoginta. Mama ma masifa ta hau yi, wai tana uwar Jamila ba a bayar da komai a kawo mata ba sai wata Nana. Jiki a sanyaye Nana ta shiga ɗakinsu, tana sake kallon kwalbar turaren. Ta buɗe ta ƙara fesawa a jikinta da hannunta, amma yaƙi fitowa. Ta ajiye turaren tana tunanin ko sharrin ƙaisar ne. Ta sake fitowa yin alwala, Baba ya zaunar da Gaddafi yana ta gaya masa abin da Imran yayi, tare da ƙorafin ya gaji da rashin mutuncin da yake aikatawa. Nana hankalinta ba ya kan abin da suke faɗa, hankalinta yana kan Suwaiba, da jini yake ta gangarowa daga hudar jikinta, kuma rigar jikinta ta rine zuwa jini. Amma normal suwaiba na ta ayyukanta. Nana ta ware a gefe, tana ta jan "wa hifzan min kulli shaiɗanin marid" Sam jikin Nana ba ƙwari ta kwanta, duk addu'a da ta zo bakinta yi take yi, ta waiwaya ta kalli in da Suwaiba take, ta jiƙe jagab da jini ga ƙarnin jinin ya cika ɗakin babu daɗin ji. Suwaiba na ta kallon kaɗe-kaɗenta a waya, har bacci ya kwashe ta. Nana ko kyakyawan ƙifta ido ta kasa yi, ganin yadda jinin ya jiƙa katifar da Jamila da Suwaiba su ke kai, ya gangaro ƙasa. Ana haka Suwaiba ta kurma wani irin uban ihu, Nana ta razana, ganin wannan bararojin da ta ba ta magani ta lasa, jikinta baƙi ƙirin ta koma kamar gawayi, fuskarta ce kawai ba a ƙone ba sai gashinta, ta tsaya a kan Suwaiba ta kafa haƙoranta a wuyan Suwaiba tana zuƙar jini. Maimakon Nana ta yi addu'a kawai ita ma sai ta saka ihu ta suma a gurin. Cikin ihu da kururuwa Suwaiba ta ce "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Mama Baba ku taimake ni, Nana za ta kashe ni, Nana tana shan jinina dan Allah ku yi mini rai Nana na shan jinina!!! Ku tuntuɓe ni kai tsaye, domin fara biyan naku kuɗin littafin. https://wa.me/2348081012143 Ayshercool 08081012143 Ko kuma ku kasance da ni a kan manhajar arewabooks @ayshercool7724 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM AYSHERCOOL YOTA/002 P11 Ɗungurungum, page ɗin yau naku ne, YOUNG TALENTED WRITERS ASSOCIATION, Tare da 'yan Ayshercool media, ina godiya sosai da sosai. A wannan karon Mama ce ta fito da gudu, jin muryar Suwaiba tana ihu. Sai dai ta tarar da Nana a gefe, tana bacci. Ta ɗago Suwaiba tana kiran sunanta, sai dai Suwaiba ta rirriƙe wuyanta, tana numfashi da ƙyar tana cewa "Nana ce, Mama ki taimake ni za ta kashe ni" Cikin kuka maman ta fara ƙwalawa Baba kira "Malam Isa ka zo Nana za ta kashe mini 'ya, na daɗe ina faragbar kar ta cutar mini da yara, gashi za ta kashe Suwaiba" Jamila ma tuni ta tashi, ta ja gefe, domin ita ma a tsorace ta tashi, saboda mummunan mafarkin da ta yi da Hajiya sa'a tana ƙoƙarin shaƙe ta, ta caka mata wata wuƙa. Baba ya ce "Wani irin Nana za ta kashe ta kuma? Ba ga Nanan a gefe tana bacci ba?" Cikin fushi da tsawa ta ce "To ka ƙaraso mana ka ga abin da take yi" Ya ƙarasa ya ga Suwaiba, ta rirriƙe wuyanta, idanunta duk sun fito waje sai kakari take, da ƙyar take furta Nana za ta kasheta. Baba ya ce "Suwaiban Baba, buɗe ido ki ganni, Nana bacci take yi me ki ke gani?" Cikin kuka da kakari Ta ce "Baba wallahi Nana ce, jinina take sha, ka hana ta zan mutu" Baba ya koma gurin da Nana take, ya kai hannunsa ya juyota, idanunta a buɗe, amma babu baƙar ƙwayar idonta, sai farar kawai. Jikinta kuma sanyi ƙalau kamar gawa. "Ni wannan wane irin abu ne haka?" "Ke Jamila, je ki ki taso mini Gaddafi" Jamila ta tashi jiki a sanyaye ta fita ƙofar gida, ta ƙwanƙwasa wa Gaddafi ɗaki. Tare suka dawo, yana tsaki yana bala'in shi tattarawa zai yi ya koma in da ya fito, ya gaji da wannan bala'in na gidan. Ɗan tsayawa yayi yana kallon in da Nana take, ga gefe Mama riƙe da Suwaiba tana kuka. Ya ce "Mutuwa Nanan tayi ne na ganta a haka?" Cikin kuka Suwaiba take miƙa wa Gaddafi hannu ta ce "Yaya ka taimake ni, Nana za ta kashe ni, jinina take sha" tayi maganar tana kuka. "Wane irin shan jini kuma?" Nana kuwa tuni ta lula wata duniyar a yanayin da take ciki. Domin kuwa Ƙaisar take gani. Ya ce "Kin ga da kin sake kin fesa turaren nan a jikinki, da jininki za a sha ba nata ba. Aike ne na musamman domin ke, da na bari kin fesa turaren nan da sai dai wata ba ke ba" Nana ta kalle shi ta ce "To ni me za ayi da jinina? Kuma meyasa ba ka hana wannan mummunar matar shan jinin Suwaiba ba?" Ya tanƙwashe ƙafafuwansa ya kaɗa kai ya ce "Saboda ke ce uwar gijiyata, alhakin kula da ke ne kawai a kaina. Duk da ba jininta suke buƙata ba, amma idan 'yar aiken ta ji daɗin jinin na ta, to fa ta samu wurin zama. Ko da su can jinin bai yi musu amfani ba, to ita za ta ci gaba da amfani da jininta, domin ta warke daga ciwon jikinta, idan ba ayi wasa ba hakan zai yi ajalinta." Cikin damuwa Nana ta ce "To ka yi wani abu a kai mana" Yayi murmushi ya ce "Zan iya wani abu a kai tabbas, amma daga lokacin da ki ka fara bani umarni hakan yana nufin kin karɓi gadon gidanku. Kuma zamu yi aiki tare" Da hanzari ta ce "A'a ni ba zan iya shirka ba na gaya maka. Amma ba zan zuba ido komai ya tafi a haka ba. Idan haka ne anya ba wannan matar Hajiya sa'a da ta kawo turaren babu masaniyarta a kan wannan abun?" Murmushi ya yi ya shafi gefen fuskar Nana ya ce "Ban sani ba, amma ke ma zan shafe komai daga kanki yanzu wani binciken ba shi da amfani sam. Mussaman ke da ba za ki yi abin da ya dace ba, idan ki na tsananta bincike wataran za ki shiga gurin da ba zan iya ciro ki ba. Kalli nan ki ga, ta waiwaya domin ganin abin da yake nuna mata. Ɗakinsu ta gani, Suwaiba ta samu bacci, Jamila kuma ta ce Allah kar ta, ba zata kwana a ɗakin nan ba tsoro take ji. Mama ta ce su tarkata su koma ɗakinta, su kwana tare da yaranta a bar Nana ta ci kanta. Baba ya kalli Gaddafi ya ce "Gaddafi, gobe in Allah ya kaimu dole mu yi sammako, mu kai yarinyar nan gurin da ka faɗa ɗin nan. Ni kaina na fara jin tsoron abubuwan nan". Gaddafi ya ce "Allah ya kaimu" Nana ta dubi Ƙaisar ta ce "Ni dama gurin mamana ka nuno mini, na ganta ko na ji daɗi" "Idan na fara karbar umarninki, haka yana nufin kin amince da sharaɗina, ni kuma zan yi miki mubaya'a na zama mai hidima a gare ki" "A'a bari ba na so" tayi maganar tana girgiza kai. Ya saka dogwayen yatsunsa yana ci gaba da shafa kumatunta ya ce "Alamu na nuna, sarƙar ƙaddara ta mayen ƙarfe na ƙoƙarin janmu wani  wuri, ta yi wani ɗauri mai wahalar kwancewa. Ko na ce sarƙar na ƙoƙarin sarƙe ki. Gobe za a wuce da ke gurin mai magani, 'yar uwakki ta shafa miki mugun tabo, tun da ta ce kina sha mata jini, babarta ba za ta yi shiru ba, za ta yi ta gaya wa mutane ne. Ga yayanki can ya sha ƙwayoyi yana ta bacci, gobe har ku tafi ba zai farka ba, domin na ƙarawa abin da ya sha ƙarfi. A duniya zan ga wanda ya isa ya raba ni da ke. Zan ga mai karambanin mai maganin da zai jarraba hakan". "Allah ne zai raba ni da kai" ta yi maganar a hasale. "Da zai rabani da ke, da bamu haɗu ba" ya bata amsa. Nana ta waro ido ta ce "Kaii zaka yi saɓo, ki ba musulmi ba ne? Ko da yake musulmi ba zai yi abin da ka ke yi ba" Ƙaisar ya yi dariya ya ce "Kamar ba musulmin ne ke neman jininki su yi tsafi da shi ba" Ya koma ta bayanta, ya zuro kansa gefen fuskarta, hakan ya ƙara adadin bugun zuciyarta, jikinta yayi sanyi ƙalau kamar wadda aka saka a cikin firinji. Ya ce "Bari na sake nuna miki wani abu, amma akwai buƙatar na tsaya kusa da ke, idan ba haka ba, wannan 'yar ƙaramar ƙwaƙwalwar ta ki bugawa za ta yi. Kalli can" ya nuna mata wani mudubi. Ta ɗaga kai ta kalla. Kawai ta ga Auwwal a kwance ana yi masa wankan gawa, gefen cikinsa na ta zubar da jini. Razana tayi za ta miƙe, amma ya riƙe ta ya ce "Kar ki zarge ni, babu sanya hannuna a cikin wannan abin, ya gama shirinsa gobe zai tafi Abuja, ɗazun nan masu ƙwacen waya suka tare shi, suka karɓi wayar suka caka masa ɗan buda. Yaran kuma da suka yi, abokan yayanki ne, nan da 'yan kwanaki idan bincike yayi nisa shi ma za a kamo shi". Wani irin yinƙuri Nana ta yi, domin ta ƙwace daga jikinsa amma ta ji an riƙeta. Ta ɗaga kanta kawai ta ganta a ana kiciniyar shiga taxi da ita, ta waiwaya ta ganta a tare da Yaya Atine da Baba. Ta ja ta tsaya ta ce "Wai ya na ga haka?" Baba ya ce "Ba ki da lafiya, gidan mai magani za mu je" "To Baba ai ban yi sallar asuba ba" Yaya Atine ta ce "Mu je, idan an je gidan mai magani sai ki yi sallar" Nana ta kalli sama yadda gari ya fara haske, ta ce "A'a ni a bari na yi salla" Baba ya ce "Ta dawo hayyacinta, a ƙyale ta tayi sallar" Nana ta shiga gida Yaya Atine ta bita, ta yi alwala. Yaya Atine ta ce "Rabi ki bari a tafi da Suwaiba gidan mai maganin nan a duba ta ita ma" Mam ta ce "Eh ko ba gidan mai magani ba, ta je ta ƙarasa lasheta a hanya ta kashe ta, babu in da za ta je, kuma wallahi kurwar Suwaiba ta fi ƙarfinki" ta yi maganar tana hararar Nana. Nana dai ta yi alwala, ta gabatar da sallar asuba, aka saka ta a cikin taxi, aka ja aka tafi, ba tare da ta san ina suka dosa ba. Suwaiba kuwa ba ta tashi daga bacci ba, sai bayan ƙarfe tara na safiya, kuma babu wanda ya tashe ta, domin ta yi salla. Sai a lokacin ta yi salla, ta nemi abin karyawa. Jin Mama na ta jera mata sannu ya sanya ta ce "Wai mama sannun me ki ke yi mini ne?" Mama ta ce "A'a abin da ya faru da ke jiya mana, wannan azzalumar tana neman kar ki" Cikin rashin fahimta Suwaiba ta ce "Wace ce? Ni fa ban gane ba" "Jiya kururwar da ki ka din ga yi ki na Nana za ta kashe ki, tana miki jini, ba mu yi bacci ba fa" Suwaiba ta zaro ido ta ce "Ni ɗin?" Jamila ta ce "Eh mana, kasa numfashi ki ka yi fa, kina ta kuka wai Nana tana sha miki jini" Jikin Suwaiba ya yi sanyi, ta ce "To ai ni tun da na kwanta, ko juyi ba na tunanin na yi, sai yanzu na tashi daga bacci" Jamila ta ce "Ikon Allah, kin ga kururwar da ki ka din ga yi kuwa, wai Nana na sha miki jini?" "Ni dan Allah ku daina wannan zancen tsoro ku ke bani wallahi kar na je, aljanun nata ne nima su ka shafe ni" Muryar Imran ce ya dawo da su kan tsakar gidan, yana ta kwaɗa wa Nana kira. Nasiru ya ce "Nana fa sun tafi gurin mai magani, bayan sallar asuba" "Kamar yaya ita da wa?" "Asubar farko, aka je aka taho da Yaya Atine daga gidanta, a taxi ɗin malam Shehu, gari yana fara haske suka tafi. Jiya ne Suwaiba ta din ga ihu cikin dare wai Nana tana sha mata jini, shi ne suka tafi da sassafe" "Kuma shi ne ba a gaya mini ba, ina ne garin mai maganin, kar aje a kai ta gurin bokaye" "Wallahi ban sani ba" Imran ya ce "Ke Suwaiba, ya aka yi Nanan ta sha miki jini, ita ba mayya ba, kar ki ja a ɓata mata suna, ni ba na son ƙananan maganganu ki bar ta ta ji da halin da take ciki mana" A fusace Mama ta ɗaga labule ta fito ta ce "Ban gane ba, za ta yi mata ƙarya ne? ko dan kai ba a gidan ka kwana ba, ba ka san a halin da ta kwana ba" "Eh Alhamdilillah, na ji daɗin hakan ma, ai da gani ku ke yi Nana tana sane, duk abubuwan da yake faruwa da ita, tana sane ita ta yi wa kanta ƙarya take yi. Yanzu idan ma ƙarya take idan ma gaske ne, ai kwa gani, kuma wallahi na ji wata magana a unguwa ta cin zarafin Nana, ko yi mata ƙage wallahi sai na saka an ɗaure mutum igiya ta yi saura" Jamila ta ce "Mama dan Allah rabu da shi, kar ya yi miki rashin kunya" *** Nana kuwa rarraba ido kawai take yi a hanya, tana ta ƙoƙarin tuna wasu abubuwa a ƙwaƙwalwarta, amma abu ya gagara. Abin da take iya tunawa, kawai hango Suwaiba tana zubar da jini, amma ta kasa tuna takamaiman yadda aka yi ta ga jini a jikin Suwaiba. Gaba ɗaya ta nemi kuzarinta ta rasa, jikinta yayi sanyi ƙalau, ko ƙwaƙwƙwaran motsi, sai ta yi da gaske take iya yin sa. Sannu a hankali, ƙwaƙwalwarta ta fara fassara mata maganganun da ta jiyo Baba yake yi. Wai ana idar da sallar asuba, ya kira Saleh a waya ya ce masa wai idan akwai kuɗi a hannunsa, ya turo wani abu za a nema mata magani. Wani irin takaici ya kama Nana, sam Baba ba ya gudun abin kunya da duk wani abu da zai zubar musu da kima. "Atine, ai yakamata tun yanzu yaron nan, ya fara ƙoƙartawa shi ma, tun da dai aurenta zai yi, duk wata hidima da za a yi mata, ya saka hannu a yi da shi" Babu kunya Yaya Atine ta ce "Gaskiya ne, ai kamata yayi ace ya ɗauke maka wasu nauye-nauyen". Baba ya ce "Sosai fa, kuma kin ga  hakan zai ƙara tabattar masa da gaske zan ba shi aurenta. Ai mu na dawowa daga gurin maganin nan kawai iyayensa su zo a wuce gurin" Nana ta rintse  idanunta, tana fatan bacci ya ɗauke ta, ba ta tunanin akwai wani wanda zai aureta ta yi mutunci a idonsa, da irin wannan halin na Baba, na son jinginawa wani ɗawainiyar da shi yakamata ace ya yi abarsa. Sun sha doguwar tafiya sosai, kafin su isa wani surƙuƙin ƙauye, sai da suka yi nisa sosai da sosai, suka daina ganin gidaje. shige da ficen ababen hawa ne, ya sanya suka tabattar da akwai mutane a gurin, domin kuwa hatta kwalta babu a gurin, sai uwar zangarniya. Yanayin surƙuƙin gurin, sai parking ɗin motar suka yi a bakin hanya, suka saukko domin takawa su ƙarasa, sai dai ƙafar Nana ta ƙi takuwa sai ma lanƙwashewa da ta yi, kamar mai shan inna. Sun daɗe a gurin, Nana ta kasa taka ƙafafuwanta, sai da ƙyar ta ɗan saki, ta  takawa a hankali. Tun da suka doshi hanyar da aka nuna musu, aka ce a nan gidan mai maganin yake, Nana take ganin garke garke na Raƙuma su na fitowa daga hanyar, jajaye da farare. Yaya Atine ce ta riƙe ta suke tafe a hankali, saboda da ƙyar take taka ƙafafuwanta. Nana ta ce "Yaya Atine dama akwai baƙin raƙumi?" Yaya Atine ta ce "A ina?" "Ga su nan su na ta wucewa, ba ki gansu ba?" Yaya Atine ta ja ta tsaya ta ce "Kai Gaddafi, ku na ganin raƙuma ko kuma nima abin nata ne zai shafe ni, nice ba na ganinsu?" Baba ya ce "Raƙuma kuma a ina?" "Yo ai ji na yi tana zancen baƙin raƙumi, ni kuma ko kofato ban gani ba balle raƙumi. Kai zo ka riƙe 'yar ka, kar na gano abin da ba shikenan ba" Nana na jin haka, ta zame hannunta daga na Yaya Atine ta ci gaba da takawa a hankali. Daga nesa suka hango gidan, mutane na ta shiga su na fita. Ja da baya Nana tayi da sauri tana kare fuskarta. Baba ya ce "Me kuma ya faru?" Cikin damuwa Nana ta ce "Baba wai ba ka gani, baƙin raƙumin nan ne yake feso mini wuta fa" Cikin takaici Gaddafi ya ce "Dan Allah Baba ku daina biyewa yarinyar nan, ku zo mu ƙarasa." Su na tunkarar gidan, amma raƙuman na ƙara yawa, Nana ta fahimci ita kaɗai take ganinsu, su ba sa ganinsu. A haka har suka ƙarasa ƙofar gidan, Ko da su ka shiga gidan, jikin Nana ya hau rawa, sai dai hakan bai hanata gode wa Allah da halin da ga tsinci kanta. Saboda yadda ta ga wasu a cikin mari su na hauka tuburan, ban da masu ciwon galhanga, shan inna da sauransu. Ɗaki ɗaki ne a gidan, ma'aikatan gidan, duk su na sanye da jajayen kaya, kamar ma'aikatan jinya a asibiti. Hankalin Nana yayi mugun tashi, da ta ga ana yi wa wasu daga cikin marasa lafiya sakiya. A saka kibiya a cikin magani, sannan a sakata a cikin wuta, sai ta yi ja sannan a soka a gurin da yake da larura. Sai da tsigar jikin Nana ta tashi, hankalinta yayi mummunan tashi. Su na ƙoƙarin shiga ƙofar da za ta sada su, da ainihin gurin da mai maganin yake ganin marasa lafiya, idon Nana ya sauka a cikin na ɗaya daga buzaye ukun da suke ƙoƙarin fitowa daga cikin gurin. Ji ta yi tamkar an watsa mata wuta a cikin idanunta zuwa jikinta, ƙara ta saki ta dafe kanta ta faɗi a gurin. Taku uku ya yi, ya ja ya tsaya ya waiwaya ya kalli gurin da Nana ta faɗi. Habu ya kama hannunsa suka yi waje. Ma'aikatan gurin, su ka zo su ka ɗaga Nana, su ka shiga da ita gurin mai magani, su Baba su na biye da su. Mai maganin ya fito sanye da rigar fatar damisa, sai warki a ƙugunsa idanunsa Jawur tamkar garwashi, baƙi ƙirin da shi. Da sauri ya ƙarasa kan Nana, tamkar likitan da aka kawowa mara lafiyan da yake buƙatar agajin gaggawa. Ya sunkuya a kanta yana kallonta sai kuma ya ɗago a gigice ya ce "Baushe, maza bi buzayen nan ka dawo da su, wataƙila ga makarin na sa ciwon a nan, maza hanzarta kar su tafi" Su Baba dai su ka tsaya sororo su na bin sa da kallo. Nana kuwa tari ta hau yi, tamka ƙirjinta zai buɗe, ganinta ta yi a cikin ƙura, ko tafin hannunta ba ta iya gani saboda yadda ƙurar ta turnuƙe gurin. Bayan wani lokaci ƙurar ta lafa, ta ɗaga kanta ta na kallon gurin, ita kaɗai ƙwal a cikin sahara. Waige-waige ta hau yi, sai dai babu tsammani ta ga mutum a tsaye a bayanta, sanye da baƙin rawani da shigar fararen kaya na buzaye, hannunsa riƙe da akalar raƙuminsa. Sai dai duk ƙoƙarin Nana a kan ta gane kamaninsa, abu ya gagara fuskarsa a rufe take da rawani. Miƙa mata hannunsa yayi, mai ɗauke da dogwayen yatsu. Duk da a tsorace take, ta fara takawa a hankali, har ta ƙarasa gurin da yake, ta miƙa masa nata hannun. Yana kama hannunta, ta ji an zuba mata ruwa mai matuƙar sanyi a jikinta. Doguwar ajiyar zuciya ta sauke, tare da buɗe idonta. Su Baba ta gani a zaune tsuuruu, kamar mara gaskiya a hannun hukuma. "Sannu Nana Asma'u" mai maganin ya yi maganar cikin sakin fuska. Nana ta tashi zaune, ta koma jikin Baba, tana jin yadda haryanzu jikinta yake a sanyaye. Mai maganin ya zura mata ido, sannan ya sake murmushi ya ce "Manya gatan wasa, wa ya isa ja da ku, idan ba wawa ba? Tuba nake uban duƙusa" dubawa Nana take ta ga da wa yake. Ya ci gaba da cewa "Asma'u, ki na ganin wani mutum a mafarki, ku na magana ko?" Nana ta yi shiru ba ta ce komai ba. "Za ki iya tuna me da me yake ce miki?" Still ta yi shiru ba ta yi magana ba. Ya sake murmusawa ya ce "Malam, gidanmu wanzamai ne, na kuma yi ƙarfa-ƙarfa a kan farauta, duk da mahaifiyata sun gaji farauta . Na daɗe ina hatsabibanci, har na zo na fara bayar da magani, na daɗe ban ga abin mamaki ba kamar yau. Aljanin da yake ɗawainiya da yarinyarka hadiminta ne, tun zamanin kakaninka ai 'yan bori ne. Kuma tun daga kansu ba a kuma samun haihuwar mai irin tauraronta ba, sai da aka haifeta dan haka dole ya yi mata hidima, ita kuma taƙi yadda shiyasa yake ta azabtar da ita. Duk ba wannan ba yanzun nan aka tafi da wani buzu, shi dama na gaya musu ba ni da maganin larurarsa, sai dai a shigowar ku, na ga wani abin mamaki da na daɗe ban gani ba, ina kyautata zaton wataƙila maganin nasa ciwon na da alaƙa da nata. Kodayake ba a kan wannan gaɓar muke ba. Yanzu ita Nana Asma'u za ku bar ta a nan, sai bayan kwana goma sha huɗu zaku dawo, aljaninta sai dai ayi sulhu da shi idan aka takura shi, ba ita ba ni kaina zai iya halaka ni." Kallonsa Nana tayi, gaba ɗaya maganganun mutumin nan ko gaske ne, mushiriki ne shi ma, jira take ta ji me su Baba za su ce, ko me za ayi ba za ta yarda a bar ta a gurin nan ba. Baba ya ce "Mu tafi mu bar ta har mako biyu kuma, itakaɗai?" Gaddafi ya ce "Ba magani ake mema ba? Ma samu mu huta kwana biyu mu ma, da wannan tamɓelen da take yi ai gara a batta ɗin, Allah ya kaimu makwanni biyun" Yanayin Baba ya nuna ba haka ya so ba. Nana ta buɗe baki za ta yi magana, ta ji kamar an saka dutse a maƙogwaronta, tayi tayi amma magana ta gagara. Ta dage iya ƙarfinta ta miƙe tsaye, amma jiri ya kwashe ta, tana ji tana gani, masu jajayen kayan nan, suka zo suka ɗauke ta, tana fizge-fizge tana komai aka kaita wani ɗaki aka kulle. Littafin BUZU 1k ne a telegram. 0069685771 Aisha Adam Stanbic ibtc Sai shaidar biya https://wa.me/2348081012143 Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM AYSHERCOOL YOTA/002 (Bright pens 3rd batch) P12 Imaran tun yana jiran dawowar su Baba da daɗin rai, har ransa ya gama ɓaci, zuciyar sa ta din ga tafasa. Mama kuwa tuni ta din ga kiran 'yan uwanta tana gaya musu, abin da ya faru da Suwaiba. Suwaiba kuwa ko a jikinta, sabgoginta kawai take yi. Ƙarshe ma da yamma, ta sha wanka za ta fita zance, ta ga turaren nan a kan kayan Nana, ta ɗauki abin ta ta ƙara fesawa ta fice. Bayan sallar magariba, Imran yana zaune a waje, sai ga taxi har ƙofar gidansu, su Baba sun dawo. Bai motsa daga gurin da yake ba, sai da ya ga duk sun fito daga motar, amma babu Nana. Su na shiga gida, ya tashi ya bi bayansu. "Wai ina Nanan take? Ya ku ka dawo babu ita?" Daga Baba har Gaddafi babu wanda ya kula shi. Ransa ya fara ɓaci ya ce "Baba ka yi magana, ina ku kai mini Nana?" "Tana gidan Atine" ya bashi amsa a gajiye, saboda sun kwaso gajiya. "To me yasa za a kaita gidan Yaya Atine? Me yasa ba ku dawo da ita gidan nan ba?" Ganin Baba ba zai ba shi cikakken lokacinsa ba, balle ya yi masa bayani, kawai ya fice ya nufi gidan Yaya Atine. Yaya Atine, ta mimmiƙe tana cin tuwon dare, saboda wahalar da suka sha. Kamar an jefo Imran ta ji sallamarsa. Ta amsa masa, ba tare da ya ko gaisheta ba ya ce "Ina Nana?" Cikin rashin fahimta ta ce "Wace Nanan?" "Baba ya ce mini tana gidan nan?" "Kuma saboda rashin ɗa'a, ko gaishe ni ba za ka yi ba, ka zo kana tambayata wata Nana, to mun sayar da ita" Ya ce "Yi haƙuri, a ruɗe nake ne" Yaya Atine ta ce "Ba wani haƙuri da zan yi, gidan uban wa ka tafi tsawon shekarun nan?" Duk da ya fara ƙuluwa ya maze ya ce "Kudu na tafi neman kuɗi, tana ina?" "Kai ban sani ba, ni ba ta gidan nan, ka koma ka tambayi uban naka" Imran ya kalle ta ya ce "Kamar yaya? Shi fa ya ce mini tana nan" "A'a tana gidan mai magani, sai nan da mako biyu za aje a taho da ita" Ashar Imaran ya yi ya ce "Wane irin magani ne, sai an kai mutum a baro shi, to ai ko asibiti ana barin ɗan jinya, balle wani shashasha da bai shiga aji ba, aje a ajiye masa yarinya shi ba muharamminta ba". "To ai ubanka za ka je ka yi wa ba ni ba. Kuma ba fin mu hankali da tunani ka yi ba, gurin akwai ma'aikata mata da suke kula da mata marasa lafiya " Imran ji ya yi kamar ya kifa wa yaya Atine mari, wannan ai ganganci ne da rashin hankali. Takalmansa ya shura, ya fita daga gidan zuciyarsa kamar ya fashe saboda takaici. Gida ya koma cikin takaici, sai dai ya tarar Baba baya nan. Labarin mutuwar malam Auwal ya karaɗe ciki da wajen unguwar su Nana, saboda an san shi sosai, saboda ya kan ja salla a masallatai daban-daban. Ga koyarwar da yake yi a islamiyya, kowa yayi masa shaidar mutumin kirki ne shi. 'yan unguwa suka yi alwashin tsayawa tsayin daka, gurin bibiyar jam'i an tsaro da tabattar da an kama waɗanda suka aikata masa haka. Cike da jimami Nasir ƙanin su Nana yake ta nanata mutuwar malam Auwal, ya ce "Allah sarki Nana, ko ya za ta ji idan aka ce mata malam Auwal ya mutu an kashe shi?" Duk da Baba yana cike da takaicin wasa da hankali da malam Auwal ya yi masa, na ƙin fitowa ya auri Nana, amma hankalinsa ya tashi bayan dawowarsu daga kai Nana gurin mai magani ya samu labarin mutuwar. Yana tsaka da jimamin mutuwar, ana tattaunawa a masallaci bayan sallar isha'i, Nasiru ya zo ya kira Baba ya ce ana nemansa a gida. Ko da ya je gida, ya tarar an daddane Suwaiba, tana ta kurma ihun Nana na sha mata jini. Cikin kuka mama ta ce "Ka gani ko? Kalli halin da Suwaiba take ciki, wallahi an cuce ni ban yafe ba, kuma wallahi ko ka ɗauki mataki ko ni na ɗauka. Dan baƙin bala'i a gaban saurayi ta faɗi tana wannan kururwar fa" Cike da damuwa ya ce "Wai Rabi ya ki ke so na yi, ki na gani domin neme wa Nana magani, a can gurin mai magani na baro ta, kuma na ce a tafi da Suwaiban ki ka ƙi yarda" "Ni wallahi ka san yadda za ka yi, dan ba zan yarda a kashe mini 'ya ba" Imaran ne yayi sallama, yana watso takalmansa da suka tsinke ya ce "Yauwwa Baba na je gidan Yaya Atine, ta ce Nana ba ta gurinta wai a gidan mai magani aka baro ta. Baba ko fa asibiti ana bar wa mutum ɗan jinya, ya za ayi a kaita gurin da babu idon wani nata da sunan neman magani? Ina ne gurin da aka kaita gaskiya zuwa zan yi na ɗaukkota" Baba bai yi magana ba, Suwaiba ta ci gaba da kakari "Baba ku taimake ni, Nana za ta kashe ni, jinina take lasa tana sha, dan zatin Allah ku hanata jikina zafi yake yi mini" Imran ya ce "Wace Nanan? Nanan da bata gidan nan?" Mama ta ce "Amma dai a yanayin da take ba za ta yi wa Nana ƙarya ba" Imran ya ce "To Nana dai ba mayya ba ce, abin da ku ke zunɗenta ne Allah ya jarrabe ku. Ni dai dan Allah Baba ka gaya mini in da ku ka kai Nana, ni fa hankalina ba zai kwanta ba ina nan tana wata uwa duniya da ban sani ba" A fusace Baba ya ce "Ban sani ba, ba zaka iya rayuwa tana wani guri ba, da ka tafi gantalinka shekara nawa tana nan ka na can gantalinka?" Cike da ƙwarin gwiwa Imran ya ce "Amma ai na san tana gida a gabanka, ni gaskiya ban ji na gamsu da wannan tsarin ba" Ga dai Nana ba ta gida, amma yadda suka ga rana haka suka ga dare, Suwaiba na ihun Nana na sha mata jini. **** A hankali Nana ta ja jikinta ta zauna, duhu kawai take gani ba ta iya gane komai, ko tafin hannunta ba ta gani. Ta shafa bayanta ta ji alamun bango, ta ja jikinta ta jingina da bangon tana sauke ajiyar zuciya. Cikin damuwa ta haɗa kanta da gwiwa, zuciyarta sam babu daɗi yau kuma nan Allah ya kawo ta. Jin ƙarar buɗe ƙofa, ya sanyata ɗago kanta. Wasu mata ne biyu sanye da uniform su ka shigo ɗakin. Suka bubbuɗe tagogi sai ga haske ya ratso ɗakin. Duk da yanayin hasken ya nuna rana na daf da faɗuwa. Ɗaya daga cikin matan ta ce "Ta ce taso" babu musu Nana ta tashi, ta bi su suka fita, sai ta ga kamar ba gidan da aka kawota ba. "Za ki yi salla ne?" Ɗaya daga cikin matan ta tambayeta. Da sauri ta jinjina kai alamar eh. Aka janyo mata ruwa a rijiya, aka nuna mata banɗaki. Ta yi alwala ta fito aka mayar da ita ɗakin nan ta yi salla. Su na tsaye su na jiranta kamar wata fursina, wata matar ce daban, ta shigo ta kawo wa Nana abinci da ruwa pure water. Nana ta kalli Abincin gasashsen nama ne, amma ta kawar da kai. "Ki ci abinci mana" matar ta yi magana cikin kulawa. "Na ƙoshi" ta faɗa a taƙaice. Babu yadda ba su yi da ita ba, amma ta ƙi ci. Har sai da ran ɗaya ya ɓaci, ta fice ta tafi gurin mai maganin. "Sarkin baka, yarinyar nan fa taƙi cik abinci" "Ahh haba dai? Ta tashi kenan?" "Eh tun ɗazu har ta yi salla ma" "Na fa gaya muku yarinyar nan ku lallaɓa mini ita, ba na buƙatar a takura mata, ko ɓata mata rai. A nemo Salamatu ta tura 'yar aike cikin gari, a samo mata wani abincin" rai a ɓace matar ta amsa da to ta fita. Nana tana zaune tana tunani, sai ga wata matar daban ta shigo da kayan saƙi shuɗaye a jikinta. Sallamar da ta yi Nana ta amsa tana bin ta da kallo. Cikin sakin fuska matar ta ce "Barka da yammaci baƙuwar sarki" Nana ta bi ta da kallo ba ta amsa ba. Ta ajiye wa Nana kwanuka, ta ce "Ga abinci an saka a canza miki" "Ina su Baba?" Salamatu ta ce "Sun tafi, sai nan da makonni biyu za su dawo" "Me yasa za su tafi su bar ni a nan? Ni gaskiya gida zan tafi" "To shikkenan, amma fara cin abincin tukuna" Da ƙyar Salamatu ta lallaɓa Nana ta ci abinci, shi ma don tana jin yunwa ne sosai shi ya sa ta ci." Nana ta riƙe alwalarta, a nan ɗakin ta gabatar da sallar magariba, sai dai tsoro ya fara kama ta, ganin ɗakin ya yi duhu babu haske kuma ita kaɗai a ciki. Ba a jin amon kiran salla, sai dai ta kintaci lokaci kawai. Ta tura kanta tsakanin cinyoyinta, ta rintse idanunta tana ta adduo'in da suka zo bakinta. Tana ji ana sallama, amma ta kasa ɗagowa, sai da aka taɓa ta sannan ta ɗago a razane tana sauke numfashi. Salamatu ce ta shigo da fitila, da kuma kayan abinci. Ta ce "Yi haƙuri, na tsorata ki ko? Ga abinci ki ci, ga kuma fitila idan ki na buƙatar mai taya ki kwana kuma sai mu kwana tare" Cikin damuwa Nana ta ce "Ni ba na buƙatar komai, gida nake so na tafi" "Haba Nana, ba kya so ki samu lafiya ki rabu da abin da yake damunki ne? Magani za ayi miki, babu wanda zai cutar da ke" ta daɗe tana rarrashin Nana, tana kwantar mata da hankali. Ta ɗan ci abincin sannan ta kwanta, tana ta adduo'i. Ji ta yi sanyi ya dame ta, ta dunƙule guri ɗaya, amma ba ta daina jin sanyin ba har cikin ƙasusuwanta, ta juya domin ta gyara kwanciyarta kawai ta ganta a cikin Sahara itakaɗai. Ga dare, sai dai farin wata ya haske saharar, sai wani irin sauti da kunnuwanta ke ji, kamar na tasowar guguwa amma ba ta san daga ina sautin yake ba. A tsaye ta ganshi a cikin saharar, a wannan karon ma fuskarsa a rufe a cikin rawani, sai dai a wannan karon dogo ne sosai fiye da kima. A hankali gurin ya ƙara haske duhun ya ƙara raguwa. Sai kuma ta ga tsayin yana raguwa har ya dawo na daidai mutane, ya saka hannu ya warware rawaninsa. Ƙaisar ta gani a tsaye, duk ba ta iya ƙare masa kallo, amma yadda yake bayyanar mata a mafarki cikin suffar mutane shi ta gani. Ta buɗe baki za ta yi magana, ya fara rikiɗewa ya zama tsoho tukuf, tun da Nana take a doron duniya ba ta taɓa ganin tufa kamar wannan ba, gashin kansa yana jan ƙasa fari ƙwal da shi, ga wasu irin kaya masu kama da yanar gizo gizo a jikinsa saboda tsabar tsufa. Nana ta fara ja da baya a hankali, zuciyarta na hakaito mata addu'a, amma ta kasa furtawa. Ya sake girgiza ya koma wani baƙin raƙumi mai muni, ya buɗe bakinsa ya fara feso mata wuta. Da wani irin gudu Nana ta juya, tana ihu, ma'aikatan gidan suka rirriƙeta. "Innalillahi wa innalillahi raji'un, Baba ka yi mini addu'a, wayyo Babana, baba Imaran, Jamila dan Allah ku yi mini addu'a na kasa yi" Cikin damuwa Salmatu da ke riƙe da Nana ta kalli mutumin da ke tsaye a kan Nana yana kallonta ta ce "Sarki ka yi wani abu a kan lamarin nan, kar fa ƙwaƙwalwarta ta taɓu" Ya durƙuso yana haska fuskar Nana ya numfasa ya ce "Ni na san za a rina. Salamatu" Ta amsa da "Na'am sarki" "Idan kin ji ana zaki bari, damisa bari faɗanku na manya wa yake shiga, sai wawa sai mahaukaci, to wannan rigimar ce. Wannan yarinyar da ki ke gani ban san ta ina zan fara yi miki bayani a kanta ba. Dole jikinta ya ƙara rikicewa saboda haɗuwarta da buzayen nan. Da ba su riga sun tafi ba, da ƙarshenta a cikin su ɗaya ya samu waraka ɗaya kuma ya mutu a haka tsakanin ita da Buzun" "Sarki ka ƙara rufe mini kai na, ban gane me ka ke nufi ba" Ya yi murmushi ya ce "Da ina buƙatar ki gane, ai gwari gwari zan yi miki salameme. Ya saka yatsunsa biyu a goshin Nana, take ta yi shiru bacci ya kwashe ta. **** Sosai Imran yake nema ya hana kowa zaman lafiya a gidan, saboda rashin Nana, ya kaɗa ya raya Baba ya ƙi gaya masa gurin mai maganin da aka kai Nana. Ɓangaren Suwaiba ma abin nata gaba yake yi, sai ana zaune lafiya, sai ta yanke jiki ta faɗi tana kururwar Nana na sha mata jini. Babu shiri Mama ta ce dole ta fita nema wa Suwaiba magani, kafin Nana ta kashe ta. Baba ya ce ta bari a kai ta gurin da aka kai Nana, amma fafur ta ƙi yarda. Washegari, bayan Nana ta idar da sallar asuba, Salamatu ta zo. A duk lokacin da ta zo gurin Nana, cikin sakin fuska da fara'a take yi wa Nana magana, hakan ya saka Nana ta ɗan fara sakin jiki da ita kaɗan, duk da ba magana take yi mata ba. "Nana taso mu je ko" babu musu ta tashi ta bi Salamatu. Suna fita daga ɗakin, ta tuna mafarkin da ta yi, sai da ta ji gabanta ya faɗi, ta fara karanto addu'oin da Malam Auwal yake bata. A take ya faɗo mata a rai, har yanzu tana jin kewarsa sai dai a wannan karon, jikinta ne yayi matuƙar sanyi. Salamatu na gaba tana biye da ita, sai da suka ɗan yi doguwar tafiya, sannan ta fuskanci a cikin gidan da aka kawo ta neman magani suke. Ta ga yadda ake jere masu taɓin hankali, wasu a cikin mari aka ba su abincin safe, lafiyayyen kunu da ƙosai. Gaba ɗaya suka zuro wa Nana ido. Masu ɗan sauran hankalinsu, su na ta gaida Salamatu tana amsa musu cikin sakin fuska. Masu rashin ji a cikinsu, su ƙi cin abinci, su na ganinta suka kama kwanukan abincinsu. A gaba kaɗan kuma ɓangaren ƙananan yara ne, masu larurar ƙwaƙwalwa, da ake iƙrarin aljanu ne su ka sanya musu. Wasu ɗauke ciwukan da a turance ake cewa (Down syndrome, autism, poliomyelitis) da sauran su wato masu shan inna, galhanga da sauran su. Suka ƙara yin gaba, suka ɓullo gurin da ake Sakiya, kamar yadda ta hango jiya da suka zo. Sai da tsigar jikin Nana ta tashi, ta rintse idanunta yau ma kibiya ake sakawa a cikin magani, sai a ciro ta a saka a cikin wuta, ta yi jawur, aka ciro ana sokawa a cikin wani mutum da cikin ya kumbura tamkar zai fashe. An tara wata tasa wani irin koren ruwa yana kwararowa daga cikin nasa mai azabar wari. Mutumin yana zaune, tamkar ba cikinsa ake hudawa ba. Salamatu ta ce "Tsoro ki ke ji har haka? Sun je Asibiti aka ce hantarsa ta lalace, sai dai ayi masa dashen wata, su kuma iyalansa ba su da hali, aka kwatanta musu nan. Lokacin da aka kawo shi, ko tafiya ba ya iya yi, yau satinsa guda a nan yana iya takawa" Cikin damuwa, a kuma karon farko Nana ta yi mata magana kai tsaye ta ce "Ba ya jin zafi kuma? Da me zai ji? Zafin wuta ko ciwon, ko kuma huda shin da ake yi, idan ya mutu fa?" Salamatu ta yi murmushi ta ce "Ai ba da ka muke aikin ba, kamar yadda asibiti suke da anesthesia, magunguna da alluran kashe zafi, mu ma mu na da su, irin namu na gargajiya, ba ya jin komai. Ilimi ne ya bawa likitoci damar sanin cuta da magani mu ma kuma haka" Nana dai ba ta gamsu ba, ta ji ne amma ba ta yarda ba. Sai yanzu take jinjina girman gidan, su shiga nan su ɓulla can, ko ina ɗaki-ɗaki ne na marasa lafiya a gidan. Wata ƙaramar ƙofa su ka shiga, amma ta ga sun fito wani katafaren ɗaki ƙato, ba wai kayan alatun zamani ne a ɗakin ba, kawai dai an tsara shi ne. Ta kalli ƙasan ɗakin, an rufe shi da fatar dabbobi daban-daban, wata ta gane ta wace dabbar ce, wata kuma ba ta gane wacce ce ba. Hatta jikin bangon ɗakin, an yi masa ado da fatar dabbobi, ta damisa kawai ta iya ganewa da kura, su ma dan tana gani a tv ne wasu lokutan. Ga kuma ƙahunhunan dabbobi su ma, an ƙawata ɗakin da su, sai kuma jakunkunan fata suma duk an rarrataye su a ɗakin. Ga curin layoyi su ma duk an yi musu guri a ɗakin. Yana zaune a kan wata karaga, mai ɗauke da ƙwarangwal ɗin kawunan zaki, bayan karagar kuma an yi mata ado da kawunan macizai. Nana ta yi tsuru, tana tunanin anya ma a zahiri take, ko dai kawai tarkacen mafarkin da ta saba yi ne. Tasowa yayi jikinsa sanye da kayan fatar giwa, yana faɗaɗa murmushinsa ya ce "Barka da zuwa baƙuwa ta mussaman, lale da ke" Nana ta yi shiru tana kallonsa, duk da ta gane shi, lokacin da aka kawota ta ganshi, amma ba a wannan ɗakin ba, kuma yau baƙinsa ya ragu. Salamatu ta ce "Sarki ga ta na kawo ta, ta tashi lafiya ƙalau" Ya ce "Alhamdilillah Allah abin godiya, Nana Asma'u na san kin gane ni, amma ba ki sanni ba, ni ne Garba mai tagwayen baiwa, Sarkin bakar ƙasar hausa, kuma ana yi mini take da Garba ga baka ga aska. Salamatu ba ta abin zama". Salamatu ta zura hannu a wata 'yar ƙaramar jakar fata, ta  janyo wani abu da Nana ba ta gane ko mene ne ba, shi ba kujerar tsuguno ta mata ba, shi dai ga shi nan. Tana tsaka da kallon abin ta ga yana motsi, ta ƙura ido kawai ta ga kan kunkuru ya leƙo ashe kunkuru aka ba ta a matsayin abin zama. Babu shiri ta doka tsalle ta ja gefe tana kallon kunkurun. Sarkin baka ya bushe da dariya, ya ce "Tuba muke, mu je ki ga yadda muke gudanar da ayyukan gidan, ko kya saki jiki ayi abin da yakamata" Wata mata ce ta faɗo ɗakin babu ko sallama, bafulatana doguwa mai tsayi fiye da kima. Tana shigowa Nana ta ji zuciyarta ta yi wani irin gigitaccen bugu, da sai da ta zata mutuwa za ta yi. Matar ba ta ce komai ba, ta shirya ƙorran da ta shigo da su a wata ragaya. Sarkin baka ya ce "Idan kin gama, ga saƙonki can" bafulatanar ba ta ce komai, ta buɗe wata randa ta ɗebo wani baƙin abu ta sha, ta zo za ta wuce Nana ta fita, Nana ta sunkuyar da kanta ƙasa ta fice daga ɗakin. "Asma'u kin ga matar da ta shigo ne?" Nana ta jinjina masa kai jikinta yana rawa. "Me ki ka gani a tare da ita?" Da ƙyar Nana ta ce "Ba ta da ƙafafuwa, a kan iska take tafiya" tayi maganar bakinta yana rawa. Ya ɗan yi shiru, Salamatu ta ce "Ya buɗe mata ido kenan tana ganin komai" Sarkin baka ya jinjina kai, ya ce "Taho muje" ya tashi ya yi gaba su ka bi shi a baya. Wani guri suka nufa, sai da suka je daf da wata ƙofa, ta fara jiyo ihu mara daɗin ji. Ya buɗe ƙofar ya shiga, sai dai Nana ta kasa shiga. Salamatu ta ja hannun Nana da ƙarfi, su ka shiga, sai gurin ya rikiɗewa Nana tamkar a film, mahaukata ne a ɗaki-ɗaki, tamkar a prison, su na ta kurma ihu sai ta ga ashe waɗanda ta gani da farko ba hauka suke yi ba, wannan ne masu yin hauka na gaske. Tamkar shirin fina-finan zombie, haka suke ihu su na ziro hannayen su. Nana tsigar jikinta ta din ga tashi, tana jin tamkar ita ma ta fasa ihu saboda rawar da jikinta yake yi, da wani irin azabar ciwo da kanta yake yi. Hatta haƙoranta da laɓɓanta rawa suke yi, ya yin da sautin ihu da kururwar mahaukatan, ya ci gaba da amsa kuwwa a cikin kunnuwanta, ta rintse idanunta tana sauraron bugun zuciyarta a cikin kunnuwanta dummm dummm da ƙarfin gaske. Tsawa Nana ta yi hakan ya sanya gaba ɗaya su ka yi shiru, su na kallonta, tamkar an yi ruwa an ɗauke, a hankali ta buɗe idanunta domin ta ga tsawar da ta yi ce ta sanya su yin shiru, ko kuwa?. Sai dai ta ga tabbas ita ɗin ce ba wani ba. Sarkin baka ya kalleta tare da sakin wani irin ƙasaitaccen murmushi da shikaɗai ya san ma'anarsa. Wannan littafin 1k ne a telegram, ta wannan account ɗin 0069685771 Aisha Adam stanbic ibtc bank Sai shaidar biya ta 08081012143 Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM (AYSHERCOOL) YOTA 002 P13 Ya sake duban Nana ya ce "Manya gatan wasa, uban duƙusa uban haɗari, ai shikenan tun da haka zamu yi da kai" Ya yi gaba yana ci gaba da murmushi, ya din ga bayar da umarnin abin da za a yi wa marasa lafiya, tare da yi wa Nana bayanin aljanun da kowanne yake ɗauke da shi, da dalilin da yasa ya kama mutum. Nana ta sha mamaki, wasu a dalilin harkar bokanci, da ta'amalli da aljanun ya sanya suka haukace, wasu kuma sun yi ƙoƙarin amfani da aljanun ne dan su yi kuɗi, su ma suka haukata su. Wasu kuma sharuɗɗan da aljanun suka saka musu, suka gaza cikawa ya sanya suka haukata su. Ya nuna mata wasu hamashaƙan 'yan kasuwa ne, da masu kuɗi a ka yi musu sihiri da aljanun da suka haukata su. Babban abin da ya bawa Nana tausayi, har da wata matashiyar budurwa, da ta zubowa Nana ido, tamkar ta haɗiye ta. A hankali Nana ta taka ta nufe ta. Ta zuro hannunta ta tsakanin ƙofar ɗakin, tana miƙowa Nana. Nana ta miƙa mata nata, ta din ga shafa hannun Nana sannan ta ce "Kin san tazarar da ke tsakanin ƙasa da iya gejin da jirgi yake zuwa a sama? Nigeria mu na da tarin karatu, goyon bayan ƙasar mu kawai muke buƙata, mu je in da zato bai taɓa zato ba. Ina da burin ina raye kafin na mutu, na kasance cikin waɗanda za su ƙera wa Nigeria jirgin sama nata na kanta. Dan Allah ki saka baki na je ƙaro karatun nan, na warke fa ki ce ya sake ni" ta yi maganar tana kuka. Sarkin baka ya ce "Kubra Yusuf, in sha Allah burin nan naki zai cika da zarar kin warke" Cikin kuka ta ce "Ai na warke dan Allah ka kira Daddy a mayar da ni gida na tafi karatun nan, kar na yi missing Flight" Cikin damuwa Nana ta ce "Dan Allah a fito da ita daga ɗakin nan, kamar ta warke fa" Sarkin baka ya kalli Nana ya ce "Ai ba da baki ake gane wanda ya warke ba, yanzu ana buɗe ta, sai ta kusa hallaka ki a gurin nan. Ainihin ta 'yar makaranta ce, degree ne da ita a engineering, kuma ita ce overaller a department ɗin su. Ta fita da makin da ba a taɓa samu ba a tarihin department ɗin su. Gwamnatin tarayya ta biya musu kuɗi su je su ƙaro karatu a kan fsahar ƙere-ƙere su biyar, ita kaɗai ce mace daga arewa. Shi ne aka yi mata asiri da wani baƙin aljani, aka ba shi jinin mutum, ta taso daga makaranta ta ba shi sadaka, shi yake ta azabtar da ita, a hakan ma zamanta a gidan nan, an rage ƙarfin tasirinsa. Cikin tausayawa Nana ta din ga kallon yadda ta koma gefe, ta zauna tana ta kuka da ƙarfinta. Haka suka wuce ta. Bayan sun baro gurin, suka tafi wani guri, shi kuma jarirai ake kawo wa sabuwar haihuwa, domin yi musu aski, kaciya da cire beli. Idan sarkin baka ya dunƙule hannunsa, yana buɗewa sai ka ga aska, ya yi siddabarunsa ya shafa kan yaro da askar, sai ka ga ya cika hannunsa da gashin yaro. Idan ya shafa aska a wuyan jariri, sai dai ya zira hannu a bakin yaro, ya ciro wata tsoka har ya cire belin. Haka kaciya, sai dai da gashin jariran, da belin, duk a cikin jakar zabirarsa yake zubawa. Sannan ya kan kama hannun yaran, ya ɗaura musu laya, ko ya sanya musu tagulla. Ya kalli wata mata ya ce "Ahh hajjaju an sauka ashe?" Ta washe baki ta ce "Wallahi sarki, gobe ma suna" Ya kalli yaron, da fatarsa duk ta yamutse ya ce "Ke ya aka yi ki ka bari mayya ta kama miki ɗa? Tun yana ciki matar da ta aiko miki da kunu, ki ka sha ta kama miki ɗa" Cikin damuwa matar ta ce "Innalillahi wa innalillahi raziƙuna, wallahi sarki ka ga ba ya gaba yaron nan, kullum cikin kuka ba ruwan nono na rasa yacca zan yi ohh ni Sakina, amma Allah ya isa wallahi" Daga yadda matar ta faɗi Innalillahi, Nana ta ƙara tabattar da jahilci a gurin matar, yadda suke ba wa maganganun sarkin baka ammana ba tare da musu ba har mamaki yake bata. Ya faɗi maganin da za a bata suka yi gaba. Wani guri suka shiga, shi kuma masu ciwon suga ne, ya yi musu ya jiki suka amsa. Bayan sun gama gaisawa ya kalli masu kula da su, ya ce "Yauwwa, kar a kuskura a karya dokokin da na saka, da sassafe kafin su ci komai a ba su magani, a basu zuma cokali biyu da garin habbatussauda, sai su karya kumallo da ruwan dahuwar yaɗiya mai ɗumi, sannan su ci ganyenta. Da rana a basu faten dankalin turawa da alayyahu, a sake basu zuma da habbatussauda, sai da daddare a ba su gurji da kwaɗon rama, sai a sake ba su magani. Yau maganin cikin ɓawon gyaɗa bibbiyu za a zuba musu a ruwa su sha. Shi ne jadawalin abincin da za a ba su yau" ma'aikatan suka amsa masa da to. Nana kuwa rasa bakin magana ta yi, sai kallon ikon Allah, tamkar likita a asibiti da marasa lafiyar sa. Sun zagaya sosai da sosai a cikin gidan, sannan suka koma wancan ɗakin da suka tarar da shi da farko. Bayan sun shiga, ya zura hannu a cikin zabirarsa ya din ga zaro gashin jariran nan, da belin da ya din ga cire musu, yana tarawa a cikin wata tasa, sai da ya cikata taf. Ya dubi Salamatu ya ce "Salameme zuba wa Fulani a randarta" Salmatu ta karɓa, ta je ta buɗe randar da bafulatanar nan ta ɗqzu sha wannan baƙin abun ta juye a ciki. Ya kalli Nana ya ce "Za ki iya tuna daga wani lokaci, ki ka fara ganin uban duƙusa a bacci?" "Waye hakan?" Nana ta tambaya cikin rashin fahimta. "Aljanin da yake zuwar miki" "Wai ƙaisar?" Ya yi murmushi ya ce "Shi" "Ba zan iya tunawa ba" ta bashi amsa. "Ina kallonsa a tare da ke ɗazu, shi ya yi wannan tsawar mahaukatan nan suka yi shiru, so nake ya bayyana a jikinki mu yi magana da shi, amma yaƙi. Masu ihun nan da ki ka gani, duk masu baƙaƙen aljanu ne masu taurin kai, wanda ko an ba su magani, suke lafawa su dawo daga baya. Nan gurin ɗaure su na yi, nake hukunta su da azaba kala-kala, a matsayin gargaɗi da kashedi. Akwai hayaƙin da ake yi musu safe da yamma an gama hayaƙin muka je, amma ƙaisar ya ƙi bayyana. A duniya aljanun da suke irin sa ba su da yawa". Nana ta yi tsuru tana kallonsa da saurarensa, tare da kallon maganganun sa a matsayin soki burutsu. "Amma ke me yasa ba zaki yadda ki karɓi abin da yake gadonku ba, ki ka gwammace ya yi ta azabtar da ke?" Take Nana ta tsuke fuska, ta tsani ta ji an danganta ta harkar bori da gadonsu, kamar wani abin arziki. "Ni ba zan yi shirka ba" Sarkin baka ya ce "Ba shirka ba ce ba, bayar da magani, idan bayar da magani shurka ne, Asibiti ma shirka suke yi. Ki amince sai mu haɗu mu ci gaba da gudanar da taimakon al'umma" Ta girgiza kai ta ce "Ni ba zan yi ba ba na so" "Anya? Ki yi tunani kar ki zo nan gana kina nema ido rufe fa" tayi shiru ba ta yi magana ba. "Salamatu mayar da ita ɗakinta, a bata abinci, idan tana buƙatar wani abin a bata" Salamatu ta jinjina kai, daga nan ta jagoranci Nana suka bar ɗakin. **** Zaune take a katafaren falonta, ta hakimce a kan kujera tana amsa waya "Hajiya Sa'a, ya mu ka ji da iftila'in nan da ya tinkaro mu, coustom sun riƙe mana kaya a Abuja?" "Aikam, mu na nan muna ta up and down, Allah ya sa su sakar mana a kan lokaci" "Amin ya rabb, wallahi hankalina duk a tashe yake, na haɗa kuɗin mutane da jarina duk na zuba na sayo kayan nan, ni dai fatana Allah ya sa kar su yi condeming ɗin kayan nan wallahi ban san in da zan saka raina ba, ga mutane sun fara ƙorafi" Hajiya Sa'a ta ce "Ahha haba Sadiya, babu abin da zai faru fa, ki kwantar da hankalinki ki yi addu'a" "To shikkenan Hajiya, na gode sosai da sosai" bayan sun yi sallama, Hajiya Sa'a ta yi murmushi ta kalli maman khairat ta ce "Safiyya mutuniyarki ce fa, Sadiya" "Ohh Allah sarki" "Duk hankalinta a tashe yake, batun kayan da coustom suka riƙe, ni ba ta son ko kaɗan kayan nan ba a gabana suke ba" Safiyya ta yi dariya ta ce "Haryanzu ita kanta a tukunya yake kenan, ba ta san dawar garin ba?" "Ina fa ta sani, a zatonta business yake tara mini kuɗi, duk wannan abin shige mini take son yi, ta ji sirrina". "To hajjaju a shigo da ita sabgar mana" Cikin sauri ta ce "A'a tana da surutu, ga ƙaryar riƙon addini, kin san kuma ƙa'idarmu, muddin aka samu mushikila akwai matsala. Ai zatonta business ɗin nan na riƙe, har take neman yin takar da ni a wasu abubuwan. Ba ta san kare yawa ne kawai ba, da kawar da hankalin mutane". "Gaskiya ne, sabgar tana buƙatar sirri sosai" "Safiyya kin ga an sake samun matsala, yarinyar ba ta yi amfani da turaren nan ba, wanda ya yi amfani da shi daban, ya ce wani aljani ne a kan yarinyar hatsabibin gaske ba zai bari komai ya yi tasiri ba. Kuma wallahi ya tabbatar mini idan aka yi amfani da jininta, za a samu alkhairi sosai taurarinta masu haske ne. Kuma idan aka yi wannan aikin ba za a ƙara bamu wani aikin mai wahala ba. Mun riga mun wuce gurin mun samu sa'a, sai da na ce anya ba sato ta zan saka ayi ba?" "Na shige su ni Safiyya, kuma Jamila ta tabattar mini da ta ba ta turaren har ta na murna" "Wallahi ba ita ta yi amfani da shi ba, an yi amfani da turaren amma ba ita ba ce ba" "Kai wannan wace irin jaraba ce? Ga shi kuma wai ba ta nan an kaita gidan mai magani an barota a can" da sauri Hajiya Sa'a ta ce "Haba dai? A ina ne na ji ko da yadda za mu yi mu samu gurin?" Maman khairat ta ce "Wallahi ban sani ba, sai dai idan ta zo na tambayeta" "To ki yi mata cikin hikima dan Allah, ki nuna mata wata 'yar uwakki za a kai, kar mu bar wani trace da za a gane wani abu" "To shikenan hajjaju bari ta zo, it ma ina daf da jawota cikin ƙungiya, za ta yi mana amfani saboda tana da mugun kwaɗayi daga ita har iyayenta" "Aikuwa nima na gani, yanzu dai a far wannan ɗin" **** Ɓangaren Nana, ta ga abubuwan al'ajabi kala-kala a gidan sarkin baka. A kwana uku da ta yi, tana iya fita da kanta ta zagaya tana ganin marasa lafiya har ma ta yi magana da su, ta basu shawarar su din ga zuwa asibiti. Tana yawan zuwa ganin Kubra, sai dai yanayin da take tarar da ita a ciki, ba ya yi mata daɗi, saboda wataran da sauƙi wataran kuma hauka take yi tuburan. Kullum idan Sarkin baka zai zagayen ganin marasa lafiya, da waɗanda ake kawo masa su ganshi, tare yake yi da ita. Aka kawo wata mata da tsohon ciki tana tafiya da ƙyar, cikinta har rinjayarta yake yi, wai shekarar cikin goma a jikinta, wasu lokutan ya tashi, wasu lokutan ya kwanta a neme shi a rasa. Su na gama yi wa sarkin baka bayani, Nana tayi farat ta ce "Ba ku je asibiti ba?" "Mun je, duk gwajin da aka yi sai ace babu ciki" babar matar ta ba wa Nana amsa. Sarkin baka ya bushe da dariya ya ce "Asma'u ma'u, su Asibiti duk abin da suka zo muku da shi, za ku karɓa ku ce technology ne, mu kuma namu da muke yi, shi ne shirka a gurinki. Shi maganin baturen kin san da me da me ake haɗawa? Kin tabattar da ingancin halaccin sa a addinance? Shi fa ilmi siffa ce ta Ubangiji, kuma yana bayar da ita ga wanda ya so, bai keɓantar da baiwarsa ga farar fata ba kawai, ku baƙaƙen fata ne ku ka raina abin da Allah ya baku na ilmi, ku ka yi amanna da bature ne kawai ya iya" Ya mayar da hankalinsa kan mara lafiyar ya ce  "Hajiya a da idan ki na al'ada ba ruwanki, duk gurin da ki ka samu yarda ƙunzugun jinin ki ke yi. Da ƙunzugun jinin hailarki aka yi miki sihiri, saboda a raba ki da mijinki, idan ba ki manta ba, kin yi ta zubar da jini tun yana taya ki neman magani har ya gaji ya yi aure ya rabu da ke. Da ki ka ce ki na da ciki ma rigima ku ka yi ta yi ya ce ba nasa bane ba" cike da amanna ɗari bisa ɗari suka gazgata sarki. Nana ta ce "To kai ya aka yi ka sani, bayan baka nan aka yi?" Ya kalli Nana bai ce mata komai ba ya tashi ya nufi kan matar. Ya saka Salamatu ta ɗebo ruwan magani, aka bawa matar ta sha. Ya dunƙule hannunsa ya buɗe tafukansa aska ta fito, ya saka aka buɗe cikin matar, ya din ga yi mata ƙananan tsagu da askar. Wannan karon sanho ne a jikinsa, (jakar magunguna) zabira (Jakar wanzamai ta kayan aski) A wannan ƙaramar jakar, ya ciro garwashi jawur, ya ɗora a kasko ya zuba wani magani a kai. Take matar ta hau tari, ya kama cikin ya lailaya ya tattara shi guri guda, sai ga wani jini baƙi ƙirin guda-guda yana fitowa daga cikin. Sai da jinin ya gama fita, ya tattare guri guda ya zama wani baƙin muzuru. A take cikin ya baje, Sarkin baka ya danƙi muzurun ya jefa a cikin sanhonsa ya ce "Aljani ne yake ta yi mata wannan siddabarun. Salamatu a kaita gurin su 'yar ƙashi ɗaya, a tsumata zuwa jibi a sallame ta" Sai da Nana ta razana da abin da ta gani. Bayan fitarsu ya kalli Nana ya ce "Idan ki ka kuma ƙaryata ni a gaban mutane, sai na je na ɗaure ki a cikin mahaukatan nan kema" Nana ta ce "Amma ka ce ƙaisar ba zai kamu ba" Ya ce "Zai kamu, ban yi niyyar kama shi bane" Ta sake cewa "Amma ya ake ka ke wannan abubuwan haka? Ta ya ya ka ke sanin abin da baka nan aka yi?" "'yan aike ne suke gaya mini " "Aljnu kenan ko? Haramun ne fa hakan shirka kenan" "Ba shirka ba ne, taimakon al'umma muke yi" "Wallahi shirka ce, har fa tsafi ka ke yi " Dariya ya yi ya ce "A ina na yi tsafin?" "Ga shi nan ina gani kana yi, ya aka yi mage ya fito daga cikin mutum, kuma ya ake yi ka ke tura abubuwa da yawa a cikin 'yar ƙarama jakar nan?" Sarki ya ce "Aljihuna ne da yawa a cikin jakar" "To buɗe in gani" ya yi murmushi ya miƙa mata jakar ya ce "Buɗe da kanki" cike da ƙwarin gwiwa ta karɓi jakar, babu fargabar komai ta fara dubawa. Ya zuba mata ido yana dariya. Sai dai ta zazzage jakar babu komai a ciki. Ta kalle shi ta ce "Wallahi tsafi ne ina magen da ka saka a ciki ya tafi?" Ita kanta Nana tana mamakin yadda ta daina kewar gida gaba ɗaya, take jin kamar ta daɗe da sanin sarkin baka. "Idan kin yadda ki bayar da magani, zan nuna miki yadda nake komai, ki koma gida ki taimaki mutane" Ta girgiza kai ta ajiye masa jakarsa. "Ki je ki huta, anjima tare za mu fita farauta da ke, ki je ki yi bacci yanzu" Ta waro ido ta ce "Da wa za ayi farautar? Amma dai ba ni ba ko?" "Eh ba ke ba" ya bata amsa Ta juya da baya da baya, ta fita. Tana zuwa ɗakin da take, ta ga hayaƙi da wani irin ƙauri mara daɗi, cikin abin da bai fi mintuna uku ba, bacci ya kwashe ta. Da Ƙaisar ta fara tozali, zaune a kan wani dutse a cikin wani rafi, ya miƙe ƙafafuwansa a cikin ruwan masu azabar tsayi kamar itacen dogon yaro. Duk da ta riga ta saba da ganinsa, ba ta fiye razana dan ta gan shi ba, amma biyo bayan tuna mafarkin da ta yi da shi, a cikin sahara ya sanya ta zura da gudu tana neman hanyar guduwa. Ta yi gudu mai nisan gaske, ta ga wani gida, kawai ta faɗa gidan, tana addu'a a zuciyarta amma ta kasa furta ta, a bakinta. Sai dai bayan shigarta gidan, ta nemi hanyar fita ta rasa, kofofi kashi kashi a gidan, duk ƙofar da ta bi babu hanya sai dai ta sake dawowa guri ɗaya. Ta dinga buɗe ƙofofin amma ta rasa hanya. "Ina za ki ne?" Ya tambayeta bayan ya ajiye wata kwalba, jikinsa sanye da fararen kaya yana ɗigar da ruwa. "Yau kuma tsoro na baki? Ko ba ki yi zaton ganina yanzu ba?" Kuka Nana ta saka ta ce "Dan Allah ka yi haƙuri, kar ka ƙona ni yau ma, dan Allah" "Yaushe na ƙona ki?" Nana ta ce"Ranar da ka zama tsoho ka koma raƙumi, ka yi haƙuri dan Allah" Ya girgiza kai ya ce "Ba ni bane" "Wallahi kai ne" "Ni ban yi wannan tsufan ba ai, ba ni bane" Cikin kuka ta ce "Kai na gani a sahara, ka zama raƙumi kana feso mini wuta" Ya sake cewa "Ba ni bane ba, tawagar buzayen da ki ka gani ne lokacin da ku ka shiga gidan. Ni ban yi wannan tsufan ba dudu sheruna nawa ban fi ɗari biyar da goma ba, yaro ne ni" Galala Nana ta saki baki tana kallonsa, shekara ɗari biyar da goman ne yaro. Tambayoyi ne fal a cikinta amma tana tsoron ta tambaye shi ya ce ta ba shi umarni ya zama hadiminta. Ya ce "Kalli can" ta kalli gurin da ya nuna mata. Suwaiba ta gani tana ta ihu ana danneta, mama na kuka tana tofa mata addu'a, sai fizge-fizge take yi tana kiran sunan Nana. Cikin damuwa Nana ta ce "wai me ya sa take kiran sunana, ba fa ni ba ce ba, ni me na yi mata?" Ya watsa wani abu daga hannunsa a gurin da take ganin su Suwaiba, sai ga wannan bararojin, tana ta zuƙar jinin Suwaiba, sannan jikin Suwaiba na ci gaba da zubar da jini ta huda-hudar nan da jikinta ya yi da ta fesa turare. Ɗif ta daina ganinsu, ta juyo gurin ƙaisar cikin damuwa, sai dai ba ta yi magana ba. "Kin san dalilin da ya sa na ƙyale mutumin nan, da ki ke gidansa? Wasu dalilai ne, ki gaya masa har yanzu bai san ni ba, duk hatsabibancinsa akwai sararin da bai isa ya jefe ƙafarsa ba. Na zuba masa ido ne na ga iya gudun ruwansa, amma dole sai na nuna masa iyakarsa, kuma zan gani tsakanin ni da shi waye zai yi maganin wani, kuma wannan abubuwan da yake yi miki akwai wani abu a ransa za ki ce na gaya miki " "Mene ne a ran nasa?" "Za ki gani, ya ce yau zai tafi da ke farauta, zai ci gaba da nuna miki magunguna. Zan ga iya ƙarshen hatsabibancinsa" Nana ta yi sororo tana kallonsa, duk da tana son tambayarsa, amma tana tsoron ya ce ta ba shi umarni ya zama hadiminta. Ya ce "Wuce ki tafi" "Ai na rasa ƙofar fita" "Bi waccan" ya yi maganar yana nuna mata hanya. Tana fita ta ganta a tsaye a ƙofar ɗakin da take tare da sarkin baka. Yana sanye da shigar hargi(irin shigar da maharba suke yi) Bayansa rataye da kwari da baka. Ba ta iya musa masa ba, ko jin tsoro ko makamancin haka ba, kawai ta saka kai ta bi shi. Daga shi sai ita yana gaba tana bin sa a baya hannunsa da fitila. Wata ƙofa suka je, ya ɗaga asabarin ya shiga, Nana ma ta bi bayansa. Suna shiga ƙofar ta gansu a dokar daji. Sai a lokacin jikin Nana ya hau rawa, tsoro ya kama ta, ta ja da baya ta domin koma amma ta ga babu ƙofar da suka shigo. Ya kalle ta ya ce "Kar ki tsorata, babu abin da zan yi miki, bari na ɗaure dajin" "Ina ne nan?" Tayi maganar cikin tsoro. "Dajin igbele ne, na jihar delta" Ta waro ido cikin kiɗima ta ce "Delta kuma? Daga Kanon mu ka zo delta?" Sarki ya ce "Eh, wata kububuwa nake son kamawa zan yi magani da dafinta. Daji ne mai haɗari ana tsafi iri iri a dajin, amma da na kama Kububuwar za mu tafi" ya yi maganar yana haɗa wuta a gurin, ya zuba wani turare yana kewaye wutar. Ita dai Nana ta yi shiru tana kallonsa. Sai da ya gama sannan ya yi gaba, ta bi bayansa. Gurin wani dutse suka nufa, daidai jikin dutsen akwai wani kogo, ya ajiye fitilarsa ya watsa wani abu a bakin kogon. Ya ciro wata raga a cikin sanhonsa ya kafa a gurin. Nana tana tsaye tana kallon ikon Allah. Ya gama ya ce "Mu je wani dajin na nuna miki wasu abubuwan" Al'ajabi ya hana Nana magana, suna tafe yana nuna mata wasu tsirran yana gaya mata amfaninsu. "Kin ga idan ki ka samu kashin giwa, da hauren toronta, wato namijin giwa, da kashin ungulu, ki ka haɗa su da kaucin kuka, da tazargade da garin ganyen kuka, da ganyen magarya arba'in ki haɗa jan miski, a haɗe su guri guda. Idan aka yi hayaƙin su, duk wani ƙaramin shaiɗani sai ya gudu, ke babban ma sai ya sha wahala wallahi, kuma aljani sai dai ya ganki ya bar ki" Nana ta dube shi ta ce "To ta yaya mutum zai samu wannan abun, duk sai mutum ya yi wannan wahalar? Najasar dabbobi ce za ta hana aljanu shafarsa? Bayan ga azkar da Alqur'ani" Sarkin baka ya yi murmushi, yana son ƙi faɗin Nana ƙwarin gwiwar ta na burge shi ya ce "Hala ke da Ƙaisar yake tare da ke, ba kya azkar da karatun Alqur'ani" Cikin damuwa ta ce "Ina yi mana, amma wasu lokutan idan ban yi ba na fi zama lafiya ma, na fara tsorata kar hakan ya sanya imanina ya yi rauni". Ya yi murmushi ya ce "Magani fa ba ƙarya ba ne ba, kin yarda bature ya baki maganin ciwon kai ki sha ki warke, wannan ba shirka ba ce ko, wannan technology ku ke wa ko?" Sai kuma ta ɗan yi shiru. Ja ya yi ya tsaya, ita ma ta tsaya, hasken wuta ta hango daga nesa, a hankali suka ƙarasa daf da gurin, suka tsaya, amma su na iya hango komai. Mutane ne tsirara sai ɗaurin ƙyalle ja a ƙugunsu, maza da mata su na kewaye wuta kowa da ɗan ƙoƙo a hannunsa. Wani mutum a tsakiya yana ta karanta wasu abubuwa, gefe wata mata a kwance ba ta ko motsi da tsohon ciki a jikinta. Ta ga mutumin nan ya nufi kan matar da wata wuƙa a hannunsa yana karanto wasu abubuwan. Razana ta yi, za ta ƙwala ihu sai kuma ta daina ganinsu, ta ga sun koma dajin da sarkin baka ya yi wa kububuwa tarko. "Idan muka tsaya, ki ka ci gaba da gani,  za ki iya rasa hankalinki" Jikin Nana na tsuma ta ce "Su suka kashe matar?" Ya jinjina kai ya ce "Eh, jaririn cikinta za su cire, jininsa za su sha, ƴan ƙungiyar asiri ne. Nan da ki ka gansu manyan mutane ne, da suka sadaukar da lahirar su domin duniya. Akwai 'yan kasuwa a cikin su, da 'yan siyasa" Jikin Nana sai tsuma yake yi, ba ta taɓa tunanin da gaske akwai ƙungiyar asiri ba, ta zata shaci faɗi ne  kawai ake faɗa. "Bari mu koma ki kwanta, da asuba zan dawo na kama macijiyar nan, naga duk a tsorace ki ke . Sai dai ina son mu yi wata magana da ke". Jiki a sanyaye ta ce "Wace irin magana ce?" "Ina son ki sadaukar mini da uban duƙusa wato ƙaisar, na din ga aiki da shi!" Littafin nan 1k ne a telegram ta wannan account ɗin 0069685771 Aisha Adam Stanbic ibtc Sai shaidar biya ta Ayshercool 08081012143 https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 BUZU AISHA ADAM (AYSHERCOOL) YOTA/002 P14 Cikin hanzari Nana ta ce "Na yarda na amince, na bar maka shi" "Ai ba da baki kawai za ki faɗa ba, akwai buƙatar yin wani aiki, idan kin amince za ki sadaukar mini da shi, za ku rabu har abada" "Eh na amince" Sarkin baka ya ce "Za mu ƙarasa maganar da safe" Kawai ta gansu a ƙofar ɗakinta, suka yi sallama ta shiga ta kwanta. Sai dai jikinta na ta tsuma da tunanin wace matar aka kashe, kuma ake ƙoƙarin cin zarafin gawarta haka. "Hmmm za ki sadaukar wa wani ni ko? Har kin yi sabo da shi haka kin yarda shi?" Ta ji maganar ƙaisar a tsakanin zuciyarta da ƙwaƙwalwarta. "Eh zan sadaukar da kai, muddin hakan zai sama mini lafiya da nutsuwa" ta yi maganar a fili. Dariyarsa kawai ta din ga ji, gidan baki ɗaya yana amsa kuwwa. Bayan ta yi sallar asuba, ta zauna tana azkar bayan ta idar, ta yi shiru tana tunani, addu'a ta din ga yi Allah ya rabata da ƙaisar, muddin abin da sarkin baka zai sakata bai saɓa wa Allah ba, za ta yi domin ta rabu da ƙaisar. Da kanta take zuwa gurin Sarkin baka yanzu, duk ta san hanyoyi a gidan. Kuma ganin ta samu sassauci daga takurar ƙaisar, da sanya mata cututtuka da sauran damuwowi ga abinci tana samu babu mai takura mata da damuwa, ga kuma sukulle da kyautatawar da sarkin baka yake yi mata, sai ta fara sakin jiki da mantawa da damuwar da take ciki. Abin mamaki, yau da Alqur'ani ta tarar da sarkin baka, bugun warshi yana karantawa, sai da ya idar sannan suka gaisa suka fita. Sai da suka fara zuwa gurin da ake harhaɗa masa magunguna, har da injin niƙa a gurin, shi ma ma'aikatan gurin daban, ga tarin saiwoyi da tsirrai. Gaggaisawa ya yi da masu aikin gurin, ya ce "An kawo saiwoyin nan kuwa?" Ya yi maganar yana kallon Salamatu. Salamatu ta ce "A'a sarki, ta rafi ake jira, ba ta kawo ba" "Aljanar nan akwai sheɗainiya, idan ta bari na nemo wani ya ɗebo mini, wallahi sai ta ɗanɗan kuɗarta" Nana ta kalle shi ta ce "Aljana kuma?" "Eh, wasu saiwoyin ai sai dai aljani ya ɗebo, ba dai mutum ba. Akwai abubuwan da a cikin ruwa muke ɗebo su, kuma akwai dai-dai lokacin da muke ɗibar su, idan ba aljani ba sai dai ka nemi masunta, su kuma idan ba su ga dama ba, ba za su baka ainihin abin mai kyau ba" Yana gama yi wa Nana bayani, ya ci gaba da maganar sa. "Akwai masu shanyewar ɓarin jiki, mutum biyu Salamatu a je a duba, idan na aljanu ne, a jira ni ki ba su taimakon gaggawa. Idan kuma na larura ne maza a haɗa musu magani, a ɗauki ɓawon kwakwa, da sassaƙen zogale, da zoɓo da ɓawon abarba, a dafa su sosai, a ƙara ruwa, a din ga basu kofi ɗaya sau uku rana. Ba cin man gyaɗa, ba cin gishiri ba cin kanwa, uzairu ya yi musu ƙaho zan zo na ga jikin nasu" cikin girmamawa ta ce "To sarki" Tun Nana tana mamakin al'amuran sarkin baka, har ta zuba wa sarautar Allah ido kawai Amma duk da haka, Nana ta kan kasa jurewa sai ta tambayi wasu abubuwan, yanzun ma ɗan gyaran murya ta yi ta ce "Sarki, su wannan magungunan da ka ke bayarwa haka da ka, ba ka tunanin ya yi wa mara lafiya illa, a asibiti akwai maganin da idan mutum yana da wani ciwon fa ba a ba shi, ku kuma nan ba tantancewa ku ke yi ba, kuma ba auna maganin ku ke yi ba" Ya gyara zaman sanhonsa ya ce "Ban da sharri irin naki, da kuma abu irin naku na 'yan boko aƙida, da ku ke cewa maganin hausa ba shi da awo, ba yanzu a kunnen ki na faɗi gwargwadon abin da za a ba su ba? Wanda ya sani fa ya sani Asma'u, wanda bai sani ba bai sani ba, galibi gurin masu neman na Abinci kawai ake zuwa, wani koya ya yi amma ba a koya masa maganin yadda yake ba, dan ba kowa ne yake yarda ya bayar da sirrin sa ba. Ni na gada kuma na koya. Bature ya yi nasa ban raina masa ba, kuma nima na yi nawa ba wanda ya isa ya raina mini. Ke shaida ce duk abin da ba ni da maganinsa ina gaya wa mutane. Kuma ni ba dan neman kuɗi nake bayar da magani ba. Ki din ga tambayata abin da ba ki gane ba zan yi miki bayani, amma muddin na ji kushen abin da nake yi, ba zan ba ki amsa ba, kuma kin yi wa kanki, dan ba ki san a ina abubuwan da ki ka koya a gurina, za su iya amfanar ki ba, ko su amfani wani ba" jin sa kawai Nana take yi, tana ganin me za ta amfani wani da wannan abubuwan da babu scientific proof ko research a kan su. Bayan sun gama da nan suka tafi ɓangaren da ba ta taɓa zuwa ba a gidan. Shi kuma garke garke ne na dabbobin dawa da na gida, wani abin ma ba ta taɓa ganinsa ba. Ya din ga nuna mata dabbobin, da magungunan da ake yi da wasu sassa na jikinsu. Yana cikin yi mata bayani, ta ga ya yi shiru ya daina magana, ta leƙa fuskarsa za ta yi magana kawai ta ga ƙwayar idonsa ta koma baƙa gaba ɗaya, jikinsa ya hau tsuma. Cikin sanhonsa ya zira hannu, sai ga shi ya fito da wani shirgegen zaka, ya gaji da riƙa cerarsa jawur da ita. Jiki na tsuma Sarkin baka ya saka hannu ya raba kan zakaran da gangar jikinsa. Ya ɗaga gangar jikin, ya tsiyaye jinin a bakinsa, ya gama ya hau cin gangar jikin zakaran a ɗanyensa da gashinsa da komai yana zazzaro ido. Ihu Nana ta saka tana karkarwa, ta juya za ta kasa da gudu, kawai ta ganta a jikin Salamatu tana shafa mata wani abu. Nana ta juya ta ga ba ta ga Sarkin baka ba, sai ita da Salamatu a ɗakin. Salamatu ta ce "Nana zamanki a gidan nan, ya ci ace kin daina tsorata a mafarki, ki koyi dakiya garin tsoron nan wataran za ki iya zaucewa fa. Shi ya sa Sarki yake nuna miki wasu abubuwan domin ki saba ki rage tsoro" Ajiyar zuciya kawai Nana take yi, cike da tsoron abin da ta gani da ta kasa tuna mafarki ne ko kuma gaske. *** Gaddafi na zaune a rumfar mai shayi, yana jiran a dafa masa noodles da ƙwai ya ci. Babu tsammani sai ga jami'an tsaro sun dira a gurin, tare da Imran. Imran ya nuna Gaddafi aka kama shi, cikin mamaki Gaddafi yake tambayar ba'asin abin da ya faru, amma ba su gaya masa ba suka tafi da shi. Sai da su ka je charge office, sannan aka ce Imran ya faɗi abin da ya kawo ƙarar Gaddafi a kai. Imran ya ce "Yallaɓai, ƙanwata ya ɗauka suka haɗa kai da yayar babanmu, aka kai ta wani guri wai neman magani. Kusan sati guda kenan na yi na yi, su gaya mini ina suka kai ta sun ƙi, kuma ita kaɗai aka baro a gurin babu ɗan jinya". Cikin mamaki da takaici Gaddafi ya ce "Amma ka cika mara mutunci, me ya hana ka saka a kama da Baban, sai ni zaka saka a kama, bayan tare muka kai ta". Imran ya ce "Eh wannan ai ubana ne, kuma Kai ka kawo shawarar a kai ta can ɗin. Ga Suwaiba nan a gidan tana aljanun ita ma, ita baku kaita ba, saboda ita ana son ta ƙanwata ce ba a so, kawai ka gaya mini ina aka kai mini ƙanwa" D.P.O ya ce "Ya isa haka, wannan maganar ta cikin gida ce, kuma shi ma yana da gaskiya, babu yadda za ayi ace an kai mutum gurin mai magani, babu wani nasa a gurin, kuma ba asibiti ba. Ko Asibiti ne?" Ya yi maganar yana kallon Gaddafi. Gaddafi ya girgiza kai. "To ka gani, shi ba ubanta ba ba ɗan uwanta na jini ba, ba ma kwa tsoron ya lalata rayuwar yarinyar. Ga ku a cikin ƙwaryar birni kamar masu hankali, amma kun yi abu kamar mutanen farko. Duk yadda ake ciki wajibi ne gobe ka wuce gaba, zan bayar da mutum biyu a nan, aje a dawo da yarinyar nan, muddin ba ku dawo da ita ba, to wani abun ku ka aikata kuma sai na rufe ku daga kai har wanda ku ka kai ta" Gaddafi ya jinjina kai tare da yi wa Imran wani mugun kallo. ***** Nana a ɗakin da sarkin baka yake bayar da magani ta tarar da shi, yana ganin wata mata da yaronta. Ƙafafuwan yaron tamkar lagwani 'yan sirara marasa ƙwari, da hannayensa. Haka kansa ma ɗan mitsitsi da kaɗan ya fi lemon zaƙi fuskarsa tamkar tsoho abin tsoro yaron. Uwar kuma sai rungume shi take yi cike da so da ƙauna. Sarkin baka ya ce "Wata rana kin kashe gizo gizo cikin dare, a banɗakin ki, lokacin ki na da ƙaramin cikin yaron nan, ba tare da kin yi bismillah ko addu'a shiga banɗaki ba, an yi haka?" Ta girgiza kai ta ce "Sarki ba zan iya tunawa ba" "To an yi, shi ya faɗi abin da ki ka yi masa, kin bugawa jaririnsu takalmi, kin nakasa shi, shi suka ajiye a jikin gizo-gizo yana wasa, ki ka dake shi da takalmi, da kin yi addu'a da ya bar jikin gizo-gizon. Dan haka yanzu ɗan su suka ajiye a jikin yaron naki, jininsa da sauran sinadaran jikin yaron ki, da za su saka ya girma, su yake sha yana girma, dan haka ko an cire aljanin mutuwa zai yi ba shi da sauran mamora sun gama lalata jikin yaron da garkuwar jikinsa" matar ta fashe da kuka ta ce "Dan Allah sarki ka taimake ni" Ya girgiza kai ya ce "Magani kawai nake bayarwa, ba ni da ikon kashewa ko rayawa, zan baki magani ki koma gida, Allah ya baki wani" Nana ta ce "Ya a ka yi ka san aljanin ne a jikinsa, kuma idan ya fita ba zai rayu ba?" Buɗe ƙwaryar can, ki ɗaukko mini habbatussauda, akwai tazargade a ciki da tsakin kuka, da garin farin muski, duk ɗebo su da kan ki ki zo" babu musu Nana ta harhaɗo kayan da ya ce ta kawo masa. Ya zira hannu a jakarsa ya ɗaukko garwashi, ya ɗora a kan wata tasa, ya ɗebi haɗin nan ya zuba a kai. Ko sakan goma ba a yi ba, yaron ya mimmiƙe ya din ga tsala uban ihu. Sarkin baka ya cewa matar "Yaushe rabonsa da kuka, ko ya motsa wata gaɓa ta jikin sa?" Ta girgiza kai ta ce "Ba zan iya tunawa ba, kullum a kwance kawai yake" "To tun da ya yi kuka yanzu har da mimmiƙe wa, kin san ba ƙalau ba, baiwar Allah ki je gida, Allah ya baki wani" Nana a ranta ta ce "Yaro ya ji wannan uban hayaƙin ba dole ya tsala ihun azaba ba". Ya ce "Kamar har yanzu ba ki yarda da abin da ki ka gani ba ko?" Ta girgiza kai ta ce "A'a na yarda" " 'yar wace ɗariƙa ce ke ne?" Ta girgiza kai ta ce "Ɗariƙa ba ta cikin sharaɗin addini, dan haka ni ba ni da wata ɗariƙa" Ya jinjina kai ya ce "Gaskiya ne, kin san kowace ɗariƙa akwai malamin da ta ke yarda da shi, da ki na da ɗariƙa da na ce ki saurari bayanin da wani babban malami ya yi a kan aljanu, amma manta kawai kin tashi lafiya?" "Lafiya kalau Alhamdilillah" ta buɗe baki za ta sake magana ta ga bakin sarkin baka duk jini da sauran gashin zakaran da ya cinye jiya, wanda lokacin da ta shigo ba bu shi a bakinsa. Zabura ta yi ta ja da ba, dan a zaton ta a mafarki ta ga ya ci zakaran ba a gaske ba, kuma da har ma ta manta ma. Sarkin baka ya sanya hannu, ya zaro sauran gashin daga bakinsa, ya kalla ya yi murmushi ya ce "Kar ki tsorata Nana, tun a zuwan ki gidan nan da na so cutar da ke, sai na cutar da ke ta in da uban duƙusa ba zai iya ba ki kariya ba. Har ga Allah bani da niyyar cutar da ke, kuma da gaske na san ba zan iya raba ki da shi ba, amma na rage masa tasiri ta wasu fuskokin daban-daban a tattare da ke. Tabbas na cinye zakara da ransa, kuma uban duƙusa ne ya zungure ni, sai da na yi a gaban ki, dan ki cire yarda da ni kar ki yarda ki sadaukar mini da shi. Da na mallake shi zan ƙara ƙarfi da ƙarin tasirantuwar magunguna na, kuma zan kerewa sa'a tsakanin mutanenmu. Ainihina ɗan wanzamai ne, na gaji wanzanci daga nan aka kai ni bara, na samu karatun Alqur'ani daidai gwargwado sai dai babu sauran litattafai na addini. Azabar yunwa ce ta sanya na fara bin matasa daji farauta, daga baya na watsar da allo na bar gurin malamin da aka kai ni gaba ɗaya, duk mahaifiyata 'yar maharba ce, amma na fi ƙarfi ga ɓangaren wanzanci. Na yi rashin ji, na yi faɗi tashi, na yi wa harkar baka haye, har na so na fi 'yan gado ƙwarewa, hakan ya saka sauran maharba sako ni a gaba, da tsaface-tsaface da ƙoƙarin son kawar da ni. Sun sha haɗa kai domin su kashe ni. Suka yi mini shiri, na zo ba na iya kama komai idan na fita harbi, ga rashin lafiya, dole na bazama neman magani a nan na haɗu da uban gidana, a masu magani ya bani maita, wadda ita ma wasu baƙaƙen aljanu ne suke tasrifinta, ya ƙara koya mini harkar magani, ga wanda na gada na wanzanci a gida. Ya yi mini girkar aljanu na zo na gawurta, na nemi na fi shi ma ko ma na ce miki na fishi ta kaowace fuska, kawai sai ya fara neman ya kashe ni, saboda hassada. Wataran mun fita farauta tare ya rikiɗe ya koma ƙaton maciji ya yi ƙoƙarin haɗiye ni, ni kuma garin ƙwatar kaina na kashe shi har lahira. A haƙiƙanin gaskiya, ba na yadda na bawa mutum duk wani abu da zai cuci mutane a kan zalunci. Ina da tarin aljanu kala-kala da nake aiki da su. Na nemi ki sadaukar mini da uban duƙusa ne domin na ƙara ƙarfin tasirina. Rabona da maita har na manta, tana nan a jikina amma bana amfani da ita, na daina ta'amalli da aljanun maita, shi ne jiya ya zunguri maitar ta motsa mini. Yanzu haka sai na je na yi jinya, kuma zan ja dogon lokaci ban yi aiki ba, sai dai yarana su yi. Hatta Salamatu da ki ke gani ba mutum ba ce ba. Ainihin matar ba ta da lafiya sihiri aka yi mata, ba ta iya komai aka kawota nan. Na saka Salamatu a jikinta take yi mini aiki, Salamatu na fita gangar jikin za ta faɗi ta ci gaba da jinya. Shirin a jikin gawa aka yi mata, aka binne gawar ni kuma ba zan iya sakawa a ciro gawa daga makwanci domin karya sihirin ba, hakan tamkar tozarta gawar ne." Jikin Nana duk ya yi sanyi da jin labarin da sarkin baka ya bata. "Yarinyata da tana raye da ta kai kamar ke, na tafi farauta abokan adawa ta, su ka kasheta da babarta, tun daga nan ban kuma aure ba,, shiyasa na yi iya ƙoƙarin da zan yi na gagare su. Zan saka a mayar da ke gida, ba sai kin yi makonni biyun ba, domin kuwa jiya an turo mini 'yan aike, ana so a haɗa kai da ni, in bayar da jininki, kuma ina da yadda zan yi na bayar, za ayi mini musaya da wani abu mai tsoka, wanda da na so, zan karɓa na bayar da jinin naki na yi maganin uban duƙusa, amma ina jin tausayin ki, ban san gaibu ba, amma akwai yiwuwar kina daf da buɗe sabon babi na ƙaddara, dan zuwanki gidan nan tuni kin yi wa ƙaddarar mukulli" Cikin mamaki Nana ta ce "wace irin ƙaddara ce kuma haka?" "A'a ba ni da damar cewa komai, amma ki tambayi ƙaisar mene ne tarihin kakaninki, za ki ga ta in da zuwanki gidan nan ya buɗe sabon babin ƙaddararki. Babu lallai ki fahimci labarin a take sai a gaba kaɗan za ki fahimta sosai da sosai. Abu ɗaya zan iya gaya miki, nima ina da alaƙa da labarin kakaninki ta wata fuskar" "To kai ka gaya mini labarin mana" Ya sauke numfashi ya ce "Ƙarfin hali kawai nake yi, maitar da take cikina ce take ta wahalar da ni, rabona da cin wani abu da sunan maita na fi shekara goma sha, saboda na sha maganin danne ta, kwatsam jiya na ci na san sai na yi jinya" Nana har da gyara zama ta ce "To ita maitar mece ce? A addini babu maita sai dai kambun baka, to ita a ina ake samun maitar kuma ya ake yin ta" Sai da ya yi dariya, Nana akwai tambaya ba kasafai take barin kanta ya kulle ba. "Tabbas babu maita a addini, sai kambun baka. Maita tsafi ce sihiri ce, wani siddabaru ne da aljanu, da yake ƙara tasirin kambun baka. Ya danganta da wadda ka ke da ita. Akwai wadda ka ke iya ganin kurwoyin mutane, a siffofi na dabbobi, akwai wadda muke amfani da ita mu lalata abu. Idan muka kalli abu, ko ba mu tanka ba zai lalace. Mu kan zuba yawunmu idan ta taso mana a cikin abinci mu bawa mutum, sai ya yi ta rashin lafiya. Ina da jar maita ne, mai bala'in fiye da kowacce tare da wani aljani nake sarrafata, shi ne idan ya buƙaci jini yake zuwa kaina, sai na sha sai ya samu nutsuwa ya sake ni. Ina iya sarrafa maitar yadda nake so, ko shi ne Uban duƙusa ya zunguri maitar a cikina" Nana ta jinjina kai ta ce "To amma ya aka yi ya iya zuwa gurin da ka ke, bayan ka na da magungunan su?" "Ban gaya miki a cikin aljanu irin ƙaisar ba su da yawa ba? Yanzu ki je zan kwanta in huta ne" Ta jinjina kai, ta tashi ta nufi ƙofa, har ta kusa fita ya ce "Ki na ji?" Ta waiwayo ta ga har ya kwanta. "Ki ci gaba da addu'a da karatun Alƙur'ani, duk da idan kin yi kin fi shan wahala, kar ki daina. Kuma kar ki yadda wani abu ya baki tsoro, wasu lokutan da tsoron ka ake amfani a cutar da kai, ki cigaba da addu'a duk tsanani akwai sauƙi a biye. Wataƙila tsanani da ƙaddarar gobe ta fi wadda ki ke ciki yau" ta yi shiru tana jinjina maganganun sa. Ta ɗago ta ce "To na gode sosai da sosai. Ka ajiye mini naman maciji an jima zan zo in gwada ci" ya yi dariya ya ce "Kamar gaske. Zo mu ga tafin hannunki" Ta koma gurin da ta bar shi, ta durƙusa ta nuna masa tafin hannunta hagu da dama. Ya yi shiru yana kallo sannan ya ce " Ki kula sosai zanen X ɗin da yake kusa da layin zuciyarki na nuni da tsagwaron gwagwarmayar rayuwa. sannan layukan ƙasan babban ɗan yatsanki suna nuni da za ki yi wasu tafiye-tafiye, wasu daga ciki na jin daɗi wasu na wahala. Sai kuma alamar ido, da ke babbar ɗan yatsarki da alamar sarƙar da ke jikin babban yatsan akwai wani abu amma ba zan gaya miki ba, shi ma wani karatun ne daban, yana da alaƙa da aure da kuma matsalar iyali" Ta kalli Sarkin baka ta ce "Abin mamakin  ka ba ya ƙarewa sarki, bayan layuka ban ga komai a hannun nawa ba, ko kana ganin wani abu da bana gani a hannun, kuma dai sanin gaibu sai Allah ai" Ya kwashe da dariya ya ce "Wani karatun ne daban, duk da na san ji na kawai ki ke yi ba yarda ki ke yi ba. Je ki an jima ki zo ki ci naman. Na so na je da ke taron wasan maharba da muke yi duk shekara, ni ke ɗauke da kambun har yanzu, sai dai ba na iya tunanin bana za ayi wasan da ni, ƙaisar ya yi mini illa. Maza je ki sai an jima" ta tashi tsam ta nufi hanyar fita tana kallon hannunta. Wannan tsohon mai kama da Ƙaisar ta gani, cikin wannan fararen kayan nasa, tamkar yanar gizo gizo saboda tsufa. Sai kuma ya ɓacewa ganinta, a hankali ta ƙarasa ƙofar ɗakin ta ga baya nan, sannan ta fita, tana tafe a hankali tana duba tafin hannunta tana kallon zanukan da sarkin baka ya faɗa, da tunanin shi kuma wani kalar siddabarun ne. Ji ta yi zafin rana ya ƙaru kamar lokaci ɗaya temperature ta canza. Ta ɗaga kai kawai ta ganta a bakin layinsu. Ta waiwaya da sauri ta ga ba ta cikin gidan sarkin baka. Ta sake dubawa ta ga dai bakin layinsu ne dai. Hatta kayan jikinta ba su bane ba, dogon hijjabi ne da aka ba ta take sakawa lokacin salla, sai kuma wata jaka da take rataye da ita ta fata. Ta din ga ƙifta idanunta domin ta ji ko bacci take yi amma ta ga ido biyu ne, kawai ta nufi gida. Ko da ta shiga gidan da sallama, babu kowa a tsakar gidan. Ta sake yin sallama Nasiru ya shigo gidan da gudu ya dawo daga aike, ya ce "Laa mama Nana ta dawo" Hakan ya yi daidai da fitowar Mama daga ɗaki, hannunta riƙe da tsintsiya da abin kwashe shara. Sakin tsintsiyar ta yi tana kallon Nana kamar baƙuwar halitta. Nana ta ƙaƙalo murmushi ta ce "Mama sannu da gida?" "Uban me yasa ki ka dawo gidan nan yanzu?" Cikin mamaki Nana t tsaya tana kallonta. "Ke idan ki na da kunya ma kya dawo gidan nan, duk da ta'asar da ki ka yi?" Cikin mamaki Nana ta ce "Wace ta'asar?" "Ban sani ba" ta yi magana tana ɗaukar wayarta a kan taga" Nana ta nufi ɗakinsu, amma Mama ta dako tsalle ta tare ta, ta ce "Ai kuma zamanki ya ƙare a gidan nan, abin da na yi na riƙon ki Allah ya ba ni lada. Ba za ki ci gaba da zama ki kashe mini 'ya 'ya ba" "Mama kisa kuma? Wa na kashe?" Ba ta kula Nana ba, ta fara magana a waya "Ko ma ina ka tafi, ka dawo ka zo ga Nana ta dawo, ka zo ka fitar mini da ita daga gida, dan wallahi ba zan zauna da ita ba" ta kashe wayar. Nana ta tsaya tana kallon ikon Allah, Fafur Mama ta hana ta shiga ɗakinsu, ba a fi mintuna goma sha biyar ba, sai ga Baba ya dawo gida. Cikin mamaki yake kallon Nana ya ce "Ina Gaddafin yake?" "Gaddafi kuma Baba?" Nana ta tambayi Baba cikin mamaki. "Eh mana, ba wancan jarababben ɗan nema ya kai ƙarar mu ba, wai mun kai ki inda ba a sani ba, aka haɗa Gaddafi da jami'an tsaro a je a taho da ke" Nana ta girgiza kai ta ce "Ni da kaina na dawo, ban ga Gaddafi ba" Suwaiba ce ta fito daga ɗakin Mama, sai da Nana ta tsorata, ta yi wani irin haske, duk da tana shafe-shafe, amma hasken da ta yi, da gani na rashin lafiya ne. "Ka fa san yadda za ka yi da ita, dan wallahil azim ba zan ci gaba da zama da masifa da annoba ba, shi kansa wanda aka ce an kashe ɗin nan, ina kyautata zaton ma ita ce ba wani ba, to wallahi jinin 'ya'yana ba zai shawu a sha banza ba" Baba ya ce "Wai Rabi me yasa ki ke haka? Idan ta bar gidan nan ta je ina?" "Ta koma gurin uwatta, ta je ta sha nata jinin" "Ba zai yiwu ba, har duniya ta naɗe, ba zan bawa maijidda ɗa na ba." Nana ta yi ajiyar zuciya cike da tsantsar damuwa da baƙin ciki. Ya sake kallon ta ya ce "Wai ba makonni biyu aka ce za ki yi ba, me ya dawo da ke gidan nan yau?" "Shi ne ya sallamo ni" ta amsa a hankali. Baba ya ci gaba da faɗa "Wallahi Ina takaicin haihuwar Imarana, ya haɗa Gaddafi da jami'an tsaro, shi kuma an zo nemansa a kama shi ya gudu, yanzu ma kalli 'yan sandan ne suke kirana ga kuma wannan masifar" "Baba a kama shi kuma? Me ya yi?" "Eh ai ke ce mai jin tausayinsa dama, sun haɗa kai da 'yan iskan abokansa, sun kashe wannan malamin naku, ana ta nemansa ruwa a jallo" Nasiru ya yi farat ya ce "Baba ba fa Yaya imarana ne ya yi kisan ba, abokansa ake nema, shi ne ake nemansa dan ya nuna inda suke" "Duk ba abu ɗaya ba ne dai?" Baba ya faɗa cikin takaici. Jikin Nana na rawa ƙirjinta na dukan uku-uku ta ce "Wai wani malamin namu?" Nasiru ya yi farat ya ce "Malam Auwal aka kashe da daddare, ya fita sayayya ana gobe za a kai ki gidan mai magani" Kanta ne ya yi wata irin sarawa, ta yi saurin dafe kanta tana tunanin kamar ta san zancen amma ta manta a ina. Iya ƙarfinta take kokowa tsakanin ƙwaƙwalwarta da zuciyarta a kan sai ta farka daga nannauyan baccin da take yi. 1k ne a kan telegram, ta wannan account ɗin 0069685771 Aisha Adam Stanbic ibtc bank. Ayshercool 08081012143. https://whatsapp.com/channel/0029VaPywxs8kyyIhWtuvh3g/9223372036854675807 *AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA 08162859027* *INGANTACCEN MAGANIN SANYI MAI WANKO DUK WANI DATTIN MARA SANYI MAI HANA HAIHUWA SA WARIN GABA RASHIN NI IMA JIN ZAFI YAYIN MU AMALAR AURATAYYA FITAR FARIN RUWA MAI WARI KAIKAYIN GABA TUSAR GABA KURAJEN GABA TUSAR GABA BUDEWAR GABA CIWON JIKI RASHIN GAMSUWA* *Maganin sanyi 5k* *Maganin sanyi* *5k* *Maganin ciwon Qoda 10k* *Maganin HepatitisB ASHA NA TSAWON WATA DAYA MUNBADA ANWARKE DA YARDAR ALLAH 40k* *MAGANIN MATA KALOLI DABAN DABAN INGANTATTU MASU LAFIYA DA KARA KUZARI AKWAI NA MATA AKWAI NA MAZA UWARGIDA DA AMARE KU GARZAYO WURIN AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA* *INGANTACCEN MAGANIN GYARAN NONO MAI TADA KOMADAR NONO DA DUK WATA TAMOWA TA NONO ZAI CIKO DA TUWON NONO YA TADA KOMATSEWARSU BANCE ZASU TASHI BA ZADAI SU CIKO SUYI KYAU* *Maganin gyaran Nono 8k* *MAGANIN RAGE TUMBI KODA YAKAI GIRMAN CIKIN YAN BIYU INSHA ALLAH KI GWADA MAGANIN AUNTY ZEE DA YARDAR ALLAH ZAKI GODE* *Maganin Rage Tumbi 7k* *MAGANIN BASUR KODA YAKAI GA YIN TSIRO INSHA ALLAH AGWADA ZA ADACE* *Maganin Basur 5k* *MAGANIN CIWON SUGAR CIKIN IKON ALLAH MUNBADA ANRABU DASHI* *Maganin ciwon Sugar 10k* *08162859027* *09070027627* *Location*KATSINA STATE* *ACCOUNT NUMBER* *8162859027* *ZAINAB SHU AIBU* *OPAY* *OR* *3968303018* *FCMB* *ZAINAB SHU AIBU* *DAN ALLAH IN KINSAN BAKI SHIRYA BA KARKI YI MAGANA DAN ALLAH KIBARI KI SHIRYA AUNTY ZEE MOM MUJAHID KATSINA TAKUCE SAI KUNZO* BUZU AISHA ADAM (AYSHERCOOL) YOTA 002 BRIGHT PENS 3rd BATCH P15 Suwaiba ta shiga banɗaki ta koma ɗaki, babu wanda ta kula a tsakar gidan. Mama kuwa bala'i ta ci gaba da yi. "Wallahi baban Jamila ba zan zauna da Nana ba, idan ta gama da yaran nan kaina za ta dawo, shi kansa wannan yaron an fara maganar saboda yaƙi aurenta ya rasa ransa". Baba ya ce "A'a Rabi, wannan dai zance ki ne, idan da wanda zai mutu dan bai aureta ba ai Suleiman ne, kuma duk abin da ake yi mata a gidan nan babu wanda ya mutu, dan Allah ki daina wannan maganar" Kamar ta mari Baba ta ce "Abin da ya samu Suwaiban bai ishe ka hujja ba, sai ka buɗe ido ka ga gawar ta tukuna? Ni fa wallahi sai dai ka zaɓa, ko ta bar gidan nan ko ni na bar gidan" "A'a ba za ayi haka ba, yanzu idan ki ka ce ta bar gidan nan ina za ta tafi? Haba Rabi Nanan nan fa 'ya ta ce ita ma. Kuma idan kin kwantar da hankalinki, kin san na karɓi kuɗin auren ta, nan da sati biyu za a ɗaura mata aure, ta bi mijinta Ikko, duk mene ne abin tayar da jijiyar wuya?" Nana tun da ta dafe kanta, ta sunkuya ba ta ko motsa ba, sai yanzu da ta ɗago ta fara magana iya ƙarfinta "Innalillahi wa innalillahi raji'un, dan Allah ku tashe ni daga baccin nan, ya za ayi malam Auwal ya mutu? Dan Allah ku tashe ni kafin ƙwaƙwalwata ta samu matsala, dan Allah ku tashe ni daga baccin nan" ta ɗago da idanunta suka yi wani irin ja kamar za su kama da wuta, hawaye ne tare da mijina suke rige-rigen zuba a fuskarta. Baba ya ce "Nana meye haka? Zuwa islamiyyar na banza dama ki ke yi? Ko ni na mutu ai ba kya yi haka ba" jefar da jakar hannunta ta yi, tai waje. Baba ya bita da sauri, amma tamkar walƙiya bai ga ko sahunta ba. Kai tsaye Nana rukunin ofisoshin malamai ta nufa a islamiyyar su. Malam Nura ta tunkara, babban abokin malam Auwal. Cikin yanayi na ɗimuwa ta ce "Wai an kashe malam Auwal? Dan Allah kai ma ka iya ruƙiyya ai ka na yi mini, dan Allah ka karanta mini koma mene ne ko zai sake ni na tashi daga wannan baccin." Ya ƙarewa Nana kallo, da gaske a ɗimauce take, cikin sigar rarrashi ya ce "Zauna mu yi magana" "Ba zan zauna ba, kawai ka yi mini ruƙiyya na tashi. A nan fa na same shi a ofishin sa, muka yi magana, ya gaya mini gaskiya ba zai iya aurena ba, kuma duk na fahimce shi, ya ce mini zai tafi Qatar, to kuma daga na yi tafiya sai ace mini ya mutu?" "Al mautu haƙƙun Nana Asma'u, mun yi rashin Auwal. Ɓata gari ne suka soka masa makami su ka ƙwace masa waya kafin a kai shi Asibiti rai ya yi halinsa, ki yi masa addu'a" Jikinta na karkarwa ta ce "Ya sayyadi Nura. Na yi rashi ba zan manta Yaya Auwal ba, yanzu waye zai din ga bani addu'oin? Waye zai yadda da abubuwan da nake ji a jikina na ciwo, ba tare da ya ƙaryata ni ba?" Tuni malamai suka cika ofishin, kowa da abin da yake faɗa, wasu na kuka domin mutuwar ta dawo musu sabuwa. Da yawa ba su san ya so ya auri Nana ba sai yanzu. An daɗe ana rarrashin Nana, da yi mata nasiha, ba a taɓa yi wa Nana mutuwa mai shiga jiki ba sai a wannan lokaci, Alkhairinsa kawai take tunawa. Halin da take ciki, bai hana kunnuwanta jiyo maganganun wasu malaman, su na cewa yayanta ake nema ruwa a jallo shi ya kashe Auwwal. Sauti komai ƙanƙantarsa Nana na iya jiyo shi, wasu lokutan da haka take gane ƙaisar na daf da ita. Malam Nura ya saka ta a gaba, ya tafi raka ta gida, suna tafe yana yi mata nasiha. A ƙofar gida malam Nura ya yi mata sallama, ta shiga cikin gida tana taku da ƙyar. Ko sallama ba ta iya yi ba, ta nufi ƙofar ɗakinsu, ta ga an saka tsumma an ɗaure ƙofar ɗakin. Ta ɗauki jakar da ta dawo da ita daga gidan sarkin baka, duk da har a wannan lokaci ba ta san mene ne a ciki ba. Ta fara ƙoƙarin kwance ƙofar ɗakin, jin motsi ya sanya Mama sake fitowa, tana ƙoƙarin nufo Nana tana bala'i. Nana ta ɗago a hankali ta kalli Mama, sai kuwa ta ja ta tsaya, dan ba ta taɓa ganin Nana ta yi mata irin wannan kallon ba. Gani ta yi tamkar walƙiya idanun Nana suka yi. Ta buɗe ɗakin ta shiga ta kwanta. Aka jima Baba ya dawo, dan yawon neman in da Nana ta yi ya yi. Yana dawowa suka ci gaba da faɗa da Mama a kan lallai sai ya fitar da Nana daga gidan. Nana tana ji Baba ya kira Yaya Atine yana roƙonta. Baba ba ya iya waya sai ya saka ta a hansfree, kuma sai ya ta ɗaga murya tamkar yana magana da aradu. "Atine dan Allah idan da hali Nana ta zo gidanki, ta zauna kafin a ɗaura mata aure. Rabi taƙi yadda ta zauna da ita, kin san halin da Suwaiba take ciki" "Wace Nana kuma? Ba tana gidan mai magani ba?" "Ta dawo ɗazu, wai mai maganin ne ya sallamo ta, kuma ga 'yan sanda sun tafi da Gaddafi a taho da ita, shi kuma Imarana ya gudu neman sa ake yi ana zargin sun kashe wannan yaron da ake ta magana a kansa a radio, wanda ya ƙi auren Nanan" Nana na jiyo Yaya Atine, kasancewar wayar Baba a ragargaje take kuma China ce ta na cewa "Taɓ lallai Isa Allah ya jarabce ka, wannan masifar duk a gidan ka? To mai magani ma ya kasa ya sallamo ta balle kuma ni, ya zan yi da ita ina ma na ga gurin ajiyeta? Ka yi haƙuri ta zauna a gurinka kafin lokacin bikin nata" Ya marairaice ya ce "Me nake da shi, ba wani biki aure kawai za a ɗaura su tafi, ai kin san ba shi ne da ni ba" Yaya Atine ta ce "To ai shikenan, amma ka riƙe 'yar ka, ba zan je nima na gogi bala'i ba, dan ni na fara tsorata da al'amuranta" "Amma yay... Ba ta bari ya gama maganar ba, ta kaste kiran. "Ka gani ko? Ita ba za ta karɓi bala'i ba, ni kuma a bar ni da bala'i ya ci gaba da kashe mu ba zai yiwu ba" Sallamar da ake kwaɗawa a waje, ya sanya Baba fita, ya tarar da 'yan sada tare da Gaddafi. Ɗaya daga 'yan sandan ya ce, "Yauwwa barka malam, zamu tafi da kai station ne" Baba ya ce "Saboda me?" "Mun je in da aka ce an kai yarinyar ɗanka ya yi ta raina mana hankali muna yawo, babu wani a gurin nan, kuma ga wanda ya kawo ƙarar ana nemansa ruwa a jallo" Baba ya ce "Ai bayan tafiyar ku ta dawo" Gaddafi ya ce "Ta dawo kuma? Ni fa har gurin da muka ajiye mota muka shiga, bamu ga gidan nan ba" "Wallahi ta dawo, tana cikin gidan nan" Sai da aka tafi tare da Nana har police station, aka yi rubuce-rubuce sannan aka saki Gaddafi suka taho gida. Tana jin yadda Gaddafi yake rantsuwa shi da sake shiga duk abin da ya shafe ta har gaban abada. Kwanaki biyu suka shuɗe, Nana ko rintsawa ba ta iya yi, sai da ta gwammace dama a gidan sarkin baka ta yi zamanta. Mama kuma ba su fasa faɗa da Baba a kan lallai ya nemi in da Nana zata zauna ba. Dama normally ma ba abinci ake ba ta ba sai an ga dama, yanzu kuwa tun da ta dawo Baba ne ma ya kan bayar a sayo mata kunu ko awarar naira ɗari, shi ma ba iya ci take yi ba, balle kuma yanzu. Dama ba su fiye shiri da Suwaiba ba, sun fi shiri da Jamila, sai dai a wannan karon tun da ta dawo, babu wanda yake shiga sabgarta, hatta ɗakin da take ba sa shigowa. Tana jin yadda idan aka yi baƙi, ko aka zo duba Nana mama take muzanta ta, tana cewa aljanunta ne suka halaka Auwal, wanda ya fasa aurenta kuma suke ƙoƙarin kashe Suwaiba. Nana tana ganin yadda wasu daga hudar jikin Nana suka fara warkewa, sai dai wasu ba su fasa zubar da jini ba. Turaren da Jamila ta kawo mata ta gani a kan tagar su, an feshe fiye da rabi. Ita dai ta san turaren nata ne, amma ta kasa tuna yadda aka yi ta same shi. Cikin dare ta kasa bacci, ta tashi zaune ta haɗe gwiwoyinta ta kifa kanta, har yanzu gani take kamar za ta farka daga bacci, ace mata Auwal bai mutu ba. Kwanakin nan da aka ɗauka kuma, ta gazagata da gaske malam Auwal ya rasu. Tana so ta je ta yi wa mahaifiyarsa ta'aziyya amma ba ta sani ba ko ta santa, ga kuma surutun da ake ta yi a kanta. "Ya Allah ka yafe mini rashin tawakalli da na yi, na bari ɗimuwa ta sanya ni yin abin da bai kamata mai imani ya yi su ba. Ya Allah Auwal bawan ka ne, mai kwaɗaitar da al'umma bin ka da manzonka, mai hidima ga addini, mai ƙaunar Manzon Allah ma'abocin Alqur'ani ya Allah ka yafe masa ka yi masa rahama" ta yi maganar kuka yana ƙwace mata. Dariyar da ta ji ne, ya sanya ta ɗaga kanta. Ta ganta a zaune jikin wata bishiyar tsamiya, ita kaɗai ƙwal a daji rana tsaka. "Iska na wahalar da mai kayan kara, yanzu duk saboda soyayyar ki ka koma haka? Kamar gaske mutumin nan ya riga ya mutu, kuma ba fa wai son shi ki ke yi ba, shaƙuwa da tausayi ne a tsakanin ku" tashi ta yi tsaye a fusace tana waiwayen in da za ta ga ƙaisar. Domin kuwa sai a lokacin ta tuna ya nuna mata mutuwar malam Auwal, kuma ya taɓa alwashin kashe Auwal ɗin, amma da ta tashi daga baccin, a  wancan lokacin sai ta manta da komai. "Kai ne ka kashe shi ko?" "Idan zan kashe shin ne zan soka masa wuƙa? Kwanansa ne ya ƙare ba zan iya kashe shi ba ai, ni ba na kisan kai sai an dame ni, kamar yadda Sarkin baka ya taɓo ni, nima na taɓa shi wataƙila na karya alkadsrinsa wannan maitar wataƙila ita ce ajalinsa" Cikin matsananciyar damuwa Nana ta ce "Kenan kashe shi za ka yi? Wai kai wani irin halitta ne azzalumi mara imani? Duk wanda na mu'malanta sai ka cuce shi?" Ƙaisar ya ce "A'a ni ba na taɓa kowa sai ya taɓa ni. Ba ya fara lallaɓa ki ki sadaukar masa da ni ba? Ba ki yi tunanin ta wace hanya zai yi amfani da ni ba, kawai saboda ki rabu da ni, ki ka amsa masa kuma ke ba ki san ya ake sadaukarwar ba, ki ka amsa. Tabbas ya shiga gona ta ni kuma na shata masa layi" yayi maganar yana bayyana a gabanta. Cikin kuka Nana take faɗin "Allah ya yi mini maganin ka ya saka mini, idan ka fi ƙarfina ba ka fi ƙarfin Allah ba ai. Kuma kana kallo aka kashe malam Auwal ba ka yi komai a kai ba, banda zalunta ta da azabtar da ni ba abin da ka ke yi" Ya yi murmushi ya ce "Zuwa islamiyyar ta ki ba shi da amfani ashe, ai idan abin da ya fi haka za ayi masa ba ruwana, azabar da ya din ga saka ki na bani, na yi farin ciki da mutuwarsa sosai, ki roƙa masa Allah gafara, dan wasu lokutan idan damuwa da gajiya ta yi masa yawa, yana shan ƙwayoyin gusar da hankali ya yi bacci mai tsawo. Sannan akwai tarin hotunan 'yan mata a wayarsa, ke har ma hirar tsakar dare a dandalin sadar da zumunta yana yi na rage zafi da 'yan mata.. "Ƙarya ka ke yi, wallahi ƙarya ne ba dai malam Auwal ba... Nana ta katse shi cikin ƙarji. Ƙaisar ya ce "Ai dama ban ce ki yarda ba, ku bil adama ma akwai wanda ya kai ku ƙarya ne. Sarkin baka kuma zan kasa zan tsare sai na ƙarasa shi, saboda ba neman sadaukar masa da ni ne kawai ya sanya na yi masa wannan hukuncin ba, wani gagarumin laifi ya tafka mini da sai na ga bayansa" "Dan Allah kar ka kashe shi, mutumin kirki ne, kuma mutane wasu sun yi imani da maganinsa, marasa ƙarfin da ba za su iya jelen Asibiti ba, yana taimaka su babu ko kwabonsu" A hankali ya fara zagaya Nana ya ce "Gaba ɗaya halayyarki ba ta da saiti, ke gaba ɗaya ba a gane inda ki ka dosa, kin gama kushe abin da yake yi, yanzu kuma kin ce a ƙyale shi, mutane na amfana. Idan ya mutu sai ki je ki gaje shi, tun da dama ya kai ki ya nuna miki magunguna. Kwanta ki yi bacci kafin ƙwaƙwalwarki ta samu matsala, ki shirya tarar sabuwar matsalar da take tunkarar mu daga ni har a dalilin zuwan ki gidan wannan mutumin. Za ta yi magana kawai ta daina ganin komai, sai juyi da ta yi a ɗakin da take, cikin magagin bacci. Ƙoƙarin yinƙurwa take yi ta tashi, amma wani irin bacci mai kama da fita daga hayyaci ya yi awon gaba da ita. Bayan kwanaki uku, jami'an tsaro ba su fasa zarya a gidan su Nana ba, a kan neman Imran. Ga fitina da mama take yi a kan zaman Nana, abu ya ƙi ci ya ƙi cinyewa, sai da maƙwabta har da mai unguwa su ka shiga lamarin, aka din ga rarrashinta, aka din ga janyo mata ayoyi da hadisai, a kan tauhidi da ɗayanta al'amura. Nauyin manyan mutanen da suka haɗu, ya sanya ta ce ta haƙura Nana ta zauna, zuwa lokacin da za a ɗaura mata aure. Nana gaba ɗaya lamarin da yake faruwa a gidan na su baya gabanta, har da batun ɗaurin aurenta da ake yi, sati biyu masu zuwa. Rashin samun Abincin nan da ba ta yi, ya fara damunta dan sannu a hankali mutuwar malam Auwal ta fara sakinta, sai dai duk lokacin da ta tuna shi sai ta yi masa addu'a. Tana zaune a tsakar gida da yamma, Suwaiba na tsakar gida tana ta jin kaɗe-kaɗe a wayarta, kanta ko ɗan kwali babu. Bararojin nan ce a zaune a kusa da Suwaiba, jikinta duk ya ciko ta warke, ta zura kanta kusa da Suwaiba tana leƙa wayar ita ma. Nana ta yi shiru tana kallon Suwaiba, tana son ta yi magana, amma tana tsoron abin da ka iya biyo baya. "Ke Suwaiba, tashi ki shiga ɗaki, dan jaraba kalli yadda ta zura miki idanu, kar ta ƙarasa tanɗe ki" Mama ta yi maganar cikin haɗe rai. Suwaiba ta kashe wayar, ta yinƙura ta tashi, aikuwa bararojin ta haɗe rai, kafin Suwaiba ta kai ɗaki, ta hankaɗeta ta faɗi ƙasa. "Kin gani ko? Abin da nake faɗa ko? Dama na ce ba zan zauna da yarinyar nan ba, gashi dai sai ta kashe mini 'ya hankalinta zai kwanta" Kawar da kai Nana ta yi gefe, ta ci gaba da zancen zucinta, dan ba hatsaniyar gidan ce a gabanta ba yanzu. Da daddare Nana ta tsaya tana ƙarewa jakar da ta zo da ita daga gidan sarkin baka kallo, tun da ta zo da ita, ba ta buɗe ta ga abin da yake cikin jakar ba. Yau ma kwanan ihu Suwaiba ta yi, cikin ikon Allah Nana kuma, tun da ta dawo ba ta ihun nan da take yi da daddare sai Suwaiba. Washegari Monday, Nana ta shirya domin jarraba zuwa makaranta, duk da ta san za ta sha bala'i gurin director, na rashin zuwanta tsawon lokaci, amma ta tafi cike da fatan Allah ya sassauta zuciyarsa ya sanya ya karɓe ta, ya biya ta Albashinta, kuma ta ci gaba da aikinta. Sai dai ta tarar da saɓanin abin da take ta fata, domin kuwa ta tas director ya yi mata, ya ci zarafinta ya ba ta takardar kora. Jiki a sanyaye ta karɓi takardar ba tare da ta buɗe ba ta ce "To sir salaryana ka taimaka ka bani na last month" "Ba za a bayar ba, shi ma last month ɗin wani zuwan kirki ki ka yi, kullum ba ki da lafiya" Nana ta sake marairaicewa ta ce "Dan Allah ko rabi ne, ka taimake ni" "Ba zan bayar ba, asarar da ki ka janyo mana, na wahalar neman wata malamar a kuɗinki" Nana ta ji zafin korar da aka yi mata, duk da ta san laifinta ne, amma dai yakamata a bata hakkinta. Ko sallama ba ta yi da sauran malaman ba, dama ba cikinsu take shiga ba, saboda yadda suke yi mata kallon Nanny kawai. Dama da ƙafa ta zo makarantar, dan haka yanzu ma ba ta da kuɗin abin hawa, da ƙafarta ta miƙi hanya. Horn ɗin da aka ishe ta da shi ne, ya sanya ta tsaya, ta waiwaya. Motar baban Muhsin ta gani. Ya ƙaraso gurin da take ya ce "Anty kwana biyu lafiya kuwa? Muhsin na ta rikici ba kya zuwa makaranta shi ba zai zo school ba" "Wallahi na ɗan yi rashin lafiya ne" Cikin tausayawa ya ce "Eyya Allah ya sauwwaƙe, mun yi magana da director ya ce sallamarki zai yi, ba yadda ban yi ba, amma ya ƙi yarda ya haƙura" Nana ta yi guntun murmushi da iyakarsa laɓɓanta ta ce "Ba wani abu, rabona ne ya ƙare a gurin kawai". "Eyya babu daɗi, to hawo na sauke ki a gida" Ta girgiza kai ta ce "a'a ba komai na kusa ƙarasawa ai" "A'a da saura ai na sani, hau dan Allah" ya yi maganar yana buɗe mata ƙofar gaban motar" ta yi bismillah ta hau. "Wallahi ban ji daɗin sallamar ki da director ya yi ba, ki na da ƙoƙari matuƙa gaya." A wannan karon ma murmushin dai ta yi tana wasa da yatsun hannunta. "Ki bani takardun ki, na nema miki admission a school of legal studies, ko koma makaranta mana" Ta girgiza kai ta ce "A'a na gode sosai" "Me yasa? Karatun ne ba kya so? Nana ba zan cutar da ke ba. Ba na wasa da duk abin da ya shafi yarana, yanzu haka Muhsin ne ƙarami, amma duk lokacin da nake gari ni nake kai shi makaranta, saboda yana son hakan. Da ɗa da dukiya ba ayi musu mugunta ba ka san wa zai amfane su ba. Amma ki yi tunani idan kin amince zan samar miki admission ba, ko ba duka ba zan ɗauki ɗawainiyar karatun naki." Cikin girmamawa ta ce "Ka na cikin mutanen da ba zan manta da su ba a rayuwata, ba zan so ka ɓata kuɗin ka ba, ina ga nan da wani ɗan lokaci za a ɗaura mini aure, kuma garin zan bari gaba ɗaya" "Allah sarki, Ubangiji Allah ya sanya alkhairi ya baku zaman lafiya. Bani wayar ki na saka miki lambata, idan lokacin bikin ya yi ki sanar da ni, zan halarci ɗaurin aure in sha Allah" Nana ta girgiza kai ta ce "Ba ni da waya ai, ka yi mini addu'a na gode sosai da sosai. Sannan a cewa Muhsin ya yi karatu da kyau, Allah ya yi masa albarka" jiki a sanyaye yake kallon Nana, haka kurum take ba shi tausayi gaba ɗaya yanayinta ya nuna akwai labari mai ban tausayi a tattare da ita. Ya yi parking daidai gurin da take sauka, tana kiciniyar buɗe ƙofar motar, ya miƙa mata kuɗi, ya ce "Ga wannan ba yawa, Allah ya baki wani abin yin." Za ta yi magana ya girgiza mata kai. Ta saka hannu biyu ta karɓa ta ce "Na gode sosai da sosai"  ya daɗe yana kallon yadda take tafiya da ƙyar ta shige cikin layuka. ***** Malamin Hajiya Sa'a yana zaune, ya duba wurin da yake gabansa, ya kalle ta ya ce "Hajiya a wannan karon ma babu sa'a fa, 'yan aikenmu sun makara, domin fafur sarkin baka ya hana yarinyar nan, ƙarshe ma ya mayar da ita gida, ya ce mu je can mu ɗauke ta, yanzu haka tana can" "Kai wannan wace irin masifa ce? Ni an taɓa bani aiki mai wahalar wannan ma kuwa?" Ya yi dariya ya ce "Ai na gaya miki hatsabibin aljani ne a tare da ita, kuma mutane irinmu, mu na burin mallakar aljani irinsa, domin kaf jinsin babu aljani mai tsananin juriya da kasada kamar sa, tun da sarkin baka ya mayar da ita ba tare da ya mallaki aljanin ba, na san akwai matsala. Yanzu ki bar wannan mu jingine ta zuwa wani lokaci kaɗan. Yanzu ga wani aiki mai ɗan sauƙi, 'yar aikenmu na kan waccan yarinyar da ta yi amfani da turare kuma ta warke ma. Ki duba dangi wanda yake jininki ki samo yaro da bai wuce shekara biyar ba, a sadaukar mata da shi, domin ta ƙara samun kuzari zan sanya ta yi miki wani aiki" Hajiya sa'a ta ɗan yi shiru ta ce "Akwai ɗan wa na, ba zai gagara ba" "To shikkenan, tashi ki je, Sa'a na tare da ke Hajiya Sa'a tun da ki na bibiya ga duk abin da aka saka ki. Ki je za a sanar da ke lokacin da ake buƙata" tashi ta yi tana jin daɗin yabon da ya yi mata. ***** Nana da ta koma gida, ta tarar an kai Suwaiba asibiti, daga gurin masu magani, wai jikinta babu jini an riƙe ta a asibiti. Sam Nana ba ta yi gigin bin su ba, ta dai yi wa Suwaiba Addu'a. Ta duba kuɗin da baban Muhsin ya bata dubu goma cif. Addu'a ta din ga kwarara masa da shi da zuriyarsa, saboda ta ji daɗin kuɗin nesa ba kusa ba. Da yamma Ummi ta zo gidan, ta tarar da Nana a gida. "Nana ke ba ki je asibiti duba Suwaiba ba?" "Hmm kin san da yadda ta yarda nake zaune a gidan nan ne ma? Su na cewa ina ƙoƙarin kashe Suwaiba, wai ina sha mata jini.. sauran maganar ya kakare mata saboda kukan da ya kufce mata mai taɓa zuciya. Jiki a sanyaye Ummi ta ce "Yanzun ma da na je, su na ta maganganu amma dan Allah ki manta da su. Ke dai Allah ya baki lafiya. Na zo ne a kan batun shirin bikinki, Baba ya ce ba za ayi taro ba. Amma ko ba za ayi taro ba ai kya fara gyaran jiki dai ko?" "Me zan gyara? Ni dan Allah ki rabu da ni" Ummi ta ce "Kamar yaya na rabu da ke? Aure fa za ki yi." "Auren jeka na yi ka ba? Ai kun san ba so nake yi ba, amma babu yadda na iya ne, shi ne sauran mafitar da ya rage mini" "Au Nana ba za ki daina maganar ba kya so ɗin nan ba ko? Ke ba kya tausayin kanki da wannan wahalar da ki ke ciki ko? Ki je ki ki yi ta yi, sai mutum ya tausaya miki, idan ki ka tafka wani rashin mutuncin zai gane ke ba abar tausayi ba ce. Ki je ki yi abin da ki ka ga dama, ni na cire hannuna a kan ki" "Allah yana tare da ni, na san shi ba zai cire hannu daga kaina ba" Nana ta yi maganar hawaye na gangarowa daga idanunta. Ayshercool 08081012143 Alhamdilillah free pages sun kammala, masu buƙatar ci gaba su na iya tuntuɓata a kan lambar wayata. 1k ne a telegram Via 0069685771 Aisha Adam stanbic ibtc sai shaidar biya ta 08081012143