*GURBIN IDO* _Ba ido bane_ *Mallakar* *Safiyya Abdullahi huguma* *Arewabooks username* *HUGUMA* ©️®️ *ZAFAFABIYAR* *ƊANƊANO* *Page 01* Faffada kuma yalwataccen daji ne iya ganinka,wanda ya wadatu da korayen tsirrai da kuma shukoki nau'i daban daban,masu tsaho da kuma gajeru,ciyawa tafasa da sauran tsirrai da ubangiji ya huwace musu su wanzu a wajen,wanda wasu ma dan adam bai san meye ba,wasunsu kuma magani ne da garkuwa ga jikkunan dan adam. Yadda sararin yayi kore shar da nau'in tsirran da kuma yawaitarsu kadai xai bayyana maka cewa muna lokacine na yawaitar saukar ruwan sama wato lokaci na damina,duk da da cewa gurin waje ne mai cike da ni'ima da kuma albarka,albarka data sanya mawuyacine ka samu wajen a bushe ko kuma a qafe.....wannan dalili ya kawo wanzuwar fulani wajen a muhallin,suka kafa bukkokinsu suka kuma tashi gagarumar ruga a wajen....saboda waje ne daya dace da muradinsu da kuma buqatar dabbobinsu,wanda buqatar dabbobin nasu sama take da tasu buqatar. Yammaci ne lis,wanda daqiqu kadanne ne zasu ratsa magariba ta shiga,lokacine da kowanne makiyayi yake qoqarin kada kan dabbobinsu zuwa gida inda zai turkesu saboda gabatowar dare,daga cikin wannan dajin mabanbantan tawagar shanu wani lokaci harda raguna da akuyoyi ke kutsowa cikin ainihin wajen da suke kira da gari a wajensu,kowanne tawaga na tafe ne da masu kula da ita,mutum biyu uku hudu har zuwa biyar idan sunyi yawa,yawancinsu maza ne,matan dake ciki daidaiku ne. Da sannu sannu wadan nan dabbobi ke wucewa zuwa guraben da muhallinsu yake,kamar sun gama wucewa.....saiga wani garken na daban na bullowa a hankali. Kyawawan shanu ne tunkiyoyi raguna da kuma awaki masu tarin yawa da daukar hankali,ba komaine ya kawo haka ba sai yanayin qoshi da kuma tsaft da garken keda yashi,kusan duk dabbar dake ciki fara ce.....sai wasu daga ciki dake da ratsin ruwan qasa......duka ba wannan ne abun mamakin ba,abu mafi daukar hankali shine Kyakkyawar matashiyar dake kara kaina daga hagu tsakiya xuwa daman dabbobin tana saita su,da fari zaka zaci ba ita daya ke wannan aikin ba,amma idan ka tsawaita dubanka a kanta zaka fahimci ita kadai dince,dauke da sanda guda daya tak. Kyakkyawa kyau na musamman kuma na asali koda cikin fulanin,irin kyan da zaka tsammaci half case ce,maimunatu nada wani irin kyau na daban wanda ke sanya duk wanda yake baqon gani a gareta ke bata lokacinsa wajen binta da kallo,saidai kuma.....duk da wannan kyau nata babu mutum daya daya aboceta wajen tahowa gida,kusan kowa ya kado dabbobinsa ya barta,babu koda mutum daya ma cikin wadanda sukayi gaba dake waiwayota ko duba halin da take ciki bare yayi niyyar tayata ta samu ta iso gida da wuri. Kusan itama hakan bai dameta ba,duk da tanashan wahala,amma ya zamar mata jiki,ta kuma saba da yanayin......sanye take da baqin saqi maimakon farin saqi da akasan mafi akasarin fulani na tu'ammali dashi,zaka iya hangen yadda kayan suka dangale mata sosai fiye da dangalewa ta al'ada da aka saba gani tattare da fulanin,don kuwa koda rigar maimunatu tayi dagewar da banda baqar rigar yadi data saka daga ciki,babu abinda zai hana mutum ya hango albarkatun qirjinta da suka fara tasawa,sai kuma yalolon baqin mayafin data sake rufe qirjin nata dashi,duk kuwa da cewa ba wani kauri ne dashi ba,bashi da maraba da abun tace koko,hakanan bashi da tsaho,don ko mazaunanta baikai ba,tun abun yana da girma da kuma kaurinsa take amfani dashi,amma har kwanan gobe ta kasa rabuwa dashi,saboda dumbin tarihin da mayanin yake dashi a gareta da kuma rayuwarta gaba daya. Zanin jikinta shima a dage yake sasai,kanta na sanye da Hular kaba irin wadda fulani ke yawaita amfani da ita da suke kira da(malafare)sakamakon yawaitar zafin rana ko kuma tunanin saukar ruwan sama,wadda ta baiwa doguwar jelar gashin tsohon kitson dake kanta bayyana sosai,kitson DOKA inji hausawa,su kuma suce dashi(BIƊEJI)(mai tudu daga tsakiya)shine a kanta,don haka jelar ga sauko dama da hagu na fuskarta da kuma bayanta,abinda ya qarawa kyakkyawar fuskarta kyau da kuma bayyana asalin yarenta. Kunnenta babu dan kunne,saboda bata dashi,bata ma ta'ammali dashi,amma hannayenta cike suke cankas da duwatsu kalar kore shar da kuma ja,irin shirin duwatsun da akasan fulani dashi,hagu da damanta gaba daya,masu yawan gaske,wasu daga ciki ma sun girme mata,amma dai wasu abubuwane da bata iya rabo dasu,tana jinsu ne tamkar fitar numfashinta. Daga qugunta salkar ruwa ce ta duma da aka fafe daure tam,abu guda daya da take da damar tafiya dashi zuwa wajen kiwo,qafafunta kuwa wasu takalman roba ne rufaffu wanda baka rasa bafulatani dashi saboda yanayin shiga daji qayoyi da sauransu,shi kadaine fari a jikinta,duk da tsufar da yayi amma fes yake,da alama ya samu kulawa. Cikin matuqar juriya da kuma jajircewa take wulga sandar tata tana maida dabbobin hanya,duk kuwa da cewa numfashinta baya sauka zuwa cikin cikinta saboda uwar yunwar dake sakadar hanjinta kamar zata tsinka mata su,cikin matuqar kulawa take kada sandar,saboda ko kadan batasan ta samu kowacce dabba a cikinsu,wannan kusan al'adarta ne,bata dukansu,saidai duk umarnin da zata basu suna ji suna kuma biye da ita,hakan ya haifar da shaquwa mai ban mamaki tsakaninsu,idan tana magana dasu wani lokaci,kai kace tana magana ne da mutane 'ya uwanta. Har mantawa take cewa ba bil'adama bane kamarta,sau tari takanji sunfi mata mutanen dake kewaye da ita take kuma rayuwa a cikinsu,idan tana tare dasu,tana jin kamar bata da wata sauran damuwa,tana daukansu ne kamar wasu 'yan uwanta. Sannu a hankali take ci gaba da kadasu cikin juriya da qarfin hali zuwa hayar da zata sadasu da gida. Tafiya me matsakaicin nisa suka bayyana a rugar ummaru,faffadan riga mai dauke da bukkoki masu yawa,ga wadanda suka zaunu kuma sun fara gini na jar qasa da kara wanda suka tasheshi a matsayin katanga. Ta bayan dakunan da suke mallakin wasu suka keta,jimawa kadan sai gasu a haggo(wajen daure dabbobi),ta waiwaya a hankali tana duban sararin gidan,babu matar daya zame mata wajibi duk sanda fa dawo ta shaida mata dawowarta,wannan qa'ida ce,wadda tsallaketa ko saba mata dai dai yake da saima kanta tashin hankali da rashin nutsuwa tsahon wasu kwanaki,idan ma batayi sa'a ba,cikin duka kwanakin da zasu biyo.....za'a yita kiranta da sunan da duk duniya babu sunan data tsana sama dashi "Miwarti inna!" Ta bude dukka kaifi muryar da Allah ya bata tana qwalawa innar kira tare da shaida mata ta dawo,saidai yanayin zaqin da muryarta ke dashi,sam bata da amsa amo ko kuwwar da kiran xai isa inda takeso "Inna miwarti!" Ta sake fadi,saidai da alama ko kusa da inda innar take basu jita ba. Waiwaya tayi gefe guda,yarone dan kimanin shekara takwas,zaune yana wasa abinsa,yayi fututu,kai zaka ce daga sansanin gudun hijira aka tsamoshi,kai ta jinjina,tanason tace dashi wani abu amma tana tsoro kada cibi ya zama qari,bata da zabi illa ta aikeshi ya kira innar "Laulo,yanoddanan inna" daga kai yayi ya dubeta yana yamutse fuskarsa dake harmutse da qasa "Owalad'o(bata nan)" ya amsa mata a tsiwace yana maida kansa ga wasansa. Kanta ta daga sama tana kallon sararin samaniya,hadari ne yake hadowa wanda bisa dukkan alamu ba zai dadeba zai bada ruwa daga yanzu zuwa kowanne lokaci,bata qaunar yanayi irin wannan,lokacin da take dawowa daga kiwo.....cike da gajiya qishi da yunwa,take fara ta turke dabbobin a muhallinsu....ta sanar da inna ta kuma shaida dawowar tata,ta wuce zuwa cikin gida,duk da cewa koda ta wuce din bata da tabbacin samun hutun da dukka jiki irin nata daya wuni yana kara kaina tsakanin jeji da jeji a tsakiyar dabbobi,ba shakka da biyu inna ke aikata hakan a gareta,sai taja da baya kadan ta jingina da wani turke tana ci gaba da duban sama,zuciyarta cike da addu'ar dawowar inna a wannan lokacin. Cikin matuqar d'ar d'ar take a wajen,duk da ba karatu ne da ita ba mai yawa....amma ta sani xama a wannan lokacin cikin turakun dabbobi abune mai hatsari,bugu da qari ma,a al'adarsu tasan yadda suke taka tsantsan da wajen a lokaci irin wannan. Sosai ta lula cikin duniyar tunani a dan zaman da tayi a waje,wanda har batasan laulo yabar wajen ba,hakanan batasan hadarin ya gama hade jikinsa ba waje guda,ya kuma fara busa iska dake hade da qura,saida qurar ta gifta ta gaban idanunta,daidai sanda ruwa ya fara sauka.....dai dai kuma lokacin da idanunta suka kai mata ga dabbobin da suka tarwatse a wajen. Da sauri ta miqe cike da fargaba guda biyu,na farko ruwan saman da zai taba jikinta duk yadda taketa qoqarin kauce masa,na biyu kuma warwatsewar dabbobin data tabbatar da cewa saita sake wani aikin kan ta hade kansu. Tana miqewa dai dai bullowar wata mata,doguwa ce sambal,farar bafulatana ta usul,sanye da fararen kayan saqi,ta yane kanta da babban mayafi kore shar da shi,a gurguje matar take,da alama itama tana gudun tabatan da ruwan saman zaiyi "Maimunatu!"ta qwala mata kira bayan taja birki tana hangota tsakiyar dabbobin cikin dan ragowar hasken da duhun hadari dana dare ya fara hadiyeshi "Na'am inna" "Muguwa!......saboda bana nan ne shine kika barmana dabbobi su wulaqanta......seto me wanna nima ɓerde(sai na bata miki rai),ki kamasu ki kallaceminsu" daga haka ta sanya kai zuwa shiyyar da dakunansu suke ganin ruwan na sake qarfi. Abinda ya daga hankalin maimunatu kenan,ta riga data saddaqar yau din mawuyacine ta samu barci matuqar ruwan yaci gaba da taba jikinta,wani irin jiki Allah yayi mata da baya qaunar ruwan sama,indai zai tabata to lallai zata kwana da zazzafan zazzabi,amma sai gashi innar ta wuce abinta ko a jikinta,nata burin dai kawai ta tattala mata dukiyarta. Duk da yadda ruwan yake dukanta hakata dinga kamasu tana killacewa,ta daure wata saniya tana laluben danta da aka haifa wancan satin,santsin tabon dake wajen ya debeta,ta tafi suuuuu idanunta a rufe tana jiran ta jita a qasa,amma sai taji wani abu ya cake gaban qafafunta,abinda ya hanata faduwa kenan,ya kuma sanyata bude idanunta d asauri wanda tun kan ta bude din haske ya cika idanun nata. Tarwai ta bude manyan idanun nata da ruwa ya jiqe gashin idanun nata,kamar yadda ya jiqe na girarta da kanta yasa suka hade gaba daya,fuskarta ta sake haske ta kumayi tarwai da wani irin kyau. Idan har idanunta dai dai suka nuna mata mutum ne tsaye a gabanta,matashin saurayi dauke da lema da kuma fitilar torch light mai tsananin haske. Da sauri taja da baya cike da tsananin tsoro,saboda tunda take kaf kafin rugarsu bata taba sanin wannan fuskar ba,abune kuma mawuyaci indai kaidin haifaffen rugarne ka tashi bakasan dan wani gidan ba"tsaya mana" ya fadi da dan qarfin murya amma a tausashe,abinda ya dan bata nutsuwar tsaiwar,yadda take dubansa ya tabbatar masa data gamsu dashi ba,don haka yace "Me kike a ruwa a daidai wanna lokacin a haggo?" Qas tayi da kanta saboda wadatuwar hasken da walqiya ta bayar a lokacin ya haska mata fuskarshi sosai,ta kuma so ta ganeshi "Ina daure dabbobi ne" kamar xaiyi magana sai kuma taji baice komai ba,ya ajjiye lemar kansa gefe,ha saqale fitilar a jikinsa,ya fara kama mata dabbobin yana tayata dauresu. Tsai tayi tana dubansa,sai kuma ta taka a hankali itama ta fara kama wadanda zaa daure din tana tayashi sunayi tare,lokaci lokaci tana satar kallonsa,kamar yadda shima yake satar kallon nata lokaci bayan lokaci,ta gaza gasgata idanunta,wani yau a rugar yasa hannunsa yana taimakonta?,abinda ba zata iya tuna lokaci na qarshe da hakan ya faru ba,rashin sabo da ganin hakan ya sanyata dari dari dashi,har zuwa sanda suka gama tas,ya qarasa wajen lemar ya dauketa yana rufeta,saboda bata da wani sauran amfani a wajensa,saboda abinda zatayi masa rigakafi dashi ya riga daya faru. *ZAFAFA BIYAR* *_Kundi kuma dausayin zaqaqa kuma da d'ad'an litattafan hausa masu cike da nishadi soyayya darasin rayuwa dana zamantakewa,tsantsar ilimantarwa da kuma fadakarwa_* *Wannan karon ma gasu tafe da wasu taskirar tsararrun litattafan guda biyar* SANADIN LABARINA Hafsat rano BABU SO Billyn abdul GURBIN IDO Huguma FARHATUL K'ALB Miss Xoxo INAYAH Mamuhghee Dukka guda biyar din akan 1k Guda hudu:::700 Guda uku:::500 Guda biyu:::400 Guda daya:::300 *_Garzaya ki biya naki a fara a kan idanunki ta wannan account din_* Hafsat Kabir Umar 2270637070 Zenith bank *Saiki tura shaidar biyanki* 07040727902 *MASU KATIN WAYA ZASU TURAWA WANNAN NUMBER TARE DA SHAIDAR BIYA* 09134848107 *_KARKU MANTA.....HAR KULLUM,SIYAN NA GARI MAIDA KUDI GIDA NE_* *GURBIN IDO*👀👀👀 *Free page 02* "Migodake" ta fada a hankali tana sharce ruwan fuskarta,dubanta yayi,ya sakar mata murmushi,wani abu me suna nutsuwa da sanyin halin daya karanta tattare da ita na dan qaramin lokaci yana burgeshi "Karki damu,ba komai" kai ta jinjina,saita juya tana nufar cikin gidan tana qudundune jikinta waje daya saboda yadda sanyi ya fara ratsata,da alama akwai damuwa kenan,yayin da shi kuma ya juya ya dauki torch dinsa ya fara gangrawa yana barin wajen,saidai sau kusan uku yana waiwayarta kafin ta qule masa yabar ganinta,ya sauke ajiyar zuciya yana maida hankalinsa sosai ga hanya,zuciyarsa na qissima masa ita,tsahon wanzuwarsa a rugar bau taba kula da ita ba,hakanan bai taba ganin macen da Allah ya zubawa kyau me sanyi da tsari irinta ba,ko wacece ita?,da wannan tunanin ya isa kofar wani gida,wanda shi dayane kaf kafin wajen dake dauke da ginin qasa da bulo. Babban tsakar gidane daya kasance wayam babu kowa saboda ruwan daketa sauka,yakai dubansa ga dakunan dake jere a tsakar gidan,har ya nufi wani daki daga ciki,sai kuma ya dakata ya juya akalarsa zuwa wani daki dake daura dashi,muqullin ya taba,a rufe dakin yake dole dai ya karbo muqullin,abinda yasa ya juya da dan sassarfa ya nufi daya dakin,yasa hannu ya dage asabarin da aka saukema qofar dakin saboda kaucema shigar ruwa. Dumine ya fara dukan fuskarsa kafin hasken fitilar aci bal bal dake dakin ya cika masa idanu,matasan mata ne guda biyu da yaro namiji guda daya zagaye da fitilar,kowannensu d kwanon tuwo a gabansa yana ci,sai babbar mace guda daya da alamu suka nuna mahaifiyarsu ce zaune gefe daya tana dubansu,jikinta nannade da mayafi me kauri,da alama sanyi takeji "noi saare daada" "Jam....alhamdulillahi,ina ka tsaya?,inata taraddadi ruwan nan sai daya dakeka" murmushi ya saki "Zan canza kaya daada,a bani maqulli" hannu ta miqa wata qwarya dake kusa da ita da alama a nan take ajjiye ajjiyenta ta dauko,ta miqawa daya daga cikin yaran "Nabugol(karbi)" ta fadi,sai yasa hannu ya karba din,sannan ya miqe zuwa inda yayan nasa ke tsaye Cikin girmama ya miqa masa muqullin yana cewa "Hamma....." Dakatar dashi yayi "Micanjato kayaa sadam,ina zuwa" "To" ya amsa yana murmushi,saboda ya qagu ya bashi labarin dake bakinsa,a nutse ya juya ya fice daga dakin ya sake nufar dakin da yayi nufin shiga dazu. Batayi wani hanzari ba wajen isa dakinsu,saboda ta riga data jiqe,kuma koda ta isa dinma tasan bata da wani wajen zama daya wuce bakin qofa,dakinsu ne su biyu,amma kuma ya zama gaba daya kamar mallakin mutum guda,wato 'yar uwarta gaaje. Cikin kula da takatsantsan ta dage assabarin dakin,hasken fitilar dake dakin ya bayyana,motsin shigowarta ya sanya matashiyar dake amsa sunan gaje din daga kanta tana dubanta,gabanta akushi ne madaidaici cike da dambu tana ci,wanda shine yawa yawan cimarsu,tuwo ko dambu,ba kasafai zaka gansu da shinkafa ba Wani kallo ta watsa mata kamar wadda taga qullin kashi "Dirdutu malama(matsa malama)" tasan neman bala'i ne kawai irin na gaje,amma inda take tsaye ma sam bashi da alaqa da wajen da gajen ke zaune,sai ta matsa gefan don kawai a zauna lpy,ta miqa hannunta zuwa ga wata tsohuwar baqar jakar bacco dake saqale jikin bango,darajarta wajen maimunatu dai dai yake da akwati a wajen kowa,duk kuwa da cewa duba daya zaka yimata kasan cewa ta sha duniya ta kuma ji jiki,a nan din take ajjiyar duk wani abu nata,duk da dewa ba komai ta mallaka ba face kayan saqinta kala daya da take boyansa saboda sallah ko wani sha'ani idan ya tashi,duk da cewar ita din ba shiga jama'a take ba,rayuwarta na maqale da wani tabo da ya hanata duk wani 'yanci da walwala da kowanne dan adam kan samu,laifin da bata da masaniya a kansa,bata kuma san sanda aka aikatashi ba. Kayan jikinta ta zame ta matsesu da kyau daga bakin bukkar tasu,sannan ta dawo ta daura wani fallen zani guda daya da take rufa dashi,ta tara hannu a ruwa bunun dake sauka ta dora alwala,sannan ta dawo ciki ta tada sallah. Sallar magrib ce kawai a kanta,saboda koda wajen kiwo bata wasa da sallarta sam,duk da ba ilimin addini gareta ba mai wani zurfi,amma tun kafin takai haka,zamanin da take rayuwa da mahaifiyarta ta koyar da ita yin salla da zarar lokacinta yayi,abu guda daya da ba zata manta da shi ba,ta kuma riqeshi har yau da kyau,kasancewarta mutum da bata da yawan mantuwa da kuma qwaqwalwa mai yawan riqe abu. Da kyar takai sallar da takeyi din saboda tsananin yunwa,takai dubanta ga kwanon da gaje ke cin abinci,tuni ta hallakeshi,dan abinda yayi saura a ciki bazai wuce loma biyu ba,ya tabbata bata da abincin dare kenan duk da dan karen yunwan da take ji?,ta rasa wanne irin azanci ne wannan....tare inna ke hada musu abinci ita da gaje,bayan bambancinsu da gajen kwatankwacin bambacin sama da qasa ne,saboda gaje irin mutanen nan ne masu shegen cin abinci,kamar ci suka kawo duniya,duk yawan abinci sai sun tasheshi....yayin da maimunatu ta kasance wata irin mace,duk yawan yunwar da takeji dan abinda zata ci maka bai taka kara ya karya ba,har wani lokacin ma idan kawai nono tafi ganewa tasha shi ko ajiyayyar madara idan tana da sauranta,kusan duk sanda aka hada musu abinci da gaje sai gaje ta kusan cinyewa ko ta cinye ma sannan take tunawa da ita,duk da cewa a yawancin lokuta bar mata take yi,amma duk lokacin data ratso da tsautsayi irin haka tana jin yunwa tofa saidai ta lashi walqiya ko ta nemi ma duk abinda zata ci din,gajen duka duka sa'anni suke da maimunatu,har maimunatun ma ta bata tazarar kwanaki masu dan dama a duniyar. "Gaje ya baki ragemin ba?" "Idan kina da wani ma ki qaro min" ta bata amsa tana sude hannu tare da ture kwanon da qafa ta gicciye anan wajen tana sakin gyatsa. Fararen idanunta masu sheqi ta dauke daga kan gajen,dan qaramin bakinta mai dauke da jajayen labba yana motsawa kamar zata ce wani abun,saidai ba komai zata fada din ba,zallar bacin rai ne qasan ranta,wanda bata isa ta furta ba,bata jun a daren zata iya runtsawa matuqat bata sanyawa cikinta wani abun ba,ga gajiya da takeji tana nuqurqusar qashinta tare da qaramin zazzabi da taji ya fara lasarta,wanda dama tana tsammanin zuwan nasa. Tsam ta miqe tana leqen waje ta qaramin window din cikin ginin bukkar,ruwan yadan sassauta,amma yana sauka kadan kadan da dan qarfinsa,saita dage qofar ta sanyo kai zuwa waje. Gabanta na faduwa amma ta daure ta qarasa qofar dakin inna,sallama tayi,shuru ba'a amsa ta ba,ta sake sallama,a sannan aka amsa daga ciki a tsawace "Wai waye!?" "N.....nice inna?" Kamar ba za'a fito ba sai kuma ta jiyo motsinta,ta dage labulen ta fito tana mata wani duba daga sama zuwa qasa "Menene kuma?" Sunkui da kanta maimunatu tayi "Yunwa nakeji inna" "Shine kika zo ki cinyeni?" Amsar data sanya maimunatu daga kanta da sauri tana duban innar hadi da girgiza mata kai "A'ah inna" "To meye?,bayan kinsan na hada muku abinci da gaje?" "Ta cinye inna" "Kina kallonta ta cinye?,to babu wani sauran abinci cikin gidan,saiki kwanta haka,kyaci gobe" "A'ah,ba za'ayi haka ba" sukaji an fada daga bayansu,rabewa maimunatu tayi gefe daya,ko bata juya ba tasan waye,mutumin da shi kadai yayi saura wanda yake dubanta da idanun rahama,ya qaraso garesu yana sanye da rigar ruwa,da alama dawowarsa gidan kenan. Da sauri maimunatu ta karbi kayan hannunsa tana tayashi saukewa hade dayi masa sannu da zuwa,inna na daga tsaye tana zabga mata harara amma bata kulaa da lamarinta,don ba zata iya ganinsa da kayan bata karba masa ba "Yaya mutum zai kwana da yunwa......ki debar mata cikin nawa mana" tuni ta cika dama tayi fam da yadda yake nuna kulawarsa akan maimunatun,uwa uba kuma ya buda ledar hannunsa ya bata bread cikin tsarabar da yayo "Wallahi ba zata ci ba....koda abincinka ne kuwa" "Ka barshi bappa,zanci wannan" maimunatu ta katsesu da sauri,saboda tasan muddin jayayyar taci gaba to la shakka a kanta abun zai qare,inna zata yi mata hukunci ne wanda ba zataji dadinsa ba,sannan babu abinda zai sanya innar ta sauya rantsuwarta,saboda ba wai tsoro ko shakkar bappan take ba,duk da tasanshi farin sani,yana sakar mata ne,saboda kasancewar maimunatu daga tsatsonta ta fito,shi yasa yake dage mata qafa,baya zaqewa cikin al'amarinsu da yawa "Shikenan,balejam(mu kwana lpy)" "jam" ta amsa tana juyawa da dan hanzarinta tabar wajen zuwa nasu dakin. "Kiji tsoron Allah fulera,kiji tsoron randa Allah zai kamaki da haqqin marainiya" daga haka ya dauka ledarsa ya rab'eta ya wuce ciki,ta bishi da harara,sannan ta sauke idanunta tabi hanyar maimunatun ta wuce da hararar itama har zuwa qofar dakin nasu,sannan taja qwafa tana sakin labulen "Tsoronka da zanji,rashin godiyar Allah ne yasa baka ganin qoqarina ai,banda ni ma waye zai riqeta?" Taci gaba da mita abinta,saidai ko daga kai bappa jauro baiyi ba bare ya kalleta,idan da sabo ya riga ya saba da halayyarta. Saman shimfidarta ta koma ta zauna sannan ta bude ledar biredin,a hankali ta dinga yaga tana turawa,cikin ranta tana godewa Allah da ya turo bappa jauro,da haka zata kwana da tsohuwar yunwarta. Yadda biredin ya fara mata go slow a wuya ya sanyaya bisa dole ta miqe cikin raunin da jikinta ya fara yi ta lalubi wani tsohon kofi nata ta tsiyaya ruwa a jallonsu dake dakin,ta sake komawa ta zauna,tana ci tana korawa da ruwan,kafin sannan tuni bacci yayi gaba da gaje,wadda maimunatu bata da tabbacin tayi sallar magariba bare isha'i. Jahilci ya sanya gaje da wata ire irensu sam basu baiwa ibadarsu muhimmanci,duk da cewa akwai makarantar islamiyya guda daya tal,wadda anan ake koyarwa da kowa da kowa cikin rugar tasu,maza da mata yara da manya,cikin hobbansa da malaman ahlussunnah sukayi suka kawo musu malami bafulatani irinsu yake zaune dasu.yana koyar dasu,saidai ba kowa bane ya fahimci alfanun hakan ba bare har yace zaije,da yawa wani kallo sukewa makarantar,dai daikunsu ke zuwa. Tana da.matuqar buri da kuma sha'awar kasancewarta daliba a makarantar,saidai inama taga lokacin da zai zama rara(saura) a gareta tsahon wuni guda,wanda bata bautar komai,da gar zatayi.amfani dashi ta ziyarci makarantar da sunan daukan karatu,kullum aiki take,babu dare ba rana,ba asabar babu lahadi,kamar yadda babu alhamis babu kuma juma'a,koda makara tar bokonsu dake da dan karen nisa,koda yuashe maimunatu mafarkin zuwanta take,bare wannan dake kurkusa dasu,gaje nada dama mai yawa da zata iya zuwa makarantar,saidai sam ita ba wannan bane a gabanta ba,bata taba ma kwatanta zuwa din ba. Dai dai lokacin da gari ya sake daukan shuru bayan daukewar mamakon ruwan saman.....dai dai lokacin da wata iska me sanyi ke kadawa,a wannan lokacin zazzabi ya fara saukar mata,yana murqushe duk wata gaba dake da sauram qwari a jikinta,takurewa tayi sosai waje guda,tana jin yadda zazzabin ke ratsawa ta qashi da tsokar jikinta,a hankali yana saukar mata da sanyi da wani irin radadi,saita cure waje daya,numfashinta na fita da qyar tana kokawa dashi. Duk da cewa wannan din ba baqon yanayi bane tare da ita,amma shi ciwo ba'a taba sabo dashi,ta jima cikin wannan yanayin tana kokawa da numfashinta,tana hangen kanta tsakanin rayuwa da mutuwa kafin ubangiji cikin tausayinsa rahamarsa da kuma jin qansa ta fara samun sassauci,numfashinta ya fara komawa dai dai,saidai qirjinta dake riqe da kuma ciwon dake ratsawa cikin jikinta yana sandarta a hankali,har wani wahalallen bacci yayi awon gaba da ita. *********** "Maimunatu!.....maimunatu....." Can tsakiyar baccinta....sannan cikin tsakiyar kwanyarta taji ana ambatar sunanta,shurin da aka kaima gefan cikinta shi ya qarasa tabbatar mata da cewa ba cikin duniyar mafarki take ba,abinda ya sanyata zumbur ta miqe daga kwanciyarta,sai kuma ta sanya hannayenta guda biyu ta dafe kanta tana furta "Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un" saboda wani nauyi da taji kan nata yayi mata,baya ga dan karen ciwon da yake mata "Ke yafi kamata a jawa innalillahi,akalluɗo(muguwa)" inna dake tsaye bisa kanta ta fada cikin fushi,bata ko motsa ba bare tace wani abu,kanta na qas tana jin yadda zuciyarta ke suya,jikinta ke tsami da kuma ciwo saboda ciwon dake jikinta "Ananata haala maimunatu?(bakyajin magana maimunatu ko)da kika zo kika kwanta kina barshi,waye zai miki tatsar nonon,waye zai fita da dabbobin?,ko uwarki ce zatazo tayimin?" Idanunta ta runtse,tana jin xafi cikin zuciyarta fiye da kowanne irin zafi,koda wasa bata qaunar inna ta dinga sanyo mahaifiyarta cikin kowanne irin sha'ani ko laifi da zata aikata mata,ta kuma tabbatar ci gaba da shurunta xai bawa innar dama taci gaba da zagin nata ne,don haka cikin murya mai cike da rauni tace "Minyauɗo inna(bani da lafiya inna)" idanu innar ta qanqance tana dubanta "Wannan keta shafa,yahudillo durgul,wurtawa(zo ki tafi kiwo,fito)" ta fada a tsawace kamar zata finciko maimunatun. Bata da sauran zabin da ya wuce ta miqe din kamar yadda inna fa buqata,duk kuwa da yadda takejin jikinta,ta dafa a hankali ta miqe tsaye,a sanda innar ke mata wani kallo "Nikam kin zamemin alaqaqai masifa" saita juya ta fita zuwa waje tana zazzaga masifarta,idan lokacin ka shigo gidan zaka tsammaci wani mummunan abu maimuntun ta aikatawa innar. Kayanta data saqale.jiya ta miqa hannu cikin juriya ta cirosu,hawaye me dumi ya subuce mata,ta zame zanin jikinta,ta fara shirya kanta a cikinsu,babu batun wanka bare akai ga abinci,dama bata lafiyarta take ba "Wurtawa fa maimaunatu" ta tsinkayo muryar innar tana fada cikin salo na azalzala "Mihosh shawai filkul(dan kwali zan dauko)" maimunatun ta fada tana duqawa a hankali ta dauki dan yalolon dan kwalinta ta dora kan sassalkan gashinta dake cure waje daya cikin kitson doka(bijaɗe a fulatance),sannan ta matsa zuwa bakin kofa tana laluben wuffajen ta(asalin rufaffen takalmin da fulani ke amfani dashi wajen kiwo. Ba zata iya duqawa ta sakasu yadda ta saba ba,dole sai datakai qasa ta zauna dirshan sannan ta samu damar sanyasu ga qafafuwanta,ta miqe tana riqe da sandarta tana takowa zuwa tsakar gidan nasu iska na kadata. Kamar kullum babu kowa a tsakar gidan,daga inna dake can rumfar da suke girki,sai gaje dake zaune tana cin tuwo,tuwon da take da tabbacin da safen akayishi,amma bata da darajar da za'a bata ta sanyawa cikinta,ko don darajar bautar da zata fita yi musu. Ganin tuwon ya tuna mata da guntun biredinta na jiya,ta sanya hannu ta dafe qaramar jakar da take daureta a qugunta taji tudunsa tabbacin yana nan,sanna ya fara takawa zuwa ma'adanar dabbobin,muggan kalaman inna sunayi mata rakiya,har zuwa sanda ta kammala kunce na kuncewa,ta kuma fara kadasu suka dauki hanya. ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 *_GURBIN IDO_* *Huguma* *Free page 03* Duk wani taku da takeyi tana yinsa ne da taimakon sandar dake riqe a hannunta,a yau madadin sandar ta zame mata ta saita dabbobin da take jan ragamarsu,sai ta zame mata mataimakiya wajen sanya diga diganta zuwa qasa. A yau din da baki ta.dinga saitasu tana basu umarni,duk da yadda magana ke mata wuya ainun,duk kalma daya idan xata fitar sai taji kamar kanta zai tsage,sun dan dauki lokaci kafin su isa inda suke qyale dabbobin,kowacce ta ni'imtu ta kums amfana daga rahamar ubangijinmu. Tana isa kamar koda yaushe,mabanbantan makiyaya dake wajen kowa ya fara qoqarin tattare dabbobinsa don gudun afkawa ko cakuduwa da nata dabbobin,ba yaune farau ba,nan da anjima kadan ma tana iya ganin wajen babu kowa sai ita daya da nata dabbobin,abune data saba da ganinsa,canfi ne da suka riga suka dasawa ransu,wanda batasan ranar da zai goge ba,hakanan babu me cire musu shi sai mahaliccinmu. A yau dinma bata damu ba kamar kowanne lokaci,bayan ta tabbatar da sun iso inda ya dace,saita fara zame jikinta daga cikinsu,tana wara manya kuma fararen idanunta da kalarsu ta jirkita saboda zafin ciwo dana zazzabi,tana neman inuwar da zata dace da ita. Babbar bishiyar mangwaro ce,mai yawam sanyi da kuma inuwa,wadda bata da wani tsaho.mai.yawa amma sai yawan 'ya'ya,daga nan inda bishiyar take basu da nisa da inda zata hangi dabbobinta,hakanan ba nisa da inda zata gangara dasu susha ruwa da zarar lokacin hakan yayi. A hankali ta zame malafare(hular kaba da suke amfani da ita" ta ajjiye a wajen,duk da hular ba nauyi gareta ba,amma sai takejin kamar ta dora wani dutse saman kanta,ta zare jakar dake qugunta itama ta ajjiyeta,da zata iya kwanciya zatayi,amma tana jin nauyin sallar da batayi ba takai mata ko ina,don haka ta juya zuwa sashen da ruwa ke gudana,ta daura alwala ta dawo ta tada salla saman dankwalin kanta data cire ga yane kanta da mayafin da akoda yaushe bata rabo da yafashi,duk kuwa da cewa baqon abune cikin al'adarsu,zata iya cewa ma kaf fadin rugar ita daya ce cikin matasan yara masu shakaru irin nata dake amfani dashi. "Maimunatu!.....maimunatu" da sauri ta daga kanta daga durquson da tayi masa,tana ware idanunta cikin matuqar kaduwa da razana,murya mafi muni da razanarwa a wajenta.....muryar da mamallakin muryar abubuwane da tunda take a rayuwarta bata taba jin abinda ta tsana cikin duniyarta sama dasu ba "Yaushe ya dawo?" Ta jefawa kanta tambayar tana wurga idanunta don tantance daga wanne bangare yake dosota. Daga can nesa ta hangeshi,tsabar kauri da qarfin muryarne ya sanya ta dinga jinta kusa da ita kamar yana gab da ya cimmata,qasa tayi sosai don kada ya hangota,sannan ta miqe a hankali,ta tattare dankwali hula da jakarta waje daya ga wurga saman bishiyar da take zaune qasanta,karo na farko da tayi ala wadai da rashin iya koyan hawa bishiya irin nata,saita saita mayafinta ta lullube jikinta da kyau,sannan ta zagaya ta bayan bishiyar ta lafe sosai a jikinta,ta yadda zata iya hangoshi,zuciyarta na wani buguwa ɗik ɗik,tana cike da fata da kuma addu'ar rashin samun sa'ar ganinta. Dube dube da waige waige ya shiga yi,yana kuma sake qwala mata kira iya qarfinsa,fuskarsa a firgice da alama ya zaqu da son ganin nata,bai kuma tsammaci rashin samunta a wajen ba,dube dube yaci gaba dayi,yana sake kiran sunan nata dai,har zuwa sanda ya sare,jikinsa da zuciyarsa kuma suka gaya masa bata a kusa "Kayyasa" ya fada da kaushin murya,yana kaiwa bishiyar dake kusa dashi karta da wani kakkaifan abu dake hannunsa,da sauri ta zame kadan saboda gudun samuwar ciwo a jikinta,saura kadan kartawar da yayi ta hada da tsintsiyar hannunta,ta dauke numfashinta cak sanda yake sake takowa da baya,sai kuma ya dura wata ashariya,yasa giyaa zuwa gaba ya taka ya fara barin wajen. Bin bayansa tayi da kallo farincikin boye masan da tayi yana saukar mata,kwata kwata kuma ko sau daya bata taba yiwa buderi kallon mutum mai hankali ba,hasalima tsoro yake bata ainun,buderi kenan,baqin bafulatani na usul,wanda ke ciie da wasu irin baudaddun halaye na wauta jahilci da hauka,irin nau'in haukan da jahilcin ne ke haifar dashi,zuciyarta cike take da mamakin me yasa shi din baya gudunta kamar yadda sauran samarin qauyen ke gaza rabarta bare su furta mata kalmar so?,me yasa shi bai gujeta ba?,ta jima tana yiwa kanta wadan nan tambayoyin. Sai data tabbatar da cewa ya yiwa wajen nisa sannan ta fito,zuwa sannan zazzabin jikinta yayi wata irin saukar da babu shiri,sai sauran dumi,ciwon kai mai tsanani saboda razana da bayyanar buderi da kuma ciwon jikin da har yanzu tana jinsa shima,ta tako a hankali ta dawo ainihin wajen da ta fara zama da farko,tana tattare jikinta waje daya. A nutse yake takowa yana kuma sake nazarin rigar tasu,yanayin yadda ko yaushe take bunqasa da tarin dabbobi da albarkar kiwo kusan ya zarce na kowacce ruga dake maqwabtaka dasu,ni'imar dake wajen ta banbamta daya sauran yankuna,hakan shi ya sanya yanayin wajen da rayuwarsu t bambanta data sauran sassa. Tun daga qasan ruhinsa zuwa saman fuskarsa cike take da wani irin nishadi,tun daga daren jiya da yayi gamo da ita.....har kawo warhaka da yake takowa cikin rugar tasu daga doguwar tafiyar da yayi zuwa cikin ainihin garinsu,tunaninta,siffa da kuma kamanninta basu bace daga idanunsa ba,duk sanda siffarta zata wulqa cikin idanu da tunaninsa sai ya samu kansa da subucewar murmushi,wani lokaci hatta da haqoransa sukan bayyana,nuni da girman nishadin da zuciyar tasa take ciki. Goye yake da baqar jaka,yana sanye da baqin wandon jeans,sai asalin rigar fulani dake jikinsa mai gajeran hannu,daga ciki kuma t.shirt ya sanya mai dogon hannu saboda hana bayyanuwar dantsen hannunsa,saman kansa ma hular fulanince,sai qafarsa dake sanye da wani rufaffen baqin takalmi na danqo. Ba qaramin qara masa kyau da haiba kayan sukayi ba,sun kima fidda ainihin salsalarsa na bafullacen usul,duk da kana dubansa zakasan cewa ya dan banbamta da sauran matasan fulani irinsa dake rayuwa cikin rugar,akwai wani banbanci na daban da kuma haske tattare dashi. Hakanan kawai zuciyarshi ta bashi yabi ta gefan ruwan,yana da tabbacin hakan zai qara masa nishadi,bayi wata wata ba yabi shawarar zuciyarsa,yana tafe yana kallon yadda dabbobin dake baibaye da gefannin kogin keta kaima cikinsu ruwan. Da kallo yaci gaba da.binsu yana sake takawa izuwa gaba,babban abinda ke sake hanashi sakewa da garin kenan,had'akar ruwan sha a gurbi guda tsakanin dabbobi da kuma al'ummar yankin,daya daga cikin burin da yake dashi idan har Allah ya cika masa burinsa,banbance ruwan shan dabbobi dana mutanensa. Dauke idanunsa yaso yi,saidai daga gefe guda dab da rafin wani abu ya dauki hankalinsa,ya rage sassarfar da yake a tafiya,ya sake qura mata idanu saboda tabbatar da hasashensa,shin itace koba ita bace,bashi da sauran zabi.bayan ya tabbatar da ita dince illa bin umarnin zuciyarsa dake azalzalarsa yakai gareta,ko zai rabauta da daddadan sautin nan da take magana dashi a koda yaushe. "Assalamu alaikum" ta tsinkayi sallama daga gefanta,bata tsorata ba duk da bataji takun tafiya ba darajar sallamar da aka gabatar mata,sai ta cira kanta dake boye tsakanin qafafuwanta. Fes ta zubesu a kansa,tadan tsura masa idanu na wasun gajartattun mintuna,qwaqwalwarta da zuciyarta nason tuna mata fuskar,ba tare da daukan dogon lokaci ba ta harbo mata wayeshi,mutumin da ya fara taimakonta tsahon xamanta a rugar ummaru,bai kyautu ba ace ta manta fuskarsa haka da wurwiri ba. Dukkan jarumta da juriyarta ta tattaro,ta sake masa murmushi wanda yayi fidda wani boyayyen kyau dake kwance saman fuskarta "Yallijam(ina yini)" ta furta da sassanyar muryarta tana sauke qafafunta dake takure cikin jikinta kai tsaye sukayi masauki cikin ruwan dake gabanta,sai daya maida mata da murtanin murmushinta,yana jin wani.abu na narka zuciyarsa sannan ya amsa mata "Jam....alhamdlh" ya amsa mata idanunsa bisa kanta,tana wasa da qafafunta cikin ruwan "Nobaluɗa ke`yen(ya kika kwana jiya)" "Lafiya alhmadlh" ta amsa masa tana masa kallo daya,saita maida idanunta ga ruwan ganin ita yake kallo "miyatti fa,na gode sosai da alkhairinka na jiya" Karamin murmushi mai sauti ya sake sannan yace "ko'en waɗi ken yen?(me akayi jiyan?" Dubansa ta danyi cikin mamaki,sai kuma ta kawar da kai ganin kallonta yake,shuru ne yadan ratsa a tsakaninsu,kafin ya buda bakinsa a hankali cikin nutsuwa yace da ita "Anaunaaki nke'yan?(bakiji ciwo ba jiya?)" Hannayenta ta kalla a hankali,tana jin yadda jikinta yake mata babu dadi "Eh" ta amsashi a hankali,sai shuru ya sake wanzuwa a tsakaninsu,jifa jiya yake satar kallonta,yana son sake mata magana ne,akwai abubuwan da yakeson sani game da ita,bazai yiwa kansa qauron baki ko ya cuci kansa ba,kansa tsaye zai iya fadima kowa cewa daga jiya zuwa yau din ta sace zuciyarsa,ta kuma tafi da hankalinsa,dan zaman nan kuma da sukayi na wasu gajerun mintuna ta sake burgeshi qwarai da yanayin tsarin dabi'arta,yawan shuru shuru da kuma alamun cikakkiyar nutsuwa,dukka sun nuna kansu tattare da ita "No'indema surbajo(ya sunanki ne 'yammata?)" Ya fada yana kallonta,fuskarsa qunshe da murmushi,yanayin yadda ya furta maganar tasa maimunatu jin wani banbarakwai "Inde'an maimunatu,daada ta tana cemin diyam" ta fadi maganar wani abu yana motsa zuciyarta,don har sai da hakan ya nuna a saman fuskarta,kai ya jinjina "endema eweli (Sunanki nada dadi....ni baki tambayi nawa sunan ba" satar kallonshi kadan tayi,bataga amfanin tambayar nashi ba,saidai tana duba da alkhairinsa gareta,don haka tace "No'indema" murmushi ya saka kadan sannan yace "Ibrahim.....anfi kira na da himu" kai ta jinjina kawai ba tare data ce komai ba,dukkansu idanunsu kan ruwan dake wucewa ta gabansu "Deko tata nwulo?(yaushe zaki tafi gida?)" "joni(yanzu)" ta samu kanta da fada,duk da ainihin abinda yake cikin zuciyarta kenan,saidai tana tunanin komawar,bataso taje ta tadda bud'eri cikin gari yana jiranta,tanajin kamar taci gaba da zamanta cikin jejin,saidai kuma dole ta koma gida,ko don yadda takejin yanayin jikinta a yanzu. "Amma kamar lokacin komawa bai qarasa yi ba ko?" Himu ya fada bayan ya gama qarewa sama kallo,wadda keda sauran rana tarwai,kai ta gyada,sai taji bata sha'awar fada masa qarya,yar kulawa daya nuna mata daga jiya zuwa yau takejin girmanta har ranta,tunda abune da bata saba ganinsa ba "Minyauɗo(bani da lafiya)" tayi maganar kanta a qas,zuciyarta na karyewa "Subhanallah" ya fada cikin rudewa kadan yana dubanta "Tun yaushe?" "Jiya" ta amsa masa a taqaice "amma hanjun foɗi gurtoyiɗa durgul?ginɗimu?(Amma shine kika fito kiwo,me yasa?" Shuru tayi ba tare data furta komai ba,shi kuma yayi tsaye yana jiran amsarta,amsar da bata da ita,tunda batasan me zata gaya masa da zai fahimta ba. Ganin bata da niyyar cewa komai,da alama shuru shuru da rashin sonyin magana cikin jininta da halayyarta suke,sai ya miqe yana ajjiye jakar dake goye a bayansa yana cewa "kowanna tama?(me yake damunki?" "Zazzabi ne" "qila inpab ɓoje(wataqil malaria ce)" shuru tayi masa,duk da tasan cewa ba malaria din bace,har zuwa sanda ya yiwa jakar ma'ajiya "imi wara(Ina zuwa" ya fada yana takawa zuwa wata hanya da zata fiddaka daga wajen kiwon gaba daya. Binsa tayi da kallo,ko waye shi?,me yasa yake rabarta?,baisan wace ita ba?,maganganun 'yan rugar tasu dangane da ita bai iskeshi ba?,saita maida idanunta ta lumshe ta sake budesu kan jakarsa daya ajjiye gefanta,ta kalli jakar me kyau da ita,kuma fes take,da alama tsafta ta wadaceta,tun ganin farko data masa zuwa yanzu ta tabbatar ga banbanta da dukka sauran mazan qauyen,ta kwantar da kanta saman cinyarta tana tariyo magangun da sukayi dashi daga jiya zuwa yau. *Arewabooks username* *HUGUMA* ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 *_GURBIN IDO_* *Arewabooks::HUGUMA* Free page 04 Sallamarsa ta yanke mata dan qaramin bacci mai dadi data fara yi,ta daga kanta tana amsa masa,da murmushi ya bita,hannunsa dauke da baqar leda qananu guda biyu,inda ya tashi dazun ya koma ya zauna,sannan ya bude ledan yana cewa "Ga magani kisha" idanunta ta lumshe gami da budesu lokaci guda cike da.mamaki,yau ita ake cewa ga magani?,anya kuwa ita dince......maimunatu?,bata sauka daga wannan mamakin ba ta sake jin muryarsa yana sake miko mata wata ledar "Amma ki fara cin wani abun tukunna,na sani idan baku da lafiya bason cin abinci kuke ba,haka innata ke fama dasu zubaida idan basu da lafiya" ya qarashe maganar yana miqewa "Bari na baki waje,amma idan bakisha maganin ba zan dawo" saiya juya yayi nesa da ita,yayin da ta rakashi da kallo har sai data daina hangoshi,sannan ta janye manyan idanunta ta mayar kan ledojin,ta sanya hannu ta jawosu tana budewa. Ledar farko magunguna ne,qwayoyi tablet sosai,sai leda fa biyu dake dauke da gurasa mai kyau,wani yawu ta hadiya,duk da yanayi na lalurar rashin lafiya da take amma sai da tsohuwar yunwa ta taso mata,batayi qasa a gwiwa ba ta dauka ta fara ci,tana ci tana lumshe idanunta tsananin azabar yunwar data tarawa cikinta,dama don bata da lafiya ne,amma duk sanda inna ta gwada mata irin wannan rashin imanin......a nan gurin kiwo take samun daya daga cikin naggen ta tatsi nono mai dumi tasha,duk da ta sani,yawanci da safe shine lokacin tatsar,amma dole tasa wasu lokutan take hakan,idan kuma ta samu ta faki idon innar sanda take tatsar da sassafen ta ɗaɗɗaki wani,shine zata wuni nata damu ba,yunwa kuma bata addabeta ba kamar yanzun,har shan nonon ya zame mata jiki,ya koma kamar shine abincin nata,abinda yasa ko kadan bata da wani jiki kwata kwata,duk sirantaka irin ta bafullace tata ramar ta fita daban. Bawai don ta qoshi ba ta janye hannunta,a'a,tayi hakanne saboda kunya kara da alkunya,kada yazo ya taras ta tashi da ita,ta bude ledar maganin wanda ya sanya ledar ruwan pure water guda daya,ta daga pure water din ta jujjuya shi a hannunta,ba zata iya tuna sanda tasha ruwan leda ba a rayuwarta,saita koma kan magungunan,ta balli kowanne kamar yadda taga anja sandunan layi ajiki ta kora da ruwan. Idanunta ta mayar tana sake lumshesu,tana jin yadda numfashinta yadan fara daidaita albarkacin gurasar data ci tun kafin magani ya soma mata aiki,a hankali take zuqan iskan wajen tana kuma sauraren koke koken dabbobi dake kai kaw a wajen,jikinta yana mutuwa murus kamar wadda aka yiwa dukan tsiya. Tun daga nesa ya kafeta da ido,idanunta dake lumshe sai suka sake qarawa fuskarta kyau,yana ganin baqonnin yanayi tattare da ita,yana son sanin wace ita sani na haqiqa,da kuma dalilin da yasa take kebance kanta take nesa da jama'a haka. Sallamarsa ta sanyata bude idanunta "A henyi?(Kin gama?)" Kai ta gyada masa tana kallon qasa,kunya tana cikata,tanajin yadda tayi abun kunya,na yadda zata zauna taci abinda ya futo daga hannun saurayi "hokkoyon dunni sauro(miko min sandar can)" ya fada yana nuna sandarta dae gefe,sai data kalli sandar sannan ta maida dubanta kanshi,ya fahimci me take nufi,don haka murmushi kawai ya sakar mata,ya taka da kansa zuwa gefanta ya dauki sandar,ga bishi da kallo mamaki fal zuciyarta "waye shi?" Tambayar da taketa nanatawa kanta kenan. Daga nan inda take tana iya hangen yadda yake tattare mata kan dabbobin nata cike da hikima da kuma qwarewa wadda ta lunka tata,da alamu shima din gwanine wajen iya kiwo,bai dauki wasu lokuta masu dama ba ya dawo gareta,yana sabe da sandar kan kafadarsa "indillo(Muje ko?)" Yace da ita,dubansa tayi sanna ta janye idanunta gefe daya,sam maganar batayi mata ba,ta yaya zata jera dashi har cikin gari?,akwai idanun mutane masu yawa a kanta,sannan tana da kunyar da ba zata iya aikata hakan ba "ummadillen(Tashi mu tafi),ko ba zaki iya tashi ba?"ya sake maimaitawa a tausashe,a hankali ta girgiza masa kai "Kaje kawai,na gode,zan qarasa kaisu gida da kaina,na gode qwarai" idanu yadan zuba mata kadan,sai ya sauke ajiyar zuciya yana sauke sandar daga kafadarsa,ya fahimci me take nufi,tabbas ga cika bafulatanar gaske. "Shikenan,zan kora miki su,tumudilli tokkirawaya gaɗa taajan banna wala kyettaiɗo ingwandi(idan na tafi ki biyo bayana,karki damu,ba wanda zai gane tare muke)" duk da hakan yayi mata,amma kuma batason dora masa wani nauyin kuma ko dawainiyarta,saidai kafin ta sake cewa komai yayi gaba,dole ta miqe,ta dauki malfajenta ta mayar saman kanta,ta dauki jakarta ta daura tabi bayansa. Bata sani ba ko shima ya kula,sharewa kawai yayi,ko kuma bai kula din ba.....da gaske ita daya ta lura,yadda mutane keta binsa da kallo a sanda aka ganshi yana kora shanun da ita ke da hakkin kula dasu,yayin da ita kums ke biye dasu a baya,kasan samun nutsuwa tayi kwata kwata,jinta take a daure,har sai da suka isa gida,ya miqa mata sandanta idanuwansa akanta,fuskarsa dauke da murmushi "Sai jaaango?" Ya fada yana sake nazartar kyakkyawan fuskarta "Miyatti" ta amsa masa a gajarce,sai ya jinjina kansa "Alla ɗaudane jamu(Allah ya qara lafiya)kisha magungunanki da kyau" "to Allah jaɓe" ta fada tana jin nauyin mixanin kyautatawarsa a gareta. Ko sanda himu yake nufar gida tunaninta ne fal cikin ransa,kamar yadda murmushi yaqi barin fuska da bakinsa su huta,sosai yake ji cewa yayi gamo da Matar aure,ta kuma zo dai dai lokacin da ya kamata ace tazo din,bayajin zaiyi nauyin baki ko jinkirin shaidawa innarsa,duk da cewa babansu baya nan,amma dai yana da kyau innar ta sani,ta kuma shaidawa baban da zarar ya dawo. Da sallama ya shiga faffadan tsakar gidan nasu,kishiyar mahaifiyarsu wadda asalin sunanta shine rahama....amma sauran dangi da 'yan rigarsu na kiranta da ramatu,su kuma yaran gidan suna kiranta da yuuma,tana duqe gaban murhu,ta kammala kwashe tuwon dare tana wanke muciyar cikin tukunyar tuwon himu ya shigo. Fuskarta dauke da fara'a take amsa sallamar tasa,macace mai matuqar kirki haquri hagen nesa da kuma sanin ya kamata,duk da kasancewarta wadda Allah bai azurtata da haihuwar yaro ko daya ba,amma sam bata kasance mai baqin hali gabyaran mikin nata ba,mutum ce mai sauqin kai,wadda take kallonsu ibrahim tamkar ita ta haifesu,tana kulawa da kowanne daya daga cikinsu,duk da zamantowar safara'u mahaifiyar ibrahim mace mara haquri da biyema zuciyarta a wadansu lokuta,amma yuuma ta danne,suna zaman lafiyar daya sanya jama'a da dama cikin karkarar ke sha'awar zaman nasu,ba tare da sunsan cewa fiye da kashi tamanin cikin dari na zaman nasu haqurin yuuma ne ya qawatashi. Barka da gida yayi mata ta amsa tana masa sannu da zuwa "Inna walaɗon(inna bata nan ne?)" "o'o immoder,one ɓayi e'ummakiɗo(A'ah tana ciki,don bata jima da tashi daga nan ba),kila barci ne ya saceta,don tacemin bata danjin dadin jikinta sosai" kai ya gyada sannan ya sake tambaya "Yaran nan fa?,su safiya?" "inna'onliliɓe,amma ɓeɓadake wartuki(Innar ce ta aikesu,amma suna gab da dawowa)" har ya taka zaiyi gaba sai ya sake tambayarta "Yaushe baaba yace zai dawo ne?" Murmushi ta sake "Yau kuma 'yan tambayar ne a kusa himu?,rana wata yau in sha Allah" kai ya gyada yana murmushi,yaji dadin jin cewa bazai jima ba zai dawo gidan,ya tafi ikko ne da wasu shanunsa zai saidasu,wanda dama.yawanci can yake kaisu,shi kansa ibarahim din yafi zama a can,mafi yawan rayuwarsa ta can ce wajen wani dan uwan baaban nasa,yanzu ma gajiya yayi da zaman can din ya dawo gida yadan huta sannan ya koma,uwa uba kuma sun samu hutun semester,don acan din bai zauna ba yana karatunsa. Ya daga labulen dakin ya samu barcinne kuwa ya dauketa,sai ya sauke ya wuce dakinsa,yayi abinda zaiyi a ciki sannan ya fito ya fara daura alwalar magriba,bai kammala ba innar ta fito tana daura dankwalinta "denattoi ɗa himu(yaushe ka shigo himu?)" Ta fada tana dubansa,ita din duk da bafullatsna ce amma sam ba ruwanta da wannan kunyar da kaara tadan fari "Ban jima ba,na leqo na samu kina bacci,ya jikin naki?" "Alhamdlh,nasha ragowar maganin nan daka taba kawomin kwanaki kafin na kwanta,kaga kuwa har ya fara sakina" "To alhmdlh,hammiyami jula miwarta(bari nayi sallah na dawo)" ya fada yana warware hannun rigarsa,a bakin kofar shigowa gidan sukayi kacibus da qannensa,yammata masu tasowa su biyu,yace maza su shige gida an fara kiran sallah,suka amsa masa amma suna binsa da.kallo,saboda labarin da suka samu a kansa tun a hanyarsu ta isowa gida. Bayan sallar isha'i ya shigo gidan,babu kowa tsakar gidan sai yuuma dake zaune daga bakin kofar dakinta ita daya,gabanta fitilar aci balbal ce,sai qaramar redio da bata rabo da ita saboda jin labarai,sannu da gida yayi mata,ta amsa masa tare da shaida masa abincinsa na wajen innarsa,ya amsa mata yana wucewa kai tsaye zuwa dakin innar,bayajin dadin yadda wasu lokuta safiya da zubaida ke barin yuuma ita kadai,duk da lokaci lokaci zaka samesu wajenta,yana matuqar jin tausayinta,saboda rashin haihuwa abune mai ciwo da kuma sanya mutum cikin kewa da kadaici. Da sallama ya shiga dakin,ya taras dasu sunata hira abinsu dukkansu,safiya zubida da sadam qaramin qaninsu,sannu da xuwa sukayi masa,ya samu waje yana zama "Ra nyam kima,hokkumoki sadam(ga abincinka,sadam mika masa)" inna ta fada,sai sadam din ya mika masa,yaja kwanon ya bude ya fara ci bayan yayi bismillah,ba qaramin son tuwon yuuma yake ba,bama shi kadai ba,hatta da jama'ar gidan,saboda yadda ta iya girki,duk da innar tasa ma ba baya bace. A hankali yake cin abincin yana kuma jefa baki a hirar tasu,saidai fiye da rabin hankalinsa nakan ta yadda zai gayawa inna maganar dake bakinsa,a qa'ida da yuuma zaiyi zancan,amma ya sani idan yayi hakan ransa ne xai baci wajen innar,saboda batason hakan,tafiso kowace magana suke da ita su sameta kai tsaye su shaida mata,itama yuuman tunda ta fuskanci haka,da sunzo sun gaya mata zata ce "Kun gayawa innarku?" Idan sukace a'ah,takan ce "Ku sameta ku fara shaida mata muji abinda xata ce". Sai da ya gama cin tuwon tas ya wanke hannu sanna ya gyara xamansa cikin jin nauyi da kunya yace "iwodi haala kaginmi gaɗen Inna....(akwai maganar da nakeso muyi inna)" "Shine tun daxu kaketa wani mutsu mutsu ka kasa gayamin?,tawi'aayanka,mojetta bi'owaka(idan baka gayamin ba wa zaka gayawa duk duniya?)" Ta qarashe da sigar tambaya tana kafeshi da idanu,yasan me take nufi,sai kawai yayi murmushi yana cewa "Babu" "iminamma(ina saurarenka)" dan jim yayi kadan sannan yace "Inna.....na samu yarinyar da nakeso fa". Zuba masa idanu tayi saboda yadda maganar tazo mata a bazata,bata tsammaci jin maganar ba a wannan lokacin,saboda tuntuni tana da tsari da kuma muradi a kansa,amma duk da haka saita danne wannan a ranta,tace dashi "Emi namma,immoi 'onni?(ina jinka,wacece?)" Kansa yadan shafa kadan sannan yace "Sunanta maimunatu" "Maimunatu ta gidansu laulo" muryar zubaida ta ratsa hirar tasu,da hanzari inna ta juya tana duban zubaida saboda yadda maganar zubaidan ta dauki hankalinta,yayin da himu shima ya juya yana kallon zubaidan saboda baisan waye laulo din ba,saidai idan ita dince yaji dadin yin maganar da zubaidan tayi,saboda baisan ta yadda zai kwatantawa innar ita ba yadda zata fahimta "Da gaske ita kake nufi himu?" "Gidansu na kusa da hanyar fegin maraba" mummunar faduwa gaban inna yayi,tabbas maimainunatun ya hango,take hankalinta yayi mummunan tashi,maimunatu 'yar uwa ga gaje?,gaje dai 'yar inna furaira "Yuuma.....yuuma.....warnano wakka haala kawela(zo kiji wani mummunan labari)" ta fara qwalawa yuuma dake xaune qofar dakinta kiran,abinda ya sanya himu zubawa innar idanu cike da mamakin meye ya gigita innar tasa haka?,har take irin wannan kiran?. "Ku tashi ku fita" innar ta fada tana waiwayawa gasu safiya dake zaune tun dazu suna kallon kallon a tsakaninsu,tsam suka miqe suna masu ficewa kowacce bakinga fal da magana,dai dai sanda yuuma ta shigo dakin a rude "Lafiya kuwa?" Ta tambayi inna tana laluben wajen zama hankalinta a tashe,sai da inna taja wani dogon numfashi mai nauyi ta furzar da iska sannan tace "Yaron nan ne yakeson dauko mana jaraba rana tsaka" sake tashi hankalin yuuma yayi tana duba inna tace "Subhanallahi,jaraba wacce iri?" Kai inna ta gyada cike da jin xafi tace "Wai yarinyar nan maimunatu ya gani yakeso?" "Maimunatu?....maimunatu?" Yuuma ta maimaita sunan tana son tuna aka wace ake magana "Diyam ta gidansu laulo" take yuuma ta fahimta,sunan kuma ya fado mata a rai,saboda ita daya keda sunan kaf rugar,hakanan kuma mahaifiyarta kadai ke kiranta da sunan,sai ta sauke ajiyar zuciya,alamun tashin hakalin da ya taso tun daga zuciya zuwa fuskarta ya fara zagwanyewa "Hankalina ya tashi sosai innar sadam,na dauka wani abun tashin hankalinne" "Yo akwai tashin hankalin da yafi wannan yuuma?""ai abinda yasa nace haka innar laulo.....kaf fadin rugarnan anyi ittifaqi babu yarinyar dake da nutsuwa da kuma kamun kai da tarbiyya irin maimunatu....." "Amma kinfi kowa sanin ainihin wacece ita ko?" "Wannan duk camfi ne ko ince hasashe....duk cikin masu hasashen babu wanda yake da tabbas kan abinda yake fada koda kuwa a gaban Allah ne,dukka abinda al'umar rugar nan keyi ba komai bane illa jahilci zalla da kima gurguwar fahimta gami da mummunan zato,koda ba zato bane hakanne,babu wanda ya taba kama maimunatu da wani mummunan aibu da za'a qita,a karan kanta maimunatu bata da wata matsala ko illa....." Idanu inna ta zubawa yuuma,a hankali a kuma sanyaye tace "Yuuma...kodai don bake kika haifi himu ba kike qoqarin wanke maimunatu gami da kore kowanne aibu daga gareta?" Ba yuuma kawai ba,hatta da ibrahim sai da maganar ta tabashi,qas yayi da kanshi yana jin babu dadi a ransa,yayin da yuuma ta rintse idanu,maganar tana sauka saman zuciyarta da wani irin dafi mai zafi,dai dai maganar take da saukar mashi saman zuciyar tata,duk yadda take zaman kawaici da innar laulon....bata taba gwaba mata magana me zafi akan yaranta ba irin wannan "Kaico!....kaico!" Yuuma ta fada tana girgiza kanta "Inama ace Allah ya bani d'a na cikina wanda yakai shekarun ibrahim....kai koda ace bai qarasashi ba,matuqar ya isa a daura aurensa,da ba shakka na tabbatar miki da cewa magana nake Miki da zuciya daya.....Allah ya kyauta,kiyi haquri bisa shishshigin da nayi miki" yuuma ta fada bayan ta yunqura ta miqe,zuciyarta na wani irin tafasa,wanda tana fita qofar dakin hawaye ya silalo mata. Shuru ne ya ratsa dakin na wucin gadi,cikin ranta innar laulo tana jin kamar bata kyauta ba,wata zuciyar kuma na gaya mata daidai ne abinda tayin,zallar mugunta ce kawai tasa yuuman bada wannan shawarar a gaban himun,bayan tasan kowa gudu da qyamar yarinyar yakeyi,ko ita bata sake ganinta tana hulda da yarinyar ba "Amma inna abinda kika yiwa....." "Kaga dakatamin" inna ta tsaida ibrahim dake Shirin nuna mata rashin dacewar abinda tayin "Kada kace min komai,maganar maimunatu kada na sake jinta a bakinka,domin kuwa ba kai ba,koda wanda na isa na gaya masa yaji ne bazan bari ya aureta ba,bare kai dan cikina,bama maimunatu ba,banason ka sake kawomin maganar kowacce yarinya,na riga na zabar maka matar aure tun shekarun baya.....kaje gidansu maimunatun ka nemi gaje ku dai daita". Tsaf kwanyarsa fa birkice,ta yaya zaizo da maganar maimunatu inna ta umarceshi da auren gaje?,gaje dai da ya sani?,ya akayi suka zama 'yan gida daya ita da maimunatun?,babu kama ta siffa ko dabi'a ko qanqani a tsakaninsu,wanne aibu ne ma wai da innar ke magana a kai da har zai zama hujjar raba sabuwar tarayyar da yanzu aka fara kiwonta tsakaninsa da maimunatu?. *FREE PAGES ZASU KARE NE ZUWA GOBE IN SHA ALLAH,ZAKI IYA BIYAN KUDINKI TA WADAN NAN HANYOYIN* Hafsat umar kabir 2270637070 Zenith bank *Saiki tura shaidar biya ta nan* 07040727902 *Idan katin mtn ne kuma zaki tura ta nan tare sa shaidar biya* 09134848107 *Thanks for choosing zafafa biyar* *_GURBIN IDO_* *LAST FREE PAGE 05* *AREWA BOOKS::HUGUMA* Cikin kwanakin da suka biyo baya gaba daya kusan rabi da rabi na dawowar maimuntu daga kiwon ibrahim ne,wasu lokutan yakanyi gaba wani lokaci kuma tana biye dashi a baya,har sukai gida,ya tayata daure na daurewa ko sharar wajen idan bata samu tayi ba,sudan taba hira sannan ya wuce zuwa gida. Duk da cewa fiye da rabin hirar shi kadai yake abarsa,na maimunatun baya wuce eh ko a'ah. Haka kawai fa tsinci kanta da jin dadin tarayyarsu ita dashi,sai takejin wani canji na zuwa ma zuciya da rayuwarta,gaba daya wannan kadaicin babu shi,tana jin kamar ta samu wani bango da zata raba ko ta jingina dashi ko yaya yake,sabanin daa da bata da wanda zai magana da ita,magana da ake kirame dadi,idan taji magana daga bakin wani to fada ne,idan taji hira akanta to ta tsangwama ce,wani lokaci takan jima kwance duk sanda taje bacci,tana tuno irin hirarrkinsu da ibrahim,wani abun takan saki murmushi ne ta kuma juya ta gyara kwanciyarta. Ta bangaren ibrahim din wani matsayi na musamman yakeji maimunatu na sake damu cikin ruhi da zuciyarsa,a dan zamansu ya fahimci abubuwa masu tarin yawa tattare da ita,ta banbanta qwarai da duka yaran rugar tasu,tana da wata irin nutsuwa da fasahar magana wadda ya jima baiga irinta jikin wata 'ya mace ba,komai nata na hankali ne da sanin ya kamata,yakan zauna yana kallon yadd take iya controlling dabbobinta da baki kawai ta hanyar basu umarni,lokaci dai daiku ne takanyi amfani da sandarta wanda xaiyi wuya ma kaga hakan. Yadda take tausayin dabbobin kamar 'yan adam,bayan dukka alamu sun nuna sun fita samun gata da kulawa,duk da har yanzu bata taba bude baki tayi masa wata magana data shafi gidansu ba,yadda take communicating dasu kawai abun burgewa ne,duk da shima cikakken bafullace ne amma ba kasafai yake ganin hakan ba,lokuta da dama idan ya tsokanetan saidai tayi murmushi kawai,wanda kusan wannan din dabi'arta ne. Ko sau daya himu baiyi nufin zuwa ga gaje ba kamar yadda daada ta buqata,wani lokaci ma sai ya rako maimunatu yake tunawa da batun,saidai yana ganin ba abu bane mai yiwuwa,yana da tabbacin komai zai daidaita da zarar bappansa ya dawo,wanda ya qara kwanaki kan wadanda yace zai dawo,saboda jiran haduwar kudadensa dake hannun mutane. **************Yammacine lis,wanda yake busa wata ni'imtacciyar iska me dadi,yanayi ne da ya yiwa halittu da dama dadi,bawai ga dan adam kawai ba,hatta da sauran tsirrai da kuma dabbobin daketa kai kawo suna kiwo a farfajiyar wajen da ya zame musu wajen yini. Daga can qasan bishiyar idan kakai kallonka wajen,bafullatana maimunatu ce cikin baqin saqinta,zaune saman koren hiramin da himu ya shimfida mata,shi kuma yana zaune daga gefanta saman wani dan mulmulallen dutse da bai cika girma ba. Murmushine ke fita daga saman fuskarta,murmushin da kana kallonsa kasan kunyace cike dashi,ko a iya zamanta idan ka.kalla da kyau kasan a takure take,hannayenta sarqafe cikin juna tana kallonsu,yayin da shi kuma ibrahim ya zuba mata dukka idanunsa yana jiran amsar tambayar daya jefa mata. Wani irin nauyi ibrahim din ke aza mata duk lokacin da ya zaunar da ita irin haka yana karanta mata kalaman soyayya......daga qarshe kuma a yau din ya tirketa kan lallai sai ta furta masa da bakinta tana sonshi,saboda bai taba jin hakan daga bakinta ba. Wani abune kuma ita din da bata jin zata iya gaya masan,kalma ce data ji ta girmi kanta matuqa,koda baya kallonta ba zata iya fada ba,bare yadda yake zaune yana kallonta. ,sirara kuma jajayen labbanta ta motsa a hankali "midelli...yamma tayi" dauke idanunsa yayi daga kanta yana murmushi,duk da yasan yau din sun gota lokacin komawarsun,amma tayi hakanne don ta kaucewa tambayarsa,yana mamakin kunya irin tata kawaici da kuma kamewa,sai ya miqe kawai ya dauki sandarta da a yanzun shike amfani da ita idan zasu koma gida. Kamar ko yaushe ya tayata suka kammala komai,yayi tsaye daga jikin wata rusashiyar bukka dake daura da wajen yana dubanta cikin murmushi "Shikenan,tunda ba zaki bani amsa ba maimunatu zan tafi,sai jaaango?" A kunyace tayi murmushi tana kauda kanta gefe daya,ya sauke qafarsa da ya harde waje daya ya fara takawa a hankali yana barin wajen "Ka gaida gida" ta fada cikin siririyar muryarta da ba kasafai ya fiya jinta ba,sai daya waiwayo cikin jin dadi ya kalleta yana jinjina kai sannan yaci gaba da takawa,hakanan taji kunya ta kamata,abinda yasa ta juya da sauri da nufin shigewa zuwa shiyyar da dakunansu suke. Saidai kuma cak ta tsaya,saboda ganin inna tsaye daura da ita,da alama taji komai ta kuma ga komai. Kallon da innar kawai ta tsareta dashi ya sanyaya mata gwiwa ya kuma sanya mata fargaba me tarin yawa,gabanta ya fara faduwa da wani mugun qarfi,duk da haka ta ari dakiya taci gaba da nufar inda innar ke tsaye tana ci gaba da kallonta "Immoi'onni?(waye wancan?)"innar ta fada a tsawace cike da tuhuma da kuma zargi,yanayin yadda tayi mata maganar ya jefa tsoro a zuciyar maimunatun,ta qanqame jikinta waje guda,tana jiran jin saukae duka daga wajen innar,don wannan din ba sabon abu bane a wajenta "Tambayarki nakeyi waye wancan din?" "Sunansa ibrahim.....ya tayani qaraso da dabbobi gida ne" "Meye hadinki dashi?" Inna ta sake tsareta da tambaya,saboda zargin da ya shiga ranta,taso taha fuskarsa amma kuma haqarta bata cimma ruwa ba,saidai batajin wanda take tunani dinne,don bata da shakka akan alqawari da yarjejeniyar dake tsakaninsu "Babu komai" ta amsawa innar kanta a qasa,tana matse hannayenta waje guda,tana jin yadda zuciyarta ke ci gaba da bugawa fat fat "Yauwa.....gwara ki rufawa kanki asiri,ke ta buɗeri ce,shi daya zai iya rufa miki asiri ya aureki,don haka kada ma ki batawa kanki lokaci ki yaudari kanki kice zaki saurari wani,kaf fadin karkarar nan bana jin akwai wanda zai iya daukarki idan bashi ba,koda an samu to yayi miki qarya,saboda haka ki kiyaye" daga haka tayi gaba zuwa garken dabbobin,tabi tana dubasu daya bayan daya tana kuma irgasu kamar yadda ta saba duk sanda maimunatun ta dawo,kai zaka zaci tana duba kaya data bawa qasurgumin barawo ajiya ne. "Wuwuɗandu(ki share wajen)" ta bata umarni tana fita daga garken tayi gaba abinta,duk yadda takai ga gajiya hakanan dole babu yadda zatayi haka ta laluba kayan sharar ta fara gyaran wajen,duk da cewa a dazun kafin su tafi ta gyara wajen,batasan me ya bata wajen hakan ba,duk da tasan ko ba yaro idan innar taso bata wahala,zata qirqiro mata aikin ko kuma wanda yayi kama dashi,duk dai don kada ta huta,bata qaunar ganinta a zaune ko da na minti daya ne. °°°°°°°°°°°°°° A nutse yayi sallama cikin rumfar innar yana yafe da koren hiraminsa,dawowarsa kenan daga sallah sadam yace masa innar tana kiransa. Abinda ya bashi mamaki shine ganinta da yayi a tsaye tana kai kawo daga wancan bangon zuwa wannan,idanunta dake cike da fushi ta daga ta dubeshi,ba tare data amsa sallamarsa ba kai tsaye tace dashi "Joɗa(zauna)" kasa zaman yayi,sai ya duqa daga gefe kawai yana kallonta,ta tako gabansa a hankali tana dubansa "Inaso naji bayan ni wace mahaifiyar kake da ita?" Sosai tambayar ta bashi mamaki,har ya tada kai yana dubanta sosai kafin ya kauda kansa ganin itama shi take kallo,yaro ne shi mai tsananin biyaya,don haka bazai iya hada idanu da daadan ba "Babu daada....amma wani abune ya faru?" Sake baci ranta yayi "Ni kake tambaya wani abune ya faru himu?,ashe ni ba uwarka bace?,ashe ban isa na gaya maka magana kaji ba?,tun a waccar ranar ban rabaka da maimunatu ba?,ban gaya maka babu kai babu ita ba?,shine kasa qafarka kayi wancankali da maganata akan diya mace saboda bani da wani muhimmanci a wajenka?" "Ba haka bane inna..." "To yaya ne?" Shuru ya gifta wanda bai gaza qasa da second hudu ba ".......ko kuwa maganar yuuma ce ta shiga kunnenka fiye da tawa ni mahaifiyarka?" Girgiza kansa yayi da sauri "Ko kadan.....kada ki saka sunan yuuma don Allah daada,ba ruwanta,batasan me akeyi ba tun wancan ranar data fita a dakinki" "Ibrahim!" Ta kirayi cikakken sunansa,abunda ya sake tabbatar masa zata yanke tsatstsauran hukunci ne,kuma kowanne irin hukunci ne hakan zata fadeshi ne ba da wasa ba "Daga yau.....idan ka sake ka sake zuwa inda maimunatu take Allah ya isa ban yafe maka ba,sannan koda bayan raina ka sake ka aureta ban yafe maka ba" qarasa zama dirshan yayi a qasa maimakon tsugunon da yayi,ba qaramin kaduwa da hukuncin nata yayi ba "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya dinga maimaitawa kansa a qasa,bai taba zato ko tsammanin hukuncin innar zaiyi tsaurin haka ba "Don Allah inna ki sassauta kiyi haquri,maimunatu bata taba yi miki komai ba,banda......." Tsawa ta dakeshi tana katseshi "Banason na sake jin komai daga gareka,wannan shine hukuncina na qarshe,tashi ka fita!" Ta fada a zafafe tana nuna masa qofa,sai da ya dafa qasa sannan ya miqe "Himu" ta kirashi sanda yakai qofa "Na baka kwana hudu kacal,ka shirya fara zuwa wajen gaje kamar yadda na gaya maka,umarnine nake baka" bayajin xai iya cewa da ita komai,don haka kansa da yayi masa nauyi kamar ya dauki kaya ya gyada mata sannan ya fice daga dakin yana jin jikinsa kamar zazzabi na shirin rufeshi. **********Sake juya rufaffen takalmin danqon hannunta tayi don ta tabbatar dabarar data yi masa zata kaita gida,ita kanta batasan adadin liqin data yi masa ba,wani gurin da garwashin wuta da leda,wani gurin kuma tana samun zaren lilo ta zarge inda yake shirin rabewa dashi. A hankali ta duqa ta ajjiye takalmin a qasa ta zura qafafunta,tadan motsa qafar ta tabbatar yayi,sai ta sauke ajiyar zuciya,tana godewa Allah da ya sake fiddata a yau dinma dai still,takalmin bai mata tutsu ba,batasan ya zata kasance mata duk randa hakan ta faru,itadai shi daya ta sani a matsayin takalmin da take dashi,wanda ita kanta batasan adadin kwanakin ko shekarunsa ba a duniya bare ta iya tantancewa. Sake waiwayawa tayi hagunta da damanta,har yanzu bata debe tsammani da ganin himu ya bullo ba,duk da cewa lokacin zuwan nashi ya gota sosai,tana da tabbacin babban abune ya tsaidashi,saidai tana fatan koma meye ya kasance yana lafiya qalau. Waiwaya tayi sashen wata saniya ke zaune,gefanta jaririn san data haifa ne a dazu jimawa kadan bayan isowarsu wajen,ta tabbatar inna batasan cikin ya isa haihuwa ba,da ba zata bar mata ita zuwa wajen kiwo ba,dole idan lokaci yayi himun baizo ba,haka zata hada da kula da sauran dabbobin,da ita wannan sabuwar haihuwar su wuce gida,yau din tana jin gajiya sosai a jikinta,ita kadai cikin wajen,cikin tsoro da fargaba saniyar tahaihu a wajenta,wanda ita kanta tasan babbar kasada tayi,saboda samuwar matsala ta mutuwar uwar ko abinda aka haifa,dai dai yake da samuwar matsala cikin tata rayuwar,ko daya innar batasan wata aba wai ita asara ba bare haquri da ita idan ta sameta,haka ta dinga kai kawo har haihuwar ta kammala. Saman dan dutsen da himun ke zama ko yaushe idan yazo ta koma ta zauna,idanunta nakan abun hannunta na shirin duwatsu green da jaa,tasa yatsanta guda daya tana wasa dasu,ta warasu wani lokacin ta hadesu,tana tuna lokacin da innarta ta zura mata su,har yanzu lokacin yaqi bacewa cikin idanunta. Ta jima zaune a nan,tana jin wata kewa da kadaici suna shigarta,lokaci lokaci tana daga kai ta dubi yanayin yadda dabbobin ke kai kawo sannan ta sake maida kanta. Karo na qarshe data daga kanta ta tabbatar lokaci yayi da ya dace su koma gida,ta sauka daga kan dutsen a hankali,ta gyara zaman hularta sannan ta dauki sandanta ta fara ratsawa ta tsakaninsu tana hada kansu. A gaba take sanyasu mafi yawancin lokuta,idan taga zasu canza hanya ko zasuyi wani abu ba dai dai ba takan tsawatar musu,suna ji kuma suna fahimta yawancin lokuta,yau dinma haka ne,hannunta na dauke da sabuwar haihuwar da daya daga cikin shanun tayi. A hankali baqaqen lafiyayyun motocin guda biyu ke kutsowa cikin rugar,tana haura duk wani tudu da kwari da kuma kwazazzabo dake kan hanyar ba tare da mutanen dake ciki sunji komai wata jijjiga ko wahala ba da ire iren wadan nan hanyoyin ke dashi a duk sanda mota zata ratsasu ba,hakan ya faru ne sanadiyyar kyau da lafiyar motar,wanda hakan yake da nasaba da irin tsadar da kowacce mota guda daya ke da ita. Motar farko mutum hudu ne a ciki,driver salmanu,sai wani zaune a gefansa hayatu,daga seat din baya kuwa dattijuwar macace,hakimce cikin shiga ta alfarma,kyakkyawar lallausar blueblack din atamfa ce wadda tayi matuqar haska farar fatarta,duk da akwai tsufa tattare da ita,amma yanayin da take ciki na hutu da kuma jin dadi ya hana bayyanuwar tarin shakarunta,daga shekara sittin da takwas,ya maidata zuwa 'yar shekara hamsin,idan ka cika qwaqwafi kuma ka qara mata da uku,hankalinta na ga window din motar,tana duban hanyoyin da suke wucewa,wanda sukanyi gamo da mutane jifa jifa,duk mutumin da suka gifta sai ya bisu da kallo,saboda abune baqo a wajensu,zasu iya irga sau nawa suka samu labari ko sukaga shigowar mota rugar tasu,wasu sukan cika da fargabar su waye suka shigo musu?,wasu kuma kyau da motar ke dashi ne yake daukar hankalinsu har sai tayi nisa ta bacewa ganinsu. Daga gefan dattijuwar kuwa kyakkyawar matashiyar budurwa ce wadda duka duka ba zata haura shekara ashirin ba a duniya,shigarta kadai zai gaya maka cewa ta fito daga gidan ilimi wayewa da kuma wadata,kacokam ta tattara hankalinta ga wani littafi dake da shafuka masu dan dama,da alama nazari takeyi. "Salmanu........saukemin gilashin nan.....naga alama wannan baqin abun da kuka lafta masa bazai bar idanuwa suyi kallo yadda ya kamata ba" ta fadi tana hade gira. Karaf matashiyar ta daga kanta daga kan littafin "Haba anni....me kuma za'a sauke miki kiji?,an kunna ac ne fa,ta yaya za'a sauke glass,kuma ta hakan ma ai ana ganin komai,tunda ba dare bane" harara ta juyo ta watsa mata "Ke....kiyi ta kanki,ni ba dake nake ba,toke da wanne mataccen idon ma kike iya gani daga nan din?,idon da komai za'ayi saida gilashi?,salmau zaka saukemin ko kuwa?" "Za'a sauke anni" yayi maganar yana sauke mata da hanzari kamar yadda ta buqata. Sai da aka sauke mata gilasan tas sannan ta sake matsawa jikin window din tana fara'a "Yawwa,yanzu naji batu,amma daa an qunshe mu kamar 'yan kidnapping,ni ba baqin hali gareni ba da kullum xan fita zance a rufeni cikin gilasai" sarai matashiyar ta fahimci da ita take,kuma idan da sabo ta saba ko kuma tace sun saba da halin anni,duk wanda ke zaune da itama ya riga da yasan halinta sarai,don haka sai ta maida mayafin da yake kafadarta zuwa saman kanta,ta kuma rufe littafin saboda hasken ya mata yawa,karatun bazai mata dadi ba ta maida jakarta,ta ciro wayarta a maimakon littafin ta soma qoqarin kunna data,saidai yanayin rashin network mai kyau ya hana wayar tata amfani,dole ta maidata itama jakar. "Ma sha Allah,kai ma sha Allah,lallai na jima rabona da adamawa,wai" anni keta fadi,fuskarta na nuna alamun jin dadin tafiyar sosai. A dan rude maimunatu ta maida hankalinta ga marabar hanyar da shanunta ke tsallakawa saboda jin wani sauti,hango motocin suna tahowa yayi matuqar daga mata hankali,na farko yadda zata tsaida dabbobin da sukayi nisa da tsallakawa ta bawa motocin dama su wuce,na biyu kuma motocin sunyi matuqar sanya mata fargaba da tsoro kamar yadda suka sanyawa mutanen da suka baro a baya,su waye a ciki?,me sukazo yi cikin rugar tasu?,wadanne irin motocine wadan nan da sam bata taba ganin koda me shigen kamarsu ba?. Yadda suke sake kusanto inda suke ya sanyata yunqurawa da hanzarinta ta fara bawa dabbobin nata umarni da dukka salon da tasan suna iya karbar umarni da hani daga gareta,tanayi tana kutsawa ta cikinsu tare da dan daga muryarta. "Kai salmanu......dakata" anni ta fada da sauri,idanuwanta suna sauka akan maimunatu,sosai ta zuba mata idanu cike da mamakin yadda take iya bawa dabbobin umarni da baki take kuma iya sarrafasu ba tare da takai duka ma ko daya daga cikinsu ba,idanun anni ya sauka ga dan qaramin dabbar dake hannunta,fari qal dashi sabuwar haihuwa,abinda yaja hankalinta kenan zuwa ga garken dabbobin,ta dinga binsu da kallo daya bayan daya "Ma sha Allah,wadan nan dabbobin gaskiya na qwarai ne,sun samu kiwo da kulawar data kamata" "Abinda nake fada a raina kenam hajiya yanxu hajiya,babban abun mamakin yadda qaramar yarinya kamar wannan take iya kula dasu gaba dayansu" cewar hayatu shima idanunsa akan maimunatu "Bari hayatu,kaga inda ake mata,ba irin 'ya'yanmu ba cima zaune da komai suna zaune ake musu" anni tayi maganar tana tabe baki. Dariya ce taso qwacewa matashiyar amma ta danneta,sai murmushi da ya fita a fuskarta,yayin da hayatu da kuma salmanu suka dan dara kadan,saboda sunsan da wadda take,a tsakaninsu suka dinga tattaunawa,har zuwa sanda maimunatu ta ratsa ta gaban motocin suka wuce da dukka dabbobin,tana dan duba da kuma waiwayen motar tana mamakin yadda suka dakata mata suka bata dama ta wuce. Ajiyar zuciya ta sauke me qarfi bayan data tabbatar sun tsallake lafiya,abinda ya taba faruwa da ita shekarun baya bai sake maimaita kansa ba,wanda ita daya tasan bala'i da masifar daga fuskanta a sannan,har yanzu tana iya tuna sanda motar ta taho a guje,bata kuma damu data tsaya ba ganin dabbobi suna qetarawa,tana hango sanda motar ta banke dan dalonta da take matuqar ji dashi,ya zube a qasa jini na fita ta hanci da bakinsa,ta bishi da gudu ta tsugunna a gabansa tana kuma saboda ta tabbatar bazai tashi ba,taji mugun cin birkin da motar tayi,da fadan da wata murya ke mata tsaye a saman kanta,fadan da yafi kama da a dakeka a hanaka kuka saboda cikin xafi da fadar maganganu marasa dadi ake yinsa,abinda ya sanyata daga kanta ta dubi.mai maganar. Kalmomin da zata gaya masa masu zafi take nema amma ta rasa,saboda ita din ba gwanar rashin kunya bace,bata ma iyata ba sam,to dawa zatayi bayan dabbobin sune qawayenta?,abu na qarshe da take ganin xata iya shine watsa masa harara gami da tsaki mai nauyi,kafin ta sauke kuwa aka sauke mata wani zazzafan mari da ya sanya wuta ta dauke mata gaba daya,ta daina gane komai,bata tashi dawowa hayyacinta ba sai bayan wani lokaci. Ko a yanzun data tuna sai data runtse idaunta,tana tuna zafin marin saman fuskarta,abinda ya biyo baya kuwa ta gefan inna azaba ce ta cita mai yawa,bata damu da yadda fuskarta ta tasa ba saboda marin data samu akan abinda ita ke da gaskiya,ta tattara laifin gaba daya a kanta,tare d adora alhakin mutuwar dan maraqin saniyar a wuyanta. Ajiyar zuciya ta sauke sanda suka iso gida,kamar kowanne lokaci ta daga murya ta sanarwa innar ta dawo,bata ajjiye dan jaririn a hannunta ba sai data qaraso ta miqa mata shi,bakinta har kunne,kai kace jika aka haifa mata na dan mutum "Dama kinsan ta kusa sauka amma baki garzayo kin kirani ba?" Innar ta fadi haka cikin tuhuma,bata amsa mata da komai ba,itadai tana duqe tana daure wasu akuyoyi,banda abu irin na dan adam,ta samu uwa da dan lafiya,bata damu da yi mata sannu na wahalar datayi da naggen ba har ta sauka lafiya,ta buge fa tuhumarta,wanda tayi imani cewa inda ta barta a can ta taho kiranta wani abu mummuna ya faru,lallai ba zata daga mata qafa ba. Tunda taji maimunatun tayi shuru tasan ba zata tanka mata ba,ita kanta ta santa da wannan halin,a wasu lokutan idan tayi mata irin hakan,yaxo akan gabar da take cikin fushi ko takejin haushinta,kamata take ta nada yadda ranta yayi mata suga. *Daga yau free pages sun qare,paid pages zasu biyo baya in sha Allah,hanzarta biyan naki kudin koki bibiyemu ta shafukanmu dake arewabooks* ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 *06* "Alhmdlh" anni ta furta sanda motocin suka faka a qofar ginin gidan bappa labaran,mahaifi ga ibrahim,qafafunta ta zuro qasa tana fadin "Hasbiyallahu la'ilaha illa huwa alaihi tawakkaltu wa huwa rabbul arshil azim" kana tayi bismilla ta yunqura,gaba daya qafafuwanta sun riqe,jikin tsufa ga kuma zaman mota "Salmanu ku jirani,idan mun gama gaisawa inajin tare daku zamu fita can cikin gari na duba masauki" cewar matashiyar,dakatawa da tafiyar da anni keyi ta waiwayo tana yamutsa fuska "Laila....me naji kina fada?,au dama ba rakiyar Allah da ma'aiki kika yimin ba?" Shaf ta manta da annin tana jinta,fuska tadan kwabe "Kuma me nayi anni?,duk wannan dawainiyar?,ina cewa flight zamu bi kikace kefa sai mota,amma ban fasa rakoki ba" "Yo rakiyar banza da wofi?,tunda ba zaki iya kwana a gidan ramatu ba" hannayenta laila ta hade waje daya "Shikenan,zan kwana abar maganar" don sarai ta sani mitar annin ba abu bane me kyau ko dadi ba,duk da hakan taci gaba da takawa zuwa cikin gidan tana ci gaba da mitar,ta dauke kanta tana sake ajiyar zuciya,idanunta na sauka ga yaran da suka fara baibayesu suna kallonsu,sannan ta dubi su salmanu "Kuyi tafiyarku kawai,amma ina buqatar ruwan sha" "Akwai ai za'a samu" yahaya ya amsa mata,sai ta juya tana bin bayan anni zuwa cikin gidan. Dai dai lokacin da yuuma ke qoqarin daura alwalar sallar magariba,wadd ta saba duk lokacin da tayi girki ta kammala,tana hadawa da alwalarta sanna ta wuce daki. Cikin mamaki ta ajjiye butar data gama zubawa ruwa ta waiwayo da hanzari jin muryar annin "Yafendo?,yafendo yau kuma ni kika tuna?" Yuuma ta fada cikin madaukakin farincikin da ya kasa boyuwa a fuskarta,kana ta kasa jiran qarasowa anni,ta taka da kanta ta cimmata a tsakiyar gidan "Nice rahama,yau dai Allah ya qaddara ganawarmu,kimin aikin gafara" anni ta fada tana kama hannun yuuma,murmushi ya kuncewa yuuman,ta shiga marabtarsu,dai dai sanda aka fara shigowa da kayan amfani na abinci,wanda ya zamewa anni kamar ibada duk sanda zata ziyarcesu,takan sauke musu kayan abincin da sai su kusa shekara basu qare ba,mota biyu takeyi,daya ta kayan abinci,daya kuma wadda zata taho a cikinta. Hajiya maryama wadda ake kira da anni,tamkar uwa take a wajen yuuma,saboda da ita da mahaifiyar yuuman 'yan mata zarr suke,'ya'yan yaya ne(namiji) da 'ya'yan qanwa,kakanninsu daya,a turance ake cewa(cousins),tun zamanin yammatanci akwai shaquwa sosai tsakanin anni da mahaifiyar yuuma,uwa uba sunansu daya,maryam da maryam,kakan yuuma asali dama bafullacene,mazaunun ruga,koda ya tashi aurar da diyarsa maryam saita auri jinsinsu,mahaifiyar yuuma a ruga tayi aurenta kamar yadda ta taso a nan,yayin da daya maryam din anni tayi aure cikin gari itama kamar yadda ta rayu a nan,saidai duk da hakan zumuncinsu bai yanke ba,duk sanda dama ta samu suna ziyartar juna su da 'ya'yansu,har zuwa sanda suka fara tara zuri'a,rayuwar mahaifiyar yuuma batayi tsaho ba Allah ya karbi abarsa,a sannan duka duka yuuma din bata wuce shekara sha biyar ba a duniya,sosai anni taso ta riqe yuuma ta kuma aurawa danta na fari,saidai kuma mahaifin yuuma yaqi bada ita,saboda ita daya ce 'ya mace a wajensa,dole ta haqura,taci gaba da kulawa da ramatu(yuuma) da kai mata ziyara har zuwa sanda aka aurar da ita ga bappa labaran,ita ta yiwa yuuma komai kamar diyar cikinta,saboda ita dinma Allah bai bata diya mace ba,sai maza da take dasu guda hudu. Tun daga sannan takan ziyarci yuuma akai akai,ramatu yuuma ta zama 'yar gata,batayi kukan rashin mahaifiya ba ko kadan,saboda anni ta tsare mata komai,bata da matsala ta kowanne fanni na rayuwa,tun daga sutura zuwa cima,ko yaushe anni naka hanya wajen yo mata aike koda bata zo ba. Sanda shekaru suka fara tafiya yuuma bata haihu ba hankalin anni ya tashi,ta kashe kudi sosai akayita duba yuuma,saidai ba wata damuwa data nuna wadda zata hanata haihuwa bare a maganceta,daga qarshe anni taso fita da ita waje,don tana cikin sukunin rayuwa sosai annin,dukka yaranta ba wanda bai zama wani ba cikin garinsu na gombe amma yuuma tace ta barwa Allah,kome za'ayi idan haka Allah yaso ganinta ba wanda ya isa ya canza mata qaddararta,hakanan dole anni ta haqura,da kanta yuuma ta baiwa bappa labaran shawaran qaro aure,da farko yaqi amma ta matsa ganin cewa shi ba abinda ya nuna bazai iya haihuwa ba,bai kamata ta rageshi ba,daga bisani ya haqura,ya laluba ya zabo karimatu mahaifiyar himu,sanda tazo gidan itama sai data shekara biyu sannan ta samu cikin Ibrahim,bayan ta haifeshin ma sai daya kusa shekara bakwai ta haifa safiya sannan xubaida,sai auta sadam. Ramatu macace mai tsananin haquri da hangen nesa,ita kanta fureran tasan da haka,shi yasa itama take qoqarin kiyaye wasu abubuwan kada ta shiga haqqinta da yawa,saidai kuma Allah ya jarabceta da son 'ya'ya,sam bata iya yiwa kowa kara a kansu,tun daga sanda bappa yace zai dauki ibrahim ko safiya ya baiwa yuuma daadar himu ta runtse ido ta dunga diga rashin mutunci sai yuuma ta sake kiyayewa,kyautatawa da nuna kulawa da duk uwa zata yiwa danta idan ya ratso tsakaninta dasu tana musu,ta daukesu kamar yaranta,amma ta kiyaye duk wani abu da tasan zai bata ranta ko yaja musu cece kuce da furera,abunda yasa xaman nasu ya sake dadi kenan,zaman lafiya kuma ya wanzu tsakaninsu,duk da wani lokacin daadan himu kan dan taba,amma hausawa sukace idan kace wargi waje yake samu,kuma sai bango ya tsage qadangare ke samun qofar shiga,dole itama wasu abubuwan fureran ke kiyayewa. Fadin irin murnar da yuuman a yau ta tsinci kanta ma bata bakine,saboda anni tadan kwan biyu batazo mata ba,ba kasafai yuuma ke zuwa wajen anni ba,saboda bappan mutum ne mai kulle sosai,itama anni bata zafafawa saboda tasan ya tsarewa diyarta komai,yayi mata riqo na amana bai barta ta wulaqanta ba,sannan ita annin a yanzu babu nauyin kowa a kanta,sakamakon mijinta ya kwan biyu da rasuwa,don haka kafin ma yuuma taje ita taje mata. Yuuma bata dubi dare daya fara yi ba,haka ta tashi takanas ta yiwa anni sabon girki,cikin cimarsu ta fulani da tasan annin tafi so,a ranar kusan raba dare sukayi suna hira,sai gab da zasu kwanta anni tace da ita "Wajen fa labaran nazo....." "Lafiya yapendo?" "Lafiya qalau ramatu,shanu nake da buqata zan qara cikin gidan gona ta,wancan yaron hamdan naso aikowa,naga zai batan lokaci nace gwara nayi tattaki nazo da kaina" murmushi yuuma tayi,tasan dramer din anni da jikokinta sarai,takan gani idan taje musu,annin irin matan nan ne da basa daukan raini,bata da haquri akan abinda tasan kan gaskiyarta take,amma tana da matuqar kirki da kuma tausayi "Aiko dai bappansu gaba daya dabbobinsa na garin yayi kudu dasu,kwana goma yace zaiyi ya dawo kinga muna ta zuba idanu shuru,amma naji suna waya da himu yace nan da jibi ko gata zai dawo,saidai ko ki tsimayeshi,cikin rugar nan nasan zai duba miki irin wadanda kikeso din" "Kash.....kuma sai da nayi wannan tunanin,amma bari mu gani,Allah yasa ya dawo kafin na wuce,don kwana uku zanyi,ranar litinin zan koma ga likitan qafata abuja" "Har abuja anni?" Yuuma ta fada tana kama baki,baki anni ta tabe "Ina zaman zamana rigimammen yaron nan ya hadani da zirga zirga,duk kusan qarshen wata sai yasa an sakani a jirgi ba gaira ba dalili na tafi ganinsa,nace ya canzamin ya kafe,wai duk nigeri shine lamba daya.....kijimin qarya ramatu" anni ta qarashe fada tana yatsina fuska da tabe baki. Murmushi yuuma ta sake tana kada kai,tana matuqar sha'awar yadda suke kula da anni,tana jin cewa dama ace itama tana da arziqin da zata ramawa anni koda dan kadanne cikin irin alkhairanta gareta "Tunda ya fada ai hakanne anni" kashingida tayi kan lallausan katifa da bargo da yuuma tayi mata shimfida da ita "Ke rabu da shi ramatu,bokon tasu ma ta wannan qarnin tafi qarfin hankalinka,ke bakya ce sunyi muhammadiyya ba" anni ta fada tana fadawa wani tunani can,wanda har sai da yuuma ta ankara "Yanzu anni har yau baki bar sana'a ba?" Idanunta ta bude sosai tana kallon yuuma "Ramatu,kome arziqin mijinki jikoki da 'ya'ya kada ki kuskura kice zaki rabu da sana'a,duk tsiya naka naka ne,koda ba'a rageka da komai ba,amma naka yana da dadi" kai yuuma ta jinjina tana gamsuwa da zancan anni,tun tale tale anni bata saba da zaman banza ba,har kawo yau da babu abinda ta nema ta rasa,ko rai tace tana so idan ana siyar dashi za'a siya mata,amma bata daina nema ba,tana da makeken gidan gona,wanda tafi ji dashi fiye da komai nata. Tun suna hira sama sama har bacci yayi awon gaba da anni,sai a sannan yuuma ta gyara nata wajen ta kwanta itama. *_WASHEGARI_* K'arfe takwas na safe yuuma ke dosar dakin daada dauke da turamen atamfa gudu hudu a hannunta da shadda ta maza yadi goma,sai takalmi na maza me kyau wanda ta tabbatar zaiwa ibrahim. Da sallama ta daga labulen dakin daadar,safiya dake zaune tana shan kunu ta amsa mata tana gaidata,dai dai lokacin daada ta fito daga uwar dakinta tana daura zani,kafadarta saqale da hijabi. Gaisawa suka fara yi da yuuma sannan ta'ajjiye mata kayan "Gashi inji anni" "Too.....anni bata gajiya,to Allah ya amfana ya qara arziqi" daadan ta fada cikin farinciki,mutum ce dake matuqar son ka yiwa 'ya'yanta alkhairi,safiya dake shan kunu tataso itama tana daga atamfofin tare da fadin "Bara na zaba tawa kafin zubaidata iso ta dauke wadda tafi kyau......gaskiya anni nada kirki,bata gajiya" murmushi yuuma tayi ta miqe,har takusa da qofa ta juyo "Af.....niko daada nace ba,ko ibrahim ya gaya miki inda yaje ne?,tun jiya anni keta tambayarsa,kuma kamar banga shigowarsa gidan nan ba tun shekaran jiya,abincinsa ma sai da safen nan na hada a dumame" tana shirin saka hijabinta ta amsa mata "Eh.....na turashi gidan sukaina" "Sukaina?" Yuuma ta maimaita a ranta cike da mamaki,saidai ba kasafai take magana akan wasu abubuwan da daada ke yankewa kan yaranta ba "Ayyah...to Allah yasa zasu hadu,don jibi annin zata koma" "Ba lallai gaskiya,inajin sati zaiyi acan kafin ya dawo" "To ba laifi" yuuma ta fada tana ficewa,kanta ya daure tamau,sukainan yayar furera ce,bata da kirki ko kadan,masifaffiya ce ta bugawa a jarida,tana aure ne a wani qauye dake maqotaka da rugarsu,ta yaya za'a tura saurayi kamar himu gidan yayi kusan sati?,duk da itama tana da samarin yara kamarshi,amma kuma tafiyar ai ba ta radin kansa bane,kamar wani qaramin yaro?,da wannan tunanin yuuma ta koma dakinta,inda tabar anni da kuma laila wadda ke jira a kawo mata qosai da yuuma ta bayar a siyo mata,tace shi take sha'awa,tunda suka tashi da safen take jiyo qamshinsa. Suna tsaka da hira daada ta shigo a shiryenta tsaf,suka gaisa da anni sannan tayi mata godiya daga bisani tace "Zanje na dawo yuuma,ba dadewa zanyi ba" kallonta yuuma tayi cike da mamaki,ina zata da safen nan,uwa uba kuma ma kusan dokar bappa ce,basa fita unguwa a gidan matuqar ya tafi kudu irin haka sai ya dawo,kamar anni tasan tunanin da yuuman take sai tace "Labaran ya sassauta tsaurin nasa kenan?" Tayi maganar tana dariya. Kai daada ta kada fuskarta na nuna zallar damuwa "Ko daya anni,dole ta kama na fita ne,zanje na yiwa wata yarinya data nacewa himu gargadi,waye zaiso hada iri da irin tsiya irin jaraba",laila dake dan sauraron voice note na watsapp ta earpiece din dake kunnenta sai ta zareshi,ta miqe ta zauna sosai tana kallon daada,saboda yadda taji maganar banbarakwai,ita kanta anni dake rayuwa cikin tsakiyar birni,cikin ahali da muhallin da wayewa da kuma boko suka yiwa katutu sai data ji maganar bawai "Tooo....ikon Allah,to....abi a sannu dai,Allah ya maganta mana" "Ameen ameen,sai na dawo" "Allah ya kiyaye" yuuma ta amsa mata. Shuru yuuma tayi tana juya batun cikin ranta,me yasa daada take haka?,akan yaranta gaba daya idanunta suje rufewa?,yanzu Allah ne kadai yasan idan taje me zasu aiwatarwa da yarinyar,tunda ta riga data sani,innar laulo qawace kuma aminiya a wajenta,ita kanta banda ubangiji ya riga da ya qaddara tafi qarfinsu,da ba qaramar wuya zata bata ba ta hannun daadan. "Wai....nace ba" laila ta fada tana duban yuuma,sai ta maida hankalinta ga laila "Wai daada kuwa cikakkiyar bafulatana ce yuuma?" Murmushi yuuma tayi,tasan me lailan ke rayawa cikin ranta "Gaba da baya,har gwara ni innata itama ruwa biyu ce,amma ita babu sirki" Tun gabanin lokacin tafiyarta kiwo yayi yau din ta shirya,da wurwuri tayi wanka don kada innar laulo ta farga ta hanata yi,ta gyara jikinta sosai,ta kama jelar gashinta ta nannadesu tayi musu wata lanqwasa me qawanya me kyau,hatta da duwatsun kwalliya na kanta da hannunta sai data qara wasu,ta sake fita bufalatana zam. Can qasan ranta takejin cewa tana yin wannan kwalliyar ne duka saboda ibrahimu,tana ji a jikinta zaiyi wuya ace yau din baizo inda take ba,saboda yaune kwanaki uku suka cika bata ganshi ba,bata saurari wani abincin safe ba,tunda ba ita zatayi ba yau,ta cika gorarta da nono wanda ta tatsa ta barwa innar laulo xatayi aikinsa za'a fiddashi kasuwar qauyen dake maqotansu wadda take ci yau. Tun kafin innar ta tashi ta kada dabbobin kiwo,yau fes takejin zuciyarta,da wani nishadi na daban,ba kuma lallai ka fahimci haka ba,amma idan ka kalli fuskarta da kyau xakaga akwai banbancin yanayi a tattare da ita. Wajen daya zame musu gurin zama ita da ibrahim din ta koma ta zauna bayan ta gama duk abinda ya kamata tayin,lokaci bayan lokaci tana daga kanta zuwa sama,ta wurga kallonta hagu da dama,tana ji kamar ibrahim din yana hanya,kamar yana tahowa inda take. "Kin fara son ibrahim ne?,me yasa zuciyarki ke canzawa?" Ta yiwa kanta wannan tambayar karo kusan na uku kenan,sai ta girgiza kanta a hankali,har yanzu batace ga dalili ba,amma rashin zuwan ibrahim din a kwana uku rak sai takejin kamar tans komawa izuwa wata duhuwa ne data fita ta bari. Duk da yadda lokaci ke qara jaa amma bata saare ba,bata rasa qwarin gwiwarta ba,taci gaba da dube dube,har daga bisani ta miqe daga wajen,ta fara kewaye cikin dabbobin,wai ko hakan zai sanya lokaci yayi gudu,ya kusantata da zuwansa wajen. "Maimunatu na!" Kakkaurar muryar mai cike da kaushi ta doki kunnenta,ta kuma zama musaya ko ince madadi ga muryar ibrahim da take ta dako da fatan ji. Buɗeri ne,ba shakka shine,saboda shi daya yake mata wannan kiran mafarautan,kiran dake sanya zuciyarta luguden bugu,ta sauke sandarta a hankali tana nufin juyawa zuwa gareshi,saidai kafin ta waiwaya din har ya iskota ya sha gabanta,taja baya da sauri saboda yadda kusancin dake tsakaninsu yayi qanqanta da yawa. Fuska ya hade yana kallonta "Meye na ja da bayan?,kin manta ke din tawa ce?" Ya fada yana nunata da yatsa,kau da kanta tayi,idanunta suka sauka ga qafarsa dake cikin huffaje,saidai shi kansa huffajen yayi daqal daqal dashi,kamar yadda sutturar jikinsa take cidin cidin,sau tari tana mamakin uban tulin qazanta irin naa buderi,abune me matuqar wuya ka sameshi fes cikin tsafta "Amma kinyi kyau maimunatuna......ina fata babu wanda ya kallemin ke" yayi maganar yana washe baki,kanta ta daga a hankali tana duban gefe da gefanta,tana fatan kada Allah ya kawo Ibrahim a yanzu har sai buderi ya wuce,tasha jin alwashi daga bakin buderin na cewa,duk randa yaga wani ya rabi maimunatunsa,wala shakka sai ya sha jininss,tana kyautata zaton wannan na daya daga cikin dalilan daya sanya babu wanda yake mu'amala da ita "Me kike nema kuma?" Ya fada yana hade rai,kai ta girgixa "Babu komai" amsarta tasa ya saki fuska "Na sani,kinfi kowa hankali cikin 'yammatan rugar nan,nasan babu wanda zaki kula,ungo wannan" yayi maganar yana miqa mata wata leda. Babu batun ma tace ba zata karba ba,don kuwa bata baki ne,don haka ta saka hannu ta karba tana cewa "Na gode" "Yauwa,medillu,dan men waratam?(zan tafi,yaushe zanzo?" Mummunan faduwa gabanta yayi,kada dai xancan da innar laulo ke gaya mata ya tabbata,buderi..... Buderi ne zai fara zuwa tadi wajenta? "Ban sani ba" sandarsa ya wulwula sama ya caketa a qasa "Shikenan,ni xan saka rana da kaina" sai ya juya abinsa ya fara tafiya,dama can shi din ba mutum ne da ya iya yin sallama ba,da ya gama abinda ya kawoshi xai saka kai ya wuce abinsa,har ya dan bata rata sai taga ya dawo da tsaya a gabanta "Baki taba cewa kina so ba maimunatu,ate ayyam?,ayid'iyam?(zaki aureni?,kina sona?)" Banbarakwai taji maganar tasa,ta kuma rasa amsar da zata bashi,tana matuqar tsiron buderi,batajin xai kasa maketa a wajen idan tace bata sonshi,amma kuma idan tace tana sonsa din tayi masa qarya,sannan yaudara ta shigo ciki. Dariya ya bangare da ita "Ja'ira,kunyar gayamin kikeji kenan.....shikenan,idan nazo saiki gayamin tunda zuwan dare ne,bana ganinki sosai" daga haka ya juya abinsa yana waqar tauri.irin ta matasan fulani yana cilla sandarsa. Baya taja a hankali ta jingina bayanta da bishiyar dake wajen,ta sauke nannauyar ajiyar zuciya tana lumshe idanunt,sannan ta saki ledar hannunta a hankali ta sulale zuwa qasa. A matakin rayuwarta gaba daya ba zata iya dorar da komai ba,ba zata iya fadin meye ainihin rayuwa ba,kamar yadda ba zata iya fadin me rayuwa ta qunsa ba,meye manufar tata rayuwar?,me ta cimma?,me takeso ta cimma?,tabbas a karan kanta tasan cewa akwai abubuwa da dama da takeso ta cimma,tana da mafarkai da burika masu yawa irin na kowanne dan adam,saidai ita kanta batasan wadanne ne burikanta ba,me takeso ta cimma din,dukka bata sani ba,rayuwata qwaqwalwarta dama komai nata na tattare ne a waje daya,a yanzun kumma innar laulo ta dauko hanyar da zara qara ruguzata zuwa pieces gaba dayanta,aure da buderi?,me hakan yake nufi?,wanne buri ne a ran innar da takeso ta cimma?. Ta jima a haka kafin ta iya bude idanuwanta,dukka wani fata da take dashi na ganin ibrahim ya fara zagwanyewa daga zuciyarta gaba daya,ganin yadda lokacin da ya dace tabar wajen zuwa gida ya gabato,jiki a mace ta miqe daga jikin bishiyar,saidai tana taku biyu takalminta ya katse "Innalillahi" ta fada gabanta yana faduwa,ta duqa a hankali da zummar daukoshi,sai tayi arba da ledar da buderi ya kawo mata wadda ta jima da faduwa a wajen,ta sanya hannunta a nutse ta budeta,sai tayi arba da gasashen naman daji,cikin tashin zuciya ta dauki ledar gaba daya tayi wurgi da ita can cikin daji,sannan ta dauki takalminta ta duba da kyau,ya gama moruwa,bataga laifinsa ba,saboda yayi mata iyakar qoqari,bata da wata sauran dabara data rage mata,abu dayane a yanzu yayi mata saura shine ta cire dayan ta dauresu a qugunta,sannan taci gaba da tafiya da zallar tafin qafarta tana fara hade kan dabbobin,tanayi tana takatsantsan kada ta taka qaya. 07 Tun batayi nisa ba gaba daya qafafunta taji sun daddaure saboda tsakuyiyin da take takawa,wani gurin harda cabalbalin daya cakude da ruwa da qasa,tuni ta jima da sanin cewa ba qaramar rahama bane takalman a gareta,rashinsu a yan mintuna kadan yasa fa fara dandana kudarta,bata kuma san sanda zata sake mallakar wasu ba. A hankali motarsu daada ke kutsawa rubibbiyar hanyar mai yawan gargada,kamar yadda sukazo a yanzunma su hudune,saidai yanzun akwai qarin saddam da zai musu rakiya,a hanyarsu ta zuwa ziyara qauyen dake kusa da rugar ummarun. Cikin motar tattaunawa suke kan yadda gwamnati tayi banza da nuna halin ko in kula da jama'ar dake rayuwa a irin wadan nan muhallan,babu ruwa ba wuta babu hanya me kya bare azo ga maganar tsaro "Subhanallah" salmanu driver ya fada yana taka burki sanda shanun suka fara keto burtalin xasu wuce,salmanu ya kalli agogon hannunsa yana cewa "Aqalla sai sun kusa minti biyar ko takwas suna wucewa,shi yasa tun dazun nake sauri mu wuce kafin su iso" "Wai daman kuna iya kula da dabbobi babu duka?" Laila ta fada cikin mamaki,idanunta nakan maimunatu dake koro shanun daga can baya "Qalilan ne gaskiya,kiwo yana da wuya fa adda laila" maganar data ja hankalin daada,ta daga kanta zuwa ga sashen da maimunatu take. Ido ta zuba mata sosai cike da mamaki da kuma burgewa,gaskiya sadam ya fada ba kowane ke iyawa ba,kula da dabba koda guda daya ne abune mai matuqar wahala,sai mutum me haqurin gaske da kuma tausayi,bare wadan nan da sun haura talatin,banda akuyoyi,yarinya qarama irin wannan me qananun shekaru,ita daya babu mataimaki,zata iya cewa bata taba ganin wannan ba,koda akwai din sai jarumar mace mai kamar maza,wadda taga jiya ta kuma ga yau. Idanun maimunatu nakan motar sanda ya rage ita daya ce zata haura hanyar,idanunta cike fal da fargaba da tsoro,karo na biyu kenan da taga motar,amma sai take ga kamar abinda ya faru da ita shekarun baya zai sake faruwa da ita,sassanyar ajiyar zuciya ta saki sanda taga ta tsallaka,dai dai lokacin da anni ta sauke idanunta ga qafafuwan maimunatu,mamaki ya cikata ganin yadda take ratsa wajen da zallan qafarta ba takalmi. Ta buda baki xatayi magana ta jiyo sautin maimaunatun "Wayyo Allah" tayi maganar a matuqar jigace tana duqawa zuwa qasa tana duban tafin qafafunta "Tsaya salmanu.....dubamin me ya samu yarinyar can" anni ta tsaida salmanu dake shirin tada motar,wajen suka kalla su duka,laila tayi kamar zatayi magana amma sai ta fasa kada qilu ta jawo bau,seat belt din jikinsa ya zare ya bude murfin motar ya fita,bai wuce minti daya ba ya dawo "Kaya ce ta shige mata qafa,ta huda wajen sosai,amma naga ta zareta ma" "Garin yaya?" Wajen da take salmanun yakalla "Qafarta ce ba takalmi,dana tambayeta yana ina sai tace ya tsinke ne" "Ina silifa din nan da nace a sakaminsu a mota?,daukomin daya a ciki" ta fadawa laila,daukowa laila tayi ta miqowa annin "Bawa salmanu yakai mata ta saka" hannu salmanun ya saka ya karba ya juya yakoma indatake,zuwa sannan ta miqe tsaye bayan ta yagi wani ganye dake gefanta ta manna a wajen. Daga kai tayi ta dubi salmanun sanda yake bata takalmin,sai taja baya kadan gami da girgiza kai alamun ba zata karba ba,abinda ya sanya salmanu dawowa inda anni ke zaune tana kallonsu "Anni taqi karba fa,kamar bata yarda bane damu" "Budeni" anni ta bashi umarni,sai ya zagayo ya bude mata qofar "Anni,karkice zakiyi magana da ita,kaf fadin rugarmu babu wanda yake kulata" sadam ya fada,a mamakance anni ta kalleshi "Saboda me?" "Ban sani ba nima,amma tsoron mata magana akeyi" shuru anni tayi na wasu sakanni sannan ta zura qafafunta waje ba tare data sake bi ta batun saddam ba Har maimunatun tayi taku daya biyu taji muryar anni "Yarinya" cak ta tsaya,a tsorace ta waiwayo idanunta akan anni,tsoro ya sake kamata,don sam annin batayi zubin mutanensu ba. "Yallijam" maimunatu ta fada a hankali ganin idanun annin har yanzu yana kanta "Jam" anni ta maida mata tana kallonta tare da karantar yanayinta "ya kike tafiya haka ba takalmi?" Qafarta ta kalla sannan ta kalla annin "Sun tsinke ne daada" yadda ta kirata da girmamawa sai yasa anni ta saki murmushi "Salmanu bata wadan nan ta saka,da hatsari wajen taka gurin nan haka" da fari kai maimunatu ta sake girgizawa kamar yadda ta yiwa salmanu,don batasan me zatacewa inna ba idan ta ganta da takalmin "Na gode daada,zan qarasa a haka" haka kawai taji ta burgeta,akwai alamun tarbiyya da kamun kai me yawa tattare da ita "Karki damu ki saka,idan ma kina tsoron fada ne a gida kice baquwa ce daga gidan bappa labaran ta baki" daga kai tayi sosai tana duban anni,idan ta canka dai dai fa kenam gidansu himu take nufi,ita a wa sa zata ambaci sunan gidan tace wani abu daga hannunsu ya fito zuwa gareta,a sanyaye ta karba takalman ta sakawa qafarta. Cif da cif kuwa kamar an aunata,wasu irin slipper ne na danqo amma me garai garai dake nuna hoton flowers daga dukka jikin takalmin kaman tangaran,kallon qafar tata tayi ta sake kalla,sai ta daga kai a hankali tace "Na gode sosai daada" duk kuwa da tana da yaqinin wannan takalmin idanunsa idanun inna ba rabonta bane,murmushi anni tayi "Ba komai" sai ta juya maimunatun tana qara hanzari don ta taddo dabbobinta da sukayi gaba,tana kuma kiransu da wani irin salo da yasa anni ta bita da kallo. "Anni....anni kenan,qaqale qaqalen mutane,tayiya jajibo jama'a ana zaune qalau" laila tayi 'ya qaramar mita ciki ciki,abinda yaja hankalin anni dake maida qafafunta cikin motar salmanu yana shirin rufe mata "Me kike cewa ke kuma?" "Bance komai ba" "Oho miki,idan ma zagina kikayi kin zagi marwanu da Aishatu" idanu laila ta lumshe tana dafe goshinta,kafin tace wani abu wayarta dake kan cinyarta ta dauki sautin kida me dadi,saita daga wayar tana dubawa "Ga marwanun nan" lailan ta fada tana hade rai tare da miqawa anni wayar "Kin fada dai dai ai,sunan ubanki kenan" ta amsata tana warce wayar daketa harbawa da sunan super dad,ta shafa ta kara a kunnenta. "Sai da salma ta gargadeni kan tafiyar nan,ashe ni zan karba gashin" bata daddara ba dai ta sake yin qorafin murya can cikin maqoshi,saidai babu yadda za'ayi anni taji,saboda tayi nisa a waya da shalelen dan nata. Sai da tayi duk wani abu daya zame mata al'ada idan ta dawo da dabbobin daga kiwo sannan ta kira sunan innar,saidai babu ita ba motsinta,dole ta fara takawa zuwa cikin gidan,qirjinta yanata dukan uku uku,don batasan me zai biyo baya game da takalmin qafarta ba. Daga qofar dakin innar ta tsaya "Miwarti ɗilaulake inna(na dawo daga kiwo inna)" shuru taji,hakan yasa ta sake maimaitawa "Dalla malama matsa ki bamu waje,kinxo kinata yiwa mutane hayaniya aka" muryar gaje ta fito daga cikin dakin,da alama itace kwance a dakin,wanda dama kusan aikinta kenan ko da yaushe,taci ta sha ta kwanta. A sanyaye ta juya don barin wajen,dai dai sanda innar ta fito daga makewaye dauke da buta,sam bata lura da yanayin da fuskarta ke ciki ba "Miwar......." Ragowar kalmar ta tsaya mata a maqoshi,sakamakon wani zazzafan mari daya sauka a kuncinta hagu da dama,a take ta gigice,ta dafe dukka kuncin nata da tafukan hannayenta tana kallon inna,wadda ta taka gefan wani qaramin rumbu dake daura da ita,take tashin hankali ya bayyana muraran saman fuskar maimunatu,tunda taga ta doshi wajen tasan me zata dauko. Tsumammiyar bulala ce,wadda ta debi shekaru ana azabtar da ita da bulalar,yadda ta tsani mutuwar ta haka tabtsani bulala,wannan ne dalilin da yasanya take dukka iya bakin qoqarinta taga bata aikata wani laifi da bulalar zata taba lafiyarta ba,zata iya cewa tabon da bulalar ta bar mata a gadon bayanta ba zaya lissafu ba. Kusan daukewa numfashinta yayi sanda innar ta ware dukka qarfinta ta zuba mata ita,kafin daga bisani qarfin dukan ya sanyata ta sulale ta duqe a wajen,tun tana iya roqarta tare da bata haquri har bakinta ya mutu,duk da batasan me ta aikatawa innar ba,sai data gamsu don kanta da yawan dukan data yi mata sannan ta tsaya tana maida numfashi "Gaje....gaje zo nan" ta qwalawa gaje dake daki abinta kira,gajen da duk yawan dukan da akewa maimunatun,duk magiyar da takewa innar bai sanyata ta koda leqo ba,hatta da sassan dake maqotaka dasu dukka kowacce ta leqo tana tsaye tana kallo,wasunsu suna qus qus a junansu tare da tir da dabi'a da halayen inna,wasu kuma suna fadin "Allah ne kadai yasan me tayi mata,kila ko yau ta dana halin uwarta ne" saidai babu ko mutum daya a cikinsu da ya isa ya tukari innar da sunan ceton maimunatu,kowanne irin hukunci ko horo kuwa zatayi mata. A gadarance gajen ta fito daga dakin,tsaf da ita cikin kwalliyar kayan saqi,wanda kusan ko da yaushe cikin canza mata su innar take,idanun gajen sun kumbura sunyi jazur,abinda.ya bayyana har saman fuskarta,da alama kuka tasha ta qoshi. Tsaye tayi saman kan maimunatu tana hura hanci tare da harare harare "Daga kanki ki kalleta.....tayi kama da sa'arki?" Inna ta fada cikin hargagi,koda ciwon mutuwa maimunatun takeji a jikinta ya zame mata dole ta kalli gaje kamar yadda inna ta buqata,idan kuwa ta saba hakan wani sabon tashin hankalin ne,da qyar ta daga kanta ta dubi gaje,suna hada idanu gajen ta sanya qafa ta haureta cike da baqinciki da kuma jin haushin maimunatun,tasa hannu ta dafe wajen saboda radadi da zafin da ya ziyarceta "Shegiya munafuka,ni zaki ha'inta,ashe yaron dana ganki dashi rannan ibrahimu ne?,to idan bakisan waye ibrahimu ba bari na gaya miki,shi din alqawarin gaje ne,bashi da matar aure sai gaje kiji na gaya miki,kusantar inda yake kuma shine babban kuskure da zaki aikatawa rayuwarki,wallahi wallahi kinjin na rantse miki,kome kike taqama dashi baki isa ki shiga tsakanin tsohon alqawari ba.....kukan da kika saka gaje yau sai kinyi mafiyinsa,ki bata haquri!" Inna ta fada tana kai mata harbi da qafa,ta sameta kuwa a gwiwarta wadda ta bugu sosai,tana dafe da wajen,cikin tsananin azaba tana dafe da gwiwarta ta fara baiwa gaje haquri,wadda keta qunci,tana jin babu abinda maimunatu zatayi mata ta huce haushin kula mata Ibrahim da tayi,tsahon wanne lokaci sukayi suna tare da ibrahim din?,tunda hatta da mutanen gari sun san da haka,baya ga haka kuma ace har sai da daadarsa tazo da kanta don yiwa tufkar hanci sannan sukasan da batun,lallai maimunatun ta cika cikakkiyar makira kuma macijin sari ka noqe kamar yadda innarta tasha fada mata. "A'ah,lafiya?,me yake faruwa?" Muryar jauro ta ratsa kunnensu,abinda ya sanyasu waiwayowa gaba dayansu,duk da cewa innar bata so dawowarsa yanzu ba amma sai ta dake "Meye hakane?,me ya faru?" Ya sake tambaya yana kallon gaje kafin ya maida dubansa ga maimunatu dake zube a qasa,hakan ya baiwa gaje damar sulalewa zuwa dakonsu,tasan halin jauro tabbas yau cikin gidan ba za'a qarke lafiya ba "Gata nan ka tambayeta maciyar amana" inna ta fada tana huci. Gabanta ya duqa yana kiran sunanta,ta daga kanta wande ta sokeshi tsakanin qafafuwanta tana duban ardo din,yanayin yadda yaga maimunatun ya tabbatar masa lallai ta daku,hatta da bakinta a kumbure yake,gefan fuskarta yayi kwanciyar jini da shacin bulala "Wanne irin rashin imani ne wannan furera?" Jauro ya fada a mugun fusace yana miqewa tsaye "Ita ya kamata ka yiwa wannan fadan bani ba,qanwar bayan gaje har ta iya hilatar maza tana binsu?,saboda rashin kintsi ta rasa wa zata bi sai ibrahimu?" "Shine kikayi mata irin wannan dukan?,inda kuma kin nakastata fa?" "Shikenan da kowa ya huta da ganin shegiyar fuskar dake daukan hankalin maza" cacar baki ce taso barkewa a tsakaninsu,ran jauro yayi mutuqar baci "Waike wacce iriyar macace furera?,maimunatun zaki yiwa irin wannan dukan?,kowanne irin laifi ma tayi miki?,don kinga ina dauke kai ina barinki saboda kina nuna min kunfi kusa ko?" "To dama meye naka a ciki?" Kai ya gyada cikin bacin rai,iskar data fara kadawa wadda ke tafe da dan yayyafi yasa jauro ya maida hankalinsa ga maimunatu "Tashi ki shiga dakinku,Allah zai saka miki,a kusa ko a nesa,baya yafe zalunci" kasa miqewa tayi,ya tabbatar ba zata iya tashi ba,cikin muryar fushi ya qwalawa gaje kira. A tsorace ta qaraso tana raba ido hadi da matse hawaye,tsawa ya daka mata "A'ah ya haka?,ka bita a sannu,rai aka bata mata fisabilillahi sannan ka bita da irin wanna tsawar?" Kallon banza ya watsa mata,yana ganin zallar son rai da son kai irin na innar "Munafuka,kamata ki kaita daki" ya fadi yana zabga mata harara,da sauri ta zabura ta matso ta kama maimunatun,irin riqon tsaurin da tayi mata na mugunta yasa maimunatun cewa "Wash hannuna" "Sassauta mata riqon kafin nayo kanki na maimaita miki irin dukan da uwarki tayi mata" "Dalili dame?,ke bi masharranciya a sannu ku rabu lafiya kada ta shafa miki jarfa ba gaira ba dalili" inna ta fada saboda tasan tsaf jauro zai aikata daga yadda ranshi yayi mummunan baci. Sakin maimunatu tayi sanda suka isa dakin,abinda ya sanyata ta buge gefan kanta,qauuuuu taji wani abu na yawo cikin kwanyarta,ya dafe wajen tana kiran sunan Allah,gaje na tsaye a kanta tana zuba mata harara "Shegiya mayya,wallahi kikayi gangancin sake rabar ibrahim sai mun kasheki a gidan nan nida inna mun binneki,kuma mun kashe banza,tunda babu wanda zai tuhumemu" daga haka ga tsallaketa kamar zata takata,ta haure kan katifarta. Ta jima tana jinta a wata duniya ta daban,kowacce gaba ta jikinta ta zame mata kamar wani gyambo,da qyar take iya motsawa. Kiran sunanta da jauro yayi ya sanyata bude idanunta da qyar "Tashi zan shigo" ya fada yana tsaye daga bakin qofar dakin,duk da yayyafin dake sauka har yanzu,jikinta taja ta miqe ta zauna sosai tana jingina da bango,ya dage labulen bayan ya shigo ya maqale shi sannan ya tsugunna daga gefe yana turo mata kwanon abincinsa "Dauki kici maza diyam" sunan da ya kirata dashi yayi matuqar karya mata zuciya,ya tuna mata da tata daadarta,itace wadda ke kiranta da sunan,suna mafi soyuwa a gareta,fararen manyan idanunta suka cika da qwalla,tasa hannu a kasalance ta jawo kwanon gabanta ta fara ci. Wasa wasa sai gashi ta kusa tashi da abincin duk yawansa,ta riga ta saba ba kullum take samun abinci ba,idan ma ta samun to sau daya ne a rana,tana ci yana mata nasiha tare da kwantar mata da hankali,gaje na kwance tamkar mai barci,ranta ya baci sosai,shi babanta wai baya kishinta?,me yasa yafi nuna kulawarsa ga maimunatu fiye da ita diyar cikinsa?. "Miyatti bappa" maimunatun ta fada a tausashe kanta a qasa cikin nuna jin dadin kulawar da ya bata "Ba komai,kema diyata ce kamar yadda gaje take" kai ta jinjina,tana kin sauqi cikin ranta,ko babu komai yau din ba zata kwana da yunwar dake da take matuqar wahal da ita ba a duk dare. Har jauro ya juya ya fita maimunatu tana binsa da kallo,sai daya sauke labulen ya qarasa ficewa sannan ta sauke nannauyar aiiyar zuciya tana janye idanunta daga wajen,dai dai lokacin da gajee tayi caraf ta miqe zaune "Munafuka algunguma,kamar a idanun inna akayi wallahi,Allah ya kaimu safiya" tsoro ne ya cika zuciyar maimunatu,saboda tasan tunda gajen ta fada sai ta aiwatar,idanunta fal da qwalla ta shiga roqon gajeen tayi haquri,maimakon ta amsa mata sai ta lullube kanta da mayafi tayi kwanciyarta gami da juyawa maimunatun baya. Sai da dukka yawun bakinta ya dauke kan roqon gajee tayi haquri,daga qarshe dole ta haqura da roqon,ta rufe idanunta,hawayen da suka taru suka gangaro mata. Wani wahalallen barci tayi mara dadi,saboda ko ina na jikinta ciwo yake mata,ko da tayi sallar asuba ma zaune tayi a wajen,saboda ciwon da jikin yake mata,inda ace shimfida ce mai laushi irin ta gaje wala'alla ta iya rabawa takwanta,amma shinfida irin tata da bata da maraba da tattauran dutse babu ta inda zata iya kwanciya taji dadi. "Maimunatu!!!,ke maimunatu!!"kiran mafarautan da ya ratsa tsakiyar baccinta ya sanyata farkawa firgigit,inna ce tsaye a kanta,hannunta riqe da robar da yawancin lokuta suke tatsar nono a cikinta,duban maimunatun take kamar zata afka mata "Yahudillo dirgul.....(zoki tafi kiwo)......" "A ina?" Maganar jauro ta katse hargagin da inna ta fara yi mata,ratsowa yayi sanye da riga 'yar shara da malfare a kansa,hannunsa riqe da baqar leda,bisa dukkan alamu fita zaiyi "Daga yau.....har zuwa ranar da maimunatu zata warke babu ita babu zuwa kiwo,wallahi wallahi wallahi sau nawa kenan?" "Tati(uku)" innar ta amsa masa tana riqe da qugunta tana kallonsa "Idan naga akasin hakan zakisan waye ainihin jauro wanda ada can baki sanshi ba,wannan shine hukuncinki na irin dukan da kikayi mata" "Wai dakata,wai me kake nufi ne?,ko kana yimin baqinciki ne da dukiyar dabbobin da Allah ya bani ne?,wanda dama an jima ana fada,ganin muna zaune shekara da shekaru tare yasa ban gasgata ba,amma ayanzu na fara ganin alamu ganin idona kuwa" dubanta yayi "Ki bari sai zuwa sanda kika tara taki dukiyar ta halastacciyar hanya saiki gayamin haka" sosai maganar daya fada tayi mata ciwo,tana ganin jauro shi daya ne mutumin da yasan sirrinta yake kuma shirin xamar mata tarnaqi a rayuwa,wannan amsar da ya bata ta hautsinata,ta dinga jifansa da kalamai,wanda kalmarta ta qarshe ita ta sanya ya tsaya cak yana dubanta "Ban sani ba ko son maimunatu ma dai kake yi a taqaice,idan sonta kake ai gwara ka fito ka gayamin,saika hadamu mu duka ka aure" "Idan ke mahaukaciya ce ni da hankalina" sai ya qara gaba kawai ya fice yabar mata gidan,ya tabbata idan ya tsaya yaci gaba da biye mata zasu raba abun fada ne gaban 'ya'yansu,wannan ba komai bane a wajen furera. 08 Fitar jauro daga gidan sai dukkan bala'i da masifar suka dawo kan maimunatun,inna nayi gajee nayi "Tunda ya daure miki gindi ko?,to wallahi baki isa ki kwanta kiyimin saqe saqe kamar gawar sababi ba,bayan jiya ya shirga miki abinci kin cinye,to kin ciyoma kanki,kinci abincinki na jiya dana yau,waryo wan en jungul!,(zoki dora mana abinci)" ta fada a tsawace,har maimunatun tana jin kanta kamar zai cire. Tuwo ne na masara miyar danyar kubewa,gaba daya kayan aikin innar ta tura mata,ta baza tabarma tayi zamanta qasan bishiyar dake basu iska. Zata iya cewa batasan ta yadda akayi take aikin ba,don komai tana yinsa ne a wahalce,cikinsu kuma babu wanda ya taimaka mata koda da firfita wuta ne,yadda bata da lafiya haka aikin yaja lokaci yaqiyin sauri,saboda rashin kazar kazar da kuma qwarin jiki,abinda ya qara iza wutar masifa da bala'in inna,ya kuma sanya maimunatun taji inama ace kiwon ta tafi a haka,tabbas ya fiye mata wannan wahalar girkin. Tana zaune tana niqan kayan miyan da zata dora miya saman dutsen markade taji sallama,ta daga kanta a wahalce tana amsawa,matashiyar da aqalla zatayi sa'a da ita ce(zubaida),sai kuma yaron dake gefanta(sadam),kasa dauke idonta maimunatu tayi daga kan fuskar yaron,saboda kamarsa muraran da ibrahimunta. Shima yaron ita yake kalla,kafin daga bisani ya dauke kansa,abinda ya bata mamaki hararan da zubaidan ta wurga mata kafin su miqa zuwa inda inna ke zaune tana kada nono,maimunatun kuma ta maida kanta ga aikin da takeyi cikin mamaki,iyaka saninta da zubaida saidai kallo daga nesa,ba abinda ya taba hadata dasu,koda gaisuwa kuwa,takan jima bata gansu ba,kamar yadda suma suke jimawa basu ganta ba,domin su din zuwansu kiwo na lokaci bayan lokaci ne bawai koda yaushe ba,koda ma koda yaushe ne,tana daukar watanni kafin magana ta hadata da wani a wajen kowo har taje ta dawo,saidai idan baqin makiyaya da ba 'yan asalin rigarsu ba sun ratso ta dajin da suke kiwo. "Maraba da zubaida da saddam" innar laulo ta fada cikin wani irin kirki da kuma fara'a,wanda ya sanya har sai da maimunatu ta tasa kanta dake mugun sarawa ta saci kallonta. Daga gefan tabarmar da take kai suka zauna,gaisheta yaron ya farayi sannan zubaidan "Dama daada ce ta ailo na gaya miki,akwai baqi da sukazo daga gombe,naggen bappa suka saba siya,to wannan karon babu,bappan ya fita dasu gaba daya,shine tace nazo na gaya miki,tasan cikin naki akwai irin wadanda sukeso,gobe zasu zo da safe kafin a fita dasu su gani" madaukakin farinciki ya kama inna furera,cikin ranta ta sake jin duk duniya bata da masoyi sama da daada din,dama ta jima tana shawarin saida wasu daga ciki,ko don ta saku ta sake badda dukka wata alama da zata iya zama shaidar rashin zamowarta mallakin dabbobin,to amma kuma batason saidawa anan kusa,tafison waje me nisa inda zasu siya da daraja "Miyatti Allah,miyatti daada,amma naji dadi wallahi,Allah ya kawosu" "Ameen,sannan tace na gaya miki,anjima yaaya himu zaizo wajen gaaje,su sake ganin juna" kamar inna furera zafa taka rawa haka tayi,takai ta kawo ta rasa wanne tukuci zata bawa zubaida,qarshe dai har suka bae gidan bakinta yaqi rufawa. Saukar zancan a kunnuwan maimunatu sai ta kasa tantance cikin wanne yanayi take ciki "Ibrahimu zaizo yaga gaaje" wannan shine dalilin da yasa ta daina ganinsa kenan?,me hakan yake nufi?. Tunanin ya sanya aikin nata ya sake yin slow fiye da dazu,tun inna na mita da baki har sai data fara kai mata duka da hannu "Me shegen baqin halin tsiya,bakyason aikinne,a haka kuma zakiyi shi". Takanas innar ta taso gaje,ta hada mata madarar shanu da lalle ta murje mata jikinta,zaka tsammaci kamu za'ayi mata irin na amare,duka a wannan lokacin ta sanyata ta tsefe kanta mai yalwar gashi,wanda datti ya dakushe tsahonsa ta wanke mata shi fes,ta raba mata gida biyu ta zubo mata da jelarsa hagu da dama. Tun yammaci aketa shiri gamida da gwada yadda zata tarbi ibrahim din,duk don saboda ta burgeshi,mudukaje(kayan saqin fulani) na can qasan kayanta ta ciro ta ajjiye,dukka abin nan da ake na maimunatu idanu ne,saidai gefe daya zuciyarta ta gaza hutawa da tunanin abinda zaije yazo. Dai dai sanda maimunatun ke saman dan mayafin da take shimfidawa tayi sallah....dai dai sannan gaje keta faman fecewa fuskarta kwalliya,ta kalli madubi yafi sau shurin masaki,ta juya ta sake juyawa har sau babu adadi,burinta shine taga komai yayi,sannan ta burge ibarahim matuqa,maimunatu tana zaune a wajen,bata motsa ba bare ta waiwaya taga abinda gajen keyi,saidai kuma kunnuwanta na samun aiken saqonnin waqe waqen da gajen keyi cikin harshen fullanci,tana yi tana juyi,abinda zai nuna maka cikin zallar farinciki take a yau din. Laulo ne ya shigo dakin,yaron da za'a iya cewa yafi gaje hankali,don wasu abubuwan da shi din yakeyi yana yinsu ne da yarinyata,da kuma rashin samun isashshiyar tarbiyya da kyau "Himu yazo,inna tace akai masa taburma" sai yaron ya juya ya fita yana tsalle tsalle abinsa. Juya idanunta gajee tayi cikin farinciki,ta jima tana qaunar himu tun ba yanzu ba,tun daga sanda inna ta gaya mata cewa shine mijin da suka zaba mata ta riqe hakan a ranta,bata taba mancewa ba,hakanan bata yarda ta kula kowa ba saboda ibrahim,duk da tarin masoyan da take dasu a rugar,don dai dai gwargwado tana da irin nata kyan. "Ki dauko tabarma ki kawomin zagaye" ta bawa maimunatu umarni kai tsaye tana ajjiye madubin hannunta,har takai bakin qofa ta tsaya ta juyo tana duban maimunatun jin bata ce komai ba "Ko ba zaki kawo bane?" "Yanzu zan tashi" ta amsa mata murya a raunace,qwafa gajee taja sannan ta sanya kai ta fice. Babu yadda zata kaucewa umarnin gajen,ya zame mata dole,hakanan ta miqe dauke da tabarmar ta nufi inda gaje ta umarceta. Salon tafiya na daban ta canza kamar yadda suka wuni suna gwadawa ita da inna furera,ibrahim din na tsaye,jingine da wani kutturen ice,qafarsa harde da juna yana duban gajen sanda take tahowa,cikin salo na nuna jin kunya ta dan sunne kai sanda ta fuskanci kallonta yake,farinciki ya cika zuciyarta,tana hangen ba wani faɗi tashi me yawa zatayi ba zata samu kan ibrahim din. Wani tattauran yawu me daci ibrahim din ya hadiye,ya rufe idanunsa yana sake tursasawa kansa da zuciyarsa daurewa da kuma bin umarnin daada,yana jin kamar zuciyarsa zata fashe saboda takaici,meye ne daada ta hango masa tattare da gaje,me yasa idanunta suka rufe ta kasa gano abubuwa masu tarin yawa da yake gani tattare da maimunatu?. Yana bude idanunsa ya hangi maimunatun biye da gaje,gaba daya sai ta wafce kallonsa,ya tattaru gaba daya a kanta,hasken wutar kara da mazauna wajen suka kunna daga can gurin zuwa can ya haske wajen sosai da har yake samun damar ganin kowacce a cikinsu "Sannu da zuwa" gajee ta fada tana dan russunawa hadi da rausayar da idanu "Sannunki" ya amsa mata murya a ciki,yana dauke dubansa daga maimunatu wadda ta qaraso wajen riqe da tabarmar "Ki shimfida masa mana kin bar mutane a tsaye,sai wani abu kike kamar mara laka a jiki.....mayya...." Hannu ibrahim ya daga mata da sauri,saboda zafi da zuciyarsa ta fara yi masa,bazai iya daukan hakan ba,a nutse ya dubi gaje "Wannan din ba bil'adama bace kamarki?,bakisan Allah ya karrama dan adam ya kuma mutuntashi ba?,matuqar wannan itace dabi'arki,to kin dauko hanyar da ba zaki sake ganina a nan ba" sosai maganar ta bata mata rai,ta kuma sake saka mata kishin maimunatu a ranta me yawa,amma a yanzun nema take,dole ta jure,don haka ta sadda kai "Kayi haquri" bai amsa mata ba,sai ya miqawa maimunatu hannu ya karbi tabarmar,ya sani sarai anyi hakanne don a tozarta maimunatun,a sake kuma nuna masa ita din ba kowa bace,tunda daadansa bata boye masa komai ba,ta gaya masa duk irin matakin da suka dauka,tayi ne da nufin jan kunne,ta kuma gaya masa zaman lafiyar maimunatu shine ya rabu da ita,abinda basu sani ba shine,wannan abun da sukayin shi ya sake zubda darajar gajee harma da inna furera a ransa,ya kuma sake sanya masa tausayi da qaunar maimunatu. Batasan cewa himu ya fara taka wani matsayi a zuciyarta,batasan cewa ya fara bude wata rufaffiyar qofar da bata tsammaci budewarta ba sai data koma daki,gaba daya ta gaza sukuni,ta kuma kasa kwanciya kamar yadda taso ta kwanta din,saboda yadda jikinta yake wani irin radadi da kuma zugi sakamakon aikin da tasha,ga kuma tabbai na duka wani wajen har ya fara rurucewa,abinda ya hade mata kenan,ya kuma saukar mata da zazzabin da ya tilasta mata kwanciyar da a daxu ta kasa yinta. A hankali ta bude idanunta sakamakon muryar gaje data jiyo cikin muryar kuka "Ke....mene....meye?" Inna furera data fito daga daki zaninta a hannu ta fada,hankali tashe tana duban gaje "Inna,kai tsaye himu fa yake gayamin wai bani bace a zuciyarsa,zuciyarsa tuni wata ta karbeta,kuma wallahi nasan ba kowa yake nufi ba sai waccar mayyar,tunda na daka mata tsawa har ya tafi banga faraga a fuskarsa ba,ki taimakeni inna,wallahi inason himu" wani dogon tsaki innar ta saki tamkar zata tsige harshenta "Ahaf.....aikin banza kenan,yo yayita fadi baya sonki.mana,qarewa ya samu amsa kuwwa ya daura,yayita bi rugage yana fadin hakan,ai yayi aikin banza,maganar nan babu me tashinsa,shi ya san wace uwarshi,tunda ta fada babu me tashin maganar,shi yasa ya biyo ta hakan don kice bakiyi,wadda kuma yake qulafucin haihata haihata shi da ita,qwalelen kare da hantar kura,yadda naci alwashi in sha maka Allahu....matuqar ina raye saikin aurin namijin da kaf rugar nan babu irinsa,ibrahimu ne,kuma shine naki,muje na karanta miki karatun zaman duniya" inna ta fada tana kama hannun gajee sukayi dakin innar. Maida idanunta maimunatu tayi ta rufe,tana fitar da numfashi me azabar dumi saboda zafin zazzabin daya ratsa kowanne sashe na jikinta,kadaici gami da kewar mahaifiya ya cikata,koda zata mutu a saman wannan shimfidar babu lallai a ankara,koda za'a lura din wala'alla sai ta kumbura ta fara fidda wari,ko kuma sanda suka nufaci tashinta don ta biya musu buqatunsu "Innalillahi wa inna ilahi raji'un" ta samu kanta da fada tana rushewa da kuka mara sauti,addu'a ce da take yawan jin mahaifiyarta tana yi,rashin uwa wani babban gibi ne a cikin rayuwa,wanda babu wani abu da ya isa ya cike maka wannan gurbin. Duk yadda take jin jikinta bayan ta idar da sallar asuba amma hakan baisa ta koma barci ba,tasan koda ta koma din ma wani tashin hankali da kuma firgici zata kirawa kanta,don haka taci gaba da zama,har zuwa lokacin daya dace ta fara aiki yayi,ta miqe a hankali ta yaye labulen zanin atamfa dake qofar dakin nasu tayo waje. Duk da yadda suke da sammako da kuma tashin wuri amma wajen tsit yake,kowa yana ta sashensa,babu komai sai kukan dabbobi dake turke a muhallensu. Sannu sannu tana aikin gari na dada yin haske,mutane na sake fitowa daga muhallansu kowa na kama sabgar gabansa. Inna furera ce ta fara fitowa daga nasu gefan,ta saki wanke wanken da takeyi ta qarasa inda take tsaye tana gaidata,bata bi takan gaisuwar tata ba tace "Ki saki wanke wanken,kije ki gyara wajen dabbobin can,nasan masu sayen suna hanya,tunda da wuri zasu zo,sannan inaso ki nutsu da kyau,na tabbatar sai an kiraki lokacin cinikin,saboda ke kike kiwonsu,kinfi kowa sanin wadanda sukafi kowanne lafiya da nada nono da kyau,to bance ki tsaya nune nune ba,ki barsu su zaba da kansu,ki kula....bazan lamunci ki jawomin asara ba" kanta a qasa take amsawa innar,bata miqe ba sai data bata umarni,ta taka zuwa inda take adana kayan sharar wajen ta debesu da qyar ta zagaya zuwa makwantar dabbobin. Sanda suka ganta sai da dukkaninsu suka motsa,ta saki murmushi itama tana isa gabansu,kwanaki biyun da bata gansu ba sai takejin tayi kewarsu ba kadan ba,suma kuma tasan hakanne,don dai kawai basu da baki bare su bata labari. Duk da jikinta babu qwari,cikin boyeyyen ciwo dake cin naman jikinta take amma cikin qawa zuci take aikin,tana yi yana musu magana kai kace da dan adam take,sai data bi kowacce dabba data saba dubawa ta dubata sannan ta fara aikin. A hankali suke takowa da qafa,tun daga gidan bappa labaran din,anni da kanta ta zabi su tako da qafan "Ku barni da qarfen nasaran nan,gwara mu taka da qafa tunda ba nisa ke da gidan ba" tace da daada,wadda da kanta tayi mata rakiya ita da safiya da kuma laila. Tahowar da sukayi din ya bawa lailan dama daada damar kallon rugar sosai,bambancin rayuwa qarara na zahiri da suke gani,wanda yayi dai dai da karin maganar nan ta bahaushe da hake cewa Allah daya gari banban,suna tafe laila na tambayar sadam wasu abubuwan,tafiyar ta zama wani mabudi na ilimi a gareta. "Maraba,lale,sannunku da zuwa" shine abinda inna furera ke faman fadi,tana kai kawo tare da qoqarin shimfida musu tabarma gaban dakinta,yayin da gajee ke zaune abinta saman kujerar tsuguno. *Don samun ci gaban sabbin galla gallan pages,ziyarci page dina a AREWABOOKS da sunan HUGUMA* 09 Tarba cike da fara'a da nuna matuqar kirki inna furera ta yiwa su anni "Ina kwana daada" gajee ta fada tana dan zamowa kadan daga saman kujerar da take zaune a kai hannunta riqe da mudubi tana ta faman kallon fuskarta da kuma kankare duk wani dan tabo ko ciwo da ta gani akan fuskar tata,so take lallai ta hango dame maimunatu ta fita ne,da har jiya himu zai iya duban fuskarta yace mata baya sonta?. "Lafiya lau gajeje,ya akaji da baqi kuma jiya?" Murmushi tayi ta noqe tana komawa saman kujerar,ita ala dole kunya,saidai hakan bai sanya tabar wajen ba,hakanan kuma batayi yunqurin gaida anni ba,duk da cewa ta girmi duk wanda yake wajen. Kallo daya itama annin ta yiwa sashen da take ta maida dubanta ga inna fureran,tana matuqar mamaki idan akace mata wadan nan din fulani ne,saidai kuma duk da ita da zafinta,amma mutum ce da ba kasafai zaka ga ta shiga abinda babu ruwanta ba,saidai idan ta kama. Gaisawa suka fara yi,sannan innar ta fara yi mata bayanin yawan dabbobin da kuma farashin da ta yankewa kowanne "Farashi ba tsada bane,indai sunyimin shikenan.......laila,leqa ki kirayi salihu ya shigo" tace da laila,salihu shine kusan manager din gidan gonarta,a yawancin lokuta shike bi rugage ya qaro mata dabbobi a duk sanda ta buqaci hakan. Ba jimawa suka dawo tare,innar tayi musu jagora zuwa makwantar dabbobin,suna tafe tana qara yi musu bayani,burinta ta gamsar dasu,su siye ta caski kudinta. Tun daga nesa idanun anni suka sauka akan maimunatun,gefanta kayan share wajen ne a zube,tana tsugunne a cikinsu,hannunta riqe da qafar wata akuya tana dubawa,idan ka kalleta da kyau zaka fahimci magana takeyi saboda yadda bakinta ke motsawa,tana kuma shafa bayan akuyar da hannunta daya cikin nuna tausayawa da tausasawa. Suna sake riskarta annin na ci gaba da kallonta,tana kallon tarin baiwar da yarinyar ke da shi,yadda take nuna kulawa da tausayawa ga dabbobin yana burge anni,tana mamakin yadda take magana dasu tare da isar musu da saqo da bakinta,tayi imani akwai wani abu tattare da yarinyar na musamman wanda ba lallai wadanda ke kewaye da ita sun fahimci haka ba. Sosai ran inna furera ya baci,ta kuma tunzura sanda ta fahimci maimunatu bata share wajen ba,ta cika tayi fam,tanason jawo mata asara ne?,ta yaya zata kawo baqi irin wannan wanda duba daya zaka yi musu kasan duniyar da suke rayuwa ya banbamta da tasu amma tabar wajen a haka?,yanzu idan suka ce sun fasa fa?.….….tunanin da ya sanyata ta kwatsawa maimunatun da batasan da tahowarsu wajen ba tsawa "Ke maimunatu!!!" Kiran yayi matuqar razanata,saboda bata tsammaceshi ba,abinda yasa tayi wata miqewa cikin matuqar hanzarin daya rage kadan ta kifa,sai data dai daita tsaiwarta sannan ta dawo da dubanta zuwa sashen da kiran ya fito,ta sauke manyan idanunta da suka rusuna saboda tsoro a kansu. Yadda take dubansu haka anni itama ke dubanta,wani abu yana taba ran anni haka kawai,matsowarsu kusa da ita da yasa ta sake kallon maimunatun sosai,akwai wani yanayi tattare da ita "Uwarki kike tun dazu baki gyara wajen nan ba?,ban gaya miki baqi zasu zo ba?,lallai dai sai kin nunawa duniya zallar baqinciki da adawar da kikeyi dani ko?,to ni nafi qarfinki,nafi qarfin kiyi takun saqa dani......" Tayi maganar yana zarar wani sanda dake jingine wajen ta durfafi maimunatun a fusace. Gam ta runtse idanunta tana jiran jin ta wanne sashe dukan zai fara sauka a jikinta?,tana wassafa radadi da azabar da zata fuskanta lokacin da dukan zai sauka kan mikin wancan dukan da yake jikinta?,ashe kiwon da take tafiya ta wuni acan wani bangaren rahama ne a gareta?. "A'ah dakata 'yar nan" muryar anni ta katse inna daga yunqurin dukan da take shirin kaiwa maimunatu,sai dukka hankula suka koma kan anni "Banda abinki.....mu ai dabbobi muka zo gani ba wajen kwanciyarsu ba,muyi abinda ya kawo mu kawai" "Allah hajiya da kin barni na bubbugeta,tsinanniyar yarinya babu abinda ta sani sai mugun hali da baqar zuciya,ka bata ci ka bata sha ka bata suttura....." "Ba haka akewa yaro ba,haquri akeyi dashi ana nuna masa dai dai da ba dai dai ba,sannan ma yarinyar nan inacewa ba itace ke fita da dukka dabbobin nan kiwo ba?" Anni tayi tambayar tana duban fuskar inna "Eh itace,haqqun" "To a ganina ai ba cancanci a daketa ba,don ko dabbobin da take kiwon idanuna bai taba gani ita din ta dakesu ba,don me ita ta cancanci duka da irin wannan sandar?" Jikin innar ne ya mutu,bawai don tana jin ta aikata kuskure ba,a'ah.....don sai tana tsoron kada tayi abinda zata jawo ma kanta asarar cinikin da za'ayi mata,don haka ta jingine sandar tana cewa "Haka yake......Allah ya shirya muna" "Ameen" anni ta fada tana maida dubanta ga maimunatu dake tsaye,wadda har yanzu bata iya bude idanuwanta ba "Muje ki nunna mana su maimunatu" anni ta kira sunanta a tausashe,abinda ya sanyata bude idanun a hankali cikin mamakin daga inda kiran ya fito,ta tsammaci dama baquwar fuska ce,hakanne kuwa,akan fuskar anni idanun nata sauka sauka,idanunsu cikin na juna,saita sadda kanta qas kana cikin girmamawa tace "Sannu da zuwa,ina kwana?" Murmushi ya wadaci fuskar anni,cikin kulawa ta amsa mata "Lafiya lau 'yar fillo,ya hidima da kai kawo?" "Alhamdulillahi" ta amsa.mata wani sanyi yana sauka cikin rai da zuciyarta,zata iya cewa tsahon lokacin da ta dauka tana bauta,bata taba jin wanda ya buda baki ya tambayeta irin haka ba. Waiwayawa tayi ta gaida daada,ganin idanun anni yasa ta amsa mata babu yabo ba fallasa,saita juya ta gaida laila,lailan ta amsa mata cikin kulawa,tana binta da kallo,kyakkyawar yarinya data tasamma zama budurwa.irin wannan,me tsananin kyau da sura,inda a birni take rayuwa.wanne irin rububi za'ayi a kanta,sai taji maimunatun ta kwanta mata a rai,yanayin nutsuwarta da sanyin halinta baiyi koda.kama dana 'yaruwarta da suka baro a bakin dakunan can ba. Cikin nutsuwa take nuna musu kowanne a ciki,yanayin yadda take musu bayani tare da zabosu kawai ya isa ya gaya maka tayi musu sani na haqiqa ba qaramin sani ba,sosai anni ta yaba da dabbobin,kamar yadda salihu yace,akwai alamun cikakkiyar lafiya tattare dasu,zasu bada nono da iri me kyau yadda ake buqata. "Waccar sanuwar fa?" Anni ta tambaya tana nuni da ita "Wancan naggen basu fiya bada irin abinda akeso da kyau ba,ba kowa keson irinsu ba,irin ne da wasu ke kasheshi don kada a sake samunsa" maimunatu ta fada tana duban saniyar. Kallon maimunatun anni tayi cike da birgewa da wani qaunar yarinyar da ya shiga zuciyarta,karo na uku kenan da tayi musu bayani makamancin haka,ta lura gaba daya cikin harkarta babu ha'inci babu rufa rufa,kayansu za'a siya,maimakon ta lullube aibunsa sai ta fidda musu da komai babu rufa rufa,gaba daya shekarunta basu taka kara sun karya ba,amma kuma dabi'u da halayenta irin na manya ne,hali na girma da muma dattako "Ma sha Allahu,kinyi sa'ar yarinya qwarai furera,samun yaro mai irin dabi'a da halayenta abu ne me wahala" anni ta fada tana gyada kai cike da burgewa "Gaskiya dai..." Salihu ya fada shima yana murmushi cikin mamakin halayyar maimunatun,saboda yasan halim mutane da dama kan cinikayya irin wannan,kowa kazo kana son siyan abunsa qoqari yake ya linke aibun abun ya baka shi ta fuskar da zaka gamsu da ingancinsa. Maganar ta sanya inna furera dauke idanunta daga hararar da take danqarawa maimunatu zuwa kan anni,bayan ta wadatar fuskarta da murmushin yaqe "Haka ai take,kuma har 'yar uwarta da muka baro a can ta fita" ta fadi tanason fidda gajenta kunya gaban surukarta da kuma baqin idanun da suke wajen "To ma sha Allah,Allah ya dorar dasu akan hakan" "Uhmmm...meen ameen"inna furera ta fada tana son nuna jin dadinta. Yadda inna furera ta fada haka anni tasa salihu ya irga kudinta cas aka tafe mata,harda qaramar rawarta saboda farincikin ganin irin kudin data karba sama ta ka,lallai a duniya bata da masoyi kamar daadar himu,wadda ita tayi mata silar wannan ciniki mai gwaggwabar riba. Har sun juya zasu wuce anni ta waiwayo tana duban maimunatu "Jikata kema ai ya kamata ace an baki wani abu ko,saboda qoqarin nuna mana zabin qwarai da kikayi" qaramin murmushi mai cike da kunya da kuma kawaici ta sake,tayi qas da kanta ba tare da tace komai ba,kamar ma kuma taga hararar da inna furera ta fara auna mata "Basai kin ban komai ba kaaka,haqqina ne nayi hakan don fita haqqin Allah a kaina" tabbas badon idanun da suke wajen ba ba abinda zai hana inna furera kai mata mangari,qiri qiri yarinyar nason jaza musu asara?,don batasan yawan kyautar da matar tayi nufin yi mata ba "Gaskiya ne" anni ta fada,saita karba jakarta a hannun laila wadda duk wannan abun da ake hankalinta nakan daukar hotuna cikin wayarta kusa da dabbobin,don ta samun abun adanawa ya zame mata tarihi,kuma ta bada labarin xuwanta rugar,don kuwa da wayonta ba zata iya tuna yaushe tazo rugar na qarshe ba. Sabbin kudi ta fitar ta irgasu a miqe ta miqa maimunatu "Naji dadin riqe gaskiyarki,wannan kyauta ce bisa hakan" dan noqewa kadan tayi kamar ba zata karba ba,har sai da salihu ya sanya baki,sai data saci kallon inna furera taga yadda take watsa mata harara sannan tasa hannu biyu ta karba tana fadin "Allah ya saka da alkhairi,ya maida ninkinsu" "Ameennn" anni ta fada cikin jin dadin addu'ar maimunatun. Bata tsammanin ko sassan nasu su anni sun bari inna furera ta miqa mata hannu,ko batayi.magana ba tasan me take nufi,shi yasa gaba daya batayi nufin amsar kudin ba,saboda tasan cewa zata raba matar da kudinta ne,ita kuma da tayi niyyar bawa ba zata mori komai a cikinsu ba,duka ta dunqule kudin hannun nata ta miqawa inna fureran,sannan ta tsugunna ta debi kayan aikinta ta fara gyara wajen bata ko waiwayeta ba. Babu kunya babu kuma tsoron Allah ko daya a tattare da ita ta hade dukka kudaden ta irge abunta cas ta soke su tayi gaba abinta tana rera waqa,yau itakam ranta fes,mutuwa batayi mata komai ba sai rana data yi mata,banda silar mutuwar ina ita wannan dukiyar?,ina ita ina mallakar wadan nan kudade?,kudi kam sunzo mata a dai dai,tanadin bikin gajenta zata farayi tun yanzu,saboda bikin gata takeso tayi mata. >>>>>>>>>>"sannu anni.....an gama komai ko?" Yuuma ta fada sanda take shigowa rumfarta dauke da kwanon sha da ta cikashi da damammiyar fura da nono wadda babu surkin sugar ko kadan a cikinsa "Mun gama komai ramatu..dabbobi lafiyayyu,har sunso sufi na labaran din ma" "Ai sunfi ma anni,sun hadu da makiyayiya mai hazaqa da iya kiwo,irin kiwon da babu ha'inci a ciki" yuuma ta fadi tana zama sosai gaban anni tana murmushi "Ai naga alama,ko ba wata yarinya maimunatu ba?" "Itafa,baiwar Allah" yuuma ta fada fuskarta na dan canza yanayi "Ai tunda na shigo Allah yake hadamu,naketa ganin abubuwan mamaki daga wajen yarinyar,na jima banga me kiwo irinta ba,sannan abinda zai sake baki mamaki da ita.....wajen cinikin nan,kowacce dabba da muka nuna manaso sai datayi mana bayanin lafiyarta da sauransu,babu ha'inci" cikin gamsuwa yuuma take gyada kai "Bata tsinta a qasa ba ai,gado ne me kyau daga wajen mahaifiyarta,Allah ya jiqan ruma" "Allah sarki,kice marainiya ce?" Anni ta fada tana jan kwanon furar gabanta tana qoqarin budewa "Marainiya ce,wadda aka kasa yi mata riqo na tsakani da Allah.....kinsan mahaifiyarta anni,kin tuna matar da kikaga wata balama me juna biyu a wajenta kikai sha'awarta shekarun baya can da suka shude,ta qara miki da kyautar wata akuya,akuyar da kikace ta miki albarka fiye da kowacce dabba a kiwonki?" "Af.....af ina zan manta da wannan baiwar Allar,dama itace mahaifiyarta?" "Itace anni" yuuma ta amsa mata tana dauko wani kwanon da ta shaqewa anni shi da dambu me dumi tana aje mata "Allahu akhbar......." Maganar annin ta tsaya sakamakon shigowar laila tana qananun mita. Daga kai anni tayi ta dubeta,daure take da zani daurin qirji da kuma qaramin hijab fari,sai jakar kayan wankanta dake riqe a hannunta,daya hannun nata kuma wayarta ce "Wanne irin sakarci ne haka zaki fadowa mutane ba sallama?,banason tsiyatakun banza da wofi fa?" Cuno bakinta tayi gaba tana sauke wayar daga fuskarta tana kallon anni "Don girman Allah anni ki karba wayar da abbi ya baki ko zamu huta da ire iren takurar su ya jabir" gyara zamanta tayi tana kallonta sosai "To...idan kuma naqi sai yaya kenan uwata?" Hannu laila ta yarfe,bataso annin ta hutsance mata,lallabata takeson yi ta karba a wuce wajen "Anni.....yanzu fa wanka zan shiga,ashe muna hanya daxun ya kirani banga miscal dinsa ba sai yanzu,ina daga wayar ko tsayawa amsa sallamata baiyi ba ya hauni da balbalin masifa,Ni bansan sanda ya koma haka ba wall....." Maganar tata ta katse saboda shigowar wani kiran,saita duba sannan tace "Gashinan ma" gaba data tattar wayar harda earpiece din jiki ta miqawa anni ta juyawa tana shirin ficewa "Wannan zaren na jiki da kika hadani dashi shi zan qaqabawa kunnena?,bada ni ba gada a maqabarta,zoki tsige abinki ki karbi naji da gayan wayar ma" dole ta dawo ta cire matan yadda ta buqata da sauri don kada kiran ya katse ta sake jazawa kanta wani sabon mita da qorafin. *Arewabooks:Huguma* *10* "Assalamu alaikum" ta furta kamar yadda yake a al'adarta duk sanda zata amsa waya,daga daya sashen muryarsa ta bayyana,cikin sanyi daya sanya annin ta shanshano wani abu daga gareshi tun kafin yace wani abu "Barka da dare" "Dare?,a garinku kenan" daga can sashen da yake sai daya dafe goshinsa,ba zata taba yarda ta karba yadda ya bata ba sai tayi challenging dinsa "To barka da safiya shikenan?" "Yanzu naji magana.....barkanmu kadai" dorawa yayi da "Kun tashi lafiya,ya jama'ar gidan?" "Alhamdulillah,lafiya qalau,jama'ar gida mun barsu a gida,mu mun danyo balaguro nan cikin adamawa" "da wannan qafar anni?" Ya fada murya a kwance cikin nuna kulawa "Eh,to ya za'ayi,duk inda Allah ya tsaga sai ka taka saika taka din kafin lokacin da takun naka zai qare" "Hakane....." Ya fada a taqaice "Banji duriyar jafar ba" ta fada cikin zaquwa da son jin muryarsa,ajiyar zuciyar da taji jabir din ya sake sai da gabanta ya fadi "Maganarshi na kira nayi miki anni" ya fada a sanyaye "Menene kuma?" Ta tambayeshi gabanta yana faduwa "Anni har yanzu dai.....har yanzun babu wani ci gaba anni,sai abubuwan sunyi kamar zasu gyaru sai su sake rikicewa" "Kuma dai?" Ta fadi cikin tsantsar damuwa,kamar tana gabansa ya gyada kai "Wallahi anni,yanzu haka tun jiya banga fuskarsa ba,nayi iya bakin qoqarina ma naga ya fito ko ruwan zafi ne ya sha idan ma bazaici abinci ba amma ko motsi yaqiyi bare ya bani alamar da zata gayamin yana raye lafiya lau" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" kalmar da taja hankalin yuuma,ta koma ta zauna daga shirin tashin da takeyi din,ta kuma kamawa daada sukakai salatin tare. Sosai fuskar anni ta nuna alamun tashin hankali da kuma damuwa,wannan wata matsala ce data zama kusan jarrabawa cikin tata rayuwar,saidai a yadda Allah yayi mata komai a rayuwa,ya albarkaci zuri'arta,to ta dora hakan a matsayin jarrabawar da ubangiji kan yiwa kowanne bawa don ya gwada imaninsa "Ka kira wayarsa?" "Ya rufeta anni,yaqi bude wayar.....amma ki kwantar da hankalinki,koda bazaice komai zan sanar dashi daga bakin qofa,awa uku suka rage ya cika awa ashirin da hudu a dakin,idan har bai bude ba ya fito zan sanarma jami'an tsaro na qasar su shigo su balle qofar su dubamin shi,duk da jikina yana bani lafiya qalau yake,tunda fitilar dakinsa naga a kunne take tun jiyan kawo yau" "Jabir.....duk yadda zakayi ka tabbata kayi ya fito haka a dakin nan,na gaji da zamanku a wannan qasar jabir,bana jin zan barku kuci gaba da zama kamar yadda kukeso" "Kada ki damu anni" "Ka kula dashi don Allah,duk abinda ake ciki ka shaidamin,kada ka yarda da maganar babanku kan kada a gayamin komai,ni hakan shine kwanciyar hankali na" "In sha Allah,i will do my best anni" Jikinta a matuqar sanyaye ta sauke wayar daga kunnenta ta ajjiyeta a gefanta,sai ta hade hannayenta waje guda "Ya Allah.....mun tuba Allah,Allah ka kawo mana qarshen wannan matsalar,wannan damuwa Allah ka yanke mana ita gaba daya,ubangiji ka aiko mana da HASKE" "Ameen......lafiya kuwa anni?" Yuuma ta tambayi annin cikin matuqar kulawa da kuma damuwa,saboda ta fuskanci koma wacce irin matsala ce lallai ba qarama bace a wajen annin "Jafar ramatu,har yanzu jafar ya kasa komawa kamar kowanne irin mutum,jafar ba jahili bane....amma bansan me yasa ya kasa yarda da qaddararsa ba,gaba daya rayuwar jafar ba ita bace a yanzu,wani jafar ne na daban da dukka muke kallon an sauya mana shi,tsahon shekara uku amma komai ya kasa wucewa?" "Jafar dai anni?" Yuuma ta tambaya tana dubanta,kai ta jinjina "Shi.....tun daga shaheeda da amra suka rasu,bamu sake gane kan ja'afar ba,babu irin roqon Allahn da ba'ayi masa ba,ana kan yi masa ma,ba irin nasiha jan hankali da ban bakin da jafar bai samu ba,ba za'ace babu sauqi ba sam,saidai tashi danganar data zo sai tazo wani iri,duk da cewa dama miskili ne mara son magana me kuma bau dadden hali.....amma hakan baisa rayuwa ta naqasa tako ina ba,yana rayuwarsa kamar kowa,yana kuma yin dukkan wani abu daya dace da mutum kamarsa zaiyi,amma tun bayan nan jafar gaba daya ba shine tare damu ba,sai abun yayi kamar zai dai daita,sai ya sake dilmiya cikin damuwa me zurfi,na dauka zaman gidansa ke sake dagula masa lissafi......sai nasa ya tattaro ya dawo cikin gida,duk da haka babu wani canji,sai na sake tunanin kodai zaman kadaici ne?,tunda a baya shi din me aure ne?,na shiga nema masa yarinyar da zata dace dashi,ta kuma kula dashi......amma abun takaicin,wallahi ramatu yadda kikasan nayi busa a iska,baisan ma anayi ba,wannan yasa duka yaran suke kasa daurewa,saboda kowacce tana tsammanin samun kulawa da soyayya daga gareshi,to duka babu ko daya da suke samu,abinda yake sanyasu sarewa kenan,su kuma ce sun haqura......ba tare da sun duba cewa a yanzun shi din tamkar mara lafiya yake ba,zuciya da qwaqwalwarsa na buqatar magani ta hanyar mu'amalantarsa da dawowa dashi ya dawo ja'afar na asali......sannan koma meye sai ya biyo baya.....karo hudu kenan,amma dukkaninsu sun gaza daurewa zama dashi.......abinda ya bani mamaki da tsoro,yasa kuma na saare shine,wadda na nema masa a karo na shida 'yar uwarsa ce,a yadda abun ya dauko naji dadi.matuqa,saboda ina hangen haske da kuma waraka,don yadda yarinyar ta jajirce,ashe akwai mummunar manufa a ranta,dukiyarsa take hange,Allah ya toni asirinta,na gano na kuma watsa tafiyar,tunda dama shi wanda ake dominsa baima san inayi ba" shuru anni tayi tana maida numfashi,abun yana matuqar damunta da zuciya,a yanzu duk duniya zata iya cewa bata da matsala sama da wannan. "Iyaka nazari da hangena,babu wata hanya da zamu samu yadda mukeso sai ja'afar ya haqura yayi aure,saboda jabir bazai taba dawwama tare dashi ba,shima mutum ne,aure zaiyi,don maganar da ake yanzun,watanni kadan suka rage akai masa kudi da sa rana,yau idan jabir ya tafi,shikenan haka zamu zuba idanu muna kallon rayuwar jafar ta dulmiya ta nutse a gaban idanuwanmu?" Kai yuuma ke girgizawa,tsahon wasu mintuna shuru ya baqunci dakin,kafin yuuma ta saki ajiyar zuciya "Maganarki gaskiya ce anni,hanya daya ce tak ta fitar da ja'afar daga yanayin da yake ciki,hanyar kuwa itace,a sama masa mace mai tsananin sonsa,so fisabillahi saboda Allah,jajirtacciya da zata iya kasancewa koda yaushe tare dashi,mai juriya da zata iya daukan dawainiyarsa.....komai nisan zangon da zasu samu dashi kafin a cimma gaci...." "Wannan shine abunda muka kasa samu har yanzu" anni ta katsi numfashin yuuma,gyara zama yuuman tayi "A nawa tunanin kaf cikin matan da kuke nema masan,kuna sama masa ne irin matan can wajejenku,wadanda idanunsu ke a bude,suke ganin cewa 'yantattun mata ne su,wadanda zasu shiga gidan aure ne da dukka iko da isa irin wadda d'a namiji ke da ita,ba bautar aure zasuyi ba,zama ne na 'yanci da cin gashin kai" shuru ne ya sake ratsa dakin,sai hayaniya daga jama'ar dake karakainarsu daga waje jifa jifa tana ratsasu. Sosai maganar yuuma ta ratsa anni,ta kuma sanyata zama ta dinga wareta daya bayan daya tana nazarinta,lallai yuuman tayi wani dogon nazari da kuma tsinkaye,wanda ita kanta bata yishi ba tsahon lokacin da aka dauka matsalolin suna faruwa. Kusan rarrabuwa hankalin anni yayi kashi kashi,tana sauraren kira daga khalid,tana kuma ci gaba da nazarin maganar yuuma,tare da tunanin inda zata kamo bakin zaren,ta damu da ja'afar matuqa,tana kuma shiga damuwa ainun game da lamarinsa. Sam hankalin anni bai kwanta ba har sai data samu tabbacin lafiya lau daga bakin jabir "Ka bani shi jabir zamuyi magana" kai jabir din ya girgiza yana duban bakin qofar dakin da yake zaune a yanzu daura da ita,kamar wanda aka bawa gadin wajen "Bai fito ba har yanzu anni,duk da munyi magana,amma ina da tabbacin nan da dan wani lokaci koda baiyi kiran kowa ba zaiyi kiranki" ya fada with full confidence,saboda yasan tsakaninsa da annin "Shikenan,ka sake kula don Allah jabir" "In sha Allah anni" ya fada shima zuciyarsa na karyewa,bayason wannan ja'afar din na yanzu,yafi qaunar ja'afar dinsa na asali,duk da dama tun asali azama da ja'afar din sai shi,duk da yadda mutane suke daukansa suke kuma kallonsa....amma zai iya cewa bai taba rayuwa da wani mutum me dadin zama irin ja'afar din ba,wasu abubuwa ne game tattare dashi da idan ka fahimcesu shikenan. Wunin ranar gaba daya anni ta qarar dashi kan tunanin maganganun yuuma,ita kanta yuuma ta fuskanci yau din annin akwai damuwa fal tattare da zuciyarta,don ko abincin rana data kawo mata bata cishi ba sai kusan gefin la'asar,ta jima sosai tana waya da daya daga cikin yayanta. Sanda rana ta kammala faduwa,wanda ya zamana lokaci ne na sallar magariba,annin na daya daga cikin mutanen da basa wasa da ibada,wannan ya sanya ubangiji ya bata kyakkyawan tsufa da kuna qwarin jiki,banda ciwon qafa babu abinda yake damunta,zaka zaci shekarunta basu kai yadda take fada ba. Tana saman abun sallah tana lazumi,hannunta riqe da carbinta,ta tsakankanin labulen dakin tana hangen wulgawar mutanen gidan kowa na sabgar gabansa. Waiwayawa tayi ga laila dake kwance tana latse latsen waya abinta sakamakon bata sallah ta watsa mata harara,ta shafa addu'arta tana shirin mata magana akayi sallama daga tsakar gidan. Tsam anni tayi da ranta,saboda sautin muryar kamar tasan me ita,hakanan sai taji kamar ta saba jin muryar dama. Yuuma dake alwala tana wanke qafafuwanta ta waiwayo,sosai mamaki ya cikata,karon farko bayan wasu shekaru da suka shude rabon da taga maimunatu cikin gidan,don haka ta miqe cikin kulawa "Lafiya maimunatu?" Tafukan hannuwanta dake a dunqule ta budewa yuuma,kyakkyawar sarqar wuya ta ainihin dutsen wuri da kuma murjani na asali ta bayyana "Kun yada wannan ne a gidanmu dazu" zubawa sarqar idanu yuuma tayi,don tasan bata da ita,dutsene maj tsada wanda su kansu fulani sunsan dajarsa "Anya kuwa?.....amma....qarasa rumfata ko anni ce,don nasan da laila ba zata saka wannan ba" kai ta gyada tana sakin siririn murmushi,sannan ta fara takawa zuwa rumfar yuuman,gabanta yana dukan uku uku,batason ta hadu daada mahaifiyar ibrahim,bare shi ibrahim din kansa,ita daya tasan irin jan kunne da kums gargadi da tasha daga wajen inna furera,ba shakka banda akwai qudurin da innar keson cimmawa ma,babu abinda zai sanyata ta kawo musu sarqar. "Wa'alaikumussalam,shigo mana" anni ta fada tana zubawa maimunatun idanu sanda take sanyo kai cikin dakin,idanunta ya sauka ga gefe wuya da kuma kunne zuwa kuncin maimunatu karo na barkatai a yau din,ita din bata jiya bace ba kuma ta yau bace,wannan tabon tun dazu data kalleshi ta tabbatar da cewa na duka ne,to amma me yarinya kamar maimunatu tayi da za'ayi mata irin wannan dukan?,me aka saka akayi mata wannan dukan dashi?,sai taji ranta yana baci abinda.bai faru ba a yanzu. Ita din wata irin macace da bata qaunar zalunci ko kadan,ko kai waye,ko yaya kake da ita,matuqar ta fuskanci kana da dabi'a ta zalunci yanzu zaku raba hanya. Gaban annin ga durqusa,tasa hannu biyu tana miqa mata sarqar,anni ta miqa hannu ta karba "Hukumullahi...ni nayar da ita,tabbas,to kinga basan ma ta fadin ba banda Allah ya tsananta rabo yanzun kin ganta kin kawomin,da haka zan yita bulayin nemanta" anni ta fada tana sakarwa maimunatu murmushi,zuciyarta da ruhinta cike da soyayya da kuma kaunar maimunatun,halayenta mabanbanta ne da halayen sauran al'umma,abar yabo ce ta gaske kuma a zahiri,godiya ta yiwa maimunatun sosai,tans juya abun a ranta ta tayar da sallah. "Anni.....gaba daya yau tunani ya sanyamin ke agaba,komai yayi zafi maganinsa Allah anni,aci gaba dai da addu'a,wataran komai zai warware in sha Allahu" yuuma dake ajewa anni kwanon tuwo ta fada,don idan annin tazo har ta koma babu ruwanta,irin tasu cimar takeci,takan ce ko a gida rashin samun me tsaya mata da irin cimar ne yadda takeso,amma ita bata da kamar irin abincinsu. Ajiyar zuciya annin ta sake tana miqe daya qafar tata data jima a lanqwashe ta fara yi mata tsami "Ramatu,inajin wani abu a jikina tattare da yarinyar nan" "Wa fa?" Yuuma ta tambayi anni tana tattara hankalinta gareta "Maimunatu" "Ohhh.....maimunatu?" "Ita.....tun dazu da mukayi magana dake ramatu nake juya zancan cikin raina,da magaribar nan bayan yarinyar tazo ta kawomin sarqa ta,sai gaba daya tunani ya damfaru a kanta,na lura da irin dabi'un da nake buqata tattare da yarinyar,ta hada juriya haquri da kuma amanar da zata iya zama da ja'afar,dabi'u da kuma halayen da tabbas zata iya dawo da ja'afar yadda yake ja'afar dinsa" "What!" Laila dane kwance ta fada cikin rata,har maganar tata taso ta fito fili "Me anni ke fada ne?,ta manta waye ya ja'afar?,ta manta waye yaa J?,the classic and unique guy?,ya ja'afar fa ake magana da wata bafulatanar ruga?,saura kadan ta miqe ta zauna,amma sai taci gaba da kwanciya,tanason jin yadda maganar zata kaya. Dukka idanunta yuuma ta fidda tana duban anni "Anya kuwa anni?,bakiyi ragon tunani ba?ja'afar fa?" "Me yasa kika ce haka ramatu?,ko hasashe na bai hasaso dai dai kan dukka nagartarta ba?" Kai yuuma ta girgiza a hankali tana juya abun a ranta,bai kamata tayi shuru ba wani abu ya kasance daga baya kuma ta zama abar zargi ba daga kowanne bangare,abu me muhimmanci ta fara gayawa anni wace ainihin maimunatu tukunna "Dukkan abinda kika hasaso akan halayen maimunatu haka suke,yarinyar har tafi haka ma,dukka rugar nan sunsan da wannan,saidai wani baqar al'ada da jahlici gami son rai sun rufe musu idanu basa ganin wannan,bari na gaya miki wace maimunatu tun daga tushe,wanda ba kowane cikin rugar nan ya sani ba,domin kuwa,ni din,nice qawa qwaya daya tilo da mahaifiyarta keda ita a rugar nan,wadda bata da kamata,wani rikici da ya faru tsakanin gidan da gidan nan yasa bappa ya yanke huldata dasu saboda wanzar da zaman lafiya,abinda ya rabamu kenan da shatu,har zuwa sanda ta koma ga mahaliccinta" kai anni ta gyada tana bada hankalinta zuwa ga yuuma,yayin da itama yuuma ta nutsu sosai ta fara yima anni magana "Furera mahaifiyar gaje,waddda kukayi ciniki a hannunta,mata ce ga jauro,wadda keda yara biyu dashi,macace mara mutunci ta gasken gaske,wadda ba kasafai ake tabota ta qyale ba,me son abun duniya ce da kuma masifar son 'ya'ya,asalinta bafulatanae gembu ce,jauro ne dan wannan rugar,muna zaune tare da ita tsahon shekaru,kwatsam tayi baquwa,wadda ta shigo rugar nan tare da furera da taje ganin gida,matar itace shatu,wadda tazo da diyarta maimunatu......sun shigo tare da tarin dabbobi wadda dukka dabbobin nan mallakin shatu da diyarta maimunatu ne,amma kuma a idanun kowa dabbobi na furera ne,don a haka ta gayawa kowa wannan labarin,ta shaidawa mutane cewa gadonsu dama taje gida karbowa ta taho dasu,ta kuma hado da wadda zafa dinga mata kiwo tana biyanta wato shatu,abinda zai baki mamaki,shatu ba kowace bace a wajen furera face 'yar uwarta da suke uba daya,bata da ikon musawa ko qi,saboda a sannan shatun na cikin wani yanayi na tashin hankalin rayuwa,tana neman mafaka,mahaifin maimunatu baqo ne,irin baqin dake shigowa garin na gembu saboda huldar kasuwanci da kuma yawon buda idanu,a nan yaga shatu ya kuma tsaya kai da fata sai daya aureta,a nan garin ya barta saboda ta nuna tafison zama cikin danginta,yana zuwa yana ganinta yayi mata kwanaki ya koma,mutum ne mai arziqi,don haka gida na alfarma ya ginawa shatu,ya zuba mata dukka kayan alatu da more rayuwa,ta yadda gidan shatu shi ya zama abu kwatance da kuma burin kowa cikin garin nasu,wannan ya haifar da hassada daga zuciyar 'yan uwanta da suke 'yan uba,saboda ita shatu su biyu mahaifiyarsu ta haifa a gidan,ita da 'yar uwarta sa'ade,kusan jinin dakinsu ne haka,sannan kuma da baiwar zallar kyau da Allah yayi musu fiye da sauran 'yan uwansu,itama sa'ade nata mijin me hali ne sosai,hakan ya sake haifar da zallar 'yan ubanci a tsakaninsu,saidai sunata dannewa saboda suna rabarta suna kuma samun akhairai da abun duniya daga wajenta,kasancewarta ba mai rowa ba,a haka ta haifa maimunatu,dukka alhaji na zuwa wajenta ne yayi mata satittika ya tafi,bayan ta.haifi maimunatu yake maganar zai kaita taga danginsa,saidai kuma wata tafiyace ta taso masa,wanda ya dauki tsahon watanni kafin ya dawo,koda ya dawo din kuma shima yana da niyyar kaita,har sun shirya sun saka rana,yace zai taho takanas daga kano ya dauketa. Shiri sosai shatu tayi domin zuwa ganin surukanta,ta shirya maimunatu da kyau wadda ke samun gata kamar babu gobe,itama haka,saidai haka ta yita jiran alhaji amma shuru babu shi babu dalilinsa,nata da wayar hannu bare ta nemeshi,haka tayita zaman jiransa har dare yayi ta fidda tsammani,ta sanyawa ranta qila wani abune ya tareshi,ta barwa gobe. To washegarin ma dai haka ta yita jiransa shuru babu shi babu labarinsa,haka wata washegarin,wasa wasa sai ga kwanaki nata tafiya shatu bata sake ganin gilmawar alhaji ba,abun ya daga hankalinta qwarai da gaske,tafi tafi watanni suka fara shudawa shuru babu shi babu dalilinsa,ga ciki da ya bayyana a jikinta,ita dai ta yarda da alhaj dari bisa dari,saboda iya tsahon zamata dashi tsakaninsu ita dashi babu komai sai son barka,mutum ne mai son addini da kuma kiyaye dokokin Allah,kusan a wajensa shatu tayi karatun addini mai dan dama wanda ta dinga koyawa maimunatu,duk da a sannan ta sanyata makarantar islamiyya da boko,amma kamar tasan yadda rayuwa zata juya musu,sai take zama duk bayan sallar magariba take mata nata karatun,ganin cewa yarinyar tana da budaddiyar kwanya dake saurin kwashe karatu,don tun bata isa sakawa a makaranta ba ta sanyata,tace tayi wayon acan,hakan yasa adan lokacin ta samu karatu me yawa,tana cika shekara tara zata shiga ta goma ta gama primary,mahaifinta nada niyyar yi mata shirin shiga makarantar gaba wannan abun ya faru" *Follow my arewabooks account for more new pages* HUGUMA *11* "Yau da gobe bata bar komai ba,hakanan zara bata qyale dami ba,dukka kayan abincin da shatu ke dasu wanda alhj ke jibge mata suka faru suka qare,ta fara kame kame,a sannan yan uwanta suka fahimta,sukayi mata caa,yar uwarta saade tace kada ta kulasu,ita ta dinga taimaka mata har zuwa wani lokaci,wanda kishiyar mahaifiyarsu wadda wajenta suka rayu sanadiyyar rasuwar mahaifiyarsu tun suna qananu ta tayar da borin qarya,ta tara manyan gari,ta fada musu qabli da ba'adi kan rashin dacewar zaman shatu ita daya cikin gidan,tace saidai lallai ta dawo gabanta da zama,saade yayar shatun bata qalubalanci hakan ba,hakan yayi,duk da tasan badon Allah inne tayi hakan baAmma kuma bayan giya akwai wata caca,maza maza tayi ta sanya aka saida gidan da shatu ke ciki,tunda mallakin alhj ne,ya ginawa shatun,ta tattara kudin ta siyawa shatun dabbobi ta damqa mata,saboda gudun abinda kaje yazo,babu jimawa shatu ta tattara ta koma gida ita da maimunatu,gidan da suka fara sabuwar rayuwa me cike da qunci da kuma takura,wahalhalu iri daban daban,zuciyar shatu na cike da qauna da kuma begen mijinta,jiki da zuciyarta sinqi yarda da zancan daketa yawo a garin kan cewa,mijinta guduwa yayi ya barta,tafi kowa sanin halinsa,tayi imani bazai aikata mata haka ba. Zama ya sake tsanani a wajenta sanda inne ta fahimci cikine da ita,tayi tsalle ta dire kan ba za'a haifa mata dan da bashi da uba ba,maganar data tsayewa shatu da saade a rai,ta kuma kusan haifar mata da ciwo,a lokacin saade bata kusa da ita,kasuwanci ya shillata ita da mijinta zuwa benin republic,wanda tayi matuqar baqincikin hakan,saboda sanin halin da 'yar uwarta take ciki,amma babu yadda zatayi dole tabi mijinta. Ana tsaka da wannan fa shine inna furera taje garin,ita tunda ta qyalla idanu taga dabbobin da shatu ke dasu tayi mata romon bakin ta biyota rugarsu tayi xamanta,ta kula da dabbobinta ta haihu a can babu takura. A zaton shatu ta samu mafaka a wajen yayartata,saidai tun basu kai ga shigowa rugar ba ta fara yanka mata sharuda tare da shaida mata dokokin da rugar ke dasu,suka kuma yi yarjejeniyar dabbobinta zasu shiga a mazaunin na ita fureran,idan ba haka ba zaayita kawo musu farmaki ana kashesu tunda ita baquwa ce. Ko a sannan shatu shekarunta basu fi ashirin da hudu ba,saboda auren wuri akayi mata kamar yadda aka saba. Shatu ta shigo baquwa a rugar nan,wadda hatta da kyanta ya banbanta da irin namu,babu tausayi ko tsoron Allah furera ta maida shatu da maimunatu tamkar bayi da basu da 'yanci,shatu bauta maimunatu bauta,Allah ya zubawa shatun wani irin haquri juriya da kuma kau da kai wanda cikin irin nata ta sanwa maimunatu,don babu lallai tayi yakai irin nata,a haka dai suke rayuwar. Abinda ya faru ya kuma janyo shatu da maimunatu suka zama abun qyama shine......a al'darmu ta fulani,baka ganin nagge ko sauran dabbobi ka nuna su tankasu,komai kyau da burgewar da suka baka,cikin irin haka,cikin rashin sani shatu taga wasu nagge na bappa labaran,yana gab da fita dasu kudu,ranar an fiddasu kiwo ta nuna wata babbar nagge a cikinsu tace a haka kamar lafiyayya me kyau da ita,amma kuma bata da lpy,suka yita fada dame kiwon,aka mata ca,ta bada haquri,saboda mantawa da tayi ta aikata hakan,kuma tace tana musu tsoron asara ne,magani ya koma a maidata gida a bata,koda suka dawo gida baice bata da lafiya ba yadda shatu ta fada,ba'a wayi gari da naggen ba ta rasu,rigima sosai daada taso a tayar,amma bapp ya hana,abinda basu sani ba ni da kaina bayan asuba na fita zan dora sanwar safe,na lura da naggen bata da kuxari yadda ya kamata,ni da kaina nasan tabbas bata da lpy,to amma dana fada qaryatani daada tayi,tace kawai dai don tana zuwa wajena ne yasa nakeson kareta,anyi wannan rigimar ta mutu,shatu da tsohon cikinta taje diban ruwa matan gidan barau daya daga cikinsu ta takaleta da fada yadda suka saba mata,tunda muke da shatu bata taba gayamin ko kawomin qarar kowa ba,amma inajin labarin yadda wasu cikin rugar suka matsanta mata,a ranar taso dauke kai amma yau da gobe,ga yanayin tsohon ciki haihuwa ko yau ko gobe,talatu bata duba wannan ba ta dinga ja mata riga shatu na gocewa,daga qarshe dai da talatu taga ba zata kulata ba sai ta tureta,wanda sauran kadan ta afka cikin rafin,Allah ne kawai yayi ruwan ba shine ajalinta ba,sosai ran shatu ya baci bayan tasha da qyar,cikin bacin rai idanuwanta cike da hawaye ta kalleta "Na dauka ko banci darajar komai a wajenki ba zanci darajar cikin dake jikina,tunda kema macace,idan kinyi hakane don ki tozarta ni kije,Allah yana gani,kuma ina fatan kiga sakayya da gaggawa anan kusa" daga haka shatu bata qara ba bata rage ba,ta dauki ruwanta ta wuce,suka taru suka yita maida magana,tare da maido maganar nagge,a nan suka fara qulla wataqil mayya ce ita din,kwana biyu tsakani kuwa talatu taje diban ruwa ruwan yayi ciki da ita,ya kuma zama ajalinta,aka fara lugwigwita magana tare da fara yada jita jitar shatun mayyace,kafin kace me?,magana ta fantsama a gari,dangin talatu da sauran mutane 'yan bani na iya suka dauki sanduna sukayi gidan furera kan sai an fiddo shatu sun kasheta,ya tabbata mayyace ita,da qyar da sudin goshi qurar ta lafa,baiwar Allah shatu,ashe sanadin wannan tashin hankalin naquda ta tasammata,furera haushin abinda ya faru tayi banza da ita,daga ita sai maimunatu ne suka yita fama,daga qarshe tace maimunatun ta lallaba ta kirawo mata ni,har maimunatu takai bakin qofa ta qwala mata kira,saita tsaya,ta yafitota da hannu ta koma gaban shatun ta duqa "Daada,akwai wani abun da kike so ne?" Murmushi ta sakar mata,ta daga hannayenta ta cirw dukka duwatsun jiki da maimunatu ta dade tana qulafucin tabar mata ta zura mata su,saidai yarinyar a sannan sam bataji farincikin da take ayyanawa zataji ba duk sanda daadar tata tabar mata dutsunan "Daada kin barmin ne wai?" Kai ta gyada "Na bar miki maimunatu......kiyi haquri kiyi haquri.....kiyi haquri kinji,ki fuskanci rayuwa duk yadda tazo miki,ki zama mai gaskiya da amana,karki yadda a kamaki kinci amanar wani,idan kinga saade,kice ina mata fatan alkhairi" sanda yarinyar ke gayan abinda uwar tace nayi mamakin yadda ta iya riqewa,hankalin maimunatu a sannan ya tashi sosai duk da qarancin shekarunta,ba kowa zai gane hakan ba sai wanda irin haka ya sameshi,cikin rudewa tace "Daada" hannu ta daga mata "Barci nake ji,yi sauri ki kiramin yuuma" maganar data sanya maimunatu tashi ta fita a dakin da gudu,fitar da ta zama silar rabuwarta da mahaifiyarta kenan rabuwa ta har abada,don koni sanda na shiga wajen shatu rai yayi halinsa,haka akayi mata sutura bata ko haife abinda yake cikinta ba,sanda na koma gida da daddare randa shatu ya rasu,tunda na tsaya na taya maimunatu da bata dame rarrashinta zama,mahaifiyarta ta rasu ta barta babu ko mutum daya da zata jingina dashi tayi kuka taji sauqi cikin ranta,Bappa da kansa ha sameni,ya shaida min ya yanke hulda da wata alaqata da duk abinda ya shafi shatu matuqar shike aure na,duk randa na kuskurewa hakan kuwa,zai dauki tsatstsauran mataki a kaina,bansan me aka gayawa bappan ba bayan fitata wajen shatu,amma dai na sani cewa akwai qullin daadar himu da kuma furera a ciki da suka sake tunzura komai,don kuwa bappan mutum ne mai sanin ya kamata,sannan ta yaya zaa rabani da maimunatu kuma abar mu'amalar dake tsakanin furera da daadar himu?,bayan duka gida daya ne,abu daya ne?,duk da furera ta cikasu da labaran qarya na cewa babu abinda ya hadata da shatun illa aikin bauta data dauketa,mutuwar shatu sai furera ta sake sakankancewa,ta mallake dukka dabbobin shatu da maimunatu suka zama nata,maimunatu bata tashi a komai ba illa me aikin bauta,ta riqeta wani irin riqo na qunci da kuma wahala,dole inaji ina gani na dauke idanuna daga kan maimunatun,nayi kamar bansan tana raye ba,saidai ban fasa mata addu'a ba da nema mata sasauci" "Yanzu 'yan wadan nan abubuwan sune suka zama hujja da kuma dalilin da ake qyamatar yarinyar bayan cikin abun babu wani abu guda daya data aikata?" "Sune anni" kada kai kawai anni keyi,wani abu ya tsaye mata a zuciyarta me taba rai,tana kwatanta yuuma da maimunatu,inda an samu sakaci ko wani abu makamancin hakan haka zai iya faruwa da yuuma kenan sanda tana qarama,duk da ita tana gaban mahaifinta ne cikin soyayya da kulawa a sannan?. "Wannan duka ba hujja bace,zallar jahilci ne da kuma son zuciya,kuma tabbas sai Allah ya yiwa yarinyar sakayya,zan dauke maimunatu daga wannan garin don bata cancanci zama a nan ba,maraya?,maraya wasa ne?,daka taba maraya hawayensa guda daya tak ya diga a qasa saboda kai,gwara ka rasa dukkan abinda ka mallaka ciki harda lafiyarka,kukan maraya masifa ne bare a sakashi a damuwa" yalwataccen murmushi ne ya bayyana fuskar yuuma "Da nafi kowa jin dadin hakan anni,tabbas zanfi kowa murna" "Kafin na wuce zan karba maimunatu zan wuce da ita,in sha Allah qarshen kukanta yazo,lallai mahaifiyarta macace mai nagarta,nagartar da nake jin yaqini da tabbcin akwaita tattare da maimunatu,tunda dukkan alamu sun bayyana" "Amma anni wani hanzari ba gudu ba.....anya kinyi duba da tarin banbanci da tazarar dake tsakanin ja'afar da maimunatu kuwa?,shirinki me yuwuwa ne?" Tambayar dake rai da zuciyar laila kenan,labarin ya dauki hankalinta cike da mamaki da kuma al'ajabi,zuciyarta kuma ta narke matuqa da tausayin maimunatu "Nasan ta inda zan bullowa lamarin,ki tayani da addu'a,kiyimin fatan dacewa" ajiyar zuciya mai qarfi yuuma ta sauke "Allah to yasa a dace,yasa ta silarki marainiya maimunatu zata samu salaama a rayuwarta" "Ameen ya hayyu ya qayyumu" anni ta fada tana lanqwasa yatsunta,tare da tunanin ta inda zata fara. *_Arewabooks::huguma_* ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 12 Ajiyar zuciya ta sauke sanda ta tabbatar ta maida sarqar wa anni,ta godewa Allah da ya hani inna furera sanya son zuciyarta a gaba ta hana a maidawa anni sarqar,ta tabbata da ta aikata haka ba zata taba samun nutsuwar zuciya ba,haka zuciyarta take,bata qaunar haqqi koda qanqani a kanta,dalilin da yasa ta guji kiwon dabbobinta da bugu kenan,ta zabi horar dasu da magana. Sosai hankalinta yayi nisa cikin zuzzurfan tunani,abinda ya sanya kwata kwata bata ankara da tahowarsa ba,sai da taji ta bugi wani abu sannan ta tsaya cak,ta kuma ja da baya da sauri tana kai dubanta gabanta. Himu ne,sanye da kayan fulani,ya fito a bafullataninsa sak,kayan sun matuqar karbarsa sun kuma haskashi matuqa,saidai babu fara'a ko walwala kwata kwata saman fuskarsa. Gabanta ne yayi mummunar bugawa sanda ta tuna da gargadi da kuma izayar da tasha hannun inna furera duka akan himu,abinda ya sanyata yin gaba da sauri ta rabeshi zata wuce,saidai cikin hanzarin shima ya matsa ya tare mata hanyar,da azama ta koma daya hannun nan ma ya bita ya tare,ya kare ko ina,bata da zabi illa ta roqeshi "Don girman Allah ka bani hanya na wuce" "Saboda me maimunatu?,me yasa kike guduna?" Tsoro ne ya sake kamata,sam bazai fahimci halin da take ciki ba,wannan tsaiwar da yayi a gabanta sai takejin kamar ana tsigar ranta "Magana nakeso muyi dake maimunatu" wace magana?,a yanzun akwai.maganar kuwa da ita din zata fahimta? "Kayi haquri,bazai yiwuba,ka barni na wuce" "Dole ki tsaya ki saurareni maimunatu,don me yasa zaki saurin bada kai akan soyyayarmu?,kodai dama bakya sona?ni daya nake kidina da rawata?" Tuni hawaye ya balle mata,himu so yake kawai ya janyo mata bala'i,baisan yanayin da take ciki ba,da bai tsaya haka a gabanta ya tilasta mata sai sunyi magana ba,bayan ita bafahimta take ba,ta juya baya a matuqar razane sanda taji takun tafiya,take qafafunta suka fara rawa,sai shima ya waiwaya yana duban hanyar. Kaf jinin jikinta sai daya daskare sanda taga inuwar mutum kuma macace a wajen,abinda ta baiwa ranta shine daada ce ko zubaida ko safiya,ta saddaqar ta gama yawo,kashinta kuma ya bushe,tun daga fuskarta zuwa tafin qafarta sukayi sanyi qalau "Kuyi haquri,na katse muku jin dadin ku ko?,zan dan wuce ne?" Laila ta fada tana dan sakin fuskarta,ta fuskanci akwai wani abu me kama da soyayya a tsakaninsu,to amma anni tasan da haka kuwa?. Jin baquwar murya da sautin da ba na fulani ba ya taimaka wajen dawowarta hayyacinta,matsawa laila himu yayi ta fara wucewa,abinda ya baiwa maimunatu damar yin wuf tabi bayan lailan "Maimunatu" ya kirayi sunanta,saita qara hanzari da kyau ta fara shawarar bi ta duhuwa don kada ma ya biyota ya jawo mata jarfa "Ina sonki.maimunatu,kuma wallahi bazan fasa sonki ba koda ke baki sona,zanci gaba da sonki har sai na sameki a matsayin matata" kalamai na qarshe kenan dataji daga bakin himu,ta qara hanzari,tana jin cewa inama itadin tana cikin nau'in mata masu hanzari wajen tafiya,lallai da tayi amfani da wannan don ganin ta sake yin nesa da ibrahim. "Haba 'yammata,saurin me kike haka?" Muryar laila dake biye da ita ta ratsa kunnuwanta,yadda ta juyo kawai zai gaya maka har yanzu a tsorace take "ya kike gudun wanda yake sonki?" Laila ta fada a tausashe bayan ta iso gaban maimunatu ta tsaya,ta kuma dora hannunta saman kafadar maimunatun zuciyarta na narkewa a tausayinta. Daddadan qamshin dake tashi jikin laila maimunatu ta zuqa zuwa hancinta,laushin turaren ya sanya zuciyarta karyewa,yadda lailan ta tambayeta cikin taushi da nuna kulawa yasa rauninta ya ninku,take hawaye ya cika idanunta,a wannan lokacin gaza tareshi tayi,sai kuka ya qwace mata. Kasa hanata laila tayi,duba na tausayi takewa maimunatu,tana kwatanta kanta a matsayinta,tana kwatanta inda itace ta yaya zata rayu babu abbi babu momma?,ya rayuwarta zata kasance?,maimunatun jaruma ce qwarai kuma abar tausayi ce ga dukka wani me tausayi. Dole ce zata sanyata ta guji himu ba din ya cancanci a gujeshi ba,bata da yadda zatayi matuqar tana son tsira da lafiyarta da kuma rayuwarta,goge hawayen fuskarta ta fara da tafin hannunta bayan taji zuciyarta ta fara mata sanyi daga radadi da suyar da take mata. "Kiyi haqurk,komai mai wucewa ne,watarana sai labari" daga kai tayi ta bi laila da kallo jin abinda ta fada,tasan wace ita ne?,tana tantama,inda tasan wace ita tatabbatar ba zata tsaya tana magana da ita ba,amma duk da haka a sanyaye sai tace "Miyatti" murmushi laila ta sake "Me kenan?" Murmushin da bata shirya masa bane ya qwacewa maimunatu,ta manta ba da daya daga cikinsu take magana ba "Nace na gode" murmushi lailan ta sakeyi "Babu komai" daga haka maimunatu ta juya tayi gaba,sai kuma a sannan fargabar kada inna taga dadewarta ta qara cikata,don haka saita qara sauri. Bin maimunatu da kallo laila tayi har sai data bace mata,ta sauke ajiyar zuciya me nauyi,a yanzun tana jin zuciyarta ta gamsu dari bisa dari da daukar maimunatu da anni zatayi,saboda hakan tamkar wani babban jihadi ne a wajensu gaba daya,to amma kuma dai dai da qwayar zarra zuciyarta bata gamsu ko kuma kwanciya da qudurin annin na biyu ba,yaa ja'afar fa?,ya ja'afar take magana,ba khalid ba,ba kamal ba,bare jabir,ja'afar take cewa,saita girgiza kai kawai tana komawa hanyar gida,don dama neman network ta fito yi,cikin gidan gaba daya network ya dauke. A ranar maimunatu tayi kuka tayi kuka qwarai da gaske,tana jin cewa farin cikin rayuwa yana sake yin nesa da ita,tana jin cewa tana sake rasa komai nata,sai ta samu kanta da addu'a a karon farko "Ya ubangijina,ka kulaa dani,ka kula da lamarina" saita juya gefe daya tana sake curewa waje guda,hawaye masu zafi na tsiyaya har zuw cikin kunnenta. **********Da fari sanda inna furera taga yuuma a gidanta tadan hade rai,amma kuma data tuna cewa dukka arziqin da tayi kwanaki biyu da suka wuce ta silar 'yaruwarta ce sai ta sakar mata fuska,harda sanya laulo ya dauko mata tabarma,ta kuma qwalawa maimunatu dake baya tana ta faman wankau na kayansu,wanda har yau ma jauro ya hana zuwanta kiwo "Wadi diyam(kawo ruwa)" a nutse ta qaraso ta tsugunna gaban yuuma tana ajjiye ruwan sannan ta gaidata,yuuma ta bita da kallo zuciyarta na tsinkewa tana amsa mata,kullum kwanan duniya maimunatun sake fita daga hayyacinta da kuma kamanninta take,amma a yanzun tayi imanin inda maimunatu zata,zaya kasance mata tamkar tana hannu mahaifiyarta,koma sama da haka. Bayan gaisuwa data biyo baya tsakaninta da inna furaira,wanda ta manta yaushe rabon irin haka ya shiga tsakaninsu,sai yuuman ta gyara zama tana lanqwashe qafafunta "Wajenki nazo furaira" "Allah yasa alkhairi?" Ta fada tana tattara hankalinta ga yuuma "Alkhairin ne,don kullum mu shike tare damu" "To ina jinki" "Ina tunanin baki manta dattijuwar da kukayi cinikayyar nagge da ita ba kwana uku da suka wuce ko?" Fadin haka kawai ya yalwata fara'a a fuskar furaira "Har nabar duniya ai bazan manta da wannan baquwar alkhairin ba" "Ashe kinsan wataran zaki bar duniya furaira" yuuma ta fada cikin ranta,amma a fili saita gyada kai "Ita din tamkar mahaifiya take a wajena...." "Allahu akhbar....." Inna furaira tayi hanzarin fada tana duban yuuma "Amma kike zaune cikin wannan rugar tare damu?" Murmushin da yafi kama dana yaqe yuuma tayi,saboda ita sam ba qaunar wata doguwar magana take ba tsakaninta da furaira "Aure ya gaji haka,yakai diya mace duk inda yaso" "Shakka babu" ta amsa tana qarewa yuuman kallo,ba banza ba ta zama macen da duk fadin rugarsu babu me sutura irin tata,hakanan yanayin hutu da jin dadi daya bayyana qarara tare da ita,hakanan cimar gidan bappa labaran ba inda labarinta bai karade ba,dama daadan ta taba bata labari kan wadda take kawowar "Itace ta aikoni,wato kinsan jikin girma,tana fama da ciwon qafa lokaci lokaci,kuma tana da buqatar mataimaki dai a kusa wanda zai dinga mata wasu ayyukan,to taga maimunatu ta kuma yaba da amanarta,shine tace nazo na tambayar mata ko zaki bata ita,zata dauketa a matsayin ma'aikaciya da zata dinga biya da albashi me tsoka,hasalima tace ki yanka dukka albashin da kikeso a dinga biyanki duk wata,sannan kuma dabbobinki da take kiwo,ki dauki.masu kiwo suma su fadi abinda za'a dinga biyansu,ita zata dinga biya shima" shuru furera tayi,fuskarta na rage kaifin fara'ar dake kanta a dazu,ga qoshi ga kwanan yunwa,haqiqa ko shakka babu wannan albishir albishir ne me dadi a gareta,arziqi kuma har cikin gidanta,saidai kuma ta yaya za'a zabi maimunatu bayan ga gaje?,saboda.matar kana kallonta kasan tana cikin sukunin rayuwa da jin dadi,ita kuwa duk duniya babu wanda takeso ya rayu cikin walwala irin gajenta,gaskiya bata jin zata iya bada maimunatu,wadda take sanya ran tana aurar da gaje ba jimawa ta aurar da ita,ta kuma dora da kiwon da take mata koda tana gidan buderi,sunyi yarjejeniya ya kuma amince,dalilin da yasa.ma ta alqawarta masa auren maimunatu kenan. "Me kika ce?" Yuuma ta fadi ganin furera ta shiga zuzzurfan tunani "nakega me zai hana na baku gaaje?,babu abinda maimunatu zatayi wanda ba zata iya yinshi ba" murmushin takaici ne ga qwacewa yuuma,tana da wannan masaniyar amma ta tattarawa maimunatu dukkan wata wahalar aiki "To ni kinga 'yar aike ce,kuma taga gaaje ta kuma ga maimunatu amma ta zabi maimunatun,ina ganin idan maimunatun ba zata samu ba,zanje na shaida mata kawai,saimu laluba cikin yaran dake rugar" yuuma ta fada tana miqewa,abinda yadan kadan hankalin furaira "Aah,ba za'ayi haka ba,amma inason a bani lokaci kadan zanyi shawara,zan gayawa kuma jauro ma" kada kai yuuma tayi,tasan ba wani jauro da zata gayawa,amma sai ta bita a hakan,sukayi sallama ta tafi. Yuuman na fita ta aiki laulo a sirrance yayi mata kiran daada,bata bata lokaci ba kuwa tazo,ta kuma rattaba mata dukan bayani,kishi ne sosai ya kama daadan,me yasa bata nema safiya ko zubaida ba?,indai ko haka ne bata ga dalilin da zata aika gaje ba su da sukafi kusa da daadan suna zaune,gwara maimunatun taje,ko da zata samu kudi daga gareta ai dai ba zata samu jin dadi da daular dake gidan anni ba "Ya zakiyi ragon azanci irin haka furera?" "Kaman yaya innar himu?" "Ta yaya zaki tura gaaje?,tafiyar maimunatu ai shine dai dai,zata je fa samowa gaje kudin aurenta da wanda zaki mata kayan daki da sauransu,don na tabbatar miki himu gini yake na kere sa'a,kinga kina buqatar kudin da zaki mata duk wata hidima,na tabbar jauro zaiyi iya abinda yaga zai iya ne,abu na biyu idan maimunatu ta tafi dole ne himu ya sake haqura da ita,ya kuma tattara hankalinsa ga gaje,saboda maimunatu tayi masa nisan da yasan bazai ganta ko ya sameta ba,kinga komai zai tafi mana dai dai babu wata matsala,sannan ke kanki yarinyar nan alaqaqai ce a wuyanki,har mamaki nake yadda kika ci gaba da riqon diyar mai miki kiwo,kinga yanzun kuwa salamun salamun" sosai inna furera ta gamsu da shawarar daada,tabbas ita din masoyiya ce,kuma maganganunta na bisa hanya,maimunatu zata zame mata tamkar wani jari,hankalinta kwance zata zama wata me arziqi tana daga kwance,da wannan gamsuwar ta taka da kanta har gidan bappa labaran,ta kuma tabbatarwa da anni cewa ta amince. "Nawa ne kudin da za'a dinga biyanki na aikinta?" Anni ta tambayi furaira da kanta tana kallonta,tsanarta na shiga ran annin,murmusawa tayi sannan tace "Ina ganin a duk wata ki bada dubu biyar" inna furera ta fada tana fatan anni ta amince da kudin data yanka din. "Na ninka miki sau hudu,zan dinga aiko miki da dubu ashirin da kuma ladan kiwo" mamaki ne ya cika furera qwarai,har ma ta rasa abinda zata fada,bata taba tsammatar samun haka daga anni ba,ashe maimunatu alkhairi ce tare da ita,ashe ita shatu ta haifawa. Cikin tsananin murna da farinciki ta koma gida,ta samu maimunatu ta gama da wanki ta kuma dora sanwar abinci,bayanta kamar zai karye saboda duqen da tasha,sanda fureran ta kirata ta shiga fargaba da tsoro "Zauna nan,ki kuma saurara da kyau kiji abinda zan gaya miki" qas tayi da kanta,zuciyarta na tsananta bugu,tana ayyano masifu kala kala a ranta,ko waccece ta sameta a yau din?. "Dattijuwar da tazo gidan nan kwana uku da suka wuce,ta ganki kuma tayi sha'awar tafiya dake domin ki taimaketa da aikace aikace,na kuma amsa mata,don haka ki zama cikin shiri,daga gobe zuwa kowanne lokaci zata daukeki ta tafi dake can garinsu" da fari maganar ta razanata,ta kuma rude sosai,ta lumshe idanunta tana kiran "Ya Allahu,ya Allahu" a hankali sai taji zuciyarta ta fara dai daita data tuna daga inda matar ta fito,daga bangaren yuuma,yummar da zata iya cewa kaf fadin rugar ita kadai ce masoyiyarta,ta tabbatar yuuma ba zata bari abunda zai cuceta ya rabeta. Ta sake maida tunaninta ga matar,akwai cikakkiyar suffar kamala dattijantaka tattare da ita,ta tuna yadda take dubanta fuskarta dauke da fara'a da kuma tarin kulawa,tabbas akwai kyakkyawan zato a kanta. "Bakiji bane!" Kakkausar muryar inna furera ta saukar mata cikin kunnuwa,sai ta bude idanunta tana gyada kanta "Kina jina ko?,wallahi wallahi kikaje kika aikata wani mugun hali,ko kikaje kika gwada musu halin maitarki kikayi sanadin da kika dawo gidan nan,na rantse da sarkin da raina yake hannunsa saikin gwammace mutuwa da rayuwa,duk da bansan matar ba a zahiri,amma na tabbatar gida ne na wadata,basu damu da abun duniya ba,duk wani abu me amfani da kikaga sunyi wasarere dashi ki dauka ki adana min,ni ina da buqatarsa,kome zakici maimunatu idan zai ajjiyu baki ajjiyemin ba Allah ya isa" maganganun data dinga yi sun yiwa maimunatun nauyi qwarai,sai tayi qas da kanta tana saurarenta har sai data gama ta sallameta. Yini tayi cikin taraddadi da kuma fargaba,duk da tana samun relief duk sanda zuciyarta ta gaya mata cewa yuuma ce,masoyiya guda daya da take da,ta bangarenta ne wannan lamarin,sai tayi qoqarin saisaita qwaqwalwarta tare da addu'ar kome meye ya zame mata sauqine na rayuwarta. *13* Tunda gari ya waye take zaune tangaram tana duban qofa zuwa window,tana lissafa wucewar mintuna da awanni da yatsun hannunta,wucewar kowacce daqiqa bugun zuciyarta ne ke daduwa,ta kalli qullin kayanta da ba komai bane a ciki illa fararen kayan saqinta,wadanda su daya ne abinda ta mallaka take kuma ji dasu,Sallamar da taji da baqin murya ya tabbatar mata ranar barinta rugar yayi,karon farko da zata fita daga rugar tun sanda suka shigo ita da mahaifiyarta. Laulo ne ya leqo yayi kiranta,sai ta miqe riqe da qullinta tabiyo bayansa,saboda tasan cewa abinne yazo wai inji mai tsoron wanka. Laila da yuuma ne tsaye a tsakar gidan,lailan cikin ado take dake nuni da zallar ilimi dukiya da kuma wayewa,ta qaraso a hankali ta gaida yuuma dama lailan,dukka suka amsa mata da sakakkiyar murya. Sosai inna furera ta kama kunnuwanta,har data dafe gefen fuskarta saboda tsananin zafi "Banda dauke dauke,banda mugun hali,iya abinda aka kaiki shi zakiyi,kada ki yarda a kawomin qararki,idan haka ta kasance kuwa kashinki ya bushe" kai take gyadawa da sauri don ta samu ta saketa,duka yuuma da laila sai da zuciyarsu ta motsu,saidai kowannensu da sauqi,saboda sunsan taqi kadan ya rage ta rabu da wannan rayuwar . Sanda suka qaraso gaban motar tsaye tayi kawai tana qarewa motar kallo,tana qissima yadda zata tsinci kanta a ciki,wai yau itace zata shiga wannan abar?. "Ki shiga maimunatu,anni na jiranmu" laila ta daga kai daga danna wayar da take ta yiwa maimunatu magana,ajiyar zuciya ta sauke sanda ta shiga motar,saidai gaba daya a takure take saboda rashin sabo,sai da suka koma ta gidan yuuma suka dauko anni sannan suka juya suka nufi hanyar barin rugar gaba daya. Duk inda suka gifta sai maimunatu tabi wajen da idanu,tana jin wata kewa tana ratsata tun yanzu,tana jin wani yanayi mara dadi cikin zuciyarta,tana qissima yaushe zata dawo?,yau ko gobe?,ko kuma ta tafi kenan tafiya ta har abada?. "Ki saki jikinki maimunatu,ki sanya a ranki zaki je kiyi rayuwa ne irin ta kowanne yaro dake gaban mahaifiyarsa" anni ta fada bayan ta karanci damuwa da tunani daya cika kwanya da zuciyar maimunatu,qas tayi da kanta tana jinjinashi,sannan tasa hannu a fakaice ta goge qwallar dake shirin sauko mata,babu abinda yake dawo mata sai wani lokaci can baya da suka baro garinsu na gembu ita da daadarta shatu zuwa wannan rugar,a zahiri rayuwar sam mara dadi ce,to a yanzun gata ra cira daga nan din zuwa wani wajen,an mata bushara da kyautatuwar rayuwarta,to amma kuma sanin haqiqanin yadda zata kaya din sai ubangiji,sanin gaibu sai Allah,ko wacce irin qaddara ce cikin wannan tafiyar kuma?. _ku biyo alqalamin 'yar mutan huguma_ Sosai maimunatu ta bude idanunta tana kallon hanya,a wancan lokacin da suka shigo garin akwai qarancin shekaru,shekarunta basu kai haka ba,don haka ta dinga kallon hanya abinta,tun daga cikin rugarsu har suka fito suka dauki hanya dodar. Bayan 'yan hirarraki motar ta dauki shiru,bacci yayi gaba da anni,haka ma yahaya,sai ita sai driver,sai laila data nutsu ta tattara hankalinta kan waya,ta karanci yadda laila ke son waya,daga dan qaramin sanin data yi mata,ta saci kallonta kadan sai kuma ta sake maida hankalinta ga titi,tana kallon yadda ubangiji ya shimfida qasarsa. Wani sashe na ranta kuma cike yake da mamaki,gashi dai tafiya suke,amma kamar a tsaye suke a waje daya,banda tana ganin yadda suke wuce dazuka da bishiyu tabbas da zata ce ba tafiya suke ba. Awa biyu cur sukayi suna tafiya kafin anni ta farka,ta sanya drivern ya shiga dasu cikin wani gari,sukayi sallah,kafin su idar kuma saiga yahaya nan ya shigo musu da takeaway,wanda suka wuce dashi mota,suka dora tafiyarsu. Tunda ta karba ledar abincin take hannunta a riqe ba tare da ta ci ba,abinci ne data jima rabonta da irinsa,tama manta lokacin,tun a zamanin da suke muhallinsu ita da mahaifiyarta,cikin ranta take tantamar anya abincinta ne?,bata sake budawa ba saida laila wadda ta gama cin nata ta kalleta "Ki buda mana maimunatu kici?,ko bakison irinsa?" Dan qaramin murmushi ta saki ta girgiza kai,sai ta buda ledar a hankali,laila ta bita da kallo,wani irin kyau fuskarta ke fitarwa fiye da wanda take dashi duk sa'ad da tayi murmushi,janye idanunta tayi,tana gyara zamanta yadda zataji dadin ci gaba da danne dannenta,zuwa lokacin maimunatu ta fara kaiwa cikinta abincin. Yawan wanda yaci sai yasa ta dinga jin kunyar suga ledar,ita kanta tayi mamaki qwarai,amma kuma daga bisani da taga laila sabgarta take a tab dinta,anni kuma ta koma baccinta sai ta sake itama. Duk yadda taci burin ganin hanya tun daga adamawa zuwa gombe amma sai da bacci yayi mata tsiya,tana gama cin abincin jikinta ya mutu murus,tsohuwar yunwar data jima a jikinta ta kwanta,tsohuwar gajiya kuma ta shekara da shekaru,basussuka baccin da batasan adadin yawansu ba suka taso mata haiqan,bata shirya ba baccin yayi awon gaba da ita. *GOMBE STATE* *_G R A GOMBE_* _DR SULAIMAN KUMO ROAD_ _Dr marwan khalid akko residence_ Katafaren gida ne wanda ya amsa sunansa ta kowacce fuska,irin ginin da aka yishi ba don alfahari fariya ko taqama gami da almubazzaranci ba,gini ne na ma'ana da sanin rayuwa da kuma abinda duniya ke ciki,duba daya zaka yiwa gidan kasan cewa daga zubi da tsarinsa ginin ya zaunu matuqar zaunuwa,hakanan yakan dauki hankalin mafiya yawan jama'a,tun baka ma shiga cikinsa ba. Gidane dake dauke da sassa guda hudu,biyu na matan gidan,daya kuma mallakin me gidan,yayin da daya bangaren ya zama mallaki ga mahaifiyar me gidan wato haj maryam Farooq kumo. Gaba daya gidan mallakin dr marwan khalid akko ne,babban limamin gombe gaba daya,shararre kuma sanannen dan kasuwa,wanda Allah ya yiwa baiwar arziqi dama dukiya gaba daya,gami da tarin ilimin addinin islama wanda shi ya kaishi ga zama cikakken dr,hakanan ta fannin boko din ma ba'a barshi a baya ba. Wani irin mutum ne da Allah ya yiwa baiwar kwarjini da kuma farinjini,mutum ne me amfani da ilimin addininsa ainun,mai yawan taimako sadaka da kuma kyauta ma gaba daya,dukka sirrin nasararsa ya ta'allaqa ne ga mahaifiyarsa,jajirtacciyar uwa da bata daukan raini ko kuma wargi komai qanqani,tsayayya akan 'ya'ya da kuma jikokinta. Marwan shine babban d'a a wajen haj maryam anni,hakan ya sanya yayi mata matsuguni cikin gidansa tun bayan rasuwar mahaifinsu,kuma dama shi din mutum ne mai matuqar qaunar mahaifiyarsa da kuma qawa zuci,hakan ya sanya itama haj maryam anni ko cikin yaranta tafi ji dashi,duk da cewa dan fari ne ba auta ba,autansu alhj sagir yaso daukarta ganin kamar shi yafi dacewa,amma gaba daya ya hanasu hakan,yace shi yafi cancanta tunda shine babba. Matan Dr marwan akko biyu,akwai haj Aishatu,wadda take da yara bakwai dashi,diyarta ta farko macace mai sunan anni wato maryam suna ce mata maama,sai ja'afar d'a na biyu a wajenta,wanda ya zamto halitta mafi soyuwa a wajensu,duka sauran mata ne,salma,hafsa,nadiya,safina,sai autansu namiji khadim,daya dakin kuwa dakin amarya umamatu tana da yara hudu ne,suma din mata ne,fa'iza ce babba,sai khadija,zahra'u,sai mai sunan yuuma rahama suna ce mata baby. Tsakanin aishatu da suke kira da amma da kuma umamatu da suke kira da ammy zama ne na fahimtar juna da kuma zaman lafiya dai dai gwargwado,yadda Allah ya dorawa kowa son ja'afar haka ammy ke qaunarsa,shi din dan gidanta ne tun farkon zuwanta gidan,amma kuma ta tattara ta miqa mata shi,shima kuma ya dauketa kamar uwa a gareta. *_Ja'afar marwan khalid akko_* matashin saurayi kuma matuqin jirgin sama,mai jini a jika,wanda Allah ya yiwa baiwar qira ta jiki,bashi sahun dogaye ko kuma gajerun maza, moderate ne,yana da murjajjen jiki mai siffar qarfi dake nuna shi din ma'abocin gym ne,kalar fatarsa ruwan tarwada ce,wadda ta samu kulawa ta gasken gaske take bada wani irin launi mai daukan hankali matuqa,baya tara suma kamar yadda shi din ba ma'abocin yin aski bane,saidai yadda yake barin sumar kansa zuwa habarsa da kuncinsa abun yana da matuqar qayatarwa da kuma daukar hankali,Allah ya zuba masa wani irin mugun kwarjini wanda yake qara masa kyau haiba da kuma cikar kamala,yana da wani irin farinjini na musamman,bawai a wajen mata kawai ba,a'ah.....hatta a wajen al'ummar gari gaba daya. Dan gayu ne na gasken gaske,gayu wanda ake kira gayu bawai muna gayu ba,mai tsananin tsafta ne daya tsani qazanta dama qazami,yana da tsari da kuma dokoki da ya sanya ba kowa ke iya mu'amala dashi ba,kamar yadda shima bada kowa yake iya mu'amala ba. Miskili ne ajin farko,irin miskilancin da zakayi tunani bebe ne ko kuma kurma,magana ko hira bata daga cikin abubuwan dake burgeshi,abu ne mai wuya ka zauna dashi kaji wata doguwar magana a bakinsa,sau tari yafi ganewa amfani da body language,kamar wani me ciwon baki ko kuma mara lafiya,yana da tsananin kamewa da kuma tsare gida,akwai jinin sarauta sosai cikin jikinsa,hakan ya sanya yake da izza da kuma rashin daukan raini,bai yarda da qasqanci ba,yana da neman na kansa sosai,mahaifiyarsa diya ce ga turakin akko,yana da matuqar girmama na gaba dashi,komai qanqantar shekarun daka bashi,duk da mutane da yawa sun masa shaidar wulaqanci da kuma girman kai. Mutum ne mai tsanani ta fannin so ko qi,bai iya so ba,hakanan bai iya qiyayya ba,idan jininku bai hadu ba ka fita a hanyarsa kawai shi yafi maka alkhairi,yana tsananin son mahaifiyarsa fiye da kowacce halitta a duniya,mahaifinsa da kuma anninsa suke da gurbi na biyu,don yakan kasa tantance cikinsu wa yafi so?,sannan gwaggwo sadiya qanwa ga anni,akwai mutanen da yake ganin kima sosai cikin rayuwarsa da zamantakewarsa. Jabir shine qawa kuma amini ga ja'afar,d'a ne ga qanin mahaifin ja'afar,mahaifiyarsa ta rasu ta barshi sanda ta haifeshi ko juyawa taga abinda ta haifa bata yi ba,akwai aminci sosai tsakaninta da mahaifiyar jaafar,kuma rana daya aka haifesu,don haka ta dauka jabir ta hada jaafar ta riqesu gaba daya,duk da taso qwarai ta shayar dashi kamar yadda ta shayar da jaafar amma anni ta hana,tace tayi haquri,yasha madara,saboda gudun samun matsala anan gaba,idan hakan ta faru zata haramta masa duk wata 'ya da ita din zata haifa jaafar yace yanaso,ko kuma wata daga cikin 'ya'yan 'yan uwanta,ba'asan kuma me Allah zaiyi ba,dukkansu sun gamsu sun kuma fahimta,taci gaba da bashi madarar,madarar kuma ta amsheshi sosai,ya tashi tubarkall,dashi da jaafar me shan nono babu bambamci,sun tashi tamkar 'yan biyu,don haka ma ake ce musu,akwai matuqar shaquwa da fahimtar juna a tsakaninsu,kowannensu bashi da kamar dan uwansa,dashi yake shawara,shi yake gayawa sirrinsa. Farinjinin ja'afar ya sanya yake da tarin 'yammata dake hauka a kanshi,saidai ko sau daya bai taba sha'awar bata lokacinsa akan kowacce yarinya ba,a haka kwarjininsa ya sanya mata da yawa sun hadiye kwadayinsu,don basa iya tunkararsa da zancan soyayya kansu tsaye,masu tsaurin idanu ke biyo ta hannun jabir,to shima jabir din yasan waye ja'afar,kuma dabi'un nasu suna dan kamanceceniya,duk da jabir bashi da miskilanci,saidai yana ararsa a duk sanda yaso,hakan yasa sau tari wasunsu baya ko gayawa ja'afar ma yake barin batun yabi iska. A sannan babban burin ja'afar a duniya shine ya zama pilot,dukka hankali nutsuwa da kuma rayuwarsa ya tattarata ne kan karatunsa gaba daya,sanda yake gab da zama pilot,a lokacin da suke komawa gida hutu daga qasar da yake karatu,a filin jirgin sama shaheeda ta fara ganinsa,d'iya ga shugaban malamai na qasa gaba daya,kuma babban limamin masallacin shugaban qasa dake abuja,yarinyar data bala'in mato masa,saidai tasirin tarbiyya data samu ya hanata bayyana masa,tana da kunya da kuma tsananin kamun kai,amma duk da haka ta kasa kanta sakat,sai data gano waye ja'afar din. Ta shiga tsananin tashin hankali sanda aka gama karanto mata waye ja'afar?,ta yaya zata shawo kansa?,da wannan tunanin ta dinga rayuwa,haka ta dinga ramewa. Kwanaki qalilan da ya rage musu su koma gida daga hutunsu suka giwa dr marwan rakiya abuja shi da jabir zuwa taron musabaqa na kasa da ake gudanarwa acan,a ture yaje bawai don yana so ba,don bai shirya zuwan ba. Cikin hall din kansa yana qasa yanata danne danne a wayarsa,yana jin jabir sunata hira da wasu matasa biyu da suka hadu a can,har zuwa sanda aka fara gabatar da musabaqar,bai daga kansa ko sau daya ba,saidai duk wanda yahau zaiyi karatu har ya sauka yana bibiyarsa a zuciyarsa,yana taya alqalan cin gyaransu,don shima Allah ya bashi haddar qur'ani izifi arba'in cif,sauran kuma biye ne da qur'ani. Kiran sunan wata daliba da akayi yaji daya daga cikin abokan hirar jabir din yace "Alhamdlh......ga sister dita din" baiyi niyyar dago da kansa ba,amma jin ana sake maimaita kiran sunanta ganin bata fito ba,sabanin sauran dalibai da kowa ake kiransa sau daya.....shi ya sanyashi daga kansa sanda yaji me kiran sunan ya ajjiye abun maganar alamun ta taso. Daga rukunin kujerin dake opposite dinsu ta taso,sanye cikin yalwataccen dogon hijabi har qasa,qafarta da hannunta duka safar hannu ne,baka ganin komai nata sai kyakkyawar fuskarta wanda nutsuwa ke kwance samanta. Kansa ya dauke ya maida ga wayarsa,amma sai ya samu kansa da dakon jin nata karatun,ta daidaita zamanta aka tambayeta wacce qira'a take amfani da ita,ta fada,mai jan karatun ya janyo mata sannan aka bata damar ci gaba. Gaba daya hall din sai daya dauki shuru sanda tayi bismillah,zazzaqar muryarta ta karade hall din cikin kyakkyawan sauti da qira'a,wanda tunda aka fara ba'ayi mata gyara har ta dire,kabarbarin mutane da yawa data burge suka dinga fitowa daga bakunan jama'a 14 Sanda aka gama musabaqar suna tsaye a jikin motar dr marwan(abbi) suna jiransa yayi kiransu,ya hadasu da mahaifin shaheeda da ita kanta shahidar suka gaisa,irin dadin da shaheeda taji ba qarami bane ganin cewa akwai sanayya tsakanin mahaifinta da nashi,ko meye zai dan zo mata da sauqi,ba kamar ace babu komai tsakaninsu ba,kwata kwata bata nuna wannan farincikin a fili ba saboda kamun kai da kuma tsira da mutunci. Babu jimawa shaheeda ta ziyarci gidan dr marwan,nan da nan ta saba da mafi yawa na jama'ar gidan,tayi amfani da hikima da kuma hankalinta da wayo ta shiga jikin anni da amma mahaifiyar ja'afar sosai,a lokacin jaafar tuni sun koma hutunsu,bata damu ba tasan tana da target a kansa komai dadewa,baka isa kace son ja'afar take ba,don ko zancansa bata taba yi ba bare ka kawo hakan cikin ranka,saidai a hikimace ta gama karantar dabi'unsa daga hirarsa dake bakin 'yan uwansa,da kuma yawan ambatonsa da anni takeyi,ta gama gane abinda yakeso da wanda bayaso,ta haddacesu tsaf bisa kanta. Sanda suka dawo hutu sun samu shaheeda a gidan,don tuni ta maida gidan wajen zuwanta,sun kuma saba sosai ta zama kamar 'yar gida,da yawa suna cewa saboda gidansu duka maza ne shi yasa tafison gidan baba dr kamar yadda take kiransa,don nata 'yan uwan duka maza ne,ita daya ce mace. Eh tabbas,zamanta a gidan na mata dadi,saboda tana da abokan hira sosai ba kamar gidansu ba,saidai nata plan din ja'afar ne,boyayyen sirrinta da babu wanda ya sani,tayi qoqari matuqa wajen ganin ta janyo hankalinsa kanta cikin hikima da basira,ba tare da shi kansa ta bari ya fahimci komai ba,komai na ja'afar din dabanne,ita ke kula da wasu abubuwa nasa. Da farko bai farga ba,saboda sam hankalinsa bashi a wajen,mma daga bisani ya soma fahimtarta,ya kira qanwarsa nadiya,ita yake nema idan yana buqatar wani abu da anni ko su amma basu iya ba ko ba zasu iya ba,wadda tasu tafi zuwa daya saboda kamanceceniyar da kuma nutsuwarta,ya yanka mata warning akan ta cire shaheeda akan duka sabgarsa sai idan shine ya buqata. Farko nadiya ta kasa gayawa shaheeda,sai ita da kanta ta fahimta,ta kuma yiwa nadiya maganar,bata boye mata ba ta gaya mata,tun daga ranar shaheeda ta fita a sabgarsa gaba daya,duk wani abu da ya shafeshi ta fita a ciki,koda zaune take a wajen yazo zata tattara tabar wajen,hakanan abu idan ya dangaceshi komai yadda ta iya babu ita a ciki,abun yana cinta a rai,tana jin ciwo amma ta danne zuciyar tata,mutum ce mai yawan addu'a,maimakon damuwa ta rinjayeta,saita rinjayar da addu'a,takan hana idanunta barci ta tashi cikin dare ta gayawa Allah damuwarta. Sannu a hankali shima ya fara noticing canzawarta,sai ya fara jin damuwa a kanta cikin zuciyarsa,shi da kansa ya dinga mamakin kansa,damuwa for what?,akan wata mace?,sannu sannu Allah ya fara matsa zuciyarsa,sai ga ja'afar da kansa ya fara nema shaheeda tayi masa wasu abubuwan,kamar kalolin girke girken da take masa a baya,amma fur sai ta murje idonta taqiyi,duk da yadda zuciyarta kan buga,taji babu dadi amma haka take mazewa. Rana ta uku daya aika tace ace bata da lpy taqiyi zuciya tazo masa iya wuya,yana zaune a sannan yana duba saqonnin da yake samu daga companies na jiragen sama dakeson yin aiki tare dashi,zare laptop din yayi daga saman qafarsa ya ajjiyeta gefe ya miqe ya fice. A dakinsu nadeeya ya samesu zaune an kafa majalisar hira,tana ta dariya tana dariya harda riqe ciki,Har kowa yayi shuru bata ankara ba,sai da taga hankalin kowa ya karkata ga qofa,sun kuma saka nutsuwa a jikinsu sannan ta ankara,tayi hanzarin jawo dankwalinta ta rufe lallausar sumarta ta fulani,gabanta na wani irin faduwa saboda zallar kwarjinin da yayi mata,tana jin kamar zaman ma ba zata iya ba. Bata ji yace musu komai ba amma sai taga kowace ta fara miqewa tana fita a dakin,ganin sunata ficewa ba tare da tasan dalili ba sai itama ta miqe tayi joining dinsu. Nadeeya ce qarshe sai ita,nadiya na fita ya matsa yayi blocking qofar gaba daya da jikinsa yana kallonta da idanunsa da suke fasa mata zuciya,tayi baya kadan ta kuma sauke kanta qas,don ba zata iya jurewa kallonsa ba,ta fara lanqwasa yatsunta,tana son tace ya matsa mata itama ta fita amma kuma tasan cewa tayi kadan ta iya fadin hakan. "Baki da kunya ko?" Ya fada a taqaice kamar me ciwon baki,abinda yasa babu shiri ta daga kanta ta kalleshi,sai kuma ta sake saukarwa saboda idonsa yana kanta "Ni sa'anki ne da zan dinga aikowa kiyimin abu kina rejecting,bakisan ba kowa nake sawa yayi mun abu ba?" Sosai maganar tasa tayi mata dadi,wani abu ya tsarga mata,gefe daya kuma rauni ya kama zuciyarta har ya sanya qwalla silalowa daga idanun nata tare da kalmar "Kayi haquri" shuru na sakanni yayi kafin ya sauke hannayensa ya juya ya fara ficewa daga dakin,sai ta bishi da kallo har yabar wajen. Kwata kwata ji tayi bataji dadi ba,cikin ranta kuma tana tsoron kada fa ta barar da damarta,a sukwane tayi kitchen ta fara hada masa abinda ya buqata a daxun,tana tsaka da aikin su safina suka shigo "Me yayi miki?,me ya faru?" Tambayar da suka dinga mata kenan "Ba abinda yayimin" ta amsa musu hankalinta na ga girkinta "To wannan abincin fa?,naga bamu jima da gama cin abinci ba" safina ta fada tana bude tukunyar "Na yaa ja'afar ne" amsar daya sanyasu kallon kallo a junansu,suka fara kuma tsegumin anya kuwa?,bata bi ta kansu ba,itadai burinta ta gama ta kai masa. Sanda khadim yakai masa dawowa dashi akayi,yace bayaso,abinda yasa hankalinta ya tashi sosai,ta kuma boye ta dinga kuka,washegari ta hada kayanta tace zataje,duk da kwanakin da takeyi basu cika ba. Kwana biyu rak a tsakani ya karanci bata gidan,yayi kaman ya share amma sai yaji ya kasa,ya kira nadeeya ta tambayeta,bata boye masa ba ta gaya masa duk abinda ta sani,ya sallameta,sannan yayi shuru shi daya yana tunani,rashin cin abinda ta aiko masa ne ya kawo faruwar hakan?,washegari sai ya tsinci kansa da shiryawa ya tafi gidan daukota,babu ko rakiyar jabir. Suman zaune tayi sanda akace mata ja'afar ne na gidan baaba dr,bai shigo ba ya dai aiko da gaisuwa wajen ummanta,sannan yace a gaya mata ta fito su tafi,saqon da ya bata mamaki,haka ta shirya kayanta ta biyoshi. Cikin motar kamar bashi ba,har ta fara cire hope,saboda ko uffan bata hadasu ba,sai da suka kusa gida sannan ya magantu "Idan kika sake wannan kuskurem sai na hukuntaki" ta fahimci da qaramar magana yake isar da saqo me yawa,maganarsa guda daya idan ka fassarata taka dauki.ma'anoni.masu yawa "Kayi haquri" tace dashi,yaji dadi cikin ransa na yadda take da sauqin kai,saidai ko ka fuskarsa haka bai nuna ba. Wasa wasa sai shaheeda ta karbe komai nasa cikin gidan,nan da nan kowa ya fara daukan haske,duk da cewa shi gogan yana jin dadin hidimarta sosai saboda ya yadda da tsaftar ta da qwarewarta wajen girki,sannan yana jinta a ransa wanda yafi ta'allaqa hakan da sabo,amma babu wata maganar soyayya data taba gittawa tsakaninsu. Tsarin gidansu shaheeda daga candy mahaifinta bashi da ra'ayi barin diyarsa mace ta qara gaba,sai kuma gashi guda daya ce macen da Allah ya bashi,a lokacin shaheeda tayi candy,mahaifinta ya tasamma aurar da ita,dr marwan na samun labari ya nemawa ja'afar bisa shawarar anni,saboda qoqarin da taga shaheeda nayi a kansa,da kuma yadda ta karabceshi tsaf,tamkar ita ta haifeshi. Kowa yayi tunanin za'a samu matsala sanda ja'afar yaji an nema masa auren shaheeda,sai gashi bai wani damu ba,hasalima kusancin dake tsakaninsu ne ya sake daduwa,hakanan itama ta sake qara qaimi wajen kula dashi,abinda yake matuqar yi masa dadi a rai,duk da dan uban miskilancinsa. Wata iriyar zazzafar soyayya yake mata silently,mutum ne shi da bai iya so ko qi ba,shi daya yasan girma da kimarta cikin ransa,ta kula da komai nasa,dai dai da lokacin sallah ta dauki wayarsa ta saita masa,hakanan duk sanda ta tashi sallar dare dai tasan yadda tayi ta tasheshi,ko.ta tura masa tex ko tayi masa flash call,duk sanda tayin kuwa sai ya gani,kasancewarsa mutum da baya bacci da wuri,ita ta koya masa sallar dare,ta kuma koya masa abubuwa da yawa wadanda daa basa cikin habit dinsa,ta samu gurabe sosai cikin rayuwarsa,wanda hakan ya qara soyayyarta da qaunarta cikin ransa ba tare da ya ankara ba. Sanda sukayi aure da shaheeda lokacin ya zaba kamfanin da zaiyi aiki,saidai ba anan nigeria yake ba,anni ta dinga fada,akanme zai zaba kamfani a wata qasar bayan yanzun yana da iyali,Allah sarki shaheeda ba haka taso ba,amma ita ta haqiqancw kan cewa babu komai,saboda fa fahimci burinsa kenan,yana matuqar qaunar piloting,tana bala'in girmama buqatarsa da burinsa saman nata,tayi kwance kwance ta dinga bawa anni haquri gami da kareshi. Suna kan hanyarsu ta komawa sashensu ya kama hannunta ya saka cikin nasa "Me yasa kike bani kariya?,bayan kema nasan ba haka kikeso ba?" Murmushi tayi sannan ta dora kanta a jikin kafadarsa "Bani da wani zabi bayan naka,bani da wani abu da zanso sama da abinda kai kake sonshi,bazan taba son wani abu sama da wanda ka zaba ba,dukka zabina dama rayuwata ta narke cikin taka,taka ce" wani abu ne ya dunga tsarga masa,baisan wanne irin so shaheeda ke masa haka ba,kasa magana yayi,sai kawai yasa hannu ya dauketa cak yaci gaba da takawa da ita zuwa sashensu,abinda tafiso daga wajensa kenan fiye da komai,tayi luf a qirjinsa tana murmushi tare da shaqar daddadan qamshin da bata taba jin makamancinsa ako ina ba sai a wajensa. Mutum ne tsayayye dan gaske,wanda komai zaiyi baya daukarsa da wasa matuqar ya sa kansa,don haka sanda ya fara aikinsa ya bashi muhimmanci qwarai da gaske,abinda ya jawowa shaheeda samun qarancin kulawa,tana jin babu dadi amma ta danne,taci gaba da haquri dashi da kuma dukka abinda zai taso,a yawancin lokuta shi da kansa yasan tana buqatar kulawarsa,amma babu lokaci,hakan ya sanya shima yaqi dauketa daga cikin gidan nasu,saboda zamanta tare dasu anni xai rage mata kewa da zaman kadaici. A haka shaheeda ta samu cikin twins,a lokacin laulayinta tasamu zama dashi sosai saboda hutun qarshen shekara daya fara yi,ya kuma dan dade. Wata takwas da sati biyu ta haifa masa kyawawan 'yan biyu dukkaninsu mata,ikon Allah dayar shi tayo,dayar kuma babanta sakkk,ya kashe kudi bakin iyawarsa,ya kuma gatanta,ta samu gift masu yawa daga gareshi. Yaran yarane masu shiga rai kamar mahaifinsu,hatta da baban nasu wata iriyar soyayya yake musu ta musamman,a haka yara suka fara wayo,ya kuma koma bakin aikinsa. Sannu a hankali yara suka fara girma,sunata wayo abinsu,har zuwa sanda sukayi shekara biyu,ya dauki hutu yazo dai dai randa su nadeeya suka hada musu birthday,akayi komai dashi,ya kuma cikasu da gifts ya koma aikinsa. Kamar dai baya haka ya koma aikinsa ka'in da na'in,a wannan karon shaheeda kanyi qorafi lokaci xuwa lokaci "Muna buqatarka,muna buqatar kulawarka,ba don ni ba ko don yaran nan" shi a kansa yasan da haka,don haka ya fara tsara musu yadda zasu xama kusa dashi ba tare da ya gaya mata ba,shi kansa yana kewarsu sosai. *_MUTUWA rigar kowa_* Tunda watan ya kama take masa complain din tana yawan jin ciwon kai,murmushi yakeyi yana tsokanarta,saboda yasan wani lokaci idan tana buqatarsa ko buqatar ganinsa da hakan take fakewa,har sai yabar dukka abinda yakeyi yazo ya gansu. Wannan karon sai yake basarwa,saboda so yake zuwa qarshen watan yayi musu suprise ya debosu suzo suyi hutu tare dashi. Sati kusan uku suna a haka,ranar wata alhamis.......... A ranar akwai jirgin da zai tuqa,awa daya saura su tashi sai ga kiran shahidan,tana shaida masa gata a qasar,da fari ya dauka wasa take masa,don last week sunyi hirar taji duka schedules dinsa na satin,amma daya duba number ya tabbatar ta qasar ce sai ya yarda da hakan,mamaki ya cikashi,da alama ta gaji da kewarsa ne ta biyoshi kenan,waya ya dauka yayi musu booking masauki sannan ya kirata yace su biyo cave ta kawosu nan,a marairaice tace "Yanxu ko sau daya?,ko sau daya ba zaka iya qarasowa na ganka ba kafin ka wuce?" Agogon dake daure a hannunsa ya kalla,lokaci ya qurace sosai,bashi da zabi illa ya bata haquri,cikin karyayyar murya ta amsa masa da "Shikenan......ga amna" murmushi ne ya wadata a fuskarsa,ya karba wayar sukayi magana sosai da yarinyar,don bakinsu dukka ya bude,abinda ya jawo ma kenan wayar ta katse sanda 'yar uwarta amra ke shirin karba,yaso suyi magana da ita,don tunda suka fara waya da amnah take cewa ta bata daddy,zata bashi wani labari. A sannan lokacin fara aiki yayi,ya kalli wayar yanason kira a bashi yarinyar amma ba hali,sai ya yanke bari suje sukai passengers,lallai a ranar zai dawo in sha Allah,cikin ransa ya dinga jin excitement na haduwarsu,ashe samun nasu da bazaiyi ba kenan saidai ya taras da gawar matarsa da kuma gawar diyarsa guda daya amra. Lamarin yayi matuqar bugarsa da kuma gigitar dashi,don saura kadan ya zauce a sannan,bai taba kawo irin hakan a ransa ba,tun daga wannan lokacin komai ya tabarbare masa,ya tashi daga ja'afar akko ya koma wani mutum na daban,musamman lokacin da yaci karo da diary na shaheeda cikin kayanta,yadda take kewarsa da yawa da tarin qaunar da take masa, movement na yaransa a lokacin da baya kusa dasu. Sosai depression ya sameshi,ya tattara komai nasa ya ajjiye,ciki harda aikin nasa da yake matuqar so,yace shine sila na faruwar komai,dukka qoqari anyishi kan jaafar don ya koma dai dai,amma inaa abubuwan sai a hankali,sai da aka tsaya da addu'a da roqon Allah sannan aka fara samun sauqi,amma sam ya canza totally,hakanan duk sanda abun ya motsa masa birkicewa yake gaba daya. Sosai jabir ya taka rawar gani,saboda tsayawa da yayi akan jaafar din,da qyar aka sha kansa ya koma kan harkokinsa,amma piloting dai ya ajjiyeshi,ya zama wani mutum me zafin rai,miskilancinsa ya sake daduwa qwarai da gaske,babu abinda yake burgeshi a rayuwa,ya sake zama wani very careless akan sha'anin kowa,yafi ganewa kadaici,wanda kadaicin kuma illa ne tattare dashi,saboda shike tuna masa da shaheeda. Wata irin soyayya yakewa diyarsa guda daya data rage wato amnah,wani irin gata yake mata,soyayyar mahaifiyarta da 'yar uwarta duka sun dawo kanta,amma fir yaqi zaman nigeria duk da babban kamfaninsa anan yake kano gombe da lagos,dole don kada su matsa masa suka barshi,suke ci gaba da binsa da addu'a da kuma fatan Allah ya kawo qarshen komai. 15 *Dawowa cikin labari* Tafiyar awanni biyu suka qara suka shigo garin gombe,a lokacin anata sallar la'asar,wasu masallatan ma sun idar. Slow da motar ta fara yi sanda suka qaraso unguwar suka fara gangarowa faffadan layin gidan dr marwan din ya sanya maimunatu farkawa,ta zauna sosai tana murza idanunta tare da kallon sabuwar duniyar da rayuwa ta kawota,murmushi anni tayi "Lallai kinsha barci maimunatu,harma kin fini jimawa" murmushi tayi cikin jin kunya ta sadda kanta,itama anni murmushin tayi tana maida dubanta ga qofar gidan da suka fara harin tsaiwa "Marwan dinma yana nan ashe" ta fada tana leqe fa window "Eh ga motarsa nan,harda baqin motoci ma" hayatu ya amsa mata "Marwanu marwanu na jama'a,hutun qarshen satin ma shi ba samu yake ba" "Wallahi haj anni,ai aljanna kawai ta ragewa alhj,amma yana samun yabo da shaida me kyau" kanta ta jinjina cikin jin dadi,ita kanta ta sani,matuqar dai aljanna qasan qafar uwa take,to babu abinda zai hanata dagewa marwanu ya shige. Kakaf hankalin maimunatu yana ga hanya sanda motarsu take shigewa cikin tangamemen gidan,ba laifi tana da dan sanin rayuwar dadi 'yar mitsitsiya,amma komawarta rugar ummaru ya sake maidata baqauya sosai,don haka ta dinga bin gidan da kallo cikin mamaki su anni,ya akayi su dake rayuwa a guri irin wannan suka iya zuwa rugarsu har sukayi sati guda?,lallai su din nagartattu ne wadanda basu maida duniya a bakin komai ba. Kafin hayatu ya budewa anni qofa ta fito wajen ya fara cika da mutane,mafi akasarinsu ma'aikatan gidan ne maza da mata,kowa na mata sannu da zuwa tare da qoqarin nuna kulawarsa a gareta,abinda zai nuna maka irin girma matsayi da kuma muhimmancin da take dashi. Waiwayawa tayi ga maimunatu wadda ke rabe bayan murfin motar da suka fito a ciki,cikin tsoro,kamar xaka ce mata ket ta zura da gudu,sannan ta dubi daya daga cikin ma'aikatan,babba ce aqalla zatayi shekara arba'in da takwas,kuma da alama ita din ta hannun daman anni ce nesa ba kusa ba "Tabawa riqo min baquwar nan ki shiga min da ita ta qofar baya" ta fadawa tabawan qasa qasa,gyada kanta tayi sannan ta juya inda anni tayi mata ishara,tunda tayi mata magana ta haka tasan cewa wala'alla abune na sirri bataso kowa da kowa ya sani. Murmushi tabawa ta sake mata sannan ta kama hannunta,ko ba komai maimunatun taji ta sake da tabawa farat daya,saboda yadda ta kama hannunta babu kyama ko alamun kyara ko kuma tsangawa,tana biye da ita har sanda duka bulla wani tangamemen falo,falo ne daya wadata da dukkan nau'in kayan alatu na rayuwa,rukunin kujeru biyu ne a cikinsa saboda girmansa,kowanne color dinsu daban,akwai qofofi a ciki dake nuna alamun dakunan bacci ne,sai wata gajerar siririyar hanya wadda kitchen yake a ciki. Kitchen ta wuce da ita,wanda maimunatu ga bishi da kallo cike da mamaki,farat daya ta gane kitchen ne,duk da na ainihin gidansu na gembu bai kama koda qafar wannan ba "Tsaya ina zuwa" tabawa ta fada sannan ta juya ta fita,bata yi koda minti daya cikakke ba ta dawo,tana murmushi ta dubi maimunatu "Kiyi haquri ko,na barki a tsaye,muje na nuna miki dakinki" kai ta gyada kawai tana maida mata martanin murmushinta,a salube kuma tabi bayanta. Dakin yafi kusa da kitchen din gidan,don shi daya ne area din,babban dakine da aka shimfideshi da tiles marbles baqaqe masu dishi dishin light blue a jikinsa,yana dauke da babban gado madubu da wardrobe ta jikin bango,gurin ajjiye takalma,da manya bedside guda biyu masu dauke da bedside lamp,tun daga curtains zuwa dan qaramin carpet din dake malale a gaban gadon duka light blue ne,abinda ya qarawa dakin haske da kuma kyau. "Anni tace nan ne dakinki,ki zauna ki huta sosai,sannan ki fadi abinda kikeso kici,ga bandaki can koda wata buqata zata kamaki,tace zata kiraki idan ta gama" kai maimunatu ta gyada,jikinta a sanyaye,tana ganin kamar taxo inda bai cancanci tayi rayuwa dasu ba,tako ina mutanen nan sunfi qarfinta sun kuma wuce tunaninta,yanzu wannan dakin shi za'a bata a matsayin dakin kwananta?,ita a wa?. "Me zakici?" Tabawa ta sake maimaitawa idanunta akan maimunatu tana nazarinta,da sassanyar muryarta tace "Ba komai,banajin yunwa,bamu dade da cin abinci ba" gaskiyarta kuma ta fada,cikinta ya riga da ya zama mara space sosai da bazai iya daukan wani abincin ba bayan awanni biyu,yunwa ta zamar mata jiki "Shikenan,amma idan kinji kina da buqata,ga waya can ki daga ki kira kitchen,za'a kawo miki duk abinda kike buqata" kai kawai ta sake gyadawa bawai don ta fahimci yadda zatayi kiran ba,sai taga tabawan ta qarasa wajen da qullin kayanta suke tana niyyar dauka "Kaya na ne" daga kai tayi ta dubeta,murmushi tayi mata sannan tace "Anni ce ta bada umarnin a daukesu,za'a kawo miki wasu kayan da xakiyi amfani dasu" bata son rabuwa da kayan,kayan suna d matuqar amfani da kuma tarihi a wajenta "Don Allah ki cewa anni tabarmin su,ina so" fasa dukan tayi,sai ta amsa mata da to,ta juya ta fita a dakin sannan taja mata qofar ta rufe A nutse ta gama qarewa dakin kallo kusfa kusfa,daga nan inda take zaune tana iya jiyo maganganun mutane sama sama,saidai kuma bata iya rabewa da abinda suke fada. Daga can bangaren anni kuwa sannu da zuwa jikokinta suke ta shigowa sunayi mata,duk da cewa ba kasafai take wannan wasan dasu ba,amma kuma su din basu qyaleta ba,duk da zafin da take dashi. Fitowar annin kenan daga wanka bayan ta fito tana zaune a qasa,ta miqe qafafunta da sukayi mata nauyi da kuma tsami saboda zaman mota,man zafi take qoqarin shafawa tabawa ta shigo dakin,dauke da wani qaramin flask din silver da cup guda daya,gefe ta zauna anni ta daga kai ta dubeta "Sannu tabawa" "Yauwa hajiya anni" ta amsa mata tana murmushi tare da qoqarin bude flask din ta zuba mata abinda yake ciki,dan yamutsa fuska tayi "Dakata mana tabawa,yaa daga dawowata zaku hau duramin magani?,ba wani abu me galmi galmi sai magani kamar bugagga?" Dan danne dariyarta tabawa tayi,ita din ba baquwar hutsun anni bace,ta riga data saba da hakan tsahon shekara goma sha "Ammi ce tace shi xa'a fada baki" "Ta rasa abun arziqin da zata yimin sai wannan?" "Abu me galmi galmin yana hanya ai anni,ita da kanta ta karba girkin abinda zakici idan zaki dawo,yanzu haka a kitchen na barta" sai a sannan annin ta saki fuska "Allah sarkiAishatu,badai qoqari ba....ba daga nan ba" ta fadi tana miqa hannu tare da karbar maganin da tabawa ta zuba matan tana kurba a hankali,ita kanta tana son maganin,saboda yana saurin warware mata gajiya daga jikinta. Kurba uku tayi aka turo qofar dakin hadi da sallama,matashiya ce sanye da rigar material da aka yiwa budadden dinki,kanta yane da mayafi plain daya dace sosai da kayan jikin nata,tabawa ce ta amsa sallamar tata tana dubanta "Ina kika shiga tun dazu ga aikinki can an dade da gamashi?" Sai data zauna gefan gadon annin ta yage mayafin kanta sannan tace "Bari kawai baba tabawa,ai na baje zanci dadi kawai aka kirani daga makaranta nazo ga lecturernmu da yace bazai samu shigo ba ya shigo,mugu ne mutumin nan na qarshe,shi yasa ba shiri na tashi na tafi" Murmushi tayi "Ai gashi can a ajjiye" "Yauwa baaba tabawa.....godiya nake" waiwayawa tayi zuwa ga anni tana murmushi "Anninmu ta mutunci......barka da sauka,kun dawo lafiya?" "Lafiya garas na dawo,gashi ma kin ganewa idonki?" Dariyar dake cin salma ta danne,don tasan anni na ciki da ita,domin kuwa ita ya khalid(shine babban jika a wajen anni ta danta na biyu me bin dr marwan)yace ta shirya ta rakata amma ta kawo nata uzurin bata je ba "Amma nafi kowa jin dadi a gidan nan,Allah da bakya nan duka gidan babu dadi,ai bansan yau zaku dawo ba don munafurci laila bata gayamin ba,da na saka an siyo miki nama a wani suya sport nan bayanmu me shegen dadin tsiya......" "Ke.....kiyi ta kanki,wato ga kuriya ko?,to ta Allah ba taki ba,bana so" fuska tadanyi qoqarin canzawa,duk a qoqarinta nason gamsar da anni duk da dariyar daketa taso mata,saboda tana da buqata wajen yayansu ja'afar,kuma ta tabbatar da zarar annin ta saka baki anyi an gama "Allah anni da gaske nake,kar kiso kiji yadda duk naji......" "Ki rabawa aishatu da marwanu biyar biyar....."annin ta fada tana danqara mata daquwa,wanda babu shiri salma ta miqe ta zari jakarta tana cewa "Allah ya baki haquri ya huci zuciyarki tsohuwa me ran qarfe" tayi waje,annin bata barta ba ta dora mata "Sannan kada uban wanda ya sake saka tabawa aiki cikin gidan nan na gaya muku,ba me aikin kowa bace ehe......" Murmushi tabawan tayi bayan ficwwar salman "Ba wani abu bane hajiya anni,koda aikin gidan nan duka zai dawo kaina indai zan iya zan yishi,keda iyalinki ai kunfi qarfin komai a wajena" kofin maganin ta ajjiye gefe "Na sani,amma ace duk ma'aikatan dake gidan basu ishesu ba?,ubansu ya lalata su ya dauko masu aiki ya zube musu kamar ba diya mata ba da gobensu a gidan aure zata samesu?,kiga yarinya batasan ta zagi jikinta tayi aiki gidan aurenta ba?,shi yasa suke wayar gari qazamai,ko cikakken tuwo basu iya yiwa miji da zaici kamar ya cire yatsunsa ba......haka yaranmu na karkara suke?" Kai tabawa ta kada tana murmushi "Sha wuya ne ai wadan nan" furucin na tabawa ya tuna mata da maimunatu "Kwarai da gaske kuwa,kin tunamin ma,akwai maganar da nakeso muyi dake tabawa" anni ta fada tana gyara zama,tabawa bame aiki anni ke kallonta ba,yar uwa take kallonta kuma abokiyar shawara,bama ita daya ba,kusan duk wanda ya girma ya tashi a gidan kallon kaka yakewa tabawa,mutum ce ita me tsananin mutunci da kuma dattako,bata aikin komai ma cikin gidan,saidai idan anni na buqatar wani abun da sun riga sun saba tabawan kadai keyi,duk da akwai masu aiki sosai cikin gidan "Kinga yarinyar dana sanya ki kaita ciki ai ko?" "Qwarai kuwa haj anni" tabawa ta fada tana bawa anni dukka hankalinta "Yarinyar kyakkyawa sosai,saidai akwai alamunrashin sukuni a tattare da ita da kuma wahala" kai anni ta gyada "Bama alamu bane,akwaisu" a nutse ta bawa tabawa labarin maimunatu,tare da qudurinta a kanta,labarin da yayi matuqar sanyaya jikin tabawan,tare da saka mata tausayin maimunatu me yawa cikin ranta "Kiyi nufin alkhairi sosai hajiya anni,kuma dama halinki wannan,Allah ya baki nasara akan hakan,yasan kuma iya bakin matsalar ce,yasa ta zamto masa haske cikin rayuwarsa" "Ameen,ameen ya hayyu ya qayyumu"anni ta fada tana jin dadin yadda tabawa ta fuskanceta "Amma kuma wani hanzari ba gudu ba.….." "Uhmmm,ina jinki tabawa" "Kinsan akwai matuqar banbanci da tazara me yawa tsakanin manya(sunan da takan kira ja'afar dashi,saboda sunan babban malamin da yaci,kuma wasu sukan kirashi da sunan) da ita yarinyar?,kinsan kuma hali da dabi'ar yaran zamani,musamman shi daya keta qasashe da dama,yaga kuma mata iri iri,inajin kamar idan akace za'a bashi yarinyar nan a haka zai zama da matsala" murmushi anni tayi "A hakan zaa bashi ita ba kuma a hakan za'a bashi ba" cikin rashin fahimta tabawa ta kalli anni don bata gane hausar ba "Abinda nake nufi shine,inaso ki kulamin da duk abinda zata ci ta kuma sha,nasan ba lallai a yanzu ta farat daya ta dauki cimarmu ta iya sakin jiki taci yadda ya kamata ba,sannan ki kulamin da tsaftarta ki jata a jiki a kiyi mata duk abinda ya kamata,sauran abubuwan zanyi magana da salamatu,abinda ya samu zuwa sanda zai zo gida shikenan,zan bashi ita a haka,shi nakeso ya qarasa rainonta,kinsan hikimar yin hakan?" Kai tabawa ta girgiza tana duban anni "Inaso ne yasan ciwonta,yasan dadi da kuma wuyarta,yadda bazai riqeta sakwa sakwa ba,sa'annan inason ya ginata kan tsari da dabi'ar da yakeso,ya dabi'anceta a yadda yakeson matarsa ta kasance,hakan shi zai bada damar da zata shiga zuciyarsa fiye da marigaiya shahida,don shahida tazo da tarbiyyar ta da kuma dabi'unta ne daga gida,ita kuma wannan shi zai saitata a yadda yakeso,zata kasance ne kan tsarin da duk yaso" sosai tunani da hangen anni ya yiwa tabawa dai dai,kuma hikimarta tayi mata,ta sha alwashin lallai zata yiwa annin duk abinda ta buqata,don tana cikin mutane na gaba gaba da takejin ciwo da zafin yadda har yanzu suka kasa shawo kan matsalar manya,tana jinsa kamar danta,don tun yana qarami take a gidan,da ita akayi rainonsa. "Dubamin ita tabawa,ki duba ma'ajiyar kayan nan da aka dinka wancan watan ki ciccire mata wadanda zasu yi mata dai dai,inason ta fito muci abinci da ita anjima kadan" "To an gama haj anni" tabawa ta fada tana miqewa. Tana shirin fita a dakin sallamarsa cikin muryar dake cike da tarin nutsuwa da kuma haske na ilimi da dattako ta ratsa falon,dr marwan ne,sanye yake da lafiyayyar shadda ruwan qasa dinkin babbar riga 'yar ciki da wandonta,kansa kuwa hula ce da ba'a iya hangota saboda fari qal din rawanin dake nade a kansa,idanunsa sanye yake da farin gilashi dake qara masa qarfin gani,akwai cikakken gemu a fuskarsa wanda furfura ta fara yiwa ado ta gauraya da baqin dake jiki. A girmame tayi maaa sannu da shigowa sannan ta juya ta fita a dakin,shi kuma ya sanya kai dakin mahaifiyar tasa,bakinsa dauke da sallama. Fuska a sake ta amsa sallamar tata,sannan ta janye qafafunta don ya samu wajen zama saman lallausan carpet din da take kai,don qasa ne wajen zamansa duk sanda yazo gaidata. "Kun sha hanya anni" ya furta bayan sun gama gaisawa da tambayar mutanen data baro. "Wlh marwanu,amma alhmdlh,gamu a gida" "Mun godewa Allah" ya fada yana murmushi "inata zuba idanu na zaci baku qaraso ba,har ina shirin kiran jibril" "Mun iso marwanu,kana tare da baqi lokacin.....na iso da baquwar yarinya ma" "Eh tabbas,muna tare da ministern ilimi ne,batun da nakeso mu tattauna kenan dake akai" kai ta jinjina "Nima akwai batun da xamu tattauna din,amma kamar lokaci bazai bamu dama ba,naga an kusa sallar magariba,inaga idan aka idar da sallar isha'i sai mu zauna" "Eh hakan yayi anni,Allah ya nuna mana" "Ameen.....amma kunyi waya da jabiru ne?" Dan dubanta yayi "Sai da ya sanar miki kenan?" "Kana da wadda ta fini ne marwanu?" Qas yayi da kansa "Babu anni,amma banason tashin hankalinki ne ko kadan" "Ja'afaru rayuwata ne,Allah ne ya doramin qaunarsa cikin dukka jikokina,idan har an aka fara boyen matsalar ja'afar saboda kada na shiga damuwa to kuwa ba'a kyautamin ba,zanyi dukkanin me yiwuwa ne don naga rayuwar jaafar ta daidaita kamar yadda take a baya" "In sha Allah ba zata sake faruwa ba,kuma maganar da nakeso muyi din tana da alaqa da jaafar din" "Allah yasa alkhairi" "Khairan in sha Allah" ya amsa mata 16 Da sallama tabawa ta tura dakin,ta ajjiye ledar kayan hannunta fuskarta dauke da murmushi tana duban maimunatu "Ki shiga kiyi wanka,ki canza kayan jikinki maimunatu ko?" Kai ta gyada mata,saidai ta maida dubanta ga jikinta,bata ga wani datti da zai sakata yin wanka ba,don yau din da safe Allah ya 'yantata,ta samu tayi wanka kafin su baro gida,kuma bataga wani aiki da tayi wanda ya bata mata jikinta ba,hasalima ta jima bata samu cikakken hutu da yanayi me kyau irin na yau ba "Muje ko na nuna miki bayan gidan" abinda tabawa ta fada kenan bayan ta ajiiye wasu maya mayai saman madubi,sai kawai ta miqe tabi bayanta. Komai na cikin bandakin ta nuna mata tare da yi mata bayani,maimunatu na biye tabawan har ta gama nuna mata komai sannan tace "Idan kin gama kin fito ki dannan nan ina daga falo,zan shigo na gyara miki kanki" kai kawai ta gyadamata,har ta fice tana tsaye tana bin toilet din da kallo. Yadda ta nuna mata komai haka tayi amfani dashi,sai gashi ta dauki lokaci me tsaho tana wanke jikinta lungu da saqo,irin wankan da daadanta ta koya mata ta dinga yi a sanda take da gatanta. Ajiyar zuciya ta sauke mai nauyi tana shaqar qamshin sabulun da tayi wanka dashi,ga wata iska tana ratsata tako ina,bata buda ledar da tabawa ta shigo da ita ba,sai ta zauna qasan tiles din tana qanqame da jikinta waje daya,saboda har wani sanyi sanyi takeji,ta kuma danna inda tace matan,a haka ta share wasu mintuna tana zaune. Gajiya da zaman jira tabawa tayi,gashi anata kiraye kirayen sallar magariba,don haka ta dawo dakin,ta samu maimunatu zaune "Ya kike zaune haka?baki kirani ba baki kuma saka kayan naki ba?" Qas tayi da kanta,tabawa ta karanci akwai baqunta sosai da kuma takura kai ga maimunatu,wataqila rayuwarta ta baya ce tayi tasiri sosai a kanta. Kayan ta fidda mata harda half vest tace ta koma bandakin ta sanya tazo suyi gyaran kan. Ta jima tana jujjuya kayan a hannunta,tamfar ba zata iya sanyasu ba,sai kuma ta tuna jiranta akeyi,abinda yasa ta budasu ta saka sannan ta daure kanta da dankwalin tayo waje,daf da zata fita ta hangi kanta ta wani dogon madubi da akayi cikin bandakin,harta gota ta dawo tana duba kanta. Farat daya ta fara canzawa daga maimunatun bafulatanar riga,babu mudukajenta(kayan saqi) babu wuffije,babu komai na fulani tattare da ita sai duwatsun hannunta da na kunnenta,hakanan fatarta haskenta ya qaru koda ba'a gaya mata ba idanuwanta sun gaya mata hakan,sai ta soma takawa a hankali tana saqe saqe masu yawa cikin ranta. "Babu ma wani datti me yawa akan naki ai" tabawa ta fada sanda maimunatu ta bude mata yalwatacciyar sumar kanta,tabbas babu datti,amma kuma tana da buqatar qyara,ita da kanta idan ta samu sarari take guzurin toka duk sanda taji kan nata ya dameta,ta tsaya daga bakin rafinsu sanda shanunta ke shan ruwa ta badeshi da toka ta wankeshi,saidai tana shan wahala qwarai,saboda wata irin suma Allah ya bata ga tsaho ga cika,babu mataimaki,a baya daadarta ke gyare mata shi fes,ta xauna duk tsahonsa ta bata lokaci ta zuba mata kitson fulani a bishi da wasu irin duwatsu nasu masu kyan gaske,duk randa zatayi mata irin wannan aikin wuni guda suke kashewa kafin a gama,amma fa duk wanda ya kalla kan sai ya kalla ya sake kalla ya kuma tanka,daadarta kadai ke iya mata wannan aikin,ita kanta duk randa ta wareshi ta wanke saidai ta cukuikuyeshi cikin dankwali ta maidashi yadda yake taci gaba da rayuwa dashi a haka,babu cikakkiyar taza bare ta samu kitson arziqi. Tabawa batayi tsammanin aikin zai daukesu lokaci mai tsaho ba,sai gashi kafin ta gama wanke mata shi ta busar a hand Drayer sun dauki kusan awa biyu,har anni ta aiko laila. Tsaye laila tayi tana fiddo idanu sanda ta shigo dakin "La la laaaaa......maimunatu,dama haka kike da suma?,ma sha Allah,kice mu fulani kawai muka rako duniya,ga inda ainihin fulanin suke" murmushi kawai maimunatun tayi,kasancewarta bame yawan son magana ba,zama laila tayi tace tare zasu tafi,tana ta qarewa maimunatun kallo,cikin zuciyarta tana tadinta,yadda cikin awanni kadan kamanninta da kyawunta sun fara fita tun ba'aje ko ina ba. Duka su ukun da sallama suka shiga falon anni,a lokacin ta nutsu tana amsa wayar jabir,sun fahimci waya take mai muhimmanci harda maimunatu dake baquwar gidan,sai suka samu waje kowa ya zauna,laila ce ta qarasa gaban tv ta dauka remote kafin takai ga zama ta canza channel sannan ta dawo itama ta sama waje ta zauna kamar su. "Shikenan......amma ka zama cikin shirin kai jabiru,ba lallai sai ka sanar masa ba,ka rabu dashi kawai kaci gaba da sabgarka.....toh....Allah ya bamu alkhairi" shine maganar qarshe da annin tayi tana sauke wayar daga kunnenta tare da bin wayar da kallo,kana ta dauke idanunta tana maidowa kansu. "Sannu tabawa,kun gama kenan?" Ta fadi tana murmushin jin dadin yadda taga maimunatun fuskarta ta sake fitowa fayau,sannan kuma tayi tarwai "Eh hajiya anni,aikinma bamai yawa bane" "Kedai sannunki da qoqari" anni ta fada tana sake kallon maimunatu "Me zakici maimunatu?" Kanta a qasa ta girgiza kai,don har yanzu cikinta a cushe yake,tana jin daga nan har gobe da hantsi zata iya zama babu komai a cikin nata "Bana jin yunwa anni" "Badai a gidan nan ba,ke lailaa,shiga madafi,ki cewa lami ta zubo tuwon nan da aishatu ta kawo,cin mutum biyu ta kawo mana" ambatar sunan da anni tayi sai taji ya tsarga mata har cikin ranta,a duk sanda aka kirayi me irin sunan,babu abinda yake tuna mata face mahaifiyarta. Sanda laila ta kawo tuwon zama tayi zataci,amma anni tace batasan wannan zance ba,ta koma can wajen uwarta taci "Wallahi anni ke kadai ta yiwa tuwon nan duk gidan nan,ko abbi babu shi a ciki" "A nan kuka fi kauri,wajen bada gudunmawar ci,da wani cikinku nace yayimin babu me katabus" ita dai laila bata damu ba,ta saka hannu a kwanon maimunatu ta fara cin abincinta tana sakowa maimunatu hira,abinda yasa anni fa sake qyale lailan kenan,saboda hakan da tayi tasan zai bawa maimunatu damar sakewa. Ta kuwa dan sake din,tana tsakurar abincin,iyakarta da hirar laila uhmm ko um um,sai kuma murmushi wani lokacin,duka anni tana ankare da ita,tausayin maimunatu take ji sosai cikin ranta,gefe guda kuma tana sake shiga ranta,komai nata mai sanyi ne,cike kuma da nutsuwa a cikinsa. A hankali a hankali 'yan mata matan gidan suka fara shigowa da daya da daya kamar yadda suke yawancin darare,suna shigowa anni su kuma dade wajenta,don ma fadanta yakan sanya wani lokaci suqi zama,amma idan suka sameta akan laushinta har kwana sukanyi. Duk wadda ta shigo sai tabi maimunatu da kallo,wasu suce "Ma sha Allah,anni baquwa mukayi?,ina kika samu balarabiya?" "Yar uwarku ce" amsar da take basu kenan taci gaba da harkar gabanta,cikin girmamawa maimunatun take gaida duk wanda ga shigo,har suka dan cika a falon,sunata hirarrakinsu tana jinsu,koda sun sakota saidai tayi musu murmushi kawai,abinda ta lura dashi,su din mutane ne masu mutunci da girmama dan adam,hakanan suna da sauqin kai,duk da adan taqin zaman nasu ta fuskanci wani yafi wani sauqin kai a cikinsu,dama haka halittarmu take,kowa da dabi'a da kuma yanayin da Allah yayi masa. Ranan kusan a nan duka suka sukaci abincin dare,maimunatu nata kallon banbancin rayuwa da kuma gaskiyar karin maganar nan ta bahaushe da yake cewa 'Allah daya gari bam bam' kowa yakanje ya diba zabinsa ne da abinda yakeson ci,ya kuma buda ma'ajiyar abunsha ya dauka kalar lemo da ruwan da yakeso,wasunsu kuma su sanya ma'aikatan gidan su kawo musu,babu kyara babu tsangwama,akwai alamun hadin kai da zaman lafiya bakin gwargwado tsakaninsu. Tabawa anni data jima da tashi a falon ta aiko kan maimunatu ta tafi ta kwanta,kusan dama ta gaji da zaman,don bata saba hira da mutane ba,duk sai zaman ya gundureta,amma ta rasa ta yadda zata tashi ta wuce dakin,don haka tabawa na idar da saqon ta miqe "Balenjam" ta fada da tattausar muryarta,sai kuma ta danyi sak ganin yadda suka zubo mata idanu "Sai da safenku" ta fada da harshen hausa,laila ce ta saki murmushi "Allah ya tashemu lafiya fillo" murmushin tayi itama sannan ta juya zuwa ciki,tana mamakin yadda suna fulani amma basu damu da yin yaren a tsakaninsu ba,don tunda tazo da hausa taji suna hira har yanzun data tashi,wala'alla shi yasa suka bita da kallo sanda ta yaara musu. "Gaskiya yarinyar nan kyakkyawa ce,tana da hankali da alama" salma data miqe dauke da.plate din data gama shan farfesun kayan ciki ta fada,dubanta laila tayi "Sosai,tana da nutsuwa sosai,tana burgeni" "Ni kaina haka" fa'iza ta amsa musu,daga haka laila bata ce musu komai ba,don tasan cewa ba wanda yasan komai kan zuwan maimunatu gidan,bai kuma kamata ita din ta fara cewa komai ba. Sanda ta shiga dakin idanunta sun fara mata nauyi saboda bacci,qullin kayanta data hana tabawa dauka daxu ta janyo ta tasa kanta dasu,bayan tayi kwanciyarta qasan tiles ba tare da tayi gigin hawa gadon ba,babu jimawa wani nannauyan bacci mai dadi yayi awon gaba da ita. *********Kyakkyawar macace wadda shekarunta na haihuwa suka kusa arba'in da bakwai,kana mata kallon farko zakasan cewa sanda take da qananun shekaru ba qaramin kasa maza dr marwan yayi a kanta ba,tana da siffa me kyau ko a yanzun ma,fara ce sosai kamar yadda akasan asalin farin bafullace,hakanan bata da tsaho can can,kamar yadda ba zaka kirata gajeriya ba,saidai alamun tsafta da qamshi da suka samu wajen zama a tattare da ita sun nuna kansu muraran. Cikin nutsuwa kamewa da kuma sanin kimar kai take shigowa bangaren surukar tata,sanye cikin atamfa england me ruwan ganye,dinkin riga da plain zani,bayanta masu aikin gidan ne wadanda ke qarqashin bangarenta masu kula da bangaren kitchen dauke da trays,sai kuma salma dake riqe da wani warmer me kyau guda daya a hannunta,a shirye take tsaf da alama wani wajen zata wuce,tana daga gefan mahaifiyarta(Aishatu amma) suna magana ita da salma din. Dakatawa masu aikin sukayi har zuwa sanda amma da salma sukayi sallama cikin qawataccen falon annin,wanda sam baiyi kama da falon tsohuwa ba,dai dai lokacin da DR marwan ke zaune gaban mahaifiyar tasa yana gaisheta,shima sanye da wata dakakkiyar shadda fara qal,kamar kusan ko yaushe kansa nannade da tattausan farin rawani na zallar auduga,da alama shima din fita zaiyi. Jinin sarauta ce ita amma sam ba zaka dauka haka ba,saboda sauqin kai da take dashi da kuma sanyin hali,Gefan anni amma ta qarasa tana zama a qasa kamar yadda ta samu me gidanta,wannan din wata dabi'a ce tasu ita da dr marwan tun suna da jajayen sahunsu,dabi'ar data maida aishatu tauraruwa a zuciyar anni cikin kafatanin surukanta,ya sanya kuma wasu daga cikinsu suke kishin hakan,duk kuwa da cewa anni tana matuqar qoqarin boye hakan,saidai ko daga yadda ja'afar keda matsayi a wajen annin kadai ya isa ya fallasa maka wace aishatu a zuciyarta. Sai data fara gaida anni sannan ta waiwaya ga me gidanta shima ta gaidashi,duk da cewa sun gaisa a ciki kafin ya fito,ya amsa mata cikin kulawa kamar ko yaushe,salma ta matsa kadan ta gaida dr sannan ta maida dubanta ga anni,murya qasa qasa tace "Ranki ya dade hajjaju anni" wani kallo ta jefi salman dashi,tasan duk me salman take wa "Allah ya baki haquri anni ina kwana" "Lafiya sumul natashi 'yar nema,duk take takeki kar nake kallonki,gwara kiyi ta kanki 'yar nan" wuri wuri salma tayi,da alama tonin silili anni keson yi mata a gaban wadanda take gudun yin maganar a gabansu,bata gama tunanin ba kuwa maganar annin tayi mata saukar aradu "Wai marwanu.....ita wannan kazar mayun har yanzu bata isa ayi maganar aurenta bane?" Ji salma tayi kamar qasa ta tsage ta shige,maganar da tayin tana nuna kuma yasa dr maida idanunsa kan salma "Me ya faru anni?" Gyara zamanta tayi "Yo ni na gaji da hada kafada dasu idan ku baku gaji ba,ina buqatar ganin wasu 'yan dagwai dagwai din,ko ka aurar dasu ko ka auro,zuri'a nake da buqatar gani me tarin yawa......yawwa......duk gidan nan billhillazi babu yaron da bai isa aure ba,ramatu ce kawai za'a iya dagawa qafa,amma ace babu me aure?,baga mazan ba baga matan ba?,to idan baqinjini garesu zan buga gangar bada sadakarsu mazansu da matansu" kafin ta diga aya salma ta kwashi takalmanta a hannu tayi waje,don taga alama yau annin me manya manya take barota. "Ayi haquri anni" abinda dr yake fada kenan,don yasan da biyu take wannan fadan,tana tunanin kamar shike qin bada auren yaran nasa,bayan kuma yaran da kansu suke sha'awar karatu shi yasa ya qyale kowacce da zabinsa,uwa uba ma duka duka salma hafsat da laila ne a makarantun gaba da secondary,samma hafsa nadiya fa'iza da khadija sune 'yan candyn bana,zahra'u na ss one,sai rahama dake j.s,mazan kuwa dukkansu ba wanda ya gama jami'a banda ja'afar da haisam,sai Mahmoud dake ajin qarshe "Yanzu fisabillahi....salma zaman me take?,shi karatun da take cewa akayi bashi yuwuwa ta qarasashi cikin dakinta?" "Ta fiddo wanda takeso anni,ai baza'a qi aurar da ita ba" "To ta fitar kuma shi take ta raragefan gaya maka kai da uwar tata" qas amma tayi da kanta,wal'alla ta gayawa anni sunyi zancan da ita kenan "To ba damuwa anni,zanyi magana da umar(qaninsa kenan me bi masa),saita turashi can yaje ya gaidasu" "To ba laifi" annin ta fada tana sassautan fadan,dai dai sanda salma tayi dake labe daga waje tayi tsallen dadi,anni tasu,anni ta wajensu,ayi tsiya ayi dadi,ga tsiya ga aiki,lallai yau dole ta yiwa annin wani tagomashi,saita juya cikin jin dadi zuwa ma'ajiyar motocin gidan,inda driver yake jiranta,ranta fari qal. Daga can falo kuwa duban dr anni ta sakeyi "Shi kuma jabiru da ja'afar fa?,da aka barsu suke zaune a wata uwa duniya,ga wancan qaton tuzurun haisam?" Miqewa amma tayi saboda kara da yakana irin tata,tana ganin ya kamata ta basu waje suyi maganrsu sosai "Ina kuma zuwa?" Anni ta fada tana binta da kallo "Zan duba meye baku dashi a kitchen" "Idan kin shiga,kiyi waya can gidansu marigayiya,ya kamata a dawo da amna,jimawar da tayi a can wannan karon tayi yawa" "To anni" ta amsa mata cikin girmamawa tayi ciki,dawo da dubanta tayi ga dr marwan tana tattara hankalinta sosai a kansa sanda ya fara mata bayani "Maganar da nakeso muyi kenan.....a jiya da kika sameni da baqi kamar yadda na gaya miki ministern ilimi ne na qasa ya kawomin ziyara,bayan mun gama tattaunawa kan batutuwa irin namu,sai kuma ya jefomin maganar diyarsa unaisa,ya yimin tayin aurenta da ja'afar kamar sanda ya taba yimin a baya ban karba ba,lokacin ja'afar din yana aviation school,magana kuma tayi nisa tsakaninsa da marigayiya,to a yanzun inajin nauyi na sake qin karba din,kada yaga kamar banason hada zuri'a ne dashi ko kuma wani abu makamancin haka,na amsa masa ne duba da cewa gaba dayanmu dama muna laluben masa abokiyar zaman da zata iya zama dashi bisa juriya da kuma haquri kan sauyin hali da dabi'arsa,na kuma tabbatar kema idan kikaji hakan zaki farinciki,tunda burinmu kenan gaba daya" Shuru anni tayi tana duban dr marwan,bawai don yayi kuskure ko kuma maganganunsa ba'a kan hanya suke ba,a'a......saidai tana tunanin wace unaisa?,akwai yiwuwar samun dacewar zama tsakaninta da ja'afar din?,uwa uba kuma ga batun maimunatu da take tafe dashi,sai takega kamar akwai matsala. _To masu karatu,muje zuwa,shin al'amarin zai yiwu?,duk da bamusan wacece unaisa ba,abbi baisan wace maimunatu ba,kamar yadda wanda aketa abun a kansa baisan wainar da ake toyawa bama_ *17* "Ni ai tuni na samarwa ja'afar matar aure"anni ta fada kanta tsaye,ba tare data jira komai ba ta dora "Ire irensu unaisa ba daya ba ba biyu ba......amma sun kasa jumuri da juriya da kuma samar mana da abinda mukeso" anni ta fada cikin cikakkiyar nutsuwa da bawa zancan muhimmanci,har yanzu ita dr marwan yake kalla,ganin haka ya sanyata ta dora "Eh,hakan yasa na sauya shawara bisa hasashen ramatu" nan ta ware masa komai kan hasashen yuuma,da yadda ta gamsu da maganarta,da kuma yadda ya zamana tashin farko maimunatu ce ta fara zuwa mata zuciya da ranta,mizani da ma'aunai masu yawa da maimunatun ta hau taga kuma tabbas ta dave da matsayin matar ja'afar. Cikin nuna gamsuwa dr marwan yake gyada kai,dukka hasashen annin dama abinda ta aikata yayi dai dai da nasa ra'ayin "Saidai duk wanda keson naka yakeson hada jini da kai ba qaramin masoyinki bane,sa'an nan wannan ba shine karon farko da ya nuna sha'awarsa kan hakan ba,to bai kamata mu watsa masa qasa a ido ba,kuma namiji mijin mace hudu ne ai,fatanmu shine Allah yasa a dace,yasa qarshen matsalar kenan" kai abbi ya gyada "Gaskiya ne anni,Allah ya saka da alkhairi,ya qara girma" "Banga abun godiya ba marwan,wajibi na nayi,babu abinda bazanyi ba saboda rayuwar ahalina matuqar bai sabawa shari'a ba,yanzu abu daya ya rage,ja'afar ya dawo cikinmu,koda zai koma sai komai ya dai daita,don ban gamsu mu bashi yaran mutane ya tafi dasu har wata uwa duniya ba" "Gaskiya ne anni,hakan yayi" "Shikenan,zan sa a kiramin jabirun ko zuwa anjima ne". Dai dai lokacin maimunatu ke fitowa daga dakinta zuwa falon,tayi wankanta ta shirya tsaf bayan baba tabawa ta leqa da safen sun gaisa,ta kuma umarceta da yin wankan,mamaki ne yaketa kasheta,duka duka yaushe tayi wankan jiya?awa nawa ne a tsakani?,duk da hakan bata musa ba tayi kamar yadda baba tabawa ta umarceta,ta kuma shirya kamar jiya,saidai yau din haskenta ya sake fitowa fiye da jiya. Da murmushi anni ke kallonta sanda take isowa wajen,daga nesa dasu ta zube har qasa tana gaidasu,abbi baisan wace ba,amma ya amsa mata cikin kulawa kafin ya maida kansa ga labaran qasa da ake gabatarwa a tashar NTA da ya dauki hankalinsa. Cikin kulawa anni itama ta amsa "Ya kwanan baqunta?" Ta tambayeta cikin salon jan mutum a jiki da kuma son ya sake,murmushi kawai tayi mata tana sad da kanta qasa "Kinsan kitchen ai,leqa kice aishatu tazo,ta taho da qarin plates" "Toh" maimunatun ta amsa tana miqewa a nutse tayi kitchen din. Kafin ta qarasa tadan dinga jiyo hirarraki da alama akwai mutane a kitchen din,ta saka kanta a hankali bakinta dauke da sallama,abinda yaja hankalin amma dake tsaye suna magana da baaba tabawa,hannunta dauke da wata roba tana duba rubutun jiki. Waiwayowa tayi,sai suka hada idanu da maimunatu,dan zubawa maimunatun idanu tayi,tana mamakin jin irin muryar data sani daga gareta,amma kuma batasan fuskar ba,bata taba ganinta ba. Gaisuwar da take mata ta amsa cikin kulawa,sannan ta maida dubanta ga robar hannun nata,saidai kuma hankalinta naga muryar tata sanda take gayawa baaba tabawa anni ce ta aikota ta kira wata,kasa fadar sunan tayi kai tsaye,saboda suna ne dake da girma da kima a idanunta "Yanzun bansan wa anni ke nema cikin madafa ba,kin kuma kasa fadi,hala sunan yana da nauyi a wajenki maimunatu" murmushi tayi a takure gami da jin nauyinsu su duka,musamman amma da hakanan taji tayi mata kwarjini. Murmushi amma tayi "Falon zan koma,muje naji wanda ake kira....tabawa qarasa aikinki,idan kin gama ki sameni keda bara'atu a sassana,zaku yimin gyaran wardrobe" "To in sha Allah" haka suka jero,amma tana gaba maimunatu tana binta a baya,har suka qaraso falon "Baquwar taki ta kasa faden wanda kk nema anni" amma ta fada tana zama daura da dr cikin shirin serving dinsu abincin data kawo musun,murmushi anni tayi "Ke na aika ta kiramin,hala kasa fadin sunan tayi" gyada kai amma tayi "Eh wallahi,anni ina kika samo mana bafullatar usul" "Daga garinsu ramatu,gata nan don Allah aishatu,inaso a kulamin da ita da kyau,so nake ta zama 'yar gida tamkar su salma" "In sha Allah"amma ta fada tana dan sake kallon maimunatu kadan,wadda kanta yake qasa har lokacin,sai kuma ta miqe,don a takure take,ba zata iya zama cikinsu ba. Anni na shirin tsaidata don taci abinci a cikinsu tabawa ta fito ta kirayeta zuwa kitchen,abinda yasa anni ta qyalesu,ta maida kanta ga surukuwarta da danta. Cikin yanayi na shaquwa da kuma fahimtar juna suke cin abincin,suna kuma tattaunawa kan lamuran rayuwa wanda suka shafesu,amma na gefe ba tare data sanya musu baki ba,wannan daha daga cikin halayyarta kenan. Gab da zasu gama akayi sallama cikin falon,kyakkyawan matashine,yana da white skin hakanan giant ne shi sosai,kamanninsa na zahiri shi da dr Marwan sun bayyana. Yayi dressing very neat cike da tsafta kamun kai nutsuwa gami da zallar ilimi,hannunsa daya riqe da lab coat dake bayyana cewa shi din tabbas likita ne,a nutsensa sannan cikin girmamawa ya tube takalman qafarsa ya qaraso falon,ya duqa ya fara gaida anni sannan dr sai amma. Kansa yadan shafa kadan da yasha saisaye me kyau "Anni,zan samu sauran abinci kuwa?" Kai tsaye anni ta kalla amma "Bakuyi girki ba yau aishatu?" "Munyi anni,sanda zan fito ma na leqasu suna gab da gamawa,zuwa yanzu nasan sun gama" qaramin tsaki taja "Shine wannan qaton gardin zaizo ya sani gaba da tambayar abinci?....kaga idan zaka wuce gwara ka wuce,kuci a waje kamar yadda kuka saba,tunda haka kuka zabarwa kanku" dama yasan za'a rina,tsautsayi yasa yayi mata maganar,tun kafin ta tafi adamawa dama taketa rikici dasu,aure kawai takeso wai kowannensu yayi,wani lokaci sai yaji gwara ma dasu JJ suka basa nan,sun huta da ciwon bakinta. Idanun dr marwan dake a wajen ya sanyashi miqewa yana sake shafa qeyarsa hadi da cewa "Allah ya baki haquri" "O'o'o'o,na kusa yiwa tufkar hanci ai" "Fitarmin da briefcase din nan,ka cewa muslimu ya tada motar gani nan fitowa" cewar dr marwan,sai haisam ya qarasa ya dauka jakar ya musu sallama ya fice,amma tana masa addu'ar Allah ya tsare. Kusan idan da sabo amma ta saba raka dr koda a gaban anni ne,idan ma bata je ba zata ce ita ta tashi taje,don haka yanzun ma ta tako masa har zuwa farfajiyar dake sassan annin "Da gaske wannan karon anni ta tada wannan rigimar kan yaran nan,gaba dayansu so take a kauda su" rausayar da aki amma tayi "Eh banga laifinta ba,tunda abinda ya kamata kenan dama ayi,kowannensu ya kamata zuwa yanxu ace bashi kadai bane" "Musamman ja'afar da yake da buqatuwa ta kowanne bangare" dr ya fada don yasan daya daga cikin abubuwan da amma ke kwana dashi ta tashi dashi ne a cikin ranta,amma kuma yakana da kara ya sanya bata nunawa ko a fuska,amma shi din sau tari yasha jinta cikin tsakiyar dare tana kaiwa Allah kukanta akan matsalar yaron nasu,ya sani dole abun zai tabata sosai ya kuma dameta kamar kowacce irin uwa. Kamar yadda ya zata din kuwa fuskarta ta dan sauya daga yadda take a daxun,hakan yasa cikin kulawa ya bata dukka hankalinsa "A wannan lokaci muna saka rai da fatan samun warwarewar komai,bake daya ba bani kadai ba,kusan duk wanda ke cikin gidan nan ya damu da lamarin,amma kuma addu'ar bawa mumini bata faduwa qasa banza" kai amma ta gyada cike da gamsuwa,koda yaushe shi din mutun ne da yake da qoqarin ganin ya kwantar mata da hankali kan dukkan wani lamari,bawai iya na ja'afar kadai bama "Idan na dawo akwai maganar da xamu tattauna,duk da ban sani ba wala'alla anni ta shaida miki kafin na dawo din" "Allah ya tsare hanya,a adawo lafiya" "Ameen een,zan samu dambun nan kuwa?" Ya fada yana murmushi,cikin nata murmushin ta amsa masa "Ka cika cikakken bafulatani kai din,zaka samu in sha Allah" da haka yana dariya ya juya ya fice,ita kuma ta koma ciki tana murmushin itama,wani sashen na zuciyarta kuma ya lula ga tunanin dan nata,wanda ta kwashe wasu kwanaki bataji muryarsa ba,abinda a shekarun baya bata saba da hakan daga gareshi ba,komai cunkushewar aiki baya iya tsallake wuni guda baiyi kiranta ba,qaddarar data afkawa rayuwarsa tasa komai ya canza. **************** Cikin sati guda rak maimunatu ta gama fahimtar abubuwa masu dama tattare da family din anni kuma familyn dr marwan khalid akko,ba shakka duk tubalin iyalin da nagartaccen uba ma'abocin ilimin addini da kuma aiki dashi ya samar dashi zaka sameshi ya banbamta da sauran ahali ta fuskoki da dama,kowanne mutum cikin gidan yana rayuwa bisa kyakkyawar tarbiyya da suka samu daga mahaifansu,mutane ne masu fahimta gami da sauqin kai da daukar kansu ba komai ba,duk da tarin dukiya da kuma arziqi da Allah ya yiwa mahaifinsu,akwai haduwar jini tsakanin maimunatu da 'yammatan,babu wanda ke nuna mata qyamata ko wani mummunan hali da zai sanya taji babu dadi cikin ranta. Gida ne da baya rabo da baqi 'yan uwa family kuma jinin marigayi khalid akko mahaifi gasu dr marwan,mutanen gidan suna da son baqi da son ganin wani baquwar fuska yazo musu,abinda yasa suka kasance masu son jama'a. Kusan dukka jama'ar gidan ba mazauna bane,idan ka cire matan gidan da anni,kusan zamansu a gidan kadanne ne idan ba weekends ba,hakan yasa ta fara sabawa da anni sosai da kuma amma,duk da cewa har yanzun bata sake sosai dasu ba,musamman amma da hakanan take jin nauyinta,tafi sakewa dasu laila. Bisa shawarar tabawa anni ta daga qafa,ta kuma fasa kiran ja'afar kamar yadda ta tsara,abinda ya karkatar da hankalin annin tasa aka maida maimunatu islamiyya cikin satin,tabawa kuma ta qara da cewa "Ina ganin haj anni,me zai hana a maidata boko ma?,tunda rannan naji suna hira da laila,da alama meson karatu ce,kuma hakan shine dai dai,ta yadda babu yadda za'ayi babban mutum ya raina zabinki" murmushi anni tayi "Haka maganarki take,amma kuma tabawa,inaso ne yayi mata hidima da kansa,ya raineta da kansa,ya kuma san ciwonta,ta yadda kome zaije yazo bazaiyi wasarere da ita ba,banqi shawararki ba,amma zan samar mata wanda zai dinga zuwa gida yana dora mata karatun bokon,har zuwa lokacin da zan fara aiwatar da abubuwan dana tsara,idan yaso shi da kansa ya samar mata duk makarantar da yaga dama,ya kuma cire kudinsa ya biya,hakan nakega sai yafi" kai tabawa ya gyada,lallai ta hangi dabaru masu yawa kan wannan shirin na anni,fatansu dai shine Allah ya tabbatar da alkhairi,ya shige gaba akan dukka lamarin. Cikin satin maimunatu ta zama cikakkiyar daliba ta kuma saje da iyalan gidan dr marwan,islamiyya dake layi na biyu dake bayan gidansu,ranar da zata fara zuwa din laila natsaye falon anni hanunta dauke da qur'aninta tana tisa haddar da zata bayar a yau din,maimunatun ta fito sanye da Egyptian hijab dinta har qasa dinkin kalar blue black. "Wow....ma sha Allah" laila ta fada tana murmushi,idanunta bisa fuskar bafulatana maimunatu,fuskar da zuwa yanzu ta sake washewa,ta fara fresh da ita saboda samun canjin weather da kuma zama waje daya gami da sauyin cima dama makwanci "Kinga yadda kayan sukayi matuqar karbarki kuwa maimunatu?,kamar don ke aka zaba kalar?" Murmushin nan nata me sanyi ta sakarwa laila,wanda kusan shi ta fiyi yi fiye data yi magana. Sai data leqa anni dake dakinta tayi mata sallama,sannan suka fito suka rankaya ita da hafsa da laila din da nadiya,fa'iza da rahama sun rigasu yin gaba,don dama ba kasafai suke jerawa dasu ba. Abinda ke bata mamaki yadda duk sanda zasu islamiyyan da qafa suke takawa,duk da cewa idan da sunso jikinsu zasu iya bin motar gidan ya qarasa dasu,amma sam basu damu ba tafiyarsu suke,babu wani girman kai ko jin cewa ubansu wani ne,ko kuma sun fito ne daga babban gida. ************* Zaune take cikin qawataccen falon anni,wanda ya wadata da tsafta da kuma qamshi ta ko ina,falon da a yanzu yake qarqashin kulawar maimunatu da bata bari koda tsinke ya sauka a kansa,ita daya ce qwal a falon,sanye take da wani milk high waist skirt na material mai santsi,sai rigarsa ta chiffon material milk color mai torches na brown,fatarta ta sake wani irin haske da kyau,ta kuma yi luwai luwai,duba daya zaka yi mata kasan cews tabbas ta samu nutsuwar zuciya da kuma ruhi a watanni ukun data shafe cikin gidan,saman kanta baby hijab ne da bata rabo dashi ruwan madara kalar skert din jikinta,wanda ya zame daga gaban kanta,ya bayyana lallausar sumar dake kwance daga gaba,kai baka ce akanta akwai manya kalba data roqi laila tayi mata ba,wansa lailan taso taqi matan,saboda sunyi sunyi ta bisu suje saloon da suka tsara zuwa a ranar saboda shirye shiryen bikin da suke a dangin ammi amaryar dr marwan kenan amma maimunatun ta qiya,ba kasafai take zarmewa da kuma zaqewa cikin lamuransu ba,don har yanzu bata saki jiki dasu yadda suke so ba,bawai don tans musu mummunar fahimta ko kuma zato ba,a'ah.....saidai ita din a koda yaushe tafi ganewa tsaiwa iya matsayinta,kada rayuwar ta rudeta ta kuma sanyata mantawa wacece ita. Komai dake tattare da maimunatu ya sauya,saidai har yanzun bata bar wasu dabi'u nata ba,saboda gudun manta asali da tushe,kamar yadda bata zubda ko cire duwatsun hannunta ba,hakanan kayan saqinta suna nan,tayi musu kyakkyawar ajiya,kamar yadda lokaci zuwa lokaci idan taji kewar gida ko dabbobinta,take sanyasu a jikinta ta wuni da abinta,su laila suyita tsokanarta,saidai ta bisu da murmushi kawai,kasancewar shine fiye da rabin amsar maganarta. Yau din gidan babu yawaitar jama'a sosai,kusan dukka kowa ya fita sha'aninsa,'yan mata matan sun fita wankin kai,anni kuma yau tana daki a kwance,don kwanaki biyu kenan bata da dan jin dadi tana fama da mura,masu aikin dake sassanta kuwa suna kitchen,wasu kuma suna bangarensu suna hutawa,ammi ta fita unguwa itama,sunata shirye shirye da hidimar biki,acan sassan nasu sai amma kawai. Yankam farce takeyi abinta da nail cutter,ta bada hankalinta sosai ga yankan,yayin da wani sashe na zuciyarta yayi nisa cikin zurfin tunani,yadda rayuwa ke gara mata,babu mahaifiya bakuma tasan inda mahaifinta yake ba,takan kalli su laila a matsayin 'yan gata gaba da baya,bawai gata na dukiya da daular da suke ciki ba,a'ah,gata na kasantuwarsu suna rayuwa gaban mahaifi mahaifiya kaka harma sa danginsu,sukan burgeta a yawancin lokuta,takanji inama ace tana da wannan gatan. Takun tafiya da sauri da asauri da kuma sautin kukan qaramar yarinya cike da rigima ya sanyata daga kanta daga abinda takeyi,ta kuma maida dubanta ga qofar shigowa falon duk da labulayen alfarmar da suka kangeshi daga ganin wanda ke tahowa daga waje,jim kadan me kukan ta bayyana,ta bankada labulen tana shigowa da sauri kamar yadda ta taho. Kyakkyawar yarinya ce ta gaske,wankan tarwada,kalar da dukka gidan mutum daya taga yana da ita,sanye da wata irin short sleeve gown mai azabar kyau,qafarta sanye da rufaffen takalmi na mata daya dace da kayan jikinta,kanta mai cike da suma me santsi da laushi kuma an masa wani irin gyara mai kyau da daukar hankali,an qawata shi da ribbons,hannunta daya dauke da wata qatuwar teddy da suka kusa yin kai daya,kai tsaye taci gaba da takowa cikin falon tana kuma kukanta,tare da rarraba idanu da alama akwai wanda take nema. Da idanu maimunatu ta bita,kuka take yarinyar da gaske,hawaye shabe shabe kan fuskarta,hakanan kawai tausayinta ya tsirga mata,duk da batasan wacece ba,batasab me akayi mata ba,saita miqa hannu a tausashe ta riqo hannun yarinyar,abinda ya ankarar da ita kenan da wani a falon,ta waiwaya a hankali tana duban maimunatu. Murmushi ta sakarwa yarinyar,duk da yadda taji idanun yarinyar har tsakiyar kanta,wasu irin idanu ne da uta masu kyau da daukan idanu,a hankali ta buda bakinta "yaki,zoki gayamin wane ne?,me akayi miki" ta fadi da taushi cikin sigar lallashi,kai tsaye kuwa yarinyar ta soma takowa zuwa wajen maimuntun,batayi qasa a gwiwa ba ta dorata saman cinyarta kana ta jinginata da jikinta,take yarinyar ta narke jikin nata. Dumin jikin yarinyar yasa maimunatun taba wuyata,da alama zazzabi kenan take,saita zagayo da kanta gefan fuskarta "Waye ya tabaki?,waye ya sakaki kuka?" Ta sake tambayarta kanta tsaye,salon tambayar da alama ya taba zuciyar yarinyar,sai ta saki kuka sosai cikin sheshsheqa tana cewa "Uncle hisham ne......." "Ya isa,yi shuru,indai shine sai mun hukuntashi,ki daina kukan haka,kinji akwai dumi a jikinki kada ya sake qaruwa" maimunatu ta fada tana jin tausayinta ba tare da tasan dalilin hakan ba. Qanqameta yarinyar tayi "Ba za'a yimin allura ba?" Ta tambayi maimunatu tana duban idanunta,murmushi ta sakar mata tana shafa tattausan gashinta "Babu wanda zai miki allura kinji" ta qarashe maganar tana jan yarinyar cikin jikinta sosai ta rungumeta,sai ta narke itama tana sassauta kukan gami da sakin ajiyar zuciya me qarfi,da alama abinda take buqata dama kenan,tunanin maimunatu yadan cilla wani waje jin yadda yarinyar tayi luf a jikinta tana sauke ajiyar zuciya,kamar tasan fuskar yarinyar a wayoyin al'ummar gidan,kamar tana ganin fuskarta a wajensu. Tsakiyar tunanin da take aka daga labulen akayi sallama wadda ke cakude da sauti na dariya a tausashe,ta daga kanta a hakali tana amsa sallamar,idanunsu suka sarqe waje guda dame sallamar. 18 Karo na uku kenan da ta taba ganinsa cikin gidan tun zuwanta,ba zata iya cewa ga ainihin sunansa ba,don babu abinda ya taba hadata dashi da ya wuce gaisuwa,daga nan take barin waje,tana da dabi'ar barin guri a duk sanda taga iyalin gidan sun hadu waje guda,har sai idan sun buqaci tayi zamanta. Cikin tsarguwa ta janye idanunta daga cikin nasa tana sake gyara zamanta gami da jan skert dinta zuwa qasa sosai,duk da dama ya sauka din,shima nasa idanun ya dauke yana shigowa cikin gami da sassauta dariyarsa "Ina yini" ta gaidashi idanunta nakan teddy din yarinyar data yar "Lafiya lau.....anni na ciki ne?" "Eh ta amsa masa a taqaice" "Yimin kiranta idan ba damuwa" da to ta amsa masa tana yunqurin tashi tare da qoqarin ajjiye yarinyar,saidai fir taqi ta qanqame maimunatu da kyau,idanunta nakan hisham. Qaramar dariya ya sake yana kallonta "Duk ki gama guje gujen naki tsaf kuma azo ayi allurar,wannan zazzabin jikin naki ta yaya za'a barki dashi" kafada ta noqe tana sake tale baki da alama zata sake sakin wani sabon kukan ne "Miqomin ita ki kiramin annin" gam ta sake riqe maimunatu tana cukuikuye dan qaramin hijab din jikinta,har sai da maimunatun tadan jashi kadan saboda jikinta daya dame "Qyaleta,bari na kira maka ita a hakan" ta fada tana saba ta a kafada,sannan ta fara takawa a hankali zuwa gefan anni. Da.kallo yadan bisu har suka bacewa ganinss,sai ya dauke idanunsa yana sakin boyayyar ajiyar zuciya,wannan shine karo na hudu daya ganta a gidan,baisan wacece ba,baisan kuma relation dinsu da ita ba,saidai akwai wani abu me fusgar hankali tattare da ita,bama kamar yanzun da sukayi kusa da juna ba kamar kwanakin da yake hangota daga nesa ba. Saman lallausar dardumar dake dakin ta samu anni,tanata danne danne a wayar da ala dole ta karbeta,saboda ciwo baki na jikokinta,bata daga kanta ba,tadai amsa mata sallamar cikin kulawa saboda hankalinta na ga wayar,har sai da maimunatun da zuwa yanzu ta maida yarinyar bayanta ta shigo dakin gaba daya "Wa nake gani a bayanki kamar amna?" Leqowa yarinyar tayi da kanta don anni ta tabbatar "Ja'ira,sai yau Allah yayi suka dawo mana dake kenan?" Anni tafada tana dariya,koda bata sake cewa komai ba maimunatu ta gane wacece,yarinyar da kullum rana ba zata fito ta fadi cikin gidan wani bai ambaceta ba,taji yadda akasha gwagwagwa da kakanninta na wajen uwa kafin su yarda su dawo da ita,saboda ita kadai ce jikarsu,jikarma kuma ta wajen diyarsu mace qwaya daya tal da suka mallaka,taji kuma ance mamanta ta rasu,take tausayi da qaunar yarinyar ya sake saukar mata fiye da dazu,qaramarta da ita tasan dacin maraicin uwa?,ko ita dake da girmanta yaya takeji a ranta bare wannan,hukuncin Allah ne,ba yadda baya tsarawa,haka bawa zai karba a duk yadda yazo masa. Kememe amna taqi sauka daga bayan maimunatu,duk yadda anni taso tazo gareta "Yar nema,zamu hadu ne,wannan din kin santa ne?,daga zuwanki zaki dafewa diyar mutane?" Annin ta fada tana dungure mata kai,abinda yasa amnan ta sunne kai a bayan maimunatu ba tare data ce komai ba,maimunatu na jinsu tana tayasu da murmushi "Yaa hisham ne yace nayi masa kiranki" ta fadi sunansa kamar yadda taji yaran gidan na fade "Ya shigo mana,baisan dakin nawa bane da zai tattago ni ina fama da kaina?" Goye da amna ta fita a dakin don gaya masa saqon annin. Waya yake dannawa,amma jin takunta yasa ya tsaya ta daga kansa yana dubanta,ta shaida masa abinda anni tace,har ya miqe kira ya shigo wayar tasa,sai yace "Ina zuwa" yana duban fuskar wayar ya fice daga falon,dai dai lokacin da daya daga cikin ma'aikatan gidan me suna sha'awa ta shigo falon tana shaidawa maimunatu malaminta yazo "To ina zuwa" ta amsa tana komawa wajen anni ta gaya mata abinda hisham din yace,taso aje mata amna amma yarinyar taqi,haka ta juya zuwa kitchen don kaita wajen tabawa,wadda dama ita ke rainonta amma sam wajen tabawan ma taqi zaman "Haba uwar gijiyata,wannan zazzabin na jikinki da kin haqura kin zauna,bakya fita gurin shukokin can ba iska ta sake kadaki" fir taqi,saboda tana tsoron kada hisham din ya biyota nan yayi mata allurar da ya ambata din,haka maimunatu ta fita da ita inda ake mata karatun tana goye da ita,hannunta kuma riqe da litattafanta. Tana cikin jikinta suna karatun,tana bala'in qaunar karatun nata,saboda.malamin ba qaramin qwarewa yayi ba da kuma sanin makamar koyarwa,cikin watanni uku kacal ta fara gogewa fiye da tsammaninta,duk da dama dai ta samu foundation me dan kyau ba laifi daga makarantar primary din da tayi a gembu. Gab da magariba suka gama karatun kamar kullum,tana goye da amna da barci ke dibanta suka shiga cikin gidan,ta taras dasu laila duk sun dawo,sun sha qunshi da gyaran kai tubarkalla,kowacce cikinsu tana da suma dai dai gwargwado irin na fulani. Duk yadda suke daukin amna tazo gurinsu taqi kowa,kowa da kalar wayon da zaiyi mata amma ta qiya,murmushi maimunatu ta sake,har fararen haqoranta suna fitowa "Saiku haqura,yau dai kam ni ta zaba" sunata yiwa yarinyar tsiya ta wuce da ita dakinta ta kwantar da ita saman gadonta,zuwa lokacin bacci yayi awon gaba da ita. Washegari amnan tana barci maimunatu ta wuce islamiyya,sanda ta farka bata ganta ba ta saka rigima,rarrashin duniya kowa yayi mata amma ta qiya,hatta da anni da amman da suke dasawa yau taqi,saboda sun bari hisham kafin ya fita aiki ya nata allura,basu samu lafiya ba sai da maimunatu ta dawo,da gudu ta taryeta kuwa tun daga bakin qofa,maimunatu ta dagata tana taba jikinta,ta samu zazzabin ya sauka,baki ta tura gaba cikin murya irin ta yaran da suka samu gata "Ba uncle hisham bane yayimin allura" "Ya salam,sannu kinji,kiyi haquri" maimunatu ta fada tana shafa bayanta,saita kwanta luf a jikinta tana bata labarai har suka qarasa cikin gidan. Cikin kwanakin wata irin shaquwa ce sosai ta shiga tsakanin amna da maimunatu,ta maisheta tamkar uwarta,duk gidan a yanzu babu wanda take dafewa kamarta,kowa yasan hakan cikin gidan,gaba daya ma ta dawo da kwananta dakin maimunatu,hakan yayiwa maimunatu dadi sosai,saboda tafi sakewa da amnan akan kowa cikin gidan,zasuyi zamansu a daki suyita hira da amnan kai ka dauka da wata babba take magana,sosai amnan ke jin maganarta,da gaske yarinyar qaunarta take,amna yarinya ce me wayo da surutu,haka zata zauna ta yita baiwa maimunatu labarin mommynta da twin sister dinta da ta rasu,takan ce "Ummu(mamam shaheeda)amma/anni sunce sunje maka,zasu dawo,zasu siyomin tsaraba me yawa ko?" Sai maimunatu ta gyada mata kai cike da tausayinta "Amma me yasa ni mommy bata tafi dani ba?,kuma ta tafi da amra ta barni?" Ire iren maganganun dake karya zuciyar maimunatu kenan akan yarinyar,yake qara mata sonta da kuma tausayinta,sau tari takan faki idanun yarinyar ta share hawayenta,saboda ita da yarinyar dukkaninsu suna cikin jarabawar maraici,har gwara amna,tana da gata gaba da baya,saboda tsabar gata ma kowa so yake a bashi ita ya riqeta,ita kuma fa?. Idan ta gama wannan kuma sai ta koma zancan mahaifinta,wanda maimunatu batasan wayeshi ba,saidai da alama yarinyar tana kewar mahaifin nata kewa me tarin yawa,a zuciyarta take jin tunda yana raye bai kamata ya nisanci yarinyar haka ba,tana da buqatarsa a kusa da ita,duk randa ko ta samu yin waya dashi,ranar gaba daya labaranta nasa ne,maimunatun takan bata lokacinta ta biye mata suyita yi,abinda ya qara sabonsu da shaquwarsu kenan da ita. Yammaci ne sosai,wanda yake dauke da lullumi sosai da zakayi tsammani damina ce zata fara,saidai maimakon daminar ana dakon zuwan zafi ne kafin gabatowarta. A irin wannan lokacin gidan yakan kasance shuru,rana ce da babu makaranta both islamiyya da boko,yawanci a wannan lokacin 'yammatan gidan sunfi kwanciya suyi barci idan basu da abinda zasuyi,idan kuma suna dashi kowa yakan kama aikin gabansa,zuwa dare kuma su hadu zaman hira,ma'aikata kuwa na kitchen na sassan biyu,sassan dr marwan ko na hajiya anni. Maimunatu ce ta dage dan qaramin falon da anni kan zauna ta huta lokaci zuwa lokaci,hannunta dauke da zobo data dafawa annin tsurarsa,babu suger bare kayan hadi sai citta da kanunfari kawai,tun zuwanta gidan takan dafawa anni shi akai akai,saboda qarin jimi da kuma gyara zuciya da sauran cututtukan hawan jini,sosai anni takejin dadinsa,don tana ganin amfaninsa a jikinta. Tashi xaune anni tayi tana amsa sallamar cikin sakin fuska,idanunta nakan maimunatu,a duk sanda ta kalleta tana jin dadin sauyin da ake samu tattare da ita,zuciyarta kuma a kullum tana gaya mata kamar lokaci yayi da zata bayyanawa maimunatu qudurinta. "Sannu da hutawa anni" "Yauwa maimunatu,ke zaa yiwa sannu" murmushi tayi ta zauna ta fara zuba mata zobon,annin ta karba tana godiya ta fara kurba,jifa jifa suna hira. "Maimunatu......qarasa jikin soket ki ciromin wayar can da Allah" amsawa tayi ta ciro kamar yadda ta umarceta "Yauwa laluba ki kamomin ja'afar" maida dubanta tayi ga numbers din dake kan wayar,ta fara laluba sunayen,har takai ga sunan da annin ta nema "Gashi anni" "Yauwa kiramin shi" ta fada tana ci gaba da kurbar zobon,zuciyarta na ayyana mata tunani kala daban daban. A nutse la latsa icon na kira,kiran kuwa ya tafi kai tsaye,take daga qasan sunan number wayar qasar waje ya bayyana,kuma sunan TURKEY ya fito daga gaban number kadan *TURKEY* *TURKEY CAPITAL* _ANKARA yanimahalle_ _Green forest mahalle_ Cikin babban ginin me dauke da apartments apartments,hawa na biyu,madaidaicin falo ne da ba zaka kirashi tangamene ba,kamar yadda ya wuce ya amsa sunan qarami,me dauke rantsatsun kujeru irin na asalin qasar turkey din,lafiyayyen carpet da curtains ash color light and dark dukka na qirar qasar,sai rantsatsiyar wallpaper kalar kayan dake falon,qananun sideel table da babbansu daga tsakiya,dining space da aka maqalawa fridge dukkansu kalolin kayan falon ne. Daga gefan fridge din lafiyayyen matashin saurayi ne jingine da fridge din,hannunsa riqe da cup daya cika da tataccen ruwan kayan marmari kala daban daban da aka markada aka kuma tacesu a mazubi guda,dogo ne me murjajjen jiki,yana sanye da shirt mai dogon hannu da kuma trouser,yayi crossing qafafunsa hannunsa daya soke a aljihun wandon nasa,daya hannun kuma yana riqe da cup din da yake kaiwa bakin nasa lokaci bayan lokaci. Kana kallonsa zakasan yayi nisa a tunani da kuma nazarin inda idanuwansa suke kallo,gaba kadan dashi inda aka tsara rukunin kujerun dake falon. Mutum biyu dake zaune cikin falon,daya farar fata ne,bature sosai,mr denis evoy dan asalin qasar Belarus,yayin da dayan ya kasance baqar fata ne,wanda ya mallaki wata sassalkar fata me kyan gani da kuma burgewa ko cikin jinsin masu baqar fatar da ake kira da chocolate color,CAPTAIN JA'AFAR MARWAN KHALID AKKO qwararren kuma sanannen matuqin jirgin sama wanda ya ajjiye aikinsa,ya kuma yi switching kansa ya zuwa babban dan kasuwa,mamallakin kamfanoni dake samar da manyan gine gine na manyan ma'aikatu jami'o'i da manyan kamfanoni tituna dama gidaje,manyan gine gine masu ban sha'awa da qayatarwa. Kyakkyawa ajin farko,irin kyan nan da a hankali yake bayyana kansa,wankan tarwada ne,a very husky man built like a football player,dukka qirar jikinsa na nuna alamun qarfi dake bayyana cikar mazantaka,yana da tsaho da kuma kauri dai dai misali wanda ya taimaka wajen sake boye ainihin tsahonsa,wasu irin shanyayyun idanu masu matuqar daukan hankali da kuma tafiya da imanin diya mace ko wacece ita,lafiyayyen qasumba ne dashi wansa bata rabo da saisaye da kuma gyara,gyaran da yake dacewa da kyawawan labbansa hancinsa me tsaho da tudu da kuma cikakkiyar girarsa,akwai wata suma ta musamman saman kansa mai sulbi da kuma sheqi ta asalin bafullace,wadda batayi yawa ba hakanan ba kadan bace. Iya lafiyayyar fatarsa da kuma zara zaran yatsun qafarsa da na hannu kadai idan ka kalla zakasan cewa a huce yake cikin cikakkiyar wadata da kuma hutu,sau tari qannensa na sha'awar yanayin qafarsa dake luwai luwai kamar ta mace,saboda yadda ta samu hutu da kuma gyara,tako ina ja'afar ya cika cikakken namiji,wanda ya samu kusan cikar komai na rayuwa......saidai abu biyu daya rageshi,na farko mutum ne shi miskili na gasken gaske,irin miskilancin dake baiwa mutane da dama mamaki,ake kuma tunanin lokaci zaizo da zai sauya,saidai har zuwa lokacin da aka tsammaci zai sauya din yazo bai sauya ba,lokacin kuma ya sake zuwa ya hade masa da baqar qaddarar rasa matarsa da kuma diyarsa mafi soyuwa a wajensa,abinda ya sake canzashi kenan,ya kuma sake cillashi duniyar miskilanci. Sosai yayi relaxing bayansa da jikin kujerar da yake zaune,very calmly yake kallon Mr Denis,sai kayi tsammanin duk duniya bashi da wata matsala a rayuwarsa dake barazana ga farinciki da kuma ci gabansa. 19 *Arewabooks:Huguma* https://arewabooks.com/chapter?id=6351005edace9b957e575eaf Saidai shi din haka yake,komai nasa a nutse yake cike da tsari da kuma nutsuwar,yana duban mr denis ne jabir dake jingine da fridge shima yana nazarinsa,cikin kwanakin nan gaba daya aikin ja'afar din kenan,ya dawo da dukka hankalinsa akan kamfaninsa,ganawa yake tayi da mutane daban daban duka akan kamfanin,wani irin huge change yake gani tatare dashi a dare daya,sau tari yakanyi sha'awar inama ace ja'afar din ya tabbata a haka?,wasu lokutan a baya sai yayi kamar zaici gaba da rayuwarsa kamar kowa,sai kuma abun ya sake tabarbarewa,but surely a wannan karon yana ganin yanayin kamar ya banbamta da na baya,ko wannan din zai dore?. Murmushi jabir ya saki,yana dora cup din saman fridge din sanda yaji mr denis na complain kan cewa "Sir, you didn't say anything since we start the negotiation" a ransa yake cewa da alama mr denis ja'afar din baqo ne a wajensa,sai ya fara takawa zuwa inda suke zaunen,gab kuma da zai qarasa wayar ja'afar din ta dauki ruri kiran anni ya shigo. Da idanu kawai ya kalla wayar,sai da yaga sunan me kiran sannan ya miqa hannu a nutse ya dauka,ya kalli mr denis "Excuse me" ya fada da wata deep and husky voice,saidai kuma akwai taushi da laushi daya cika muryar. Shi ya fara yiwa annin sallama cikin ginshira da nutsuwa gami da wani irin kamun kai kamar mace,daga can sashen anni ta amsa tana sauke ajiyar zuciya "Anya?,anya babban mutum?" Anni ta fada tana nuni da yatsanta kamar yana gabanta "Barka da warhaka anni" yayi fatali da zancanta ya maye gurbinsa da gaisuwa "Barka kadai,kuna lafiya?" "Alhamdulillahi,fatan kowa yana lafiya" "Lafiyar dai da sauqi" anni ta fada zuciyarta fal kewa da kuma rashin dadi kan sauyawarsa "Subhanallah,wani abu ya faru ne?" Ya tambayeta yana gyara zamansa kadan gami da yamutsa fuskarsa,abinda yasa girarsa dake cike da gashi ta kusan hadewa waje daya "Mene ma bai faru ba ja'afar?,fisabilillahi.....yanzu ace haka rayuwa zata ci gaba da tafiya" qaramar ajiyar zuciya ya sauke,shi kansa yana damuwa,yana damuwa kan yadda ya kasa moving forward yadda ya kamata,yana damuwa kan damuwar da mutanen nan masu muhimmanci a rayuwarsa ke shiga damuwa saboda shi,yana damuwa da yadda kowa hankalinsa yake kansa,to amma ya zaiyi?,shaheeda ta daban ce,tayi masa wani mummunan tasiri me matuqar qarfi da kaifi a rayuwarsa "Aci gaba da tayamu da addu'a, everything will be okay in sha Allah" nannauyar ajiyar zuciya ta sauke "Addu'a kam ita aketa yi babu fashi,babu kuma kama hannun yaro.....sai yaushe ka shirya dawowa qasarka?" Ta jefa masa tambayar da shi kansa baisan amsarta ba,gani yake kamar bashi da wani sauran zama da zaiyi a qasar "Ban shiryama hakan ba anni,har yanzu da sauran lokaci" fuska tadan hade kadan "Kamar yaya ja'afar?,bakasan har yanzu zamanka a nan bashi da wani amfani ba?,idan kuma akwai ka gayamin"ta masa tambyar da salon titsiye,maimakon ya amsa mata sai ya sanya hannu saman kansa yana shafa lallausar sumarsa "Ina amna?" Kamar tace masa sai yanzu zai tuna da ita?,sai kuma ta bari,don a yanzun babu abinda take da buqata irin dawowarsa "Dazun maimunatu ta kaita wajen Aishatu" "okay.......aci gaba da yimin addu'a,ita nafi buqata,am little busy,zan kiraki anni" "Ja'afar!" Ta kirayeshi da kakkausar murya "Naam" "Ina jiran kiranka,akwai magana me muhimmanci da nakeso muyi dakai,ka tabbatar kome kakeyi ka kirani bayan ka kammalashi" kai ya jinjina,domin annin mutun ce me kima a idanunsa,ba kasafai yake mata kallon kaka ba,yafi mata kallon uwa "In sha Allah" daga haka suka yanke wayar,yana dan tunani cikin ransa wacce magana zasuyi da annin?,duk da jikinsa ya bashi tatsuniyar gizo dai ba zata wuce ta qoqi ba. Sanda yake qoqarin kiran ammansa yaji annin ta kirayi jabir,baisan me take ce masa ba,saidai jabir din ya tashi daga wajen ya fita yana amsa wayar annin. Saida amma ta sauke ajiyar zuciya sanda taga kiranja'afar din nata,abune me matuqar wuya ta daga waya ta kirayeshi,saboda zallar kara da yakana irin tata,zamantowarsa dan fari a wajenta,ta ajjiye rigar amna da take ninkewa wadda yarinyar ta cire yanzun ta dauki wayar. Kamar ko yaushe cikin girmamawa da qanqan da kai ya gaidata,ta amsa masa cikin nuna kulawa tare da tambayarsa jikinsa,wanda daga nan bata iya qara cewa komai ba,sai shine ya tambayi amna "Yanzun nan maimunatu tazo ta dauketa suka fita" "Okay amma" yayi mata sallama yana ajjiye wayar "Maimunatu,maimunatu dai?,wacece haka?" sai yaji ransa yadan sosu,don yaso jin muryar yarinyar,yayi matuqar kewarta har baisan iyaka ba,yanason yazo ko don ita,amma duk sanda ya ganta tana karya masa gwiwa ne,don tana tuna masa da mahaifiyarsa da kuma 'yar uwar tagwaitakarta. Last time da ya kira haka akace tana wajen maimunatu,har kusan sau uku yana kira amma ana sake gaya masa tana wajenta,abinda ba al'adarsa bace maimaita kiran waya,wacece ita din ma?,amsar da baisan ta ba,haka kawai yaji kansa ya dauki zafi,sai ya dubi mr denis "I heard everything you said,i need a time to think about what we discuss,i will contact you " kai mr denis ya kada masa,sannan ya bashi hannu sukayi musabaha,me denis ya tattare takardunsa ya masa sallama ya fice zuwa qofar gidan,inda PA dinsa ke zaune cikin mota yana jiransa. Zazzafar iska ya furzar daga bakinsa wadda ta fito hade da sassanyan qamshin alawa me taste din mint da baya rabo da ita,hannunsa a saman goshinsa yana murzawa a hankali,ya daga shanyayyun kyawawan idanunsa ya aza kan agogon dake manne a falon,wanda yake nuna lokaci daga qasa kuma kwanan wata. Duk rana irin ta yau rana ce da yake tafiya Istanbul ya kwana,washegari ya shiga ziyartar guraren tarihi da suka shafi annabawa da sahabbai,da wahala yayi missing ranar ba tare da yaje ba,abune me muhimmanci cikin rayuwarsa,yana daya daga cikin ababen tarihin da shaheeda ta barwa rayuwarsa,ita ta koya masa hakan,ita ta sanar dashi wanzuwar wajen,sai ya miqe da hanzarinsa dake nuna zallar lafiya da kuma cikar kuzari,ya dauki wayarsa da kuma agogon hannunsa dake saman table ya nufi dakinsa,dai dai lokaci jabir ya dawo falon,yabi hanyar da kallo,sai kawai ya rufa masa baya. Goye yarinyar take a bayan maimunatu,suna takowa. Ahankali daga sassan amma zuwa wajen anni,tun sanda ta fuskanci anni waya zatayi ta zame daga dakin,ta kuma fake da dauko amna,hakan tafi nutsuwa da hakan,ko babu komai annin zata sake tayi wayarta yadda ya kamata,tun annin tana qorafi harta saba,indai wannan ne halin maimunatu ne. Dariya yarinyar keta yi abinta,hankali kwancw tana jin dadin labarin da maimunatu ke bata. Kusan minti goma kenan da dawowarsa cikin gidan,amma bai shiga ciki ba,ya tsaya daga bakin motarsa yana amsa waya,hannunsa dauke da briefcase dinsa da kuma lab coat,harda qarin baqar leda. Siririyar muryarta dake cike da wani irin taushi ce ta ratso ta inda yake tsaye,abinda yaja hankalinsa kenan,ya daga kansa a hankali yana dubansu daga inda suke takowa. Sanye take da skert high waisted wanda ya kama qugunta ya kuma baje sosai daga qasa,sai wadatacciyar rigarsa me hannu wanda ya tsaya mata iya gwiwar hannunta,kanta lullube yake da mini hijab wanda shima ya taimaka wajen suturce jikinta,saidai kuma yayi matuqar haskata kasancewarsa peach color. Samun kansa yayi da binta da kallo,dan qaramin bakinta me siraran tausasan labba suna motsawa,tana da wani irin kyau me sanyi da fusgar hankali,tun ranar da ya fara ganinta ya tantance hakan,ta dauki hankalinsa ta kuma burge shi qwarai,duk da kasancewarsa mutum da ba kasafai mata ke burgeshi ba,bama shi kadai ba,kusan duk haka mazan gidansu suke,dalili da ya sanya ake musu kallon masu jin kai kenan "La la la,kika yarda kike goyata a bayanki saita karya miki baya?" Maganar haisam ya ratsa kunnenta sanda take shirin giftashi ba tare data kula da tsaiwarsa a wajen ba,hada idanu sukayi,ya bita da murmushi,sai tayi maza ta janye idanunta tana sakin wani qaramin murmushin ba tare da tace komai ba. Gyara tsaiwarsa yayi,yana maida wayarsa gaban aljihun rigarsa tare da sake cewa "Baki gani ta kusa kamoki a qiba?,amna bakisan yanzun kin girma ba,saura kadan ki cika 4years fa" kafada ta noqe tana buya bayan maimunatu sanda yake shirin karbarta,a dole ya haqura da amsar nata,maimunatu ta wuce da ita bayan ta gaidashi,ya amsa yana binta da kallo har sanda ta bacewa ganinsa. Cikin jikinta takejin wani iri a duk sanda haisam yake mata irin wannan kallon,batasan ma:anarsa ba,ba kuma tasan dalilinsa ba,ya mata shige da kallon da himunta yake mata,amma dai tana jin nauyi da kunya sosai. A dining area suka tadda khadim,shi ya karba amna daga wajenta,ta bashi ba don ta gaji ba,sai don khadim din shima mutumin amna ne na gaske,saidai tun bata isa dakin anni ba sai ga amnan ta sake biyota,ta kama hannuwanta tana dariyar meya hadota da khadim din taga ta bata rai,bata amsa mata ba suka wuce. A hankali anni ta ajjiye wayar gefanta tana fidda ajiyar zuciya,dai dai lokacin maimunatu ta shigo dakin,goye da amna a bayanta,kusan wannan al'adarta ce,mtuqar zasu tattaka zuwa wane waje kamar haka sai ta dauketa ta aza a bayanta,dukkaninsu fuskokinsu dauke suke da dariya,da alama wani labarin suke baiwa junansu. Idanun anni a kansu,wani abu ya darsu a ranta,kusan tafi kowa jin dadin qulluwar wannan kyakkyawar mu'amalar tsakanin amna da maimunatu,taci gaba da kallonsu a fakaice,farinciki ne shimfide saman fuskarsu,wanda abune da ba kasafai ake ganinsa akan fuskar amna ba,tun daga sanda ta rasa mahaifiyar da 'yar uwarta da suka kwanta ciki daya. Kwarin gwiwa gami da yaqini taji yana shigarta,zuciyarta na bata shawarar tunkarar maimunatu,gwara tun yanzun tasan da maganar,tana ganin kamar hakan zaifi dacewa,akan ta samu zanca lokaci daya,amma kuma idan ta aikata hakan maimunatu zata ci gaba da walwalarta da sakewa dasu yadda take a da?,babu gamsashen tabbaci akan hakan,abinda yasa hankalinta yafi karkata da barin maganar a cikinta,har zuwa sanda zata gama magana da ja'afar kan ainihin lokacin da zai dawo cikin ahalinsa. Ta baya jabir ke kallon ja'afar kadan kadan,cikin ransa yana juya maganar da suka fara yi da anni a kansa. Yana tsaye ne yana shirya kansa cikin wasu lafiyayyun suit saqar qasar Italy kamfanin kiton k-50 wine color masu dan haske kadan,agogon hannunsa gold color ne na companyn lange and sohne mai asalin tsada da kyau. Bayan ya feshe jikinsa da mayen tattausan turaren bad boy,ya zauna baya a hankali yana saka socks dinsa,sai a sannan jabir yayi magana,ganin cewa tunda ya shigo shi din bai ce masa komai ba "Ina zaka ne haka a wannan lokacin?" Sai daya daga kai ya dubeshi sannan ya sauke yana ci gaba da sanya safar "Ka manta yau wacce rana ce?" Dan tunani kadan jabir yayi sannan ya amsashi "Oh,yeah,amma kamata yayi ka jirani mu fita tare" "I finished bazan iya jiranka ba,saidai ka sameni a mint garden" "Alright,ba case" ya fada yana miqewa ya nufi toilet,shi daya ne keda wannan alfarmar a wajen ja'afar din,banda shi din yasan bazai tsaya jiransa ba. Kamar yadda yace din kuwa,ya cimmashi a mint garden cafe and bistro,saman table din shi daya ne,yana kurbar coffee din me zafi a hankali yana duban wani sashe na daban, joining dinsa jabir yin yayi,idanunsa kan fuskar ja'afar din kafin ya sauke cup din yana dubansa. "lokaci yayi fa,daya kamata ace ka sake ajjiye wasu family din da zasu zame maka makwafin wadanda ka rasa" tsaf ja'afar ya daga kai ya kalli jabir,tsahon wasu sakanni kamar bazai amsa ba kafin yace "Kai ka taba ganin inda GURBIN IDO ya zama idanu?" Tambayar data sanya jabir zuba masa idanu,yana hasashen irin dagar da za'a diba nan gaba kadan,shi da kansa ya qarashe amsar tambayar bayan ya miqe tsaye ya zuba hannayensa a aljihun wandonsa "Banajin har kawo yau an haifi macen da zata mayemin gurbin shaheeda,ita kadai ce,kuma ta tafi da dukkan abinda zai burgeni daga diya mace" daga haka ya fara takawa sannu a hankali. Tabbas jabir ya sani,ba abune mai sauqi ja'afar yaso wata diya mace ba,koda a nesa ne balle nan kusa,ko kafin shigowar shaheeda rayuwarsa,shi din ba irin mutanen nan ne da ake samun soyayyarsu da sauqi ba,bare kuma wannan babban al'amari yazo ya yiwa rayuwarsa karan tsaye. A wajen jiran jirgin qasa me tafiya da lantarki ya sameshi,tsaye yana kallon gefensa guda,hannunsa cikin aljihun wandon nasa,duk da yaji takunsa amma bai waiwayo ba,matsawa gaba kadan yayi ya daidaita tsahonsa da nashi,kusan kansu daya,amma ja'afar din ya darashi "Dole dole ja'afar ka dai daita rayuwarka zuwa yadda take a baya,koda komai bai dawo ba,shekaru uku ba wasa bane,kana tunanin shaheeda zataji dadin wannan halin da ka sanya kanka?,wanda ya mutu ya riga da ya mutu,bazai taba dawowa ba,indai bakayi qoqarin saita kanka ba tabbas nan da lokaci qalilan zaka ji sanarwa daura maka aure,confirm" wani kallo ya juyo ya watsawa jabir,daidai lokacin da jirgin ya tsaya,sai ya taka zuwa gaba sannan yace "Mafaashi" qaramin murmushi jabir din yayi,sannan yabi bayansa a hankali shima yana amsa masa "Zaka gani kuwa" 20 Sannu a hankali rayuwa ke juyawa,cikin wani yanayi me dadi ga maimunatu,dukkan wani ci gaba a hankali yake samunta,ta zama cikakkiyar diya ga Dr marwan,bai taba bari an banbantata cikin duka hidimar da zaiwa iyalinsa ba,bata da matsala da kowa kasancewarta yarinya me haquri kawaici da kuma sanyin hali,zallar biyayya da kuma girmama kowa koda na qasanta ne,wannan ya siya mata soyayya sosai daga wajen iyalin gidan dr marwan,saidai a rayuwa ba kowane zai soka ba,hakanan bazaiyiwu ace kowa gudunka yake ba,cikin surukai da kuna sauran jikokin anni ba za'a rasa wadanda suke mata wani kallo na daban ba,duk da babu wanda yasan daga ina fa fito,ko kuma ita din wacece. Babu abinda yafi mata dadi irin ilimin da take samu,batasan cewa a baya rayuwar da take rayuwa ce dake cike da zallar duhu ba sai yanzu,batasan haka ilimi yake da dadi ba sai yanzu,duk cikin abinda anni tayi mata babu abinda take jin ya mata dadi fiye da kima irin karatun da take,qoqarinta kan karatun ya ninka adadin karatun da ake mata,wannan ya sanya ake qara mata karatun da yawa,yake kuma mugun gudu,hakanan ta fannin boko,shi kansa malamin yakanyi mamaki idan yaga wasu guraren da yawa ta iyasu kafin suxo wajen,dole hakan kuma ta kasance,don kuwa duk sanda ta koma gida bita take sosai,tare da duba duk wani karatun da ya shafi wanda aka qara matan,koda yaushe baka rabata da dan qaramin dakin karatu dake gidan,wanda dr ya qirqireshi saboda yaran,su din kuma ba wani damuwa sukayi dashi ba,ba kasafai suke shiga,zuwan maimunatu da yawan shigarta wajen sai wajen ya soma rayuwa,a kullum zata tsaftaceshi,ta kuma bata lokaci a can tana nazari,daga fannin bokon har na addini. Zuwa lokacin maimunatun ta goge sosai,a hakan ma don ba ita din ba me yawan buri ko son qyale qyale bace,sau tari idan zasu shopping ko wani abu makamancin haka bata binsu,suyita mata tsiya da kazar gida,saidai ta bisu da murmushi,ta gwammace ta zauna da amna suyita labarai,tatsuniya da sauransu,ko ta tsefe kanta ta gyara mata tayi mata kitso ko kalba,ita kanta yarinyar tunda maimunatu ta fara kula mata da kanta ta daina yarda a kaita saloon,har yanzu tana nan a bufulatanarta,bata bari ta jirkita komai nata ba baya ga suturar jiki da kuma tsaftarta data qaru. ************K'arfe uku na azahar anni ta sanyata ta shirya don rakata gidan uncle abbas qani ga dr marwan,zata duba diyarsa da bata da lafiya ita da yaron da amaryarsa ke goyo,magana tayi da maimunatu kan ta shirya tayi mata rakiya ita da tabawa,babu musu ta shirya din,karo na biyu kenan da zata fita tun zuwanta gidan,fitar farko ma hisham ne ya debesu ya kaisu wani eatery sukaci abinci saboda qarin girma da ya samu a asibitinsu,shima tun suna shirin take kallonsu,duk da sun mata tayi amma tace a'ah,zata zauna da anni,kada a barta ita kadai. Har sun fita suka dawo sukace yaa hisham din yace ta fito suje "Kuje kawai ku dawo ina jiranku" "A'ah,tashi ki shirya kuje" anni tace da ita,a dole ta sauya kaya ta bisu. Kusan daga tafiyar har dawowar a takure take,saboda yadda yace ta zauna gaban mota,suna tafe kuma yana janta da hira da 'yar tsokana,abinda ya aza mata nauyi sosai,yasa ta dinga jin kunya ta kuma gagara sakewa har suka dawo. Bala'in nauyin hisham din takeji,saboda yadda yake mu'amalantarta ya banbanta da yadda sauran mutan gidan suke mu'amala da ita,yana da kirki sosai,yawan barkwanci musamman idan a cikin gida yake cikin family dinsa. Tsaf ta shirya cikin doguwar rigar atamfa,sabuwa ce,cikin dinkunan da anni tasa akayi mata,ta yane kanta da madaidaicin mayafi,dankwalin yana riqe a hannuta saboda rashin sabo da daurashi "Ma sha Allah"anni ta samu kanta da furtawa,saboda wani irin kyau da maimunatun tayi mata,tana ji a ranta ko a yanzu ja'afar ya dawo bai isa ya kushe maimunatu ba,don ta goge qwarai,ta tabbata ko a rugarsu yanzun sai sunyi mamaki idan suka ganta. Daga ita sai annin sai amna suka tafi,drivern gidan shike tuqa su,jifa jifa suna hira da anni,hankalinta kuma na sama hanya,tana sake ganin ainihin garin na gombe,tafiyar duka duka bata wuce minti talatin ba suka isa unguwar,unguwa ce itama me kyau dake dauke da gidan masu wadata. Maimunatu na dauke da amna suka fara takawa zuwa cikin gidan,jikokin annin uku suna biye da ita suna ta tsokanarta,saidai taqi kulasu,da alama a qule take dasu,saida sukazo qofar falon daya daga cikinsu tace "Anni,bari na cire miki takalman"ta fada tana dariya gami da duqawa "Ke arcan,kiyi ta kanki,ni ba take nake ba,gwandamar banza,wallahi ina tafe cikin gidan nan,duk saina bada sadakarku" ihu yammatan suka saki,namijin na musu dariya harda dafe ciki "Eh,ba zaku saka min 'ya'ya a gaba kuna cinye tattalin arziqinsu ba,kowa ya kama gabansa mazanku da matanku" tasa kai cikin falon abinta tana sakin sallama,yayin data barsu suna ihu da dariya na tsiyar data lafta musu. Karbar girma amaryar uncle abbas tayi musu,ta dinga nan nan da annin,da alama yar gaban goshinta ce,saida suka gama shafe wasu mintuna sannan dayar ta shigo,haj munubiya,uwar gidan uncle abbas. Da kallo anni ta bita kafin ta dauke kai tana amsa sallamarta,ta samu waje cikin jin izza ta soma gaida anni,saidai cikin girmamawa ne,sanin cewa annin bata daukar raini sam,daga nan ta zauna ana taba hira da ita lokaci lokaci. Karo na kusan biyar idanunta suka sake kaiwa kan maimunatu dake wasa da hannayen amna "Anni a ina aka samo mana bafulatana haka?" Waiwaya tayi ta dubi maimunatu sannan ta dawo da dubanta ga munubiya "Surukarku ce" "Matar wa kenan?" Dan qaramin murmushi annin ta sake "Ina fatima.....ke fadima" ta qwalawa daya daga cikin 'yammatan gidan kira ,dubanta tayi sanda ta qaraso "Dauketa ki kaita dakinku,daga nan ki duban idan hafsatun ta farka" "To anni" ta amsa da girmamawa,da alamu dukka cikin yaran ta fisu nutsuwa da hankali,waiwayawa tayi fuskarta dauke da murmushi ta cewa maimunatu ta taso. Tana gaba tana biye da ita,har zuwa sanda suka isa isa qofar wani daki,ta tura ta saka kai da sallama a bakinta maimunatun na biye da ita. Wata matashiya ce zaune saman gadon,ta jingina bayanta da fuskar gadon,sanye da wata doguwar riga cotton me yankakken hannu,kanta hula ce baqa da ta dan jata baya kadan,fuskarta babu alamun annuri,da alama itace mara lafiyan da annin taxo dubawa. "Ya hafsa,anni tazo dubaki,tace na duba naga idan kin tashi" fuska ta yatsine,murya kuma can qasa tace "Banga amfanin zuwa duba nin data yi ba,tunda ba zata iya maganta min komai ba" maganganun da maimunatu ta jisu wasu iri a kunnuwanta,har sai daa dan saci kallonta,wadda take qoqarin sake shigewa cikin bargo ta kuma kwanciya abinta "Ayyah yaa hafsa,wai me yasa kike irin wadan nan maganganun ne?" "Kinfi kowa sanin dalilin,ja'afar ne,ja'afar shine dalili" dubanta fatima tayi,sannan ta matso gefanta kadan ta zauna "Me yasa ba zaki haqura da yaa ja'afar ba yaa hafsa?" Idanu ta zubawa fatiman,tana kuma qanqanceshi,tsahon wasu sakanni sannan ta amsa mata da "Ashe baki da hankali fatima,hala bakisan meye ainihin haqiqanin ma'anar so ba ko?,ta yaya zan bar ja'afar?,kinsan yadda nake sonshi kuwa?,wait.....waye ma ya gaya miki ja'afar irin mutanen da ake iya haqura da soyayyarsu ne?" Kai fatima ta rausayar "Amma dai yaa hafsa,bake kadai cikin family kike da irin wannan qudurin ba,kuna da yawa,ke surayya hannah da walida,ga madina dama sauran wadanda basu bayyana ba,kunfi kowa sanin waye yaa ja'afar tun sanda yake lafiyarshi lau ma bare yanxu da kura tayi hauka,ke kinsan wayeshi,duk cikinku bana jin akwai wadda zata iya dashi idan aka barku,wannan dakatarwar da anni tayi muku ma kamar taimakonku tayi,ta kuma tsare muku mutunci da martabarku" "Ta barmu din yafimin,yafimin wannan kisan mummuqen......" "Don Allah ina bandaki?" Maimunatu ta katse musayar maganganun da suke a tsakaninsu,sai a sannan fatima ta waiwayo "Yi haquri don Allah,na barki a tsaye,gashi can" ta fada tana mata nuni da wata qofa dake kulle,takawa tayi a hankali ta nufi bandakin,saidai zuciyarta cike fal da mamakin maganganun hafsah,har yanzu dama akwai irin wannan soyayyar?,waye ne shi wanda takewa irin wannan soyayyar?,wannan tunanin ya tuna mata da himunta da kuma buderi,ko a wanne yanayi kowannensu yake ciki?,ta tabbatar himu yana can yana dakonta,yana kuma nege da shauqin ganinta,wanda kusan ita dinma tana jin hakan a ranta a kansa. Fitsari tayi sannan ta daura alwala,ta fito daga bandakin tana gyara rolling din mayafinta "Ba zaki gane ba fatima....na jima inason yaa ja'afar,ba zaki gane me nakeji ba a kansa" kalaman hafsa da suka sake shiga kunnuwanta kenan,ta dan kauda kanta tana jin kunya da mamakin yadda budurwar keta haqilo akan namiji,ta tayar da sallah abinta. Kafin ta idar sun gama maganar,wanda fatima ce ta sakar mata ganin ba zata fahimci abinda takeson nuna mata ba,a nan suka zauna suna taba hira ita da fatima,wanda dukka kusan akan islamiyya ce,da alama itama mayyar islamiyyar ce kamar yadda maimunatu take,kusan bata taba ganin fatima a gidansu ba,saboda yawanci tana islamiyya,ko a makarantar boko bangaren islamic take,abinda ya bawa maimunatu sha'awa sosai,har taji itama islamic take sha'awar yi inda zata samu dama,saidai ba zata iya buda baki ta yiwa anni ko dr maganar ba. Daya daga cikin yaran gidan ne ya leqo bayan sallar magariba,yace maimunatun tazo inji anni taci abinci zasu wuce gida,da hanzarinta ta tashi,abinda yasa fatima zolayarta "Dama kin gaji da gidan namu,da alama so kike dama a tafi" murmushi maimunatun ta sakar mata ba tare da tace komai ba "Allah yasa ki iya zuwa mana ma da bikin anty amira ki kwana" "Allah ya kaimu" ta amsa mata tana murmushi,sai fatiman ta taka mata zuwa falon da annin ke zaune. Tun kafin ta qaraso muryar mai kauri da zurfi take ratso inda suke,matashi ne mai cikar haiba da kamala zaune sosai gaban annin suna magan,da alama akwai sabo sosai a tsakaninsu,farin bafullatani sak,wanda yake diban kama ta sosai da haj munira. "Dole cikin satin nan kije,ko fatima saita rakaki,tunda kina jin dadin maganin bai kamata a fara fashi ba,zan kirashi na gaya masa sati daya zakuyi" ya qarashe maganar yana daga kansa,dai dai sanda idanuwansa suka sauka kan fuskar maimunatu dake takowa a hankali jere da fatima. Tamkar haduwar mayen qarfe da maganadisu haka yaji wani abu mai qarfi ya fusgeshi,duk yadda yaso ya dauke idanunsa daga kanta hakan ya gagara,harta qaraso ta soma gaidashi a darare tana lafewa daga gefan anni. Da mamaki fatima ke satar kallon yaa khalid din,shi da baya yiwa mace kallo uku amma yau gashi ya kafe idanunsa akan maimunatu?,sai daya fuskanci fatiman na kallonsa sannan yajanye idanun nasa ya kuma bata rai yana komawa ga batunsu shida annin,saidai lokaci lokaci yana satar kallon ta. Iya tafiya ta tafi dashi,duk da bata qarasa kalar macen da yakeson aure ba,amma fa hada komai da komai,special care kawai zata samu ta wasu bangarori ta yiwa mata fintikau. "Nidai bansan me kakeson maidani ba khalid,wannan jewar fa ta isheni,nidai a barni,ciwo ai ba mutuwa ba,idan lokaci kuma yayi dole na tafi" anni tayi statement din qarshe tana miqewa tsaye da zummar tafiya,bayan maimunatu taqi cin abincin da aka kawo mata,sam ba zata iya ba,tana jinta ne duk a daure saboda kallon data fuskanci saurayin yana ritsata dashi,wai shin kam haka samarin family dinsu suke ko kuwa su din su biyun daga garesu ne?. Shi ya musu tattaki har zuwa bakin motar da sunan yiwa anni rakiya,fiye da rabin hankalinsa yana kan maimunatun,duk da yana yine yana basarwa har motarsu ta daga. Yayi tunanin da sun yafi shikenan,saidai kuma kasa nutsuwa zuciyarsa tayi,har sai da yakai kansa gida dr marwan,ya kuma sakeyin ido biyu da.maimunatu,tun daga sannan abun ya zame masa kamar wani jarrabi,duk bayan kwana biyu daga office yake zartowa nan din,baya barin gidan sai bayan sallar isha'i. *********Karfe shida suka dawo daga islamiyya,tana sanye da babban hijabinta da ya saukar mata har qasan qafafunta,kalar blue black,abinda yasa yayi matuqar haskata tare da yi mata kyau,tana rungume da qur'aninta a qirji,laila na gefanta tana amsa waya. Suna sallama a falon sukayi idanu biyu dashi,qirjinta yayi mugun faduwa,taja da baya kamar zata koma sai kuma ta kasa,ganin ya ganta sarai,cikin zuciyarta bata son haduwarta dashi,saboda kallon da yake tsareta dashi da kuma sanyata cikin lamuransa da yawa,har fiye dasu laila da suke jininsa. A hankali ta biyo bayan laila kamar me tsoron wani abu zai iya kamata,tana jin laila na masa sannu da zuwa sai itama tabi sahunta,ta kuma sulale da niyyar wucewa dakinta,saidai ya tsayar da ita da tambayoyi kan karatunta,abinda ya bawa laila damar wucewa ta barsu su daya a wajen. Sallamar hisham daga bakin qofa ya ja hankalinsu duka,suka hada idanu da dukka su biyun,take fara'ar dake saman fuskarsa ta bace bat,ya fara shigowa falon cikin rashin walwala yana faman shan qamshi. Kowa a cikinsu cikakken matashi ne mai jin kansa,wanda ya hada komai da komai,musabaha sukayi da juna kowa yana dauke wuta,ba kamar yadda suka saba ba,har zuwa sannan kan maimunatu yana qasa,ta yiwa hisham sannu da zuwa,maimakon ya amsa,sai ya koma da baya ya zauna cikin daya daga cikin kujerun falon yana cewa "Je kitchen ki kawomin ruwa" a hankali ta tashi tana jin wani nauyi na raguwa daga cikin zuciyarta,zamanta a wajen tana jinta ne kamar cikin wani matsatstsen keji ne da babu sakewa. Shuru ne ya biyo baya a falon,hisham na danne danne a wayarsa,khalid kuma yana kallon news,kowanne da tunanin da yake a ransa game da dan uwansa,ba tun yau ba duka sun tsargu da juna,sun kuma fahimci mawuyaci ne idan basiu tarayya akan wani abu guda ba. Ruwan ta kawo masa hade da cup,ya dauki gorar ruwan yana cewa "Ba daga islamiyya kike ba?" Kai ta gyada masa "Bita ce ta kamaceki ba ki zauna kina surutun banza ba...wuce daki ki ajjiye qur'anin hannunki" cikin jin kai da isa khalid ya gyara zamansa sosai yana kuma dubansa kai tsaye "Dakata mana hisham?,wanne irin nonsense ne zaka same mu tare sannan kace ta wuce ciki?.... please kada ka shiga hurumin da ba naka ba" wani kallo hisham ya watsawa khalid sannan ya saki murmushi "Nonsense?......hmmmm,dani da kai za'a samu wanda ya dace a gayawa hakan,wuce maimunatu tun raina bai fara baci ba" "Ba zata wuce ba!" Khalid ya fada a tsawace,dai dai sanda anni ke qarasowa falon,ta bisu da kallo cikin mamakin yanayin data taras dasu. _To fa masu karatu,khalid dinne ko hisham?,ko kuma ja'afar?,waye zaiyi wining?,muje zuwa yanzu aka fara wasan_ 21 "Kai.....kai,meye hakan?" Anni ta dakatar dasu cikin tsawa,ganin zasu fara sa'insa a tsakaninsu "Ya zaizo ya samemu zaune,sannan kawai yace sai ta tashi ta shiga daki anni?,wannan wanne irin raini ne?" Khalid ya fada cikin jin ciwon abinda hisham yayi masa,yana jin ya disgashi abinda ba'a taba yi masa ba "Anni,dawowarta kenan daga makaranta,da alama ko ke bakisan ta dawo ba,don nace ta shiga ta ajjiye qur'aninta sai ya zama laifi?" Shuru ne ya biyo baya,anni tana nazartar kowannensu cikin sakannin da basu wuce biyar ba,sai taji hankalinta ya dan tashi,zata iya cewa bata taba ganin irin wannan sabanin ba a tsakanin jikokinta,wannan shine karon farko da hakan fa faru,duk da tasan dama tsakanin khalid da hisham ba jituwa bace can can,amma kuma basa cecekuce,tabbas ya kamata ta yuwa tufkar hanci da wurwuri "Wuce ciki maimunatu" anni ta bawa maimunatu dake daskare a wajen umarni,da hanzarinta kuwa qafafunta na rawa tayi ciki,kamar ta tashi sama haka takeji,har ta samu ta isa ga dakinta,ta tura qofar ta shige,ta zame a hankali a qasa ta zauna qafafunta suna rawa saboda tsabar tsoro,me ya kaisu fada a kanta?,shin wai basu duba kamanninsu da darajarsu ba da zasu tsaya suna fada a kanta?,kamar ita maimunatu?,wadda bata da komai?,bata kuma mallaki komai ba?,me yasa?,abinda ta dinga tambayar kanta kenan cikin mamaki da kuma tsoron abinda ya farun yanzu. "Ku zauna" anni ta fada musu itama tana lalubar wajen zaman "Ka zauna mana nace!" Anni ta fadawa khalid tsaye cikin matuqar bacin rai a tsawace. Sun kusa minti biyu shuru kowanne anni tana karantar fuskarsa,kafin daga bisani ta kirayi sunan kowa a cikinsu "Me idanuna suke gani?" Ta jefa musu tambayar da ba wanda ya shirya amsa mata,sai cin d'aci da kowannensu yakeyi "Tun ina raye hakan zata fara faruwa ina ga ace qasa ta lullube idanuna?......to in sha Allahu wannan abun ba dai cikin ahalina da zuria'ta ba,haihata haihata,bazan lamunta ba kuji da kyau,na meye zaku dinga sa'insa akan maimunatu?,to dukkaninku ku dauketa a matsayin qanwarku,banason kowa ya sanya wani abu a ransa bayan wannan.......kuma inaso a yanzu yanzu ku baiwa junanku haquri" "In sha Allah" kowa ya fada a cikinsu saidai murya ciki ciki,hisham ne ya fara bawa khalid din haquri,tunda ya girme masa da watanni kusan shida,shima khalid din ya maida masa,sannan khalid din ya miqe hannayensa zube a aljihunsa yana shaidawa anni zai tafi "Aiba yanzu k saba tafiya ba,ko don na muku fada?" Kai ya girgiza yana duban agogonsa "A'ah,dama da wuri naso na koma yau din,ina da abinda zanyi" tabe baki anni tayi "Oho maka.....a sauka lafiya" qaramin murmushi ya sake ya juya yana ficewa daga falon,qasan ransa yana juya maganar anni da tace su dauketa matsayin qanwa kawai,shikam.dai Allah ya sani ya gani yana so,zai kuma yi duk iyakar bakin qoqarinsa,zai kuma fafata da kowa don ganin ya samu maimunatu,bawai ya haqura bane. Sun fita sun bar anni ne da dogon nazari da tunani,tana tsoron kada abubuwa suzo su kwabe ba kamar yadda take shiryawa ba,tana hangen al'amura masu nauyi a idanun kowannensu tsakanin hisham din da khalid,wannan tunanin ya sanyata daga waya ta laluba number dr marwan,ta shaida masa idan ya shigo gida da wuri a yau tana son ganinsa,idan kuma bai shigo akan kari ba gobe da sassafe ya nemeta kafin ya fita ya amsa mata da to,saita maida akalar kiran nata zuwa number jabir. "Me kuke har yanzu a qasar nan ne jabiru?" Ta tambayeshi kai tsaye ba tare data tsaya bi takan tambayarsa,sumarsa yaci gaba da tsanewa da towel "For now dai ni na gama duk schedule din da nake nasu a turkey,matsalar tana ga mutuminki,sam bashi da sha'awa ko nufin tahowa" gyara zamanta anni tayi sosai "Nan da yaushe kake ganin harshi xai iya dawowa gida?" "Karshen watan nan nan da 2weeks kenan komai nasa zai kammala" "To ka shaida mana,lalai dakai da shi din ina da buqatar dawowarku qasarku zuwa farkin sabon wata......kai kaga ma,hadani dashi a waya" "Okay, hold on karki kashe" yayi maganar yana maqale da wayar,gami da ajjiye wandon hannunsa da yake da niyyar sanyawa ya fita a dakin. Kofar dakinsa da sassanyar qamshin turarukansa suka kamashi ya tura,luf luf dakin yake,saidai bashi a nan,ya kalli a gogo,lokacin da yake shiga gym ne,tabbas yana can,don haka ya juya da 'yar sassarfa yayi can. Sanye yake da farin wando qal me ratsin green daga gefe da gefansa,iyakar wandon wasan gwiwarsa,hakan ya sanya sambala sambalan qafafunsa dake cike da gargasa suka bayyana,sai rigar kayan armless shirt,yana tsaye daga bakin window,hannunsa riqe da qaramin towel yana goge zufar jikinsa,idanunsa kuma na ga waje. Duk da yaji sautin bude qofar amma bai juyo ba,haka ya sanya jabir din takowa ya iskeshi a wajen da yake tsayen "Anni na magana" ya fadi masa a taqaice,kamar bazai motsa ba,sai kuma ya cilla towel din gefe yana juyowa duk da har yanzu idanuwansa naga wajen "Duk randa mutanen can suka shiga gonata zasu gane shayi ruwa ne" ya fada fuskarsa na nuna alamu na bacin rai,wajen jabir yakai idanunsa,wasu 'yan asalin turkey dinne,baisan me yasa mutanen suke da jin kansu da alfaharin su turkawa bane,ba yau ba sun saba wulaqanta baqar fata kamar yadda yanzun sukewa wasu,duk da laifinsu ne,yawanci suke zubar da kansu "Kar ka fara,ka rufa mana asiri,a qasarsu kake fa?" "And so what" ya fada cikin nuna halin ko inkula,kana ya miqa hannu ya zame wayar daga kunnen jabir ya maidata kunnensa,yana qara taku zuwa gaba gami da gaida anni. Waje ya samu ya zauna bayan ya gama jin dukka bayananta,yatsunsa ya nutsa cikin lallausan gashin kansa,baisan me zai gayawa anni ta fahimta ba,kamar yadda ya rasa gane taqamaimen dalilinta na birkice masa,tare da bashi umarnin tahowa gida next month,bayan kuma shi bai shirya hakan ba,banda amna ma,baya tunanin xai koma nan kusa "Zan duba,zanyi qoqarin zuwa" wannan itace amsar daya bata. Sanda anni ta ajjiye wayar saita qwalawa tabawa kira "Ina maimunatu ne?" "Tana dakin karatu,kinsan lokacin karatunta ne yanzu,kin santa kuma da himma" murmushi anni tayi,ita kanta tasan yarinyar daban take cikin dukka yara data sani,ba sawa ba fitarwa ba,babu hayaniya hakanan babu hargowa,uwa uba bata dauki rayuwarta da zafi ba,har cikin ranta kullum kwanan duniya tana jin nutsuwa da kuma gamsuwar hadin da take shirin yi da yarinyar "Kiramin ita tabawa,wannan maganar ce ta taso,inajin lokaci yayi da zata san da zaman maganar,saboda ta sama zuciyarta tun kafin qarasowarsa,bawai sai daga bisani taji maganar sama taka ba,uwa uba ina hango wutar rikici dakeson ruruwa,gwara na yima tufkar hanci" kai tabawa ta gyada "Gaskiya ne wannan haj anni,ubangiji ya tabbatar mana da alkhairi,yasa komai yazo mana cikin nasara da sa'a,ya kuma sanya qarshen abun ne yazo" cikin jin dadin addu'o'in tabawa anni ta amsa "Ameen,ameen ya hayyu ya qayyumu tabawa" daga haka tabawan ta juya ta fice. Sosai yau din takejin dadin karatun,hakanan Allah ya sallada mata qaunar hadith,dalilin da yasa zaiyi wuya ayi musu qarin hadith bata haddace su ba,kamar yau din,saura guda biyu ta gama haddar qarin da akayi musu jiya juma'a tabawa ta turo qofar tare da sallama ta shigo. Qaramin murmushi ya wanzu saman fuska da siraran labban maimunatun,ta rufe hadith din tana duban tabawa "Yau ban shigo kitchen ba ko?,karatu ne ya tsaidani amma na kusa kammalawa" murmushi itama tabawan ta maida mata,maimunatu nada saurin shiga rai saboda sauqi da dadin mu'amalarta "A'ah muna,bansan me yasa kike takura kanki ba wajen zuwa kitchen kullum" "Bana takura baaba tabawa,inajin dadin zuwan sosai,na qaru da kalolin girke girken da bansan ana yinsu ba,ina kan qaruwa ma,hakan yana min dadi" "Gaskiya ne" tabawa ta amsata tana murmushi,don ita shaida ce,tuquru maimunatun ke maida hankali tana koyar duk wani girki da tazo ta samu zasuyi,daga inda taga anyi sau daya a gabanta to tabbas ta haddaceshi kenan,idan ta maimaita irinsan kuwa zakayi mamakin yadda ya bada ma'ana,kamar wadda ta jima tanayi. "Yanzun ma anni ce take kiranki" "Tom,gani nan zuwa" tace da baba tabawan tana qoqarin ajjiye Hadith dinta a take,ta kuma miqe tabi bayan baba tabawa,suna dan zancan islamiyyarsu,har zuwa sanda suka isa qofar dakin annin "Tana ciki,zan koma kitchen mu qarasa hada abinci,don yau anan Alhj Dr(haka tun da baba tabawa take kiran dr marwan) zaici abincin dare" "Idan na fito zan sameki a can saimu qarasa in sha Allah" ta fada saboda gwada kyautatawarta akansu itama komai qanqantarsa "To ba laifi" ta amsa mata tana komawa zuwa hanyar kitchen,ita kuma ta tura dakin anni ta shiga,bakinta dauke da sallama. ,kamar ko yaushe,cikin nuna matuqar kulawa ta amsa mata tana gyara zamanta "Kinga miqon wancar jakar kafin ki zauna" anni tace da ita tana mata nuni da wata jaka dake gefan gadon,miqa matan tayi sannan ta zauna tana fuskantar annin. Zuge jakar anni tayi,ta fiddo wani abu,sannan ta daga kai tana duban maimunatu tana sakin qaramin murmushi "Yau hira zamuyi dake" murmushin nan nata dake nuni da nutsuwarta gami da kamun kai ta sakewa anni "So nake naji samari nawa kika taba yi maimunatu,sannan a cikinsu wa kikafi so?,inaso kuma naji har yanzu kina sonsa?" Sosai maganar anni tayi mata nauyi fiye da zaton ita annin,taji kamar qasa fa tsage ta shige ciki,ta yaya zata fara irin wannan hirar da anni?,bayan ko dasu laila ba zata iya wannan maganar ba?. "Uhmmm,ina jinki,ki bude baki ki gayan" sake daureta kunyar annin tayi,sai kawai ta hau kada kai a hankali,dan bata fuska tayi "Kina nufin ba kowa?" Da sauri ta daga kai alamun eh,sai annin ta motsa tana ajewa maimunatu hoto a gabanta "To ga jikana,zaki iya aurensa?" Kasa daga kanta tayi bare ta kalli hoton,tanajin kamar ta kulle idonta ta bude taga bata a gaban anni,kayan kunyar yayi yawa "Da gaske nake miki maimunatu,zaki auri ja'afar?" Wannan karon sautin muryar annin ya fito da wani irin amo dake nuna babu wasa cikin maganganunta,abinda ya sanya maimunatu cira kai,a maimakon ta kalli hoton sai ta kalli anni,suna hada ido ta jinjina mata kai "Inaso ki taimaki rayuwar ja'afar,ki aureshi,inajin qamshin alkhairi a tattare dake,bansan me yasa zuciyata take gayamin ke zaki fitar dashi ba" a nutse ta zayyanawa maimunatu waye ja'afar,ta koma dora da "Kiyimin wannan alfarmar maimunatu,bansan me Allah yake nufi ba da yasa nakejin ke zaki iya....." "Kiyi duk abinda ya dace dani anni,don Allah basai kince neman alfarma kike daga gareni ba" maimunatu ta fada,dukka jiki da muryarta suna rawa. Kai anni ta girgiza tana kallonta a nutse "Aiba baiwa bace ce,'ya ce ke kamar kowa,don haka ya zama dole a nema daga wajenki cikin baki cikakken 'yancin yin zabin eh ko a'ah,kije kiyi tunani maimunatu,na baki dama,idan har kikaji baki gamsu ba,ko ba zaki iya wannan alfarmar ba,kada kiji komai,ki gayamin kanki tsaye,ni kuma nayi miki alqawari har tsakanina da ubangiji na,zamu ci gaba da riqonki ba tare da komai ya sauya ba.....tashi kije" kasa cewa komai tayi,ta miqe cikin wani irin yanayi data gaza fassarashi,kamar anbi kowacce gaba ta jikinta an zare sinadarin dake bata kuzari,komai na jikinta yayi sanyi qalau,maimakon ta wuce study room ko kitchen kamar yadda ta tsara yi,saita wuce dakinta kawai,ta tura qofa ta kuma haye gado. Inda batasan wace anni ba da sai tace wasa take mata,ja'afar dai da takejin sunansa a bakunan al'umar gidan nan?,koda batasan fuskarsa ba amma mutum ne da kowa ke ganin girma da kimarsa,kamar ita?maimunatu?,bafullatanar ruga 'yar qauye?,ta yaya zatayi kan kan kan da mutumin da take da tabbacin a yanzu ma baya qasar nijeria?,ta yaya zata iya wanke wannan babban tabon daya nannade rayuwarsa?,kai tana ganin a rayuwar gida irin ta dr marwan,koda drivern gidansu darajane dashi,koda drivern gidan ya fita daban da sauran drebobi,koda shi aka ce ya aureta tana ganin kamar ya zarce mata,bare ace dan gida,dan gidan ma irin ja'afar dan gata ta kowacce fuska,anya kuwa zata iya?,idan ba zata iya din ba kuma zata iya kallon anni tace mata A'AH?,.....kalmar tayi nauyi da kuma muni da yawa,anni mutum ce guda har da rabi,wadda 'yantata ta kuma maidata cikakkiyar mutum. Ire iren wadan nan tunanukan su sukaci gaba da kassara maimunatu,suka kuma cika mata kwanya taf,ta rasa yadda zata sarrafasu su dace da hange da kuma fikirarta. Ajiyar zuciya anni ta sauke bayan fitar maimunatu,fatanta daya komai ya daidaita,komai yazo da sauqi,don muddin maimunatu ta amince,to fa babu daga qafar da zata yiwa ja'afar har sai ta tabbatar komai ya kammala,wannan shine buri da kuma fatarta. Wannan magana da sukayi da anni sai ta zamewa maimunatu kamar wani dabaibayi,dukka kuzari karsashi da walwalarta suka yi qaura sosai,duk da dama ita din miskila ce,wadda bata damu da hira ko hayaniya ba,tafi ganewa karatu,to shima karatun a dan tsukin nema yake ya gagareta,idan ta buda littafin sai ta tafi duniyar tunani,sai ta kasa qulla komai har ta gama zamanta ta tashi. A wani yammaci ne,tana dakin karatun dauke da qur'aninta tana tilawa,saidai can tsakiyar karatun nata tunanin da ya zame mata jiki ya kutso mata kai,sai taci gaba da riqon qur'anin kawai ba tare data iya ci gaba da karatun ba. A wannan lokacin baba tabawa ta shigo dakin,hannunta dauke da cup data cikashi da kunun gyada fari sol sai maiqo da qamshi gyada da yakeyi,daya daga cikin cimar da maimunatun keso kenan,tayi firgigit tana amsa sallamar baaba tabawa.gami da gyara riqon alqur'aninta,sai baba tabawan ta sakar mata murmushi tana miqa mata cup din,sannan ta zauna saman kujerar dake fuskantar maimunatu "Na lura kwana biyu kin zama wata aba,don wannan kunun qilan saidao a zubda ba tare da kinzo kin dauka ba" dan murmushi tayi tana juya spoon din dake cikin kunun,cikin ranta tana ayyana yadda mutanen birni ke kashewa ciki kudi,suci wannan suci wancan "Shawara nazo baki muna,don banaso kiyi asara har irin wannan a rayuwarki" daga kai maimunatu tayi ta dubeta cikin rashin fahimta,idanun baba tabawa cikin nata ta gyada kai tana tabbatar mata da duk abinda zata ji "Maimunatu,tun zuwanki gidan nan naji kin kwantain,ina kuma qaunarki,maimunatu,naji na kuma san abinda ya sanyaki kika canza gaba daya,ba zancan ja'afar ba?" Tayi zancan da sigar tambaya,saita sad dakai,wato kowa ya sani kenan?,ya kuma fahimta?. "Duk yadda zakiyi kada ki bari ja'afar ya subuce miki,duk yadda zakiyi kada ki soma wauta ko gangancin cewa baki sonshi,ja'afar yana cikin dai daikun mazan dake da wuyar samu duk da wahalar sha'aninsu,samunsa kuma sai mace mai matuqar sa'a kuma 'yar baiwa,bawai don yana da kyau da kudi ba,a'ah.....yana da wata irin nagarta da kuma kebantattun kyawawan halayen da ba kowa bane ya sansu,ba shakka kowacce mace da tasan abinda takeyi zata yiwa wadda take so ko qauna fatan kasancewa da shi a mazaunin miji.....maimunatu,a shawarce.....ki aminta da maganar hajiya anni,ina mai baki tabbacin ja'afar gaba yake da nagartaccen miji idan ma akwai" shuru maimunatu tayi tana jujjuya maganganun tabawa cikin zuciyarta,tana ganin matsayinta baikai inda anni keson kaita ba sam "Akwai abinda kike tsoro ne?" Tabawa ta tambayeta kai tsaye,a wannan karon batayi nauyin baki ba "Bansan waye ubana ba,bafullatanar ruga nake,har na isa na hada kafada da zuri'ar anni?" Murmushi tabawa tayi "Zallar karamci irin na hajiya anni babu abinda ba zaki gani ba,sa'annan ke din halastacciyar 'ya ce,babu abinda ya nuna baki da.uba ne,ke koda haka ne,ina me tabbatar miki tunda hajiya anni tayu niyyar aiwatar da hakan,babu abinda zai dakatar da ita,ba kowanne mutum ke ganin baiwar da Allah yayi masa ba,kamar ke din,kina da wasu kebantatattun halaye da siffofi dani kaina nake saka ran akwai alkhairi me yawa a tare dake" shuru maimunatu ta sakeyi,tambayar qarshe kuma wadda take ta cin ranta "Shi ya santa ne?,yana kuma sonta" maganar data fito sarari,sai murmushi kawai taga tabawa tayi "Muna.....ke din ta musamman ce,hakazalika kina da tarin baiwar da namiji bai isa ya kalleki yace baiso ba,saidai idan wani abun daban kuma ba wannan ba" tabawa tayi matuqar sanyata cikin nazari,tana jin kokwanto tana kuma jin qwarin gwiwa,wanne zata rinjayar?. "Anni ta damu qwarai,kin amince a shaida mata ko zata samu nutsuwa" 22 Bata da wani sauran zabi,sai ta samu kanta da gyadawa tabawa kai. Unexpected wata guda ta ratsa kunnuwa zuwa kwanyar maimunatu,ta rintse idanunta tana jin wani abu na mata yawo,wanda yake cakude da zallar fargaba da kuma kokwanto. "Alhmdlh alhmdlh alhmdlh" shine abinda anni ta dinga maimatawa fuskarta kamar wata dam daren sha hudu,bakinta yagaza rufuwa,hakanan Allah ya sanya mata qaunar maimunatu da kuma tausayinta a ranta. A haka maimunatu taci gaba da rayuwa,cikin kunya nauyi da kuma fargabar al'amarin dake tunkararta,saidai kuma ta sake maida hankalinta ga karatunta,wanda a yanzu ta sake maida hankalinta dari bisa dari a kai,ranta da zuciyarta na gaya mata idan tayi aure shikenan,ta rabu da karatunta,tunda abinda ta taso kenan ta gani,matan aure kowacce tana gidanta a zaune,zuwa makaranta na 'yammata ne. Saidai a kullum tana tambayar kanta ta yaya lamarin yazo kamar mafarki?,yaya kuma zaici gaba da kasancewa?. **********Duk yadda yaso ya taushi zuciyarsa ya taho nigeria abun ya faskara,haka kawai yakejin baison zuwa din ko kadan,akwao memories masu tarin yawa da ya binne wanda baison tunosu,ko sau daya zuciyarsa bata sassauta daga tunani da kuma kewar shaheeda ba,wanda cikin jikinsa yakejin da wannan ciwon zai qarasa rayuwarsa ya kuma mutu shima,mutuwar da inda zabi take bayarwa shi zaice ta dauka ba shaheeda ba,koda kuwa ta dauketa zai zabi ya bita shima. Duk wata hanya da jabiru yake jin zaibi ya shawo kan ja'afar abun ya faskara,hakanan itama annin tabi duk hanyar da ya kamata ta lallashi amma abinda take son bai samu ba,ranta ya fara baci,don haka a wani dare ta nema ganin dr marwan *_08:pm Dr marwan khalid akko residence_* Dr marwan ne zaune gaban anni,sanye da wata jallabiyya ta matsa ruwan hanta saqar qasar oman mai budadden hannu,an qawata gabanta da adon zare ruwan madara mai turuwa kadan,fuskarsa na dauke da wani annuri na zallar nutsuwa ilimi gami da samun cikakken hutu da kwanciyar hankali,yana da cikar haiba kwarjini da kuma kamala sosai a fuskar tasa da wani bangare nata ya fara samar da furfura. Ya miqa hankalinsa matuqa zuwa ga mahaifiyarsa "Kaji duka irin abubuwan dake faruwa,banyi tsammanin abun na ja'afar yakai har can ba,ina ganin ya kusa fin qarfinmu dai" da hanzari dr marwan ya girgixa kai "Kiyi haquri ki daina fadin haka,bai isa ba wallahi,koda bana raye koda aishatu bata raye,bare gaba dayanmu da ranmu.....bai isa ba don ubansa,banda wancan matsalar ma harda iya shege na fuskanta ciki lamarin nasa,ai mu muka haifeshi bashi ne ya haifemu ba,ya zubda komai da kowa nasa saboda mutuwar matarsa da diyarsa kawai?,zan nuna masa mu muka haifeshi kam tabbas,karki sake bi ta kansa anni don Allah,abinda za'ayi shine.....ki shirya ki kuma saka lokaci zuwa adamawa gurin magabatan maimunatu cikin satin nan,ni kuma zanyi magana da honorable commissioner ya tsaida randa za'a kai kudin auren tasa diyar" hakan ya yiwa anni dadi qwarai da gaske,ta dinga sanyawa dr marwan albarka,yana da tsananin biyayya,abinda yasa a kullum yake sake shiga ranta. Shiri ta fara yi gadan gadan na tafiyarsu adamawa,sanda ta shaidawa maimunatu wani dadi taji ya tsarga mata,amma kuma wani sashe na zuciyarta sai taji tana tsoro da fargabar wacce tarba zata samu daga wajen innar laulo dama gaaje?,dama kuma bata da wata fargaba akan jauro,duk inda mutumin kirki yakai yakai nan. Saura kwanaki biyu su wuce da wani yammaci anni ta kirata,tace taje aishatu tace a turota ta kama mata aiki,haqiqa tana matuqar jin kunya da nauyin matar,tunda tasan itace mahaifiyar ja'afar,duk da cewa wata magana data shafeshi bata taba hadasu ba. Atamfa ce a jikinta doguwar riga,sai ta zura hijab din da bata jima da cireshi daga jikinta ba saboda sallar data idar,ta zura wasu slippers dinta ta nufi sashen amma,tana tafiya a hankali tana shaqar iskar yammacin,duk bata jin dadin gidan saboda dauke amna da dangin mamanta sukayi,sun roqi alfarmar a basu ita akwai bikin da ya taso zasuyi can dangin mahaifiyar shahidan,dr yace a basu. Gab da zata shiga sassan ta gamu da ammi,kishiyar amma tana fitowa ita da khadim,bisa dukkan alamu unguwa zata je Cikin girmamawa ta gaidata,tadan tsokani khadim kadan sannan tayi musu a dawo lafiya ta wuce ciki. Masu aikinta biyu ta samu a falon suna kai kawo,kowa da abinda yakeyi,ta gaidasu kamad yadda ta saba,daya daga cikinsu tace "Tana kitchen" saita miqe zuwa hanyar da zata sadata da kitchen din. Kamar kowanne lokaci,a duk sanda maimunatun tayi magana ko tayi sallama sai taji kamar tasan muryar,yau ma da sauri ta juyo,sai taga maimunatun ce,ta sakar mata murmushi tana fadin "Shigo ciki" kanta a qasa take takowa,tana mamakin yadda amma ga daukaki gayu,da wahala ka sameta ba cikin kwalliya ba,wannan ya zame mata jiki,kamar yanzun da take sanye da atamfa dark blue da yarfin baqi da kuma fari a jiki,jikinta yana fidda ni'imataccen qamshi,gashinta yananan da tsahonsa da kyansa,duk da girma daya fara nunawa. "Matso ki tayani hada wannan dambun,babanku keso,sai daya taho hanya kuma yayi magana" amma ta fada tana murmushi,saita amsa da to,ta janye hannayen hijabin nata zuwa baya sosai sannan ta ja zogalen dake cike da kwando ta fara gyarawa. Da fari shuru kitchen din yayi,sai qarar kayan amfani,amman ce ta katse shirun da cewa "Inafata baki takura ba ko da maganar auren ja'afar?" Amma ta fada a tausashe,tana son ta bincika ta dabara ta tabbatar babu wata matsala,kunya ce ta bijirowa maimunatu,ta duqar da kanta hannunta ya fara dan rawa saboda hakan,amma ta fuskanci haka,ranta ya sake fari,don dama halaye da dabi'un maimunatu ba baqinta bane,tanason yin maganar daga ita sai maimunatun tun a wancan lokacin da dr ya shaida mata komai,to sai yau ta samu wannan damar,ta umarci masu aikinta duka su fice,don tana kunyar su jita tana maganar da maimunatun,kamar yadda tayi imanin itama yarinyar ba zata sake ba "Sai kinyi haquri da ja'afar,zuciyarsa nada tsananin so,tun yana qaraminsa,idan yaso abu yana masa wahala sanda zai barshi,saboda ba qaramin so yake masa ba,hakanan idan yaqi jinin abu,akwai mata da yawa da muka saka rai a kansu kan zasu kawo canji ga rayuwarsa,saidai babu wanda mukaci nasara,ko a yanzunma zuciyata da jikina duka sunfi bani hope a kanki maimunatu,don Allah kiyi haqurin zama da ja'afar,don Allah,kada rayuwarsa ta tabarbare a rasa kuma sauran me zama dashi" sosai wani tausayin amma ya kamata,ashe itama abun yana damunta har haka,amma kunya da kawaici suka sanya bata nunawa?,a sanyaye a kuma kunyace ta gyadawa amman kai. Tare suka dinga aikin,amma.tana qoqarin sanyata sakewa da ita,cikin hikima ta dinga nuna mata itama kamar mahaifiya take a wajenta,ta dauketa kamar hakan. Sanda suka gama aikin gift amma ta bawa maimunatu na set din kayan wanka,cream,shower gel, perfume,body spray,hair mist da sponge a ciki,kallo daya tayi musu ta tabbatar masu shegen tsada ne,don qamshin da suke fitarwa ma na daban ne,don haka ta ajjiyesu,batason fara amfani dasu bare zuciyarta ta zarme. Sanda ta isa qofar sassan anni taji hayaniyar mutane,taji muryoyin wasu daga cikin yaranta maza,tabbas sune,don dazu da safe taji suna magana da umar kan zuwansu gidan commissioner,don haka taja da baya ta koma can bayan gidan tayi zamanta,don yau gidan duka basanan,sun tafi gidan babbar 'yar amma,wadda taci sunan anni,saboda yau din suke dawowa daga tafiyar da sukayi ita da mijin nata har na tsahon shekara uku,sai yau suka dawo,yau dinma babu yadda basuyi ta bisu ba tace aah,zataje watarana,haka suka tafi suka barta. **********K'arfe uku da wasu mintuna akai suka sauka a adamawa,motarsu kuma ta kutsa kai cikin rugar ummaru a hankali tana keta burtali da kuma hanyoyin da mazauna rugar ke amfani dasu. Watannin da suke shude sun zamarwa maimunatu wasu sababbin shafukan rayuwa ne a gareta,cuke da tarin sauyi wanda yayi wancakali da qalubale wahala bauta da kuma azabtarwa data fuskanta a baya na tsahon wasu shekaru,ware idanu maimunatu tayi,tana kallon duk wani bigire daya zame wajen kiwo ko wucewa a wajenta,kewa sosai ta cikata,ta dinga tuno mummuna rayuwar mai cike da jahilci da kuma wahala,a yanzun da take ganin muhallan da hakan ya faru da ita,sai take ganin kamar mafarki. Duk inda motarsu ta keta sai ta kwashi idanu,saboda abu ne da ba kasafai suke ganinsa cikin rugar tasu ba,basu tsaya ko ina ba sai qofar gidan yuuma ramatu. Fa'iza da khadim wannan karon sune 'yan rakiyar,kusan sunfi kowa son tafiya muhallin daba nasu ba ba kuma su sanshi ba,sune a gaba janye da akwatin kayansu,maimunatu na biye dasu anni a bayansu. Cikin wani hanzari yuuma ramatu ta fito daga dakinta bayan bankade labule data yi,wani irin farinciki mara misaltuwa ne ya saukar mata,a wannan karon maimunatu ta fara rungumewa cikin matuqar farinciki tana cewa "Miyatti Allah,miyatti annabi,maimunatu?,kece haka?" Murmushi maimunatun ta sake cike da kunya,yuuma kuwa baki ta saka cike da mamaki tana kallonta "Kinga ta canza miki kenan ramatu" anni ta fada tana 'yar dariya "Ba kadan ba kuwa yafendo" yuuma ta amsawa anni tana maida dubanta kanta,sai a sannan ta marabcesu gami da yi musu jangora zuwa dakinta,bakinta har kunne,ta rasa inda zata sakasu. Bata zauna ba tahau dora musu abinci na musamman kamar yadda ta saba,duk yadda yuuma taso maimunatu tayi zamanta amma ta qiya,tare suka dinga shirya komai,suna aikin suna hira,yuuma tana tambayarta labarin rayuwa a can,bata boyewa yuuma komai ba,ta yabi anni ainun kan irin tarin karamcinta da yadda ta sauya mata rayuwa "Indai yafendo ce,bakiga komai ba,a jininta yake,dabi'arta ce" jinjina kai maimunatu tayi,tana sake gasgata zancan yuuma. Tunda suka fara aikin take satar kallon qofar dakin daada dake a rufe,bata ji motsinta ba bata kuma ganta ba daga ita har yaran,cikin ranta take tunanin inda suke,daga bisani taji yuuma na gayawa anni suna ta tafi maqotan rugarsu,qanwarta Ayaana ce ta haihu,sun tafi duka ita da yaran,cikin ranta take tambayar shi kuma ibrahim fa?,ba zata iya tambayar yuuma ba,abun ma baiyi tsari ba,tunda tasan ainihin dalilin ma daya kawosu garin,wanda tabbatuwarsa zai sake nisantan tsakaninta da ibrahim din har abada. Gefin magriba suka gama komai,maimunatu na saman abun sallah,ta idar kenan saiga sallamar daadan ita da iyalinta,cikin murna da zumudi ta zarto dakin yuuma,don ta sani tabbas zuwan anni alheri ne,bata zuwa haka hannu babu komai. A girmame ta gaidata,fa'iza da khadim da sukayi zaman cin tuwo suma suka gaidata,sai maimunatu ta waiwaya kadan itama ta soma gaidata. Dan jim tayi na sakanni saboda ji da tayi kamar tasan muryar,amma canzawa maimunatu da kuma rashin wadatar haske a dakin ya sanya bata gane wacece ba,har sai da zubaida ta ankarar da ita "Daada fa kamar maimunatu na gani a tare dasu" harara ta balla mata "Maimunatun da aka kai aikatau ce zata koma haka,ke arcan" "Wallahi tallahi daada" shuruu tayi tana nazari,ita kanta kuma taji muryar kamar tatan "Toooo,anzo wajen,Allah yasa ba wata tsiyar ta shuka suka dawo da ita ba,in kuwa hakane nita cuta,saboda kayan dana buqata na aurensu da himu ko rabinsa ba'a gama siya ba.....maza tashi safiya kije ki shaidawa fulera zuwansu,don na tabbatar batasan tazo ba,tunda dazu da zamu gitta ta shiyyarsu mun hangi juna mun gaisa amma bata yimin maganar ba" rai safiya ta bata tana duban daada "Haba daada,daga zuwan ta,kawai saiki fassara zuwan da mugun tunani,don Allah ki daina haka,irin wannan abubuwan su suka saka ya himu fa kullum bashi da cikakkiyar lafiya" da murfin tukunya ta jefeta,ta kuma balbaleta da masifa,a dole safiya ta miqe tana qunaqunai ta wuce gidan inna furera. Sanda labarin ya isketa saita kasa zaune ta kuma kasa tsaye,fargaba ta cikata,ita ba abun ta tafi gidan yanzu taji meye ba'asi ba,haka dai ta daure,ta cewa safiya tace musu tana musu sannu da zuwa. Bayan sun gama cin abincin daren anni ta sanya khadim da fa'iza suje su raka maimunatu ta gaisa da inna furera,a sannan ta samu sararin yin magana da yuuma,ta shaida mata abinda ya kawosu. "Alhamdulillahi,alhamdulillahi,lallai wani hanin ga Allah baiwa ne,Allah ya tabbatar da duka alkhairi,Allah ya baki ladan wannan jihadi da zakiyi yafendo,ubangiji yasa alkhairi ya kuma hade mana kansu fiye da yadda muke zato da tsammani" "Ameen ramatu,ameen" "Kinci sa'a kuwa kawunsu yana nan,nan da bayan isha'i zai shigo gidan" "To alhmdlh" anni ta fada tana jin zuciyarta wasai. Zau biyu maimunatu tana yin sallama inna furera bata amsa ba,sai idanu data bita dashi bayan fa dgaa fitila ta hasketa da kyau,sai datazo gab da ita sannan ta zabga salati,zuciyarta cike fal da qunci da rudanin ganin maimunatun tamkar an sauya mata halitta,maimunatun kamar wadda aka yiwa wankan inji,duk da cewa tana nan itama lalitarta suna cika duk qarshen wata da kudin aikin maimunatun "Ke yarinya,ina fatan ba wata muguwar aika aikar kika tamfatsa ba aka maidoki ba,don wallahi ban gama hada kudin auren gaje ba,kika sake kuwa haka ta faru dake na rantse miki da Allah na lahira sai ya fiki jin dadi" takaici da mamaki suka cakude suka hadewa maimunatu,wai ita din yayar mahaifiyarta ce,sannan ita din a yau baquwa take ga inna furera,amma irin tarbar da zata samu kenan daga wajenta "Babu abinda ya faru inna,kawai zuwa mukayi gaisheku" ta amsa mata tana nemawa kanta wajen zama bayan ta nunawa su khadim inda zasu tsuguna suma. A gaba ta sanya maimunatu da tambaye tambaye,tambaya maras ma'ana tabin qwaqwafi,har maimunatun ta fara jin kunyar idanunsu fa'iza,saboda tambayar tayi yawa. Zuwa jimawa kadan saiga laulo ya ashigo shi da gaje,yaja ya tsaya turus a gabanta ya zuba mata idanu,sai kuma ya washe baki yana kiran sunanta,abinda yasa gaban gaje faduwa,ta kuma waiwayo tana duban tsaleliyar matar da ake kira da maimunatu. "Turqashi" ta fada qasan ranta,qarara baqinciki da kuma hassadarta ta bayyana,don takawa tayi gabanta ta kuma duka taba kiran sunanta don tabbatarwa ita dince,maimunatun kuwa ta amsa da kyakkyawar zuciya,ta kuma bi gaje da murmushi,murmushin da gaje ta dinga jin cewa da biyu tayi mata shi,kawai saita miqe tayi daki fuuu. Ganin zaman da suke bana wani abu bane sai na banza ya sanya maimunatun tace da.inna furera "Inna zamu wuce,sai da safe" "A'ah,ki wuce ina?,ai kuma kinzo kenan,ke da tafiya sai zaku koma,wala'alla ma gajee ta ta fansheki,taje itama ta dandana ta dawo" maimunatu naji na gani inna fureta tace mata nan kwana fa,ko raka su khadim zuwa hanya don ba zasu gane ba ta hanata,sai laulo ta sanya ya rakasu,ita kuma taci gaba da zama a nan tana amsa tambayoyin innar,don yanzu ta samu guri sosai ganin yaran sun tafi. Shuru innar tayi,wani abu yazo ya tsaya mata a wuya,tana tsoron kada fa maimunatu a nan gaba ta zama wata,ta kuma fisu a komai,anya ba fitittike musu zata yi ba?,tayi kwance kwance ta zayyano musu aibubbukan data dade da laqabawa maimunatu ta bata ta a wajensu ta basugaje itama taje ta dandali wannan arziqin?. *Arewabooks:Huguma* ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 23 Sallamar jauro ita ta kubutar damaimunatu daga tulin tambayoyin inna furera,shikam karon farko ya gane maimunatun,yayin data miqe kamar yadda ta saba a baya tana masa sannu da zuwa gami da karbar ledar hannunsa. Yana shirin xama ta duqa har qas ta gaidashi,ya amsa cikin nuna kulawa,tamkar diyarsa gaje "Baki tafi gida kin kwanta ba?" Wani kallo inna furera ta jefeshi dashi a fakaice "Akwai inda yafi nan ne?,naga dai nan dinne gidan" "Qwarai kuwa" "Tun daxun ma nake tsimayin shigowarka..." "Eh nadan tsaya ne muna magana da labaran,ashe bidar alkhairi ne ya kawosu garin ma" sosai inna furera ta bada hankalinta ga jauro "Kamar yaya kenan?" Huffijen qafarsa ya cire,ya zauna sosai yana tanqwashe qafafunsa "Wato Allah ne kadai yasan alkhairi dake tattare da yarinyar nan,uwar dakinta hajiya anni,ita tazo ta shaida mana cewa,suna so mu basu dama zasu turo a nemawa jikanta auren maimunatu" Kamar ya dauko qaton qarfe ya doka mata a tsakiyar kai haka inna furera taji,sai taji gaba daya ta daina ganewa,kwanyarta ta dode "Ban gane abinda kake magana akai ba jauro,kace me?" "Nace gidan da taje aiki,uwar dakinta tazo nemawa jikanta izinin turo magabatansa neman auren maimunatu" zumbur kamar wadda kunawa ta harba haka nan ta miqe,take ta hada zufa da kuma gumi,zallar tashin hankali yana nuna kansa saman fuskarta "Wallahi wallahi ba zata sabu ba,aini ba haka mukayi da ita ba,ba kuma abinda na turata yi kenan ba,ni arziqi na turata nema mana bawai aure ba,hasalima ni ban shirya aurar da ita yanzu ba....."saita waiwaya bangaren da maimunatun take "Don uwarki don ubanki dama karuwanci kika je yi?,aure nace kije ki samo ba kudi ba?,shegiya mayya,kinje da idanunkin nan kin lashe kurwar dan mutane?" Inna furera ta fada cikin hargowa da fada matuqa "Ah.....kinga dakata furera,me kikeson kice ne?,.....ke maimunatu,tashi ki wuce daki wajen 'yaruwarki ki kwanta" ya baiwa maimunatu data cure waje guda saboda tsoro umarni,ta manta da irin wannan rayuwar sam,ta manta rabon da wani ya daga murya a kanta sai yau,sai ta miqe da hanzari ta durfafi dakin gaje,duk da shima batasan me zata taras ba. "Zauna furera" jauro ya bata umarni kai tsaye yana dubanta "Na zauna nayi me?,aini na gama magana,babu uban da ya isa yasa maimunatu tayi aure yanzu ehe" cikin matuqar mamaki yake kallonta "Awala hankali furera?,wanne irin batu ne na wai maimunatu ba zatayi aure ba?,ina cewa nan tanadin auren gaje kike yi?,sai kuma yanzu zaki ce ita maimunatu ba zatayi aure ba?,.....to......to,na gama fahimtar inda kika saka gaba,tsaf na karanceki,to bari kiji,idan kin saba watangaririya da rayuwar yarinya,idan kin saba saka rayuwar yarinya a gaba kiyi duk yadda kikaso ina zuba miki idanu,to wannan karon tayi qaura,kuma baki isa ba,yadda suka zo neman izinin auren maimunatu zasu sameshi kuwa da yardar Allah,muddin bake kadai kika rage a doron qasa jinin shatu da maimunatu ba" ya miqe cikin tsananin fushin data jima bataga yayi ba,sai tabi bayansa da kallo tana cewa "Me kake nufi jauro?" Ko tankata baiyi ba,yasa kansa abinda ya wuce dakinsa. Komawa tayi jabar ta zauna a wajen tana fidda zazzafar iska daga bakinta,kwanyarta ta cika taf da tunani,mutanen nan koda bataje ta ganewa idanunta ba tabbas tasan masu tarin arziqi da wadata ne,ta yaya maimunatu zata shiga cikin irin wannan ahalin alhalin gaje na zaune a qauye?,duk da babbar sa'a tayi na samun himu cikin qauyen?,shawara ta qarshe da zuciyarta ta bata shine,ta tunkari jauro kai tsaye,ta fayyace masa abinda yake zuciyarta,ai shima gaje diyarsa ce,kuma bazaizo ci gaban maimunatu fiye da diyarsa ta cikinsa ba. Wani kallo ya dago ya watsa ma furera sansa ta kammala bayananta "yanzu na fahimci bayan ciwon mugunta da hassada dake damunki,harda ciwon hauka kadan a kwanyarki,toki sani.....ni ba qaramin mutum bane,yadda suka furta maimunatu babu abinda zai sauya wannan in sha Allah saidai idan sauyin daga wajensu ne" maganar ta sake harzuqa inna furera matuqa,ta miqe cikin masifa "Nidai bansan ko dakai.akayi cikin maimunatu ba,banda haka,ta yaya ga jininka zaka ajjiyeta kafifita wata bare akanta?" "Duk yadda rai da zuciyarki ya baki haka ne" abinda jauro yace da ita kenan,don ya fuskanci tayi nisa bata jin kira,ba zata fuskanci duk wani bayani sai abinda zuciyarta da shaidan suka qawata mata. Yadda maimunatu batayi cikakken bacci ba a daren saboda maganganun da gaje ta dinga gasa mata har zuwa sanda bacci ya dauketa......haka itama inna furera bata runtsa ba,Kuka irin wanda maimunatu ta jima bata yishi ba tun barinta gidan a yau ta yishi,tana cike da tantamar anya inna furera yayar daadarta ce da gaske kuwa?,sam ko daya cewar da tayi ba zata auri jika ga anni ba shine damuwarta ba,a'ah.....yadda a kullum ta bude baki mugunyar kalma ce ke fita daga bakinta a kanta,bata taba ambatar alheri a kansu,daga ita har marigayiyar mahaifiyarta,ta duba ta kuma dubo amma ta gaza gano laifi guda daya tak da suka yiwa inna furera wanda suka cacanci wannan abun daga gareta,bata damu da zantukan gaje ba dama ta saba dasu,amma qiyayyar inna furera tana mugun taba mata ruhi. Ita kuwa inna furera kaf a daren tunaninta ya tafi ga yarda zata turgude maganar auren maimunatu ne,idan da hali ma ta maida akalar zanca ya koma kan gaje,bata damu da koma wanne irin kallo daadar himun zata yi mata,indai suka haye wannan bigiren shikenan komai yazo qarshe a wajenta. Shawarar qarshe data yanke da ita ta kwanta,ta kuma miqe tun kiran assalatun farko ta buga sallarta,ta zauna tana dakon kira na biyu ta fice a gidan. Sanda ta fita din kuwa ko sallamewa daga sallar ba'ayi ba adan masallacin dake tsukin rugar tasu,sai a hanya dab da isarta gidan bappa labaran aka idar,ta kutsa kai gidan babu cikakkiyar sallama saboda bataso daadar tasan tazo,ta nufaci dakin yuuma kanta tsaye. Dai dai lokacin da yuuma ke tsaye tana shirin zare hijabinta daga jikinta bayan ta idar da salla,yayin da anni ke saman abun salla tana lazumi itama. Tsorata yuuma tayi da ganin furera a irin wannan lokacin,ta matsa da baya tana amsa sallamarta sanda ta shigo ta yiwa kanta mazauni,tsaf anni ta gane matar,don haka bata katse lazuminta ba sai data cika dari cif sannan ta sauke carbin bayan ta shafa,inna furera ta fara gaidata cikin tsantsar ladabi,anni ta amsa tana dubanta a kaikaice,don tana da tabbacin kome meye ya futo da ita da asussubar fari to ba alkhairi bane. Rai rai ta fara jerowa anni maganganun da tun a jiyan ta gama shiryawa kanta game da maimunatu,da dukkan wata siga da zatayi baqi a idanunta,anni na kallon ta,bata ce da ita komai ba hakanan bata dakatar da ita ba,har sai data dasa aya "Kin gama?" Anni ta tambayeta "Eh....to shine naga gwara na shaida miki,tunda dai kinga amana ce ta hadamu,bai kamata na rufeki ba kada ubangiji ya tuhumeni,ni kaina yarinyar kaffa kaffa nake da ita da kuma neman maganin tsari daga maita,shine fa kikaga mun kawo har warhaka lafiya lau bata taba kowa a cikinmu ba" Sosai yuuma dake zaune daga gefe ta cika tayi famm,fata take annin ta bata dama ta wanke furera mara tsoron Allah data iya kaikaicewa ta yankarowa jininta mummunar qazafi da qarya har haka saboda kawai zallar hassada da baqar zuciya "Yanzu me kikeso ayi kenan?" Anni ta tambayeta cike da gatse,wanda ita furera bata fahinta ba,sai murna data saukar mata,ta kuma karkace ta gabatar mata da gajenta,bayan ta gama kodata "Kinga dakata baiwar Allah,kiyi ta kanki kinji,banason wannan soki burutsun,banda ma baki da hankali........idan maimunatu mayya ce ku zaku kubuta ne?,ko ce miki akayi ba wanda yasan alaqarku da ita?" Gumin tashin hankali ne ya yankowa furera,ya akayi wata halitta tasan da wannan?dama kowa kallonta yake kenan?. "Ai....to,ai dama ita din.....maitarta ta can jikin kakarta ne.....bawai daga ubanmu bane,daga kakarta ne......sai....sai ta tsotsa daga nonon uwarta itama" "Ke!......ki kiyayeni fa?,wallahi tallahi ina sake jadda miki kiyi ta kanki,yo banda tambadewa irin taki,ina ake irin haka?,to bari kiji na gaya miki,ki kama.kanki,idan ba haka ba in na tashi tafiya billahuwallazi kaf garken maimunatu da uwarta da kika danne kike qafafa dasu sai nasa anyi awon gaba dasu,gwara ki.saita kanki aci gaba da tafiya ahaka,wata shari'ar sai a lahira" sosai jikin inna furere ya dauki bari jin ana shirin yi mata bankada. Ta tambayi kanta Wanne tsinannen ne yake fitar mata da sirri haka?,anya ba daadar himu bace?,babu shiri ta kwashi takalmanta a hannu ta fice don anni ta fara daga mata murya. Abinda ya sake kada mata hanji kuma shine kallon banzan da daadar himu ta watsa mata sanda sukayi kacibus a tsakar gidan,saita qarasa daburcewa,ko taji abinda yake tafe da ita ne?,don haka ta hadiye gaisuwarta tayi waje,don ta soma zargin daadar cikin ranta,saboda tasan kaf fadin karkarar ita kadai tasan da wannan maganganun. Tunda ta idar da sallar asuba tana zaune bata koma ba,lokaci lokaci idanunta suna kan gaje daketa sharbar bacci abinta,babu shiri ko niyyar tashi tare da ita bare ta sauke farali,har yanzu halindai ashe yana nan ta raya hakan cikin ranta. Haka kawai tayi sha'awar tashi tayi irin ayyukan data saba yi a baya,don haka ta miqe a hankali,ta zura hannunta inda ta cusa takalmanta watannin baya sanda zata bar gidan,cikin sa'a ta samesu,murmushi ta sake,duk da sun ratattake,suna tuna mata da abubuwa masu yawan gaske da suka gabata,saita miqe dogayen qafafunta da a yanzun suka qara haske suka kuma yi luwai luwai ta zura su,sannan tayo waje. Tana fitowa jauro na dawowa daga salla,ta gaidashi cikin girmamawa ya amsa mata cikin kulawa yana tsokanarta kan yau ta tuna kwanan ruga,tana murmushi ta soma aikin gidan,sai gashi ya fito yana tambayarta inda fureran taje "Ban sani ba kawu,yanzu nima na futo" sai ya jinjina kai,har yayi gaba ya dawo yace mata ta aje aikin ta koma ta kwanta "Ba komai kawu,hakan yana min dadi" kansa ya jinjina cikin tausayi da qaunar yarinyar,ya shige dakinsa,babu jimawa ya fito da koren hirami na maza jikinsa daya yafa,ya wuce dakinsu,tana jinsa yana rafkar gaje kan ta tashi tayi sallah,kana yayo waje yana ce mata zaije ya dawo,tayi masa a dawo lafiya tana ci gaba da ayyukanta,saidai har ta gams gaje bata futo ba. Ganin ta gama saita wuce kanta tsaye zuwa haggo,tun daga nesa take kallon dabbobin cikin kewa da shauqi,tayi matuqar kewarsu ba kadan ba,amma abinda yadan taba ranta ya kuma bata mamaki,yadda yawansu kyau da tsaftarsu suka ragu sosai,taga sabbin fuskoki dake nuna an hayayyafa,to amma indai hakane me ya hana su qara yawa?. A nutse taje ta kwance wadanda suke daure,ta zari sandar data gani a jingine a wajen,ta kuma soma korasu cikin nutsuwa da tsohuwar qwarewa zuwa makiyaya. Kusan za'a iya cewa kallo ne ya koma sama,duk inda ta wuce dai ta kwashi fiye da rabin hankalin mutanen wajen,wasu da yawa basu ganeta ba,suna mata kallon baquwar fuska,don atamfa ce a jikinta dinkin doguwar riga,ba kayan saqi ba. Dukka wajen data saba ta'ammali dashi a wancan lokacin sai data tsaya a wajen tana tuna komai daya wuce,daga qarshe ta dangana da qasan bishiyarta,wadda a yanzun ta qara yawa da rassa,tana shirin zama taji sallama da muryar da ta kasance sananniya a wajenta. A nutse ta daga kai tana amsa sallamar,bafullatanin saurayin nan daya taimaki rayuwarta a shekarun baya,himu,shine yau tsaye a gabanta bayan shudewar wasu watannu masu tsaho,yana nan a yadda ta sanshi,saidai kuma yayi rama ba kamar a baya ba da yake da cikar jiki.....Ya tsinke sosai ya qara tsaho,har yanzu wannan murmushin nasa yana nan saman fuskarsa,sai ya tako daura da inda take zaune,ya zauna saman dutsen daya saba zama shima "Maimunatu....'yammatan birni" maganar data sanya siririn murmushi kubuce mata,ta kuma soma gaidashi,ya amsa mata cikin matuqar kulawa "Tafiya haka katsam babu bankwana maimunatu?,saidai na laluba naji wayam babu ke?" Har yanzu himu nada wata kima da daraja a ranta,yana kuma cikin jerin mutane masu muhimmanci a rayuwarta "Kayi haquri,haka tafiyar nima tazomin,kuma a sannan bansan inda zan ganka ba" kai ya gyada,shima yasan da wannan "Hakane,to yaya bayan rabuwa?,duk da alamu sun nuna komai yana tafiyar miki yadda ya kamata" ya fada kansa tsaye yana hango canji qarara daga wajenta,canjin da yasa ya saare,ya sake kuma sallamawa bayan kunnuwansa sunji ana zancan aurenta da wani. Mintuna kadan ya miqe bayan zaman shuru da sukayi shi da ita "Sallama nazo muyi,saboda nasan ba lallai bane na sake samun dama irin wannan,ban taba kawowa a raina zan rasaki ba,sai gashi qaddara ta wanzar mana da hakan,duk da zuciyata ta soki matuqar so,bazanyi jayayya ba,saboda bansan me Allah ke nufi da hakan ba,kin cancanci samun kyakkyawar rayuwa fiye da wadda nake miki tanadi,ina miki fatan alkhairi a dukka rayuwarki maimunatu" daga haka ya juya ya soma barin wajen. "Na gode sosai" abinda ta iya gaya masa kenan tana bin bayansa da kallo,tausayinsa da kuma wani irin yanayi na cika mata zuciya,har ya bacewa ganinta. Ko awaguda bata rufa ba inna furera ta aiko kan ta tattaro mata dabbobinta ta dawo mata dasu,tayi hakanne saboda tsoron daya cika zuciyarta kan kada ta rasa dabbobin data qwallafa rai a kansu,fitar da maimunatun tayi dasu sai take ganin kamar wani shiri ne. *Follow my arewabooks account for more latest pages* *Arewabooks:HUGUMA* ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 24 Kai tsaye jauro ya damqawa anni rubutaccen kwatance har zuwa gembu mahaifarsu maimunatu tushensu asalinsu,inda yake da tabbacin zasu samu qannen kakan maimunatu da sauran danginta na wajen uwa da zasu iya aurar da ita. Koda inna furera ta samu wannan labarin hankalinta yadan kwanta kadan,saboda tasan babu wadda zasu fara samu sai babarta inno,ta kuma san cewa duk kanwat jaa ce,inno ba zafa taba amincewa ba matuqar taga irin wannan ci gabanne zai samu jinin shatu. Saidai cikin rashin sa'a ga inna furera,sa'a gasu anni,sai suka samu qanin kakan maimunatu,wanda ya karbesu hannu bibbiyu,ya kuma laluba bangaren mahaifan shatu ya sanar musu da abinda ke faruwa,sukayi murna qwarai,suka kuma amshi su uncle umar wanda dr marwan ya wakilta nemo auren maimunatun,karba ta girma karamci da kyautatawa irin na fulani. Sun karba kudin auren maimunatu,sun kuma amince da satittikan da aka yanke na daurin auren maimunatu,an rabu cikin mutunci da mutuntaka,zuciyar dangin maimunatu fes,a yanzun duk wata shakka da suke da ita kan rayuwar da maimunatu ke ciki ta kau,hankulansu suka sake kwanciya. Sosai hankalin annin ya sake kwanciya,ta kuma sake nutsuwa,hukuncin kuma da suka yanke na wanzarwa da ja'afar komai ba tare da sun sake bi ta kansa ba taji bai dameta ba,tunda anyi me wuyar,sauran kuma zata sanar masa da kanta idan suka koma gida suka huta suka kuma nutsu. Sati daya kacal sukayi a adamawa suka tattaro sukayo gombe,anni cike da farinciki da murnar yadda aka basu maimunatun,kamar yadda honorable ya basu auren diyarsa shima,aka sanya rana kuma dai dai da wadda aka saka ta maimunatu,a yanzun abinda ke gaban anni shine shirin auren. Yammacin wata asabar,cikin daya daga cikin falukan annin wanda aka qawata da tattausan carpet,tana zaune ta miqe qafafunta sosai,daga gefanta surukarta ce,matar uncle usman,mahaifiya ga hafsat,shigowarta kenan gidanma gaba daya. Suna tsaka da gaisawa maimunatu ta shigo falon,sanye da brown din chiffon skert,sai rigarsa me dogon hannu,ta yane sassalkan gashinta da mayafin kayan light brown,fuskarta ta fito fayau tayi kyau sosai,duk da kasancewarta ba ma'abociyar son kwalliya ba,saika tsammaci ta fito ne daga yankin larabawa. Sai data isa gaban annin,ta ajjiye hadin fruit salad data yi,wanda duk cikin girke girken da take koya ne hannun tabawa tana murmushi ba tare data ce da annin komai ba "Da kyau,sannu da qoqari muna" ta ambaceta da sunan da baba tabawa ke kiranta wasu lokutan,sai ta juya sashen da momy kamar yadda suke kiranta take ta soma gaidata. Sama sama ta amsa mata,maimunatun bata wani lura ba ta miqe abinta ta fice,duk da annin taga abinda ya farun,amma sai tayi kamar bata gani ba,ta jawo fruit salad dinta ta fara ci,dai dai lokacin da momy ta motsa kadan,ga duk wanda ya qare mata kallo yasan maganganu ne fal harshenta "Su ja'afar kuma ashe ankai kudi,saiga daddynsu ya shigo da zancan" "Eh,anyi haka" anni ta fada ba tare data dubeta ba "Diyar commissioner ko?,samiha,sai kuma wata agwai,wannan yarinyar data shigo" cak anni ta dakata da shan fruit salad din da take,ta sanya hannu ta zare gilashin fuskarta da takanyo amfani dashi wasu lokuta "Inaji yanzu kikaji na kirayi sunanta ko?,to ba agwai sunanta ba,kada na sake jin wannan sunan daga bakinki,maimunatu take" "Ayi haquri,bada gangan na fada ba,sunanta ne ga kwantan" "Ato,gwara kiyi ta kanki" ta amsata tana maida gilashinta,maganar data tsayawa haj munubiya Momy a rai,wanne irin so annin ke gwadawa yarinyar ne?,duk yadda su shaffa'u ke gaya mata bata yarda ba sai yanzu da dukka alamu suka nuna,tanaso tayi shuru hakanan amma kuma maganganun bakinta basu qare ba,don haka fa sake motsawa "Amma yanzu anni,fisabilillahi ba za'a duba halin da yarinyar nan hafsat ke ciki ba?,gida bai qoshi ba za'a kaiwa dawa?" Sake dubanta tayi wannan karon kallon tsakiyar idanu,tafi kowa sanin wacece munubiya,kaf surukanta babu wadda take fama da ita kamarta "Shi sagirun da yazo da zancan,bai gaya miki anihin abinda nace dashi bane?" Kai ta gyada tana jinjina taurin kai irin na annin "Ya gaya min" "To du Allah du annabi munubiya,banason maida hannun agogo baya kinji ko" sai ta gyada kai kawai,zuciyarta fal takaici,taso ace diyarta ta samu ja'afar,ba tun yanzu ba,tun aurensa na fari,a sannan hafsat din bata wani nuna da yawa ba,take gani shine silar data gaza jan hankalinsa har ya auri shaheeda,a yanzun kuma da take ganin komai yakai anni tayi ruwa tayi tsaki ta hana wannan damar. Miqewa tayi tana rataya jakarta,annin ta dubeta "Zan wuce anni,Alla ya sanya alheri" "Ameen,ki gaida gida,a gaida yaran" har tayi gaba ta sake cewa da ita "Yauwa,ji mana" tsaiwa haj munubiya tayi "Ki turon khalid,na gaza samunsa a waya,kice ina nemansa" dole hakanan ta amsa mata da to,sannan ta taka ta fice. A hanya ita kadai kamar ta taune zuciyarta saboda baqinciki,haka ta fitoma daga gidan babu wanda ta yiwa sallama,duk irin bautar da khalid din kewa annin har yau bata jin tana masa rabin son da takewa ja'afar,a bakinsu shaffa'u takejin kamar ya soma son yarinyar amma annin ta hanashi ta bawa ja'afar,duk da bata taba jin qaunar yarinyar ba amma taji zafin hakan,hakanan ta hana hafsat ja'afar ta bawa wasu baare daban,wannan babu abinda yake nunawa illa zallar qin da take mata,qwafa taja gami da dogon tsaki,zata gamu da khalid dinne. "Allah ya sawwaqe,ya yaye miki munubiya" anni ta fada tana jan wayarta "Shima zan gamu dashi,shegiyar kafiya da riqon abu a rai,wannan wanne irin SO BAYAN RAI ne?,tana nan tana yaqi a kansa bai sani ba,tana ta baqin jini wajen jama'a. Tana ta bulayin nemansa khadim ya shigo "Kiramin jafaru da wayarka" "Allah yasa ya daga,na canza sabon layi" ya fada yana laluben wayar a aljihunsa,sannan ya zauna daga gefan annin yana tambayarta me zaya samu cikin dakin nata "Ban sani ba,zaka kamomin shi ko sai ka cinye kurwata tukunna" ta fada tana harararsa,don tace khadim din ya cuka kwadayin tsiya,yana qunshe dariyarsa ya dannan kiran ja'afar din,saidai har tayi ta tsinke bai daga ba,sai da ya maimaita kiran ana uku ya dace ya daga,kai tsaye ya miqawa anni wayar ya koma corner falon yayi zamansa yana daukar wayar annin. Dan madaidaicin waje ne dake bayan gine ginen gidajen nasu,wanda ke shimfide da korran ciyayi,kujerun qarfe ne masu kyau guda uku da table dinsu a tsakiya,saman table din akwai glass cup daya cika da lemo yana kurba time to time,tsaye yake ya baiwa table din baya,hannuwansa riqe da wasu fararen takardu kusan guda shida,wanda ya bada hankali sosai a kansu,da alama akwai muhimmin abu da yake dubawa a ciki,sanye yake cikin shirt da trouser masu taushi duka na kamfanin Louis Vuitton,iskar wajen ta gauraya da daddadan turaren jikinsa tana bada wani yanayi me dadi,wasu slippers ne masu kyau na fata sanye a qafarsa,hannayensa goye a bayansa,lokaci lokaci yakan cire hannun ya shafi tausasan labbansa. Karamin tsaki yaja sanda wayarsa ta sake qara,karo na kusan uku kenan,sauke takardun yayi daga fuskarsa a hankali,kyakkyawar fuskarsa dake fidda wani irin kwarjini da kuma calmness irin nashi ta bayyana,taku biyu yayi baya ya isa gab da table din inda wayar tasa take,har yanzun wani busar sarewa take me dadin sauraro. Sai daya kalla screen din some few seconds sannan ya shafa wayar ya karata a kunne "Assalamu alaikum" ya fadi with husky voice,daga can bangaren anni ta amsa,saiya dan sauke numfashi kadan jin anni ce,ya maqale wayar a kafadarsa yana gyara takardun bayan ya soma da gaisheta "Lafiya alhmdlh,manya,me yasa kake mancewa da gida?" "Taya zan mance daku anni?,akwai abubuwa ne da har yanzu bayi settling dinsu ba" haushi ya cikata,koda yaushe maganarsa kenan,to itakam koma meye dai ai ta kawo qarshen abun,don haka cikin kaushi tace dashi "Kullum maganar dai kenan,tamkar kaine kafi kowa sabga a duniya,to koma dai meye wannan matsalarka ne,mukam ba zamu zauna mu zuba idanu rayuwarka taci gaba da tangal tangal a haka ba,bayan ko talatarka bakaci ba balle laraba,ban sani ba ko dan uwanka ya labarta maka" ta sauke maganar tana jiran amsarsa,dai dai sanda ya gama gyaran takardun ya duqa yana niyyar ajjiyesu saman table din "Me kenan?" "Kai kudin aurenka wa 'yammata biyu,nan da sati hudu kuma in sha Allahu kowacce zata shigo gidanka a matsayin matarka,saboda haka ka maida hankalinka,ka tattaro kayo gida,koma meye daga baya zaka qarasashi" "What a funny story anni" ya fada cike da tantama yanayin fuskarsa na sauyawa zuwa ga yanayi na son yin murmushi,saisai murmushin bai fita ba,saboda yadda yaji labarin yafi masa kama da tatsuniya "Anni,zancan aure fa kike da mata har biyu" ya fada sounding like dariya zata kubce masa,yanayin da anni tagama karantoshi tsaf,saita hade muryarta itama "Kafi kowa sanin wacece maryama farouq akko ko?" Yes,yasan anni fiye da kowa a gidan dama family dinsu,tuna hakan ya sanya duk wani shakku dake ransa wankewa,uwa uba yadda ta kirayi sunanta in full ya sake tabbatar masa she's serious "Seriously?" Yayi tambayar da wani irin tune,tambayar da baisan dawa yake ba,da anni yake koda kansa? "Inadai gaya maka,sati hudu kacal suka rage" "Ya salam ya Allah,anni why?, Me yasa?,mu nawa ke zaune a gidan,amma why me?" Ya fada yana jin wani irin zafi na taso masa har saman fuskarsa "Bakai kadai ba,wannan karon duk wanda yakai munzali sai ya bar gidan nan ya tafi nasa,abun ya isa hakanan" "Okay okay fine.....zan dawo zanyi packing komai nawa zan bar gidan,but..... please anni,kada kiyi punishing nawa ta wannan hanyar,bazan iya zama da kowacce mace ba anni please" ya fada cikin kwantar da murya,tare da fatan zai shawo kan annin. Baki ta tabe daga can,dama tasan za'a rina,tasan halin ja'afar sarai,tasan komai zai iya faruwa,kuma dama bata tarki abun ba sai data shirya masa "Kaga babu fa wannan zancan,an riga an gama magana da magabantansu,ba zaka maidamu qananan yara ba,kuma ba gidan mukeso ka bari ba,zaman aure mukeso kayi" zaman aure kamar wani mace?, Ya qiyasta hakan cikin ransa "Anni,ki fahimceni mana,ta yaya za'a auramin mata har biyu bayan babu fahimtar juna a tsakanina da kowaccensu bare azo maganar soyayya wadda already nayi banning dinta" "Zaku fahimci kawunanku a dakunanku ai" ya zuwa yanzu ranshi ya sake baci fiye da dazun "Anni!" Ya kirayeta da murya mai kaushi kadan,wanda shi kansa baisan yayi hakan ba "it will not be possible,ta yaya hakan zai yiwu?" "Ahap gashinan kuwa?" Da gaske take ba zata fahimceshi ba,saidai ma idan bai wasa ba ta sake tunzurashi,don haka sai kawai ya yanke wayar da sauri,sannan cikin wani irin zafin nama yaja kujera guda daya gabansa ya zauna a kai bayan ya jefa wayar saman table din,baya ko tsoron ta fashe. Dukka hannayensa ya cusa cikin gashinsa yana yamutsawa tare da fadin "No...no,it can't.....it can't.....am not ready.....am not ready to face it this challenge" ya fada cikin zafi,sai kuma ya sake miqewa,yana buqatar yayi magana da wani,sai ya janyo wayar yana furzar da zazzafar iska daga bakinsa ya soma laluben number ammansa,gab da zata shiga ya sauya shawara ya kashe,sai ya maida kiran kan jabir "Where are you?" Ya tambayesa kai tsaye,tsabar bacin rai yama manta inda yace masa zaije,tunda jabir din yaji muryarsa yasan cewa akwai matsala,cikin ransa yake fatan Allah yasa ba depression mode dinsa ne ya motsa ba "Am on my way,is there a problem?" "Zaka dauki mintuna nawa?" "Few" ya amsa masa a taqaice "Okay,am waiting for you, please don't stay long" bai jira amsarsa ba ya katse wayar ya sake jefata inda ya dauko,dukka hannayensa ya zura cikin aljihun wandonsa,yahau kai kawo tsakanin wannan bangaren zuwa wancan,wanne irin hukuncine wannan da zasuyi masa?,wannan auren aiko mace a wannan zamanin ba za'ayi mata shi ba,wadanne irin mata ne su kansu da suka dauki kasadar aurensa ba tare da sun gana dashi ba?,kawai sun amince da auren mutumin da bashi ya nema yardarsu ba?,anni tana tunanin akwai macen da zata cike masa GURBIN shaheeda ne?,babu?,sam babu,yanajin cewa daga kanta an gama haifar diya mace a duniyarsa,wadan nan matan data debo GURBIN IDO ne kawai,fanko ne,ba zasu taba zamtowa IDO ba wato shaheedansa,yayi imani da hakan har cikin zuciyarsa. Kafin jabir yakai ga isowa ya duba agogo sau babu adadi,a gaban idanunsa cave ta saukeshi,ya fito dauke da niqi niqin siyayya a manyan ledoji,sai a sannan yayi noticing wani abu,kwana biyun jabir fita yake siyayya kusan koda yaushe,kamar wanda ke shirin komawa gida. Sai daya shiga gida ya aje kayan sannan ya sake fitowa,kafadarsa ya dafa daga baya "Meye haka ne man?" Waiwayowa yayi ya dubi jabir,idanunsa a sannan har sun kada sun sauya kala saboda zallar bacin rai,wanda ta nan ake iya gane qurewar bacin ransa "Yanzu kamar ni?,kamar ni anni zatayi forcing dina akan aure?" Tuntuni ya shanshano komai,don yasan da komai din,ya samu labari,saidai baiyi gangancin shaidawa ja'afar din ba,ya zuba idanu yaga ya caftar zata kaya. Dubansa sosai jabir yayi "That's right...." Sosai maganar ta baiwa ja'afar mamaki,ta kuma sake qular dashi "Like how? what are you trying to say jabir?" Ajiyar zuciya ya sauke,shima ya maida hannayensa aljihunsa "Ja'afar,ka gaza nutsuwa ka karbi qaddarar rayuwarka kayi moving forward yadda ya dace....." "Yanzu qoqarin me nake?" Ya fada da zafinsa "Yes,naga canji,kanata qoqarin maida harkokinka yadda ya dace,amma bata iya wannan fannin kawai ya kamata ka maida kai ba wajen gyarawa,ya kamata ka sake building a new family da zasu debe maka kewa,su sake maidaka cikakken mutum,abinda kai ka gaza yi anni ta tayaka ginashi,so bai kamata ka zargeta ko kaji haushi ba,a shawarce ka tsaya ka nutsu,ka yiwa abun kallo na fahimta,don't upset please" "Okay na gane,kaima kana goyon bayan abinda tayiminkenan?, wait.....waima wa yace musu a yanzun ina sa buqatar wata mace cikin rayuwata?,dolen sai na rayu da wata,a barni nayi rayuwata a haka mana,me na ragu dashi" jabir zai sake cewa wani abu ja'afar din yaja tsaki ya daukin wayarsa a fusace ya wuce cikin gida da sassarfarsa. 25 Kamar jabir din ya shareshi,sai kuma ya kasa,ko babu komai yana buqatar kwantar da hankalinsa kada kuma ya birkice musu a koma 'yar gidan jiya,bayan abubuwan suna danyi kyau ba kamar can baya ba,don haka sai ya kwasa shima ya bishi. Cikin rashin sa'a ya sameshi ya kulle kansa a dakinsa,yayi ta bugu ya bude masa amma yayi kunnen uwar shegu dashi,ya sani ya qulu sosai,kuma cikin bacin rai yake,haka dole ya haqura,saidai yana fatan kada ya jima a kulle a dakin temper tayi masa yawa. Komawa yayi ya zauna saman kujerun falon,kam kujerar dake fuskantar dakin,lokaci lokaci yana danna wayarsa yana kuma duban qofar dakin tare da fatan ya bude,saidai har kusan awa guda da rabi ba motsinsa ko alamar budewa,abun da yadan saka jabir yaji shakka a ransa,sai ya sauka daga game din da yakeyi don dama ta fara isarsa,ya kirayi layin anni. Gaisawa suka fara yi sannan ya gaya mata abinda yake faruwa,duk da taji fargaba itama cikin ranta amma saita dake "Rabu dashi,zaiyi ne ma ya gama,kayi sabgarka,idan ya gaji ya fito" ta fada cikin dakiya,murmushi jabir yayi,don shi kansa yasan dakiya kawai annin tayi. Suna gama wayar ya isa ga makunnin kayan kallonsu ya kunna tv din,sannan ya maida channel din dake kai zuwa saudi qur'an da madaidaicin sauti,ya ajjiye remote ya wuce dakinsa ya sauya kayan jikinsa daga shi sai farar singlet da boxer,ya fidda siyayyar da yayo,yakai daki sa,saura kuma ya wuce kitchen dasu. Abinci ya fara shirya musu,yana aikin amma hankalinsa yana falo,yana yi yana leqawa ki ja'afar din ya fito,saidai har ya gaji da leqan baiga ya fito ba,tilas ya haqura har ya gama abincin. Yana fitowa daga kitchen din yana qoqarin fidda afron din jikinsa jaafar din na fitowa a dakin,sosai jabir din yaji dadin hakan,ganin fushin baiyi tsaho ba,a yanzun ma ya sake wanka ne don kayan jikinsa na dazun ba sune yanzu ba. "Ina zuwa?" Jabir ya tambayeshi yana fidda ruwa daga fridge "Zamu fita da mr mickey,akwai meeting da zamuyi,so if i stay long kada ka jirani" "Abincin fa?" "Ka cinye kayanka" dariya ce ta qwacewa jabir,ya sani fushi yake dashi,yaji haushin that's right da ya fada,da kuma goyon bayan anni da yayi,fushinsa ne ya shafi abincinsa "Cikinka ba nawa ba" ya bashi amsa sanda yake takawa zai fita daga falon,saidai bai waiwayo ba ya fice abinsa,kamar ma baiji abinda jabir din ya fada ba. Diban iya wanda zai isheshi yayi ya sanya masa sauran a fridge,yasan idan ya dawo zai nema abincin da kansa,don duk abin nan nasa baya wasa da cikinsa ko kadan. Shirye shirye ake gadan gadan daga gidan dr marwan akko na aurar da ja'afar din,wanda tun ranar da sukayi waya da anni bai sake neman kowa ba,kamar yadda itama annin ta watsar dashi,hakanan daga ita har dr babu wanda ya sake nemansa,shima hakan yayi masa,don kuwa ya riga ya gama shiryama ransa komai,baiga ta yadda yana namiji me cikakken hankali,ba auren fari ba za'ayi masa irin wannan karan tsayen,ya tuhumi kansa da kansa kan ceqa ya bawa anni dama ne da yawa cikin rayuwarsa shi yasa tayi wannan tunanin,bama su da suke nigeria ba,hatta da jabir baibi ta kansa,ya shiryama ransa zai koma nigeria ne a duk sanda ya gama uzurorinsa a nutse. Ta bangaren jabir kuwa duk da ya damu,yana kuma ankare da abinda ke faruwa amma bai nuna ba,shima shirin tafiya gida yake,saboda a yanzun aurensu su biyu za'ayi,sbi da ja'afar din,anni taso a hada harda su salma amma sai aka samu tsaiko,hisham bai fidda gwanarsa ba,hakanan salma tana kan qadamin kammala nata karatun ita da hafsat da kuma laila,don haka annin tace a barshi zuwa sanda zasu gama din watanni shida nan gaba masu zuwa. ********Dai dai lokacin da suke shigowa farfajiyar gidan sanye da hijabansu na makaranta suna taba hira,motar dake fake a parking lot na gidan ta tsaya,mamallakiyar motar ta budeta ta fito. Zabgegeyar farar bafulatana,fara tas,wadda kamanninta da haj aishatu ta nuna qwarai,sanye take da wani danyan lace daya kwanta a fatarta,komai na jikinta matching ne,jikinta ba abinda yake sai fidda wani tatausan qamshi,tana rungume da baby boy wanda duka duka bazai wuce shekara daya da watanni biyar ba. "Auty maama" 'yammatan suka kusa hada baki wajen kiran sunanta,tana rufe motan da key ta waiwayo tana dubansu,fuskarta ta wadatu da fara'a sosai,macace m'abociyar fara'a da kuma kirki,bata debo a qasa ba,ta debo kyawawan halayen mahaifiyarta haj aishatu umar sanda da kuma dr marwan akko "Yammatan gidan baaba dr" ta fada sanda suka qaraso gaba dayansu,murmushinsuka sako,don dukkansu sunji dadin zuwan nata,saboda akwai shirye shiryen da suke akan bikin gidan,wanda sun tabbatar bazaiyi armashi yadda suka tsara ba saita ce wani abu,a matsayinta na babbar yayarsu,wasu na shirin amsar yaron hannunta,yayin da khadija ta amshi hand bag dinta,suka soma rankayawa ciki bayan sun gaisheta hira ta balle. "Ina kuka baro maimunatun kuma yau?" Anty maama ta tambaya sanda suke gab da shiga ainihin ginin gidan,inda zao sadaka da qofar kowanne sashe dake cikin gidan,sai a sannan suka laluba suka ga ba maimunatun,da alama guduwa tayi saboda anty maaman "Tare muke guduwa tayi halan,kinsan halinta,halim fulani ne har yanzu a jikinta,bada kowa yanzu take iya haduwa cikin gidan nan ba,hatta amma wasan buya sukeyi" murmushi ya kufcema anty maama,kunyar yarinyar da kamun kanta yana matuqar burgeta,duk da a cikinsu take amma bata yada dabi'ar kunya ba,har yanzu yarinyar batasan hanyar gidanta ba,da hirar maimunatun suka rakata ta gaida ammi sannan ta isa sassan mahaifiyarta amma,bayan ta aikawa anni da saqon gaisuwa gami da sanarwar ta iso zata shigo. "Ina duka yaran?" Amma ta tambayi anty maama "Suna islamiyya,amma for now nasan ma sun taso,nace ma iliyasu driver ya wuce dasu wajen haj,idan na dawo zan biya na debosu" "Yayi kyau,Allah ya taimaka" amma ta fada,don ba wani dogon hira suke da ita can can ba,kasancewarta diyar fari a wajenta "Wai maimunatu nita gani ta gudu amma?" Anty maama ta fada tana dariya,sai amman tayi murmushi "Kyagaji da gani indai maimunatu ce,yanzu ko sassan nan bata zuwa" kai anty maama ta gyada,kamar ba zata ce wani abu ba sai kuma ta magantu "Allah dai ya tabbatar da alkhairinsa,ubangiji yasa ta zame ma rayuwar ja'afar haske,nafi sanya hope a kanta amma akan samiha gsky,duk da ba'asan maci tuwo ba sai miya ta qare,Allah yasa dai manya ya riqesu da kyau" ajiyar zuciya amma ta sake,don abinda taketa tsoro da fargaba kenan,musamman da yadda kwanaki suketa matsowa,amma bataji.batun dawowarsa ba,koda kuma sunyi waya baya ce mata komai kan dawowar tasa ita kuma bata taba tambaya ba saboda.kara da kuma alkunya,amma dai duk sanda tayi sujjada tana gayawa Allah,wannnan shike bata nutsuwa. Bata jima sosai ba tace bari taje wajen anni ta fita a sashen. Bayan gama gaisuwa da 'yar tsokana da wani lokacin take kwasan annin da ita,sai anni ta kirayi sunanta "Inaso kiyimin total na kayan jere dana kitchen,babanku ya buqata,zai siyawa maimunatu" "A ina anni" "Oho,wani kamfani ne yace anan da suke kawo kaya daga turkey,da so yayi aje can direct,to kuma lokacin ya qurace,danginta daga can gembu sun nema ya barsu suyi kayan,yace ai diyarsa ce,duk da haka saida suka aiko da kudin kayan,to nace gwara a siya wani abun me daraja da kudin a bata,tunda shi yayi niyyar yin kayan" "Ma sha Allah,abbi ya kyauta,kuma hakan yayi,ko gold ne sai a siya mata,ba matsala anni" ta amsa mata tana fiddo wayarta daga jaka "Yauwa,sannan kuma,bashi nakeso ki bani" kai ta daga tana duban anni tana 'yar qaramar dariya "Me zakiyi da bashi kuma tsohuwa,bayan duka lalitar familyn farouq kumo na hannunki" "Ke banson iya shege,kiyi ta kanki,magana nake miki ta gaske,aron kudi zaki bayar,amma ni ba kawomin zakiyi ba,lefe nakeso ki hada na maimunatu dana samiha,banason sanya kudina nazo na kasa tambayar jafar,idan nakine sai nafi maida kai ya maida miki kudinki akan kari,so nake komai yayi da kudinsa saboda sai yafi jin auren a jikinsa" dariya anni ta bawa anty maama,ta wani fannin kuma jikin anty maaman yayi sanyi "Wai har yanzu baice komai ba?,baya cewa komai?" Kai anni ta jin jina "Eh,amma ki barni dashi,idan yasan wata ai baisan wata ba,kallonsa kawai nakeyi,zai shigo hannuna ne,baisan wace maryam kumo ba har yanzu" ajiyar zuciya anty maama ta saki "To Allah ya kyauta,ya kuma shiga lamarin" "Ameen ya hayyu ya qayyumu,jabiru ya turo nasa kudin ta hannun hisham,duk da naji yace akwai wasu kayayyakin daya siya musu shida jafar din,daso yayi ya biya harda na jaafar din na hanashi" "Eh gwara da bai biya din ba,gaskiyarki anni,gatan sai yayi masa yawa ya gaza riqe abun da muhimmanci" "Shina gani ai" anni ta fada da qwarin gwiwa,shi yasa takeson anty maama din,saboda tana da matuqar hankali da nutsuwa "Ba damuwa,naga wasu akwatuna sabbin design masu goma goma,zan siyawa jabir a matsayin gudu mawata,shi kuma zan siya masa set daya,set daya kuma zan saka cikin lissafinsa" "Yayi dai dai,Allah ha saka miki da alkhairinsa kema,ya qara muku zumunci,Allah ya qara hadamin kanku" anni ta fada cikin jin dadi "Ameen summa ameen" daga nan suka shiga tsara yadda komai zai kasance daga kan kayan lefen zuwa sauran hidimomi na bikin,harda yadda za'a gyara maimunatu duka anni ta dora saman wuyan anty maama. Bayan ta gama da anni kuma ta koma bangaren qannenta,a sannan su salma sun shigo,nan suka zauna suka tsara komai bisa tsari da kuma burgewa,saidai har suka ci suka cinye hirarsu babu giccin maimunatu. Can cikin garden na gidan ta boye kanta,batajin komai a kan auren tunda batasan meye gundarin abinda ya qunsa ba,bata gama wayewa da sanin meye shi ba,bata saba da zabin abubuwa a rayuwarta ba bare tace wannan zabin bai mata ba,kota damu,kawai dai tana jin kunya da kuma nauyin mutan gidan,tunda tasan meye surukuta,ta gefe guda kuma wani lokacin zuciyarta nayin rawa da kuma d'ar d'ar,tunda ta sani cewa kowacce mace tana auren namijin daya ganta yace yana sonta,itama ta maida masa martanin tana sonshi,amma ita nata angon batasan wanne kala bane,daga wacce duniya zaizo?,yaya kuma zai karbeta?,wadan nan sune kawai abubuwan sa takan nanatawa kanta lokaci zuwa lokaci,saidai yadda taga kowa ya daukaki abun a gidan yana bata mamaki,sannan yadda su laila ke sanyata a gaba,suyita gaya mata abubuwa game da angon nata sai ta yita mamaki,don ita bataga alfanun hakan ba,kiyi kaza kiyi kaza,kullum maganarsu kenan,sun canza mata abubuwa masu yawa,kama daga manta turarenta sa sauransu,itakam duka bataga wannan takurar da tsare tsaren na meye ba,badai a daura aure bane kawai a kaita can gidan ba shikenan dai?,amma magana daya biyu sai suce kina da kishiya,saikinyi kaza kinyi kaza,itakam bataga wani abun damuwa da damun kai ba. ********Cikin tsari ilimi da kuma gogewa anty maama ta hada lefe na alfarma,kowacce amarya ta rabauta da akwati goma goma,rana daya aka kai na samiha dana amaryar jabir Aaliya,said kuma kumbo da ammi abokiyar zaman amma ta qarawa kowacce amarya guda hurhudu,shima kowanne shaqe yake da kayan al'adun aure dana zamani,abun dai ya qayatar ya kuma bada sha'awa sosai. Tarbar girma suka samu daga kowanne bangare na gidajen amaren,suka dawo gida suna yabon tarbar da suka samu,suna kuma tattauna yadda suka fuskanci dangin hajiya Aayah dama ita kanta haj aayah din keji da samiha,kasancewarta diyar fari a wajenta da zata fara aurarwa,su uku kuma kacal Allah ya bata. Gembu aka yanke za'a kai lefan maimunatu,za'a kuma tafi ne har da ita,daa sunce abar kayan basai an kawo ba saboda gudun wahala da kuma zirga zirga,amma anni tace sam,aure za'ayi mata na gata da kuma 'yanci cikin danginta kamar kowacce diya,za'a kai mata kayan kamar yadda aka kaiwa kowa,kuma za'a daukota daga gaban danginta a kawo musu ita. Wannan abun da anni tayi yayi matuqar qara mata kima da daraja a idanun dangin maimunatu,ya kuma qara musu qaimin fidda maimunatu kunya,tare da nuna ita din jininsu ce,duba da abunda bare tayi mata?,ina ga su da suke jininta?. Kamar yadda annin ta tsara kuwa haka akayi,bikin saura sati biyu suka daga gembu da maimunatu da kayan aurenta. Gidan kawu sule suka sauka,qani ne ga mahaifin shatu mahaifiyar maimunatu,mutum ne mai zumunci ba laifi,qaddarar abubuwan da suka farun zasu faru yasa ya barwa fulera riqon shatu dama maimunatu,uwa uba kuma da yadda ta nuna tsananin tausayawar tata ga 'yar uwarta,abinda yaja kawu sule kenan,ya dinga tunanin ko wannan abun ya kawo jituwa da gyaruwar alaqa tsakanin su shatun da yaran inno,yayi tunanin ya barta ko Allah zai sake dai daita al'amarin,kuma har yanzun nan baisan rayuwar da shatu da diyarta maimunatu suka fuskanta ba,yayita yabawa fuleran ma,ya tsammaci aiki tayi da hankali tace a kawo auren nan wajensu sabida girmamawa,baisan ko labari bata dashi ba,sai bayan da yuuma ta tabbatar sun sauka a gembu sannan ta aikaqa fulera da saqon ankai kayan,abinda ya dugunzumata,ya kuma bata mata rai,kamar yadda suke da maimunatu amma ace sai daga wajen baare zata samu labarin aurenta?,ta kuwa ci alwashin tafiya gembu cikin satin ko satin gaba,lallai sai ran kowa ya baci,idan sunsan wata ai basusan wata ba. 😊😊😊😊😊 *_SHIN KINA YIWA KANKI DA JIKINKI TANADIN SABULAN WANKA MASU KYAU MAI DA TSOHUWA YARINYA KO KEMA HAR YANZU DANGWALI YABA KIKE SAWA JIKINKI?_* *_SABULUN DAKE GYARA JIKI DA FUSKA YA MAIDA FATA TAMKAR TA JARIRI SABUWAR HAIHUWA?_* *_SABULUN DA DUK INDA KIKA SHIGA FATARKI ZAKI FITA DABAN DATA SAURAN MATA?,YA MAIDAKI TAMKAR WATA DAN DAREN SHA HUDU?_* *NASAN ZAKIYI TUNANIN A INA ZAKI SAMU WANNAN INGANTACCEN SABULUN?AMSAR ITACE_* *_J-SKIN CARE PRODUCTS (JANNAT SKIN CARE PRODUCTS)_* _SUKE SAMAR DA KALOLIN SABULAI NA KECE RAINI KAMAR HAKA_ Black soap Kiddies Black soap Sugar body scrub Body butter Kojic acid soap Turmeric soap Goat milk soap Honey soap Carrot soap Face and body cream Hair growth oil *_dukka wadan nan kalolin sabulai J-SKIN CARE PRODUCTS sun samar muku dasu bisa farashi dai dai da aljihun kowa_* *_Baya ga haka kuma,wani abun qayatarwar,suna karbar kwangilar yin sabulun cold process ga masu yin biki ko suna_* *Zaku iya dubasu a shafukansu na sada zumunta* *Instgram*:J-skincare products *Tiktok*:jannatskincare *Ko ki tuntubesu kai tsaye ta wannan number wayar* 0813 801 1240 *J-skin care products,DUNIYAR SABULAI MAI DA TSOHUWA YARINYA* 26 Kulawa me kyau maimunatu ta dinga samu daga wajen yadikko matar kawu suleman,itace matarsa ta biyu,kuma tafi daada saratu quruciya,don haka ta zage da bawa maimunatu duk wasu kaye kaye irin nasu daya kamata ace amarya tayi amfani dashi,sannan ta zage ta dinga karantar da maimunatun mene ne aure?,waye miji da sauransu,abubuwan da suka sake fadada tunanin maimunatu,ta wani fannin kuma suka sake haifar mata da wani tunanin na daban "Wannan shine aure?,irin zaman da zanyi kenan da mutumin da bansan waye shi ba?,shima baisan wacece ni ba?" Abinda ta yita juyawa kenan cikin ranta. ***********Zaune yake gaban laptop dinsa,ya baje takardu yanata shigar da wasu bayanai cikin system din,gaba daya hankalinsa kacokam yana kan aikin,wanda ya share kwanaki uku yana yinsa,burinsa ya kammale komai waje daya ya kuma gama da wannan aikin. Wuninn ranar ko abincin kirki baici ba,sai uban coffee da yaketa danqara,lokaci lokaci kuma ya hada da cake,ko a yanzunma mug din daya sake tsiyaya coffee din na gefansa,ya dauka a hankali yakai bakinsa ya kurba ya maida ya ajjiye,dai dai sanda jabir ke qarasowa wajen,hankalinsa akan ja'afar,hannunsa kuma riqe da wasu rantstsun invitation cards,mamaki fal randa da zuciyarsa na yadda baiji ja'afar din yace komai ba kan yadda IV din nasu keta trending yana yawo tsakanin family and friends,duk da ya lura aiki yakeyi wurjanjan a kwanaki ukun nan. Yaji isowarsa amma bai juya ba sakamakon shigowar wasu emails har kusan hudu a jejjere,sai yayi minimizing abinda yakeyi ya tafi kai tsaye ga email din,don dama yana jiran wasu bayanai daga secretary dinsa,yace masa a daren ya kammla su ya turo masa. Maimakon secretary dinsa sai yaga saqon daga wajen hamza BBY yake,daya daga cikin abokansu tun na makaranta ake kuma tare har yanzu,budewa yayi gajeran rubutune da kuma hoto daga qasa sa bai budu ba _Allah ya sanya alkhairi manya,da ba'a gaya mana ba JB ya gaya mana,Allah ya nuna mana lokacin big boos,i salute you🫡,biyu ka b'aro ashe_ Danna hoton yayi, within seconds ya bude, invitation ne dake dauke da sunansa,da sunan samiha da maimunatu,mutuwan zaune yayi,wani bacin rai yana ratsashi,ya dunqule hannunsa waje daya yana furzar da wata iska daga bakinsa,da gaske suke kenan,ba zasu fasa ba?. Dai dai lokacin da jabir ya zagayo gabansa,yaja wata kujerar ya zauna yana zube masa IVs din a gabansa "Ga hard copies" wani kallo ya watsama jabir din,wanda banda ya saba da irinsa ba shakka sai ya razana "Are you in your sense?, what did you do?,su suna nasu kenan kai kana naka?,to sai kasan ya zakayi da mutanen daka gayyato da labarin qanzon kuregenka,don banga abinda zai kaini nigeria a yanzu ba bare na fuskanci abinda yake shirin faruwa" sai ya miqe ya fara tattara abubuwansa masu muhimmanci,huci kawai yake kamar wani maciji "Da kaje da kada kaje babu abinda zai canza,so gwara ma ka nutsu ka karba abun hannu biyu,ka kuma fuskanci abinda ke gabanka dude" baiko daga kai ba bare ya bashi amsa,ya gama kwashewa ya wuce yabar masa wajen. Dariya jabir ya saki yana kada kai,duk duniya su qalilan ne suka iya zama da ja'afar,cikinsu shi da shaheeda sun shiga ciki,shi yasa kowa yake jinjina mata har yau da bata raye,yana da murdadden hali da kuma wuyar sha'ani qwarai. Sanda ya shiga dakin kasa ci gaba da aikin yayi,ji yake kamar yaci kansa,wani irin bacin rai ya dinga taso masa,yakai ya kawo yana jin wani huci na fita saman fuskarsa,idanunsa suka kai kan dan qaramin frame dake dauke da hoton shaheeda,sai ya qarasa wajen ya duqa "Why did you go and leave me?" Ya furta a hankali yana kai hannunsa saman fuskarta dake qunshe da faffadan murmushin nan nata me sanyi,sai ya miqe da sauri da nufin yiwa zuciya da harshensa linzami,ya kuma ja da baya yana fadin "Astagfirullah wa'atubu ilaika" yaqi yake da kansa ba tare da sanin kowa ba,bayason maida hannun agogo baya,bayason wannan mode din da yake zama out of sense,yanaso yayi nisa dashi,sai kawai ya fidda wayarsa ya duba cave mafi kusa dasu ya kirasu suzo su fiddashi,kayan jikinsa ya fidda ya sauya wasu ya jefa wayarsa a aljihu ya fito,jabir na zaune anan yana ta duba tarin saqonnin mutanensu,baice masa komai ba yadai bishi da kallo gami da tabe baki har ya fita. Cikin mota kwanyarsa ta cake sosai,neman dukka hanyoyin da zai kaucema wannan auren yake,ana tsaka da wannan kiran wayar dr marwan abbi ya shigo wayarsa. Sai daya sauke gauron numfashi sannan ya daga wayar,sallamarsa kawai dr ya amsa ya hau balbaleshi da fada,ta inda yake shiga ba ta na yake fita ba,maganarsa ta qarshe itace "Duk abinda kakeyi ka barshi,kada ka sake jabiru ya baro turkey ba tare da kai ba,ka biyoshi ku dawo gida" daga haka dr ya kashe wayar. Hannunsa guda daya ya sanya yana yamutsa sumar sa gami da kallon yadda suke wuce titi bayan ya sulalar da wayar gefansa,jin abun yake kamar mafarki,duk inda bacin rai yake ransa yakai nan wajen baci,zuciyarsa ta gaya masa jabir ne ya shaidawa abbi abinda yace "I will deal with you jabir,definitely" ya fada cikin huci kamar jabir din yana kusa dashi. ********Kwanansa uku cur bai dawo gidan ba tun ranar daya fita,jabir yayi kiran yayi kiran har ya gaji,gashi dai kiran yana shiga,amma sai ja'afar din yayi rejecting,daga bisani jabir ya daina baiwa kansa wahala ya dakata da kiran nasa,don yasan tabbas a yanzun bazai daga ba,bazai kuma saurareshi ba. A rana ta hudu ya iso gidan,tunda yayi knocking sau uku ya tabbatar jabir din baya nan,sai ya sanya key dinsa samfurin katin cirar kudi na atm ya bude qofar ya shiga. Sai daya kunna qwai haske ya gauraye falon sannan ya wuce dakin baccinsa,yana tura qofar idanunsa suka sauka kan hoton shaheeda,sai yaji kamar ya jima bai kalli hoton nata ba,don haka ya qarasa a hankali,ya zauna gefan gadon nasa,sannan ya dauki frame din hoton. Yadan dauki wasu sakanni yana kallon fuskarta,kafin ya ajjiye frame din bayan yayi kissing hoton,ya kuma karanta mata addu'a cikin ranta kamar yadda ya saba. System dinsa ya dauko hade da charger dinta ya fito daga dakin,don dama kusan itace ummul'aba'isin dawowarsa gidan,sai kuma ya koma da baya,saboda tunawa da yayi da maganar da sukayi da abbi,ya buda wardrobe dinsa ya ciro passport dinsa ya sanya a aljihunsa ya dawo falon,ya jona caji a system din ya kunnata sannan ya wuce kitchen, fridge ya bude yana laluben abun sha,duk ya gama bulayin sa daga sama zuwa qasan fridge din amma baiga drink din da yayi masa ba. Wani mix fruit ya dauka,saidai yana gama karanta rubutun jiki yaja tsaki ya maidashi,a qa'ida shan abun sha na kwalba gwangwani ko roba basu dameshi ba,yafison abun sha irin namu da gargajiya da za'a hada a gida,kamar kunun aya zobo da sauransu,daga qarshe ya dauki wani matstsen ruwan lemon zaqi hade da cup ya dawo falon. Bai jima da fara aikin ba jabir ya iso,daga sallamar sa daya amsa bai sake bi ta kansa ba,shima jabirun sai ya shareshi,saboda ha fuskanci abun sai 'yar tursasawa kadan ta shigo ciki,dole sai an ma ja'afar haka idan anaso rayuwarsa ta dai daita nan kusa,don haka shima sai ya wuce daki abinsa. Sai da yayo wanka ya canza kaya sannan ya dawo falon,saman hannun kujerar dake daura da ja'afar din ya zauna yana fadin "Ka gama yajin kenan kayo bikon kanka da kanka" maimakon ya amsa masa,sai kawai ya ciro passport dinsa ya cillawa jabir din. Bin passport din yayi da kallo,kafin ya sanya hannu ya dauka ya soma budewa yana dubawa. Idanu jabir ya fidda waje sannan ya dorasu saman ja'afar din "Over stay?" Kamar bazai amsa shi ba,sai kuma yace "Yes" a daqile yana ci gaba da concentrating kan aikinsa,ajiyar zuciya jabir ya fitar yana daga passport din daga fuskarsa "Ya Allah,why ja'afar?,kasan visa dinka ya qare amma kaci gaba da zama musu a qasa baka biya anyi expanding maka ita ba?ka sani turkey ba kamar kowacce irin qasa bace, you know how people suffer before they get the visa....shine ka samu suna baka whenever you need zakayi wasa da damarka?" "I don't like noises please,idan zakayi abinda ya dace kayi,if not ka ajjiyemin passport dina ka qara gaba ka barni naci gaba da zama,dama ban shirya tafiyar ba" gimtse dariyarsa jabir yayi,ya gano shi sarai,neman duk hanyar da zaya kubucewa komawa yakeyi "Alright,sai kamin transfer abinda za'a kashe ta account dina,kasa dole sai na nema baaba ambassador" ya fada yana bata rai shima hadi da miqewa "Bani dako sisi" ya fada kansa tsaye "Kut!" Jabir ya fada yana fito da ido waje,dariya kuma na masa yawo can qasan ransa,lallai ja'afar din mugun dan rainin wayo ne,recently yaga amount din dake qaramin account dinsa ma,wanda shine baya ajiya kudi mai yawa a ciki,the amount is very huge,kamar yasan me yake tunani,sai ya daga kyawawan idanun nan nashi dake dauke da wani irin sinadari mi qarfi ya zubewa jabir su "I mean bani dako sisin da zan batar don komawata gida,bcoz ban shirya ba" dole dariya ta subucewa jabir,cikin ransa yace "Kayi ka gama,komawa gida dole,mu lafiyarka da hankalinka mukeso,tafi mana kuma komai" "Okay,.....duk naji,but bani zan maka komai ba,you know,dole kaje da kanka,tunda kai mai laifi ne a wajensu yanzu" kamar bazai amsa ba kafin yace "Naji" ciki ciki,kada kai jabir din kawai yayi yana nufar kitchen,cikin ransa yana fadin "Allah ya shirya ja'afar,mai zama dashi sai ya shirya,zuma ga zaqi ga harbi ga kuma ba tsoro" . Abinci ya shiryo musu,ya kuma kawo har nan inda ja'afar din yake,yanata wani ciccijewa da basarwa amma jabir yayi kamar bai gane me yake nufi ba,ya gama daagiyar duka ya sauko suka fara cin abincin. Yadda jabir din yaga yana ci ya tabbatar masa a kwanakin da ya qauracewa gidan bai cin wani abincin kirki,dama can shi din irin mutanen nan ne da ba abincin kowa suke iya ci ba,sau tari sun gwammace su haqura da abincin,sai yaji tausayinsa ya darsar masa a rai,yaji har cikin zuciyarsa yana fatan wannan auren ya zame ma rayuwar ja'afar din wani babban sauyi da kuma ci gaba,suna gamawa kiran amaryarsa ya shigo,don haka ya miqe yabar wajen,jaafar ya bishi da tsaki da kuma harara,ganin yadda yaketa zumudin amsa kiran nata. 😊😊😊😊😊 *_SHIN KINA YIWA KANKI DA JIKINKI TANADIN SABULAN WANKA MASU KYAU MAI DA TSOHUWA YARINYA KO KEMA HAR YANZU DANGWALI YABA KIKE SAWA JIKINKI?_* *_SABULUN DAKE GYARA JIKI DA FUSKA YA MAIDA FATA TAMKAR TA JARIRI SABUWAR HAIHUWA?_* *_SABULUN DA DUK INDA KIKA SHIGA FATARKI ZAKI FITA DABAN DATA SAURAN MATA?,YA MAIDAKI TAMKAR WATA DAN DAREN SHA HUDU?_* *NASAN ZAKIYI TUNANIN A INA ZAKI SAMU WANNAN INGANTACCEN SABULUN?AMSAR ITACE_* *_J-SKIN CARE PRODUCTS (JANNAT SKIN CARE PRODUCTS)_* _SUKE SAMAR DA KALOLIN SABULAI NA KECE RAINI KAMAR HAKA_ Black soap Kiddies Black soap Sugar body scrub Body butter Kojic acid soap Turmeric soap Goat milk soap Honey soap Carrot soap Face and body cream Hair growth oil *_dukka wadan nan kalolin sabulai J-SKIN CARE PRODUCTS sun samar muku dasu bisa farashi dai dai da aljihun kowa_* *_Baya ga haka kuma,wani abun qayatarwar,suna karbar kwangilar yin sabulun cold process ga masu yin biki ko suna_* *Zaku iya dubasu a shafukansu na sada zumunta* *Instgram*:J-skincare products *Tiktok*:jannatskincare *Ko ki tuntubesu kai tsaye ta wannan number wayar* 0813 801 1240 *J-skin care products,DUNIYAR SABULAI MAI DA TSOHUWA YARINYA* 27 *********Sosai maimunatu takejin dadin zama gidan bappa sule,saboda tana samun kulawa qwarai da gaske,ga kuma 'yammatan 'ya'yansa da suke kusan sa'anni da ita,hanne da hauwa,sun fita wayo da kuma gogewa,don inda suke din ba za'a kirashi da karkara ba,maraya ce,jininsu ya hadu sosai saboda kirkinsu da yadda suke nuna mata qauna da janta a jiki,nan da nan shaquwa ta shiga tsakaninsu,abun na yiwa maimunatu dadi,ashe dangi dadi garesu,koda ace batasan dangin mahaifinta ba,amma a qalla samun wadan nan a kusa na dauke mata kewa da fargabar rasa dangin mahaifi da kaso hamsin cikin dari. A lokacin maimunatu ta sake tabbatarwa kanta lallai inna furera shigo shigo babu zurfi tayi musu,a duk sanda tazo gembu ashe nuna musu take komai lafiya lau,sannan maimunatu najin dadin can shi yasa taqi biyota nan ganin dangi,abunda yayi matuqar baiwa maimunatu mamaki,kasancewarta miskila ba kasafai takan buda baki tacewa inna furera zata bita b,saidai ita kanta takan karanci tsantsar yadda maimunatun ke son biyotan,don tasha gwaba mata baqar magana kan cewa duk ta gama nacin da qwallafa ran,wataqila ita da gembu sai idan taje yawon arba'in idan ta haihu gidan buderi,wani lokacin saidai ta sakaye taci kukanta,wani lokacin kuma har hanya take bin inna furera cike da fata da kuma burin zataji tausayinta ta tafi da ita,saidai ko sau daya bata taba sauyawa ba,daga bisani data qara wayo sai ta tattara ta qyale,ta sanyawa ranta dangana da haquri. A sannan maimunatu taga kara ta dangin mahaifiyarta da zumunci,kowa da abinda zai kawo bisa al'adar auren fulani,basu duba cewa DR yace abar komai zai mata ba,cikin qaramin lokaci aka tara mata kayan amfanin kitchen irin nasu kala kala,wanda ba lallai a sameshi a can ba. **********Biki ya rage saura sati guda kacal,tun a lokacin hidima ta balle daga kowanne bangare,gidan dr da kuma gidan minister harda gidansu amarya ga jabir wato fatima,saidai hidimar da ake gidan minister zata baka mamaki,kai kace bikin yara shida za'ayi ba yarinya daya ba,tun a kwanaki bakwai din da sukayi saura gidan ya fara karbar baki. *********Katafaren beauty parlor ne,wanda aka tanadeshi musamman saboda gyaran jiki,turara jiki,fidda duk wata dauda,tada komada da maida tsohuwa yarinya a zamanance,waje ne na wane da wane,waje ne na idan ka isa ka shiga. Daga cikin wajen fira ce ke tashi,da alama mata an hadu,kuma an samu abunda ake buqata,qawayen amarya samha ne,kowacce da abinda ake mata a wajen,wasu gyaran manicure and pedicure,wasu gyaran gashi,wasu kuma lalle ake zana musu,yayin da wasu kuma ake musu gyaran fuskarsu don su sake kyan gani a wajen bikin. Gefe guda amarya unaisa ce cikin wata irin riga data lullube jikinta da ita,sai kanta kawai ake gani,hayaqi dake cike da qamshi ne yake futowa daga wuyanta,magana suke qasa qasa ita da wata matashiya kamarta dake gefanta,wanda hayaniyar da sauran keyi yasa ba zaka iya jin me suke fada din sosai ba saika matsa kusa dasu "Na samu information.....jibi zai dawo nigeria" "Na rasa wanne irin so kike masa samiha,ta ya zaki auri mutumin dako zance bai taba zuwa wajenki ba bare ayi maganar so?" Murmushi ta saki tana girgiza kai "Ba zaki gane ba husna,ja'afar na daban ne,irinsa ba'a jiran sai sunzo zance kafin su cancanta a auresu,na musamman ne shi,sabodashi naqi aure har sai da na samu cikar burina ta hanyar daddy,na nace duk da yayi aure,har Allah ya qaddara rabona ne,matarsa da yake matuqar so ta rasu,saboda shi naqi auren unais naqi auren ahmad naqi auren hanif ke da duk wanda kika sani" kai husna ta jinjina "Amma wanne qwarin gwiwa kk dashi na cewa zai soki?,da har zaki auri mijin matacciya wanda yake cikin halin SO BAYAN RAI?" Murmushi ta sake saki "Karkiji komai,duk abinda kk so baka gajiya dashi,soyayyar da nake masa ita zata ja mana ragama,i will do all my best naga ya soni,kada ki manta,ni ba qaramar mace bace,na hada komai da kowanne namiji zaiyi sha'awa ya kuma burgeshi" "But kin manta kina da kishiya kenan" murmushin dake nuna hankalinta a kwance yake ta saki "Kusan hakan gaskiya,yarinya ce qarama wadda ta fito daga ruga,kinga yaushe zata tsoratani?,beside ma kuma itama hadi ne,rigima ce irin ta kakanni kawai,abun ma dariya yake ban idan na tuna,namiji irin ja'afar da wannan a matsayin mata idan banda rigimar tsofaffi?very classy guy,har na fara imagining yadda zai fatattaketa wlh a kurkusa duk sanda suka fara haduwa da ita" ta qarashe fada tana sakin dariya,don ta tabbata abinda zai biyo baya kenan,wannan shine yaqini bisa hasashenta. Ita kanta husna data hasaso ja'afar din,ta kuma san wayeshi da yadda yake,sai taji hasashen unaisan haka yake,'yar ruga?,ba shakka kam bazai iya zama da ita ba,kamar yadda tayi amanna ba zata iya goga kishi da kyakkyawa kuma me aji irin qawarta unaisa diyar minister ba. _ba'asan maci tuwo ba sai miya ta qare,muje zuwa_ **********Ƙarfe hudu na rana agogon turkey,biyu na rana agogon nigeria jirgin Turkish airline ya sauka a filin sauka da tashin jirage na malam aminu kano,dauke da tarin passengers,ciki harda jabir usma khalid akko da ja'afar marwan khalid akko. Dukkansu sanye suke da wasu lafiyayyun Italian suit,kalolin da suka dace da gayu aji da kuma kyansu,duk wanda ya kallesu sai ya maida kansa ya dada kallonsu,zaratan fulanin samari guda biyu,wadanda ilimi hutu da kuma kudi ya ratsa kowannensu,jikoki kuma jinin khalidu akko. Zaman jiran jirgin da zai tashi zuwa gombe sukayi,wanda duka duka bai wuce awa guda ba suka daga zuwa gomben. Ta gefan idanu jabir yaketa karantar ja'afar tunda suka sauka a qasar,fuskarsa kadaran kadaham take,babu walwala hakanan ba wata fara'a bace saman fuskar tasa ba,hannunaa guda daya yana soke a aljihunsa,har zuwa sanda suke nufar motar da tazo daga gidan Dr marwan domin kaisu gida. Muslimu driver din abbi shine yazo daukansu,cikin wata baqar range Rover,ko ba'a gaya maka kasan cewa sabuwa ce,sai qyalli take da daukan idanu,jabir yayi tsammanin samun masu tarbarsu bayan muslimun da zai tuqa su,saidai babu kowa saishi din,sai ya alaqanta hakan da shakkar ja'afar da sukeyi,don ba kasafai ko a baya zasuyi tafiya tare a samu masu tarbarsu ba. Cikin matuqar girmamawa da jin dadin dawowarsu muslimu ya gaidasu,sannan ya sanya jakankunansu a mota,ya shiga ya tada motar suka dauki hanya. Tunda suka hau hanyar idanunsa na bisa titunansu,yana qiyasta watanni da ya share bashi qasarsa,watanni ne masu dan dama,dashi kansa baisan gudun da suke ba sai yanzu. Tazarar dake tsakanin gidan dr marwan akko da airport din ba mai yawa bace,dalilin da yasa basu dauki wani lokaci mai tsaho ba suka isa gidan. Bin ginin gidan nasu yake da kallo kamar wanda a yau yafara arba dashi,ba komai yake kallo ba sai sabon fenti da yaga anbi gidan dashi duk da girma da fadinsa,cikin qanqanin lokaci yaji zuciyarsa na masa qunci,da gaske shirin bikin suke kenan,sai ya dauke kansa daga inda yake kallo din,ya sanya hannu ya bude murfin motar ya fito ya biyo bayan jabir. Tun a harabar gidan tarin ma'aikata dake aiki a qarqashin gidan suka fara musu maraba,kusan da jabir ya barsu,dama shike da wannan juriyar,ya sanya kansa zuwa cikin gidan,a yau din da yake a cikin gidan,sai yaji wani irin kewa da zumudi mai yawan gaske nason ganin mahaifiyarsa ita da gudan jininsa amna,baisan yayi kewarsu kamar hauka ba sai yanzu da yake a kusa dasu. Da tattausar muryarsa mai zurfin nan yayi sallama cikin falon nasa,haj aishatu dake nutse saman kujerun alfarma da aka yiwa falon nata qawanya dasu ta daga kanta daga duban farar takardar dake dauke da rubutu a hannunta tana amsa sallamar tasa,idanunsu suka gauraya da juna,ta saki boyayyar ajiyar zuciya mai nauyi "Alhmadlh ya rabb" ta fada can qasan zuciyarta,sai ta dubi matar da suke tare "Ki shiga ciki kice ina samra?,ta baki waje kici abinci,zan kiraki mintuna kadan" miqewa tayi tana godiya,sannan tabi hanyar da zata sadata da farfajiyar sassan haj aishatun da take kamae qaramin tsakar gida mai siffar garden da aka wadata da wasu fararen duwatsu na wuta. Ci gaba yayi da takowa cikin falon,yayin da amma wannan karon tayi qoqarin ajjiye kunyar dake tsakaninsu "Maraba lale,ashe kuna gab da isowa?" Wani dan qaramin miskilin murmushi ya subuce masa,ya qaraso gabanta ya zube ya soma gaisheta,tana amsa masa itama cikin kulawa tare da karantar yanayinsa. Baiyi wata qiba ba sam,saidai jikinsa a murje yake kadan,sai kuma fatarsa data sakw fresh da kuma haske,alamin weather din qasar data karbeshi,akwai maganganu masu tarin yawa dake ran amma,saidai a yanzun kamar yayi wuri tace komai,don haka ta barwa lokaci na gaba idan suka gama warwarewa daga gajiyar tafiya. Yadda ja'afar ya zube mata haka jabir,don marabarsa da ja'afar din daukan cikinsa ne na tsahon wata tara ne kawai batayi ba. Kusan shi ya fara fita yabar jabiru da amma,wanda dama koda a baya abun kusan haka yake,hirarsu da amman bata qarewa,zaka sauka jabir ya haifa ba ja'afar ba. Yana fitowa sukayi kacibus da ammi,kana kallonta kasan an fara shiga hidima,daga boys quarters na gidan take,taje ta duba yadda aka gyara gami da tsara wajen saboda saukar baqi 'yan biki. "Oyoyo,saukar yaushe?,ina ta ciki ban jiku ba?" Murmushin gefan baki yayi,ya gaidata itama a girmame kamar yadda suka saba "Me zakuci?,don gidan gaba daya a hargitse yake,banjin zaku samu kalar abincin da kuke so" "Ki turo mana hisham kawai ammi" muryar jabir dake tahowa daga baya ta bata amsa,don yasan halim ja'afar din sarai,tsaf zai iya cewa "We are okay" bayan shi magana ta gaskiya yunwa yakeji "Banajin zaku samu hisham cikin gidan nan jabir,gidan yau kusan babu kowa sai baqi,yana can hidimar saukar nasu baqin" "Ba damuwa zan kirashi" jabir ya fada suka soma gaisawa sannan shima yabi bayan ja'afar wanda ya wuce sassan anni,ammi tayi gaba tana tunanin abinda zata sa a samar musu me dan sauqi da zasu iya ci. Sanda ya sanya kai falon har yayi kamar zai koma saboda muryoyin baqi da yaji sai kuma yaci gaba da cusa kai,sai daya shiga din sannan ya fuskanci su waye a falon,anty maama ce,sai ummi badi'a matar uncle abbas. Qaramin tsaki yaja qasan ransa,su kadai amma sun cika falon da hayaniya kamar mutum dubu,dukkansu maraba suke masa banda anni da taja bakinta ta tsuke,ya qaraso ya zauna saman hannun kujera yana amsa marabarsu,kafin dukansu su biyun su miqe anty maama tana cewa "Anni bari muje,nan da awa biyu idan bamu dawo ba don Allah hayatu ko muslimu suje su debomin yaran nan" "Zan gaya musu,amma kada kuje ku zauna kuma" "Muna samo abinda mukeso zamu dawo" "Allah ya tsare" suka amsa suna ficewa,sai falon ya rage saura shi da annin. "Barka da warhaka" ya fada cikin rusunawa "Barkan ka" ta bashi amsa a taqaice tana bata fuska,saidai a yau din baiji bata fuskarta ya dameshi ba kamar yadda suke da ita a baya,yana jin a wannan bigiren shi yafi cancanta ya bata fuska akan kowa "Ina wuni?" "Daban wuni ba zaka ganni?,ai da zamanka kayi a sassanka,ni yafi cancanta nazo na gaisheka ai,tunda yanzu ka zama uban kowa,sai abinda kakeso ka tsara zamu dinga bi,tunda kaika haifi kanka" kyawawan idanunsa ya lumshe kana ya budesu,ita tsohuwar batasan abinda yakeji bane?,batasan irin qunci da ciwon data haddasa masa ba haka siddan yana zaman zamansa yana lallaba rayuwarsa? Muryoyin sallamarsu ta katse anni daga ruwan tijarar data debo ta shirya sauke masa su tas yau a kansa,duka 'yammatan gidan ne suka shigo,wansa dawowarsu kenan daga gyaran gashi. Da hayaniya suka shigo saboda yadda sabgogin bikin suka fara musu dadi,amma suna hada idanu kowacce sai tayi turus,ta kuma saita bakinta,kudin goro ya yiwa gaisuwarsu ya amsa su gaba daya,babu wadda tayi gigin zama dukka suka juya suna barin sashen,daidai lokacin da amna wadda aka yiwa kanta gyara na musamman take rugowa cikin falon riqe da leda a hannunta cike da kayan qwalam tana qwalawa anni kira gami da cewa tazo suci. Cak ta tsaya sanda tayi idanu hudu da mahaifin nata,sai kuma ta watsar da ledar hannun nata,ta take da gudu tayo wajensa tana kiran "Dadddyyyyy...." Qasa ya sauko ya tanqwashe qafafunsa,ya kuma bude mata hannayensa gaba daya,yana jin wata irin qauna da qarfin jini dake tsakanin uba da diyarsa yana fusgarsa,ta kuwa iso ta fada jikinsa,ya sanya hannayensa gaba daya ya rungumeta cikin jikinsa yana sauke ajiyar zuciyaSosai ta qanqameshi itama kamar zata koma jikinsa "Daddy" ta sake kira tana sauke ajiyar zuciya bayan shuru da tayi na wasu sakanni,dukka gaba dayansu shida annin sai tausayinta ya lullubesu,ya dagata sosai ya sake tallafarta yana dubanta "Amnee" ya kirata da sunan da shaheeda kadai take kiranta da shi "Daddy....kaima shine ka tafi ka barni?,mommy ta tafi,amra ta tafi,kaima haka?" Kai ya girgiza yana shafa sumarta da tasha gyara tana ta qyalli "Am sorry my little angel......daddy yana neman afuwa,bazai sake tafiya ya barki ba" fuskarta ta washe sosai,da alama taji dadin maganarsa,sai kuma ta sake cune fuska "Adda maimoon ma ta tafi,har yanzu bata dawo ba,daddy zaka je ka dauko min ita?" Anni ya kalla da alama yana da buqatar qarin bayanin sanin wacece ita,kamar kuma ya jijji sunan a bakin annin da ammansa,ganin anni bata bashi wani hint da zai gane wacece ba sai ya gyada kai kawai "Zan dauko miki ita lil princess" qanqameshi tayi tana murna "I love you daddy" "Love you more amne na" sai ta shige jikinsa tana sauke ajiyar zuciya dake nuni da samun cikakkiyar nutsuwa. Karamin tsaki anni ta sake "Kalli.....wannan daukar hakkin har ina?,Allah ya kyauta wannan banzar zuciyar taka data kasa daukan kalar tata qaddarar" bai tankawa annin ba,don yasan jiqaqqiya ce tsakaninsa da annin,kuma ba zata qyaleshi ba tabbas sai ta maida masa kai tsaye ko kuma a fakaice. Koda ya tashi tafiya qin yarda amna tayi ta sauka daga jikinsa,tana maqale dashi,da ita yatafi sassansa,ya samu.jabir har ya fito a wanka,yanata fama da wayoyin al'umma. *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 28 Wani kallo ja'afar ya watsa masa,da alama gayyar al'umma yayo musu,wanda shi baisan da hakan ba,bai kuma shiryama tarbar kowa ba,dakinsa ya wuce ya sauke amna saman gadonsa,tana ta faman zuba masa surutu,labarai iri iri,a lokacin idan kaganshi kai baka ce miskilin ja'afar din nan bane,mai yawan dakiya tsare gida da kuma shan qamshi,duk yabi ya cika fuskarsa da fara'a,hakanan duk tambayar da amna tayi masa sai ya bata amsa,saidai da yake halin a jininsa yake,ba jimawa yaji kansa ya fara cakewa da surutun amnan "Amnee.....pls be quiet for a while,ki huta kada maqogoronki yayi ciwo,zanyi wanka,idan na fito then sai muci gaba" kai ta gyada masa,sai dai tun bai gama fidda kayan jikinsa ba taci gaba daga inda ta tsaya. Yana daga toilet din ma yana saurarenta,murmushi kawai ya saki ya girgiza kai "Surutun waye tayi haka?,shaheeda?,nooo....shaheeda nada hira,amma bata da surutu me yawa,salma?,laila?,hafsah?,maybe ya amsawa kansa da kansa yana tabe baki. Sanda ya fito ya taddata da jabir,da yake shi din sarkin yara ne ya biye mata sosai sunata sabgarsu,sai ya juya ya buda walking wardrobe dinsa ya shiga yana duba kayan da zai saka,kafin ya futo sun fita,sai ya fasa shirin fitar da yayi niyya,ya saka boxer dinsa kawai ba tare daya nema ko singlet ba,turarukansa ya fesa,sannan ya shafe lallausan baqin gashin dake cike aqirjinsa wani irin azababben oil perfume,yabi lafiyar gadonsa ya kwanta,bayan ya ragewa dakin haske ta hanyar sauke duka labulayen dakin,ya kuma kashe duka fitilun dakin. Bacci yayi sosai mai wani irin nauyi da dadi wanda ya jima baiyi irinsa ba,knocking da ya dinga ji sama sama cikin barcinsa ya sanyashi bude kyawawan idanunsa da suka qara girma saboda bacci,yadan mutstsukasu kadan,sannan ya ture lallausan duvet din daya rufe jikinsa dashi,ya zuro qafafunsa qasa yana miqewa,ya isa qofar ya bude. Jabir ne dauke da amna,kwalliyar jikinsa ta bambanta data dazun "Wanne irin bacci kake?,ko a masallaci ban ganka ba" "What?" Ya fada calmly,ya aza idanunsa ga agogo,sai yaga har bakwai tayi,a hanzarce ya saki handle din qofar ya shige toilet don ya daura alwala. "Na shirya zan fita mukaci karo da abbi yana dawowa,yace na gaya maka yanason ganinmu after isha prayer" kai kawai ya gyada masa,yana budewa amna hannunsa,ta taho da hanzari tana ci gaba da zuba masa surutunta,tare da bashi labarin inda sukaje dazun,sai jabir ya miqe ya fita ya basu waje. Yana shirin fita sallar isha din hisham ya shigo,cikin girmamawa ya gaidashi,ya amsa masa yana sanya qaramar hular tashi ka fiya naci saman sumarsa "Ina kaje duka yau?" Kansa yadan shafa "Ina da patient ne yau a asibiti da yawa da zan gani,so bayan kuma na gama dasu na wuce wajen gidan yaa jabir,na sallami companyn da suka zuba home decor na gidan" kansa ya gyada kawai,hisham din ya daukar masa abun sallah suka fito zuwa masallacin suna taba hira kadan kadan. Sai daya sake komawa ya duba ammansa,sannan ya wuce sassan anni,ya nema abinci wajen baba tabawa,wadda dama tun da can gurinta ko wajen ammansa yake cin abinci duk gidan,to sassan amman nasa yaga ya soma cinkoso,bazai iya tsayawa karbar komai na sassan ba,don bashi da tabbacin amman itace ta girka duk abinda za'a bashin. Yana ankare da yadda annin keta faman cin magani,sai shima ya basar kamar bai gani ba,ya zauna sosai hankali kwance yana cin abincinsa,cokali daya bakinsa,cokali daya bakin amna hira,duk tabi ta cikashi da zancen adda maimoon,kome yayi mata sai tace 'haka adda maimoon takemin'. Yana gamawa cikin sa'a yaji shigowa abbi,don haka ya miqe yana dauke da amna "Kaje ka dawo,kazo muyi lissafin kudin kayan lefen da maama ta ranta maka ka zube mata abunta" "lefe?,lefen wa?" "Au da tattabaru kayi zaton za'a aura maka?,ko kuma babyn roba na wasan yara?,'ya'ya ne kamar kowa masu gata,ehe" anni ta maida masa amsa sannan ta fuske,sai kawai ya juya baice da ita komai ba ya fice,yana jin haushi yana sake cika masa zuciya. Da sallama ya shiga katafaren falon dr marwan khalid akko,can ya hangesu saman dining shi da jabiru,da alama zamansu kenan,yayi masa izinin ya qaraso,yana jawo kujerar sake daura dashi hadi da nuna amna yace ta zauna,tayi daraf kuwa fa haye ta fara masa surutun nata,har sai da ja'afar yace cikin lallausan muryarsa,very calm "Amnee,pls....keep quiet" narai narai tayi da idanunta,don bata gama bawa daddy dr kamar yadda take kiran abbi ba labarin da take bashi,to amma ita kanta duba daya uban nata yake mata take laushi,dole tayi shuru,ta fara saka yatsanta tana dangwalan romon pepper soup din kifi da aka yiwa abbi. A sannan ya samu suka gaisa da abbi din,ya musu maraba,sannan ya tura masa warmers din yace ya diba abinci yaci "Am full abbi,yanzu na gama ci wajen anni" "Yayi kyau" yace yana ci gaba da cin abincinsa,sai dinning din yayi shuru,kasancewar dabi'ar abbi din,ba kasafai yake cin abinci kuma yana magana ba,har sai ya kammala,shurun da ya sanya ja'afar ciro wayarsa,yanajin abbin da jabir suna magana jefi jefi,wanda kusan duka kan tsare tsaren bikinsu ne. "Bismillahi" abbi ya fada yana zama saman kujerun falon,yayin da jabir da kuma ja'afar kowanne yayi matsugunni a qasa "Kai jabir alhmdlh,mun gama duka maganar da zamuyi dakai.....am ja'afar,abinda yasa na kiraka" abbi ya fadi yana gyara zamansa sosai,gami da cire hularsa ya aje gefe "Inason in tambayeka......wacece ta haifeni?" Girma maganar ta yiwa ja'afar sosai,har sai daya dago suka hada ido da abbi,kana ya maida idanunsa qasa "Anni ce abbi" "Ma sha Allah,to ban sani ba,ko ka manta ne,dani da umar da sagir da abbas da usman.....dukkaninmu anni ce ta haifemu,kuma qarqashin ikonta muke damu da dukka abinda muka mallaka,ba zanyi magana me tsaho ba,saboda nasan kasan matsayinta a wajenmu,hatta da mahaifiyarka zabin anni ce idan baki sani ba,shi yasa ta zamto ta musamman a wajena,na kuma yi dacen da maza dubu basuyi ba,dukka hukuncin da anni ta yanke a kanka yatabbata,kuma ba komai bane ya janyo hakan ba ina da.imanin qauna ce da kuma damuwa da halin da kake ciki,Allah yayi maka wata iriyar zuciya data banbamta data kowa,amma ka sani,jajircewa da karbar al'amura a yadda sukazo suna iya kawo sauyi,hakanan lokaci yana iya warkar da kowanne irin ciwo komai girmansa,duk wani abu da zakayi a yanzu akan aurenka shizai nuna dai dai matsayin anni a wajeka,idan ka wulaqantata ko ka watsa mata qasa a idanu to ni ubanka marwan ka yiwa haka,idan ka karba abun da kima da mutunci,ka kuma riqeshi da daraja to ni ubanka marwanu ka mutunta,saboda haka zabi ya rage naka,dan halak dai shike rama halacci,anni kuwa halacci tayi maka ba butulci ba,zanga dame zaka sakawa mahaifiyata". Maganganu ne gajeru marasa dogon zango,saidai nauyinsu yafi qarfin wani ma'auni ya iya gwadasu,shigen shigen magana irin wannan bata taba hadashi da mahaifinsa ba sai a wannan karon,nauyin maganganun da har dr ta sallamesu basu bar dukan sassan jikinsa ba,har sun kusa fita ya sake kiransa "Ka shirya daga yau zuwa gobe,kaje gidan minister ka gana da unaisa" "Unisa?" Ya fada cikin ransa,yana jin he knew the owner of the name UNAISA,to amma a ina?, somewhere..... somewhere,for sure,indai gidan minister ne,bu he may not remember ainihin inda yasan ta din. Dukka wannan shi da zuciyarsa yake wannan tadin,wanda tuni ya riga yace da abbi "To" yabi kuma bayan jabir sun fice. "Ya?,yau din zamu wuce?,don inason naje naga fatima gaskiya,i missed her badly" yana jin iya maganarsa ta yau ta qare,so saboda haka bashi da abinda zai cewa jabir din,saidai ya masa wani kallo,yana shirin yi gaba jabir din yasha gabanshi "Shawara guda daya J.pls and pls,kayi qoqarin bin maganar abbi,indai har kai din masoyin shaheeda ne da gaske,na tabbatar da tana raye itace mutum ta farko da zata fara tursasaka kabi abinda dukka magabatanka suke so,for the first and last time may be da sukeso kayi musu wani abu cikin rayuwarka,we will see if you can do it" jabir yakai qarshen maganar yana duba yanayin ja'afar,duk da cewa ya bashi baya,kamar yadda ya zata din,baice masa komai ba sai gaba da yayi ya barshi a wajen. Sassansu ya yanke ya koma kawai,saboda kansa gaba daya ya gama daukan zafi,tako.ina abbi ya gama daureshi,tun jabir baice komai ba dama ya riga daya yankema ransa dole ya tsaya ya fuskanci komai,zaiyi duk yadda abbi da anni keso for the sake of them. Ya jima a haka kafin yayi qoqarin dai daita nutsuwarsa,ya daga waya ya turama hisham tex kan ya kawo masa amna,ba jimawa sai gashi da ita,ya dire masa ita ya juya. Jaka guda ta kayan wasan daya jima yana siya ya tura mata,duk sanda ya fita yaga wani abun wasa saiya tuna da ita,sai kuma ya siya ya ajjiye,murna ta ishi amna,ta dauki wancan ta ajjiye,ta dauko wannan ta ajjiye,komai sai data nuna masa,kamar ba shi ya siyo ba. A gaba ya sanyata yana kallo kawai,iya wannan farincikin nasa ya sauke kaso mai yawa daga cikin nashi bacin ran,abu na qarshe da yarinyar ta fada shi ya tashi zaman nasu,ya kuma dawo da mutuwar shaheeda da twin sister dinta amra danya a ransu duka su biyun,kewa da maraicin shaheedan ya kamasu "Daddy.....mommy taqi dawowa,taqi kawomin amra muyi wasa,daddy yaushe zasu dawo?,zanyi fushi fa daddy" cikin jikinsa ya rungumeta,yana shafan gadon bayanta "Kada kiyi fushi,kita musu addu'a kinji?,zamu hadu dasu in sha Allah sooner or later"ya fada yana qoqarin hadiye wani abu mai tauri daya tsaya masa a wuya. Ta jima a haka kwance a jikinsa,yana jin yanayin saukar numfashinta da yadda ta qara nauyi a jikinsa ya tabbatar tayi bacci,sai ya miqe sabe da ita,daya hannun nasa kuma yana riqe da jakar kayan wasanta yayi sassan ammansa da ita. Yana shiga tana shigowa itama falon daga ainihin qofar baya na sassan nata da zata sadaka da masaukin baqi na gidan,ita da masu aikinta su biyu,lili da laraba,suna dauke da jibga jibgan duvet da ana fiddosu yawanci a lokacin taro irin wannan musamman saboda baqin. Jikinta sanye da Egyptian hijab daya saukar mata har qasa,duk da dare ne amma akwai eye glasses tare da ita,wanda takanyi amfani dashi lokaci lokaci idan taji bata jin dadin idanuwanta. "Karbeta lili,ki kaimin ita dakina,idan kin shiga ki rage qarfin acn nan,don naji kaman mura nason kamata" a ladabce ta amsa,ta dauki amna da ja'afar ya shimfide mata saman kujera ta wuce ciki "Manya" ta kirayeshi da sunan da takan kirashi dashi don ba kasafai zakaji ta kirayi sunan nasa kai tsaye ba "Zauna muyi magana" kamar yadda ta umarceshi haka yayi,ya koma ya zauna din yana bata hankalinsa "Kayimin wata alfarma man" sosai yake duban amman tasa,abinda yasa ta fahimci tambaya yakeson yi kan alfarmar data ambata "Don Allah na roqeka,ka daure ka karba qaddararka a duk yadda tazo maka,kada kayi wani abu da kasan cewa ba dai dai bane,ka riqe amanar da aka baka bisa gaskiya da na sanka da ita,don Allah" "Ku daina roqata hakanan amma,kunfi qarfin haka a wajena" ya amsa mata yana bata assurance din haka ta cikin qwayar idanunsa,ta san yana da qoqarin bin umarnin na sama dashi daman,saidai sanin halinsa yasanya mata shakku kadan,amma a yanzun hankalinta ya gama kwanciya gaba daya "Allah yayi ma rayuwarku albarka,shikenan sai da safe" A daren gaba daya ya gama lissafa yadda zai tafi da komai,yadda zaibi umarnin mahaifansa ta gefe guda ba tare da rayukansu sun baci ba,hakanan ba tare kuma da matan da aketa qoqarin liqa masa sun dameshi ba,don haka a washegari bayan ya shirya ya fito,ya nema ma'aikata daga cikin kamfaninsa,ya tsara musu abinda yakeso. Cikin gidaje hudu da yake dasu ya zaba daya,wanda yake dan nesa kadan da nasu gidan,yasa aka hau aikinsa baji babu gani,don dama gidan kusan an gama komai nasa,fenti da saka qwayaye da sauran kayan qawata gidanne kadai ya rage,abinda yasa yayi saurin yin hakan,don bayason abbi ko anni wani yace su zauna a ainihin gidansa dakegovernment house road,don yafi kusa da nan gidan nasu,gidane iya gida,wanda ya amsa sunansa,kuma ya ginashi ne musamman a sannan saboda shaheeda,a sanda ta haifa masa twins,ya zuba musu komai da komai,sanda zasu tashi zuwa gidan suturar jikinsu kawai suka dauka,kuma ko bayan rasuwar shaheedan babu abinda ya bari aka taba cikin gidan,hatta da suturarta,da anyi maganan kwasan wani abun sai a rasa kansa,sai aka yanke shawarar a jinkirta ko yana kan tsinin zafin mutuwar ne,saidai har kwanan gobe komai yana nan a muhallinsa,a baya cikin gidan yake rayuwarsa,saidai yadda yake dada komawa yasa anni ta yanke shawarar ya tattaro ya dawo gida cikin jama'a,a kulle wancan gidan ko za'a samu sauqin wasu al'amuran,an dan samu din,saidai babu abinda ya canza shaheeda daga zuciyarsa har kwanan gobe ita da amransa *SO BAYAN RAI* Gidan daya zaba din gida ne sama dake da babbar haraba da zata iya daukan motoci goma,akwai balcony da zaka shiga wanda yake dauke da babban falo,hagu da dama na bangon falon qofofi ne guda biyu,kowacce qofa akwai babban falo hade da bedroom a cikinsa, kitchen daya ne wanda yake falon,saidai babba ne,babu wanda zai takura wani,hakanan side biyu gareshi,a falon akwai stairs da aka qawata da wasu irin makarai masu kyau,marbles ne zube har zuwa saman,inda zai sadaka shima da falo babba ne dakuna guda uku ne a saman kowanne manne da toilets dinsa,sai wani balcony din daga sama wanda zai baka daman ganin ainihin harabar gidan fetal,a qasan akwai spare din daki guda daya,sai dakunan baqi maza da na me gadi daga can wajen gidan. Gidan yana da girma,don kowanne daki da falo babbane qwarai,hakanan yadda aka tsara ginin ya bada sha:awa ainun,saidai jabir da ya gani yaga gazawar ja:afar din,a matsayin da Allah ya bashi,duba da gidan da zai dauko unaisa "Idan gidan bai mata ba saita fasa dani ta zaba wani fine,iya abinda zan iya kenan" ya gayawa jabir,kamar shine unaisan. Duka kudin anty maama na lefe ya tura mata abinta ba tare daya sake wani musu ba,hakanan dukka wata zirga zirga ta samarwa da baqinsu masauki tare dashi aka yita,saidai sau tari har suje su dawo ba zakaji yace kanzil ba,lokutta mafi yawa wayarsa na a hannunsa ne,cikin abokansu guda biyun da suketa zirga zirgan tare babu wanda ya kawo komai ransa,saboda sunsan wayeshi,captain j din haka nan dabi'arsa take sun sani tun ba yau ba,magana ko surutu shine assignment mai wahalar cinyewa da zaka hadashi dashi. Sai daya qara kwana biyu sannan ya samu ya sukunin saka time na zuwanshi gidansu unaisa kamar yadda abbi yayi masa umarni,ganin yadda yake shiga cikin sabgogin yasa abbi bai tanka masa,don yana ganin sauyi muraran da kuma qoqarin bin umarni daga wajen ja'afar din. A ranar yayi zamanshi a sassansu kamar bashi da plan na zuwa ko ina,tab ce saman cinyarsa yana duba wasu abubuwa,sanaye yake da bawin boxer wanda ya fidda ainihin qirar tsayayyun qafafunsa dake cike da tarin gargasa,jabir ya turo qofar dakin ya shigo,a shirye tsaf cikin shadda,sai yaja turus ya tsaya "Me zan gani?,J baka duba agogo ne?" "What happened?" Ya tambayeshi a nutse abinsa,kamar ma baisan meke faruwa ba "You are very stubborn manya,me yasa kakeso ayita maimaita magana daya?,just simple instruction amma ka kasa bi" idanu ya watsa masa bayan ya kashe tab din "Yaushe na gaya maka fasa zuwa na?" "Ai banga alama ba" "Kamar?" Ya tambayeshi yana shafa dan qaramin gemun dake manne a habarshi,ya kuma hade da zagayayyen gashin dake kumatunsa zuws qasan hancinsa "Gashi nan kuwa ina gani,you are sitting properly,dafa'an kamar babu inda zaka?" Yatsansa ya sanya yana bin tsahon karan hancinsa daga sama zuwa qasa,ya lumshe idanunsa kana ya budesu yana furzar da iska,sai daya sauke qafafunsa qasa daga samam glass table din da take kai sannan yace "Okay,so kake kazo ka sameni ina ihu guri guri ina announcing ma mutane zanje naga hurul'een ko?" Idanunsa ya lumshe yana sake girgiza kai alamun a'ah "You should remember.....ita din ba kowa bace a wajena face GURBIN IDANUN da ba zasu taba zamowa idanu ba,koda zasu shekara miliyan anan din" daga haka ya miqe a nutse yana ajjiye kayan hannunsa ya nufi toilet "Oho dai,no matter how dolenka kaje,na baka minti ashirin ka taddani falo,idan kuma ka wuce hakan....,basai na qarasa ba" Kusan sai da jabir yayi dana sanin fadin wannan maganar,saboda sai da ja'afar ya ninka ashirin sau uku,don sai daya dauki awa daya cif sannan ya fito,saidai ya dauki kyau iya kyau yadda ya kamata,sanye yake da wani lallausan farin yadi na maza dake da shara shara,takalmin qafarsa baqi ne dan qasar Italy,hular dake kansa tun daga nesa take qyalli kamar farin tangaran,sosai kwalliyar tabi jikinsa,ta kuma dace da yammacin,hatta jabiru sai daya yaba da adon,amma sai ya fake da qorafin dadewa da yayi,bai kulashi ba,saima seat mai zaman banza da yayi zamansa,ya fidda wayarsa yana aikawa wani client dinsu saqonni,ya kuma turawa saubam secretary dinsa saqon ya sameshi a wani eatery goben yanason su tattauna. Cikin wata farar Rolls-Royce ghost v12 mallakin ja'afar din suka fita,suna cillawa saman kwalta jabir ya qarawa motar gudu sosai,bayan ya cikasu da ac kamar yadda suka saba amfani da ita,basa ko ji ga jikinsu. 29 _ZAFAFA BIYAR💯💕_ _ZAFAFAN LITTATTAFAI GUDA BIYAR🤌_ _YAN BIYAR MASU BIYAR DIN:_ _1-DARUSSAN RAYUWA_ _2-FADAKARWA,_ _3-WA'AZANTARWA, 4-NISHADANTARWA_ _5-TSAFTATACCIYAR KAUNA MARAR GAURAYE_ _KADA KU MANTA, YAN BIYAR DIN NA TAFE NE CIKIN TAFIYA TA KARO NA 7, SABON SALON TAFIYAR DATA FI KOWACCE INGANCI DA DIMBIN DARUSSA NA RAYUWAR YAU DA KULLUM_ _KU SHIGO A DAMA DA KU DON JIN ME KE FARUWA ACIKIN LITTAFIN *SANADIN LABARI NA*: NA *HAFSAT RANO*, LALLE AKWAI BABBAN SANADIN DA ZAI WAKANA ACIKIN ZUKATAN BIYU... DON SANIN SU WAYE SAI KU GARZAYO A DAMA DAKU._ _SHIN *BABU SO!!! (MIYA KAWO KISHI?)* NA *BILYN ABDULL* LALLE LAMARIN FA AKWAI GUMURZU. DOMIN TSAFTACEN *SO* SHI KE JANYO ZAZZAFAN KISHI A TSAKANKANIN MASOYA BIYU. KU ZO A CIGABA DA TAFIYA DA KU._ _*NAYAH....(RIBA BIYU)* NA *MAMUH GEE* RAYUWAR AYSHA INAYA NA DAUKE DA WASU SINADARAI NA TACACCIYAR KAUNA. AMMAN WANENE GWARZON DA ZAI SAMU NASARAR CAFKE WANNAN RIBA BIYU? TA KAUNAR INAYAH DA INAYAH DIN KANTA. KU TAHO MU TAFI DA KU A TAFIYAR MU_ _*FARHATAL QALB (FARIN CIKIN ZUCIYA) NA MSS XOXO* FARIN CIKIN ZUCIYA MAGANI NE NA ZUKATAN DA KE CIKIN DAMUWA. LALLE AKWAI NASARAR FARHATAL QALB GA DUK ZUKATAN BIYU DA SUKA TSINCI KAN SU CIKIN BEGEN JUNA . KU ZO MU KARASA WANNAN TAFIYAR DA KU_ _*GURBIN IDO (BA IDO BA NE) NA SAFIYYAH HUGUMA* ... SO BAYAN RAI..... KAUNA CE MARAR YANKEWA DAGA ALLAH. SU WAYE ZASU SAMU NASARAR CIKE GURBIN DA KE IDO? ZUKATA BIYU NE..KU BIYO MU DON GANEWA IDANUN KU CIKEWAR GURBI_ _DUKA WADANNAN LITTAFAI GUDA BIYAR. NA MARUBUTAN ZAFAFA NE WANDA KE YIN SU A YANZU._ _WANNAN TAFIYAR ZAFAFA MA TAZO MUKU DA TSARIN TALLACE TALLACE WADANDA ZAMU KAI MANHAJOJIN MU NA:_ _*FACEBOOK, INSTAGRAM, YOUTUBE, WHATSAPP GROUPS DA STATUSES, TELEGRAM DA MA WATTPAD... MUNADA DIMBIN MASOYA DA KE BIBIYAR MANHAJOJIN SHAFUKAN MU. SU KE KUMA KOKARIN SIYAN DUKKANIN KAYAYYAKIN DA MU KA TALLATA._ _MUNA TALLATA HAJOJIN KU CIKIN FARASHI MAI RAHUSA._ Tafiyar mintuna ita ta sadasu da unguwar cikin gidan minister,sun samu tarba me kyau bayan haj Aaya ta samu sanarwar zuwansu,waje na musamman cikin gidan tasa aka kaisu,sannan tasa aka taso mata unaisa dake barci a sannan,ta fara shiryata da kanta bayan ta sanyata ta sake wanka,cikin wani material na alfarma mai dan banzan kyau da tsada. Karo na biyu ja'afar ya sake duban agogon hannunsa,yayin da yake biye da maganar da jabir din ke masa kan dakunan da aka kamawa baqinsu sunyi kadan,za'a qara wasu da kuma yadda suka tsara event din da za'a gudanar "Komai yayi,amma banda ni a taronku,saboda babu abinda zanje a ciki,walima ce kawai ta zama sunnah,ita dince ma nake tunanin zanje,anma fa babu tabbas itama,kada ka zura jiki da yawa" yayi dukka wannan maganar yana kallon lafiyayyen agogon dake kwance a fatar hannunsa "Time up" yafada yana miqewa tsaye cak,sai jabiru ya bishi da kallo "What do you mean?" Sai daya zuba hannayensa duka cikin aljihun rigarsa yana duban jabir "Mintuna takwas nayi niyyar ware mata a yau din,kuma ta cinyesu wajen jira, you know.....i don't wait for anyone,amma dai na cika maganar abbi tunda nazo" dubansa jabir yake cike da mamakinsa,ja'afar.....ja'afar?. "Amma dai abbi ba cewa yayi ka shigo gidan ka fita ba ko?,cewa yayi kuga juna,ka ganta ne J?" "Na meye sai na ganta?,no need" ya amsa masa yana dage kafadarsa,sai ya juya da zummar takawa yabar wajen,dai dai sanda ta iso,cikin matuqar ado,mutum uku cikin masu aikin gidan na biye da ita da.manyan trays da aka jerawa kayan ciye ciye da shaye shaye. Idanunta a kansa,kamar yadda fuskarta ke baibaye da murmushi "Hello" ta fada tana waving hannayenta,murmushin fuskarta na sake fadada "Welcome our bride" amsar jabir kena data qara ninka farincikin dake zuciyarta "Thank you " ta amsa masa kafin ta sake maida dubanta ga ja'afar wanda har yanxun yake tsaye "am sorry,i keep you waiting ko?" Ta fada tana murmushi,sai ya motsa kafadarsa "Don't mind,ina cika umarni ne" gatsal jabir yaji maganar tayi masa,bai murmure daga wannan ba yaji unaisan na cewa "Have a set please?,kaman maganan zaune tafi ta tsaye" "It's too late......lokacin zamana ya cika,i have a lot to do,see you later" ya fada yana qetareta zai wuce abinsa. Wani abu ne ya tsayawa unaisa a wuya,duka wannan lokacin data bata amma ko na minti uku cikakke bai kasance da ita ba zaice tafiya zaiyi?,uwa uba ma sau daya tak taga ya kalleta ya dauke kai?,tana da tarin.abubuwa masu yawa da takeson su tattauna dashi,don haka batayi qasa a gwiwa ba tabi bayansa tana tsaidashi Cak ya tsayan,sai taji abun ya mata nauyi kasancewarta maje mai bala'in jin kai,sai itama fa tsaya tana duban ingarman bayansa take tsaye sosai tsakanin mayalwatan kafadu dake cike da siffar qarfi da cikakkiyar tsaiwa ta cikakken namiji,a hankali taga ya waiwayo,ya kuma tako zuwa gabanta ya tsaya,tsaiwar da taji ta har tsakiyar kanta,saboda tazarar dake tsakaninsu bata da yawa,uwa kuma wani shegen kwarjini yayi mata,wanda ya mamayeta kota ina,qamshin lallausan turarensa ya ziyarci hancinta,sa'annan kuma hucin fitar numfashinsa data rasa me yasa yake fita da nauyi haka?,bata gane amsar tambayar tata ba sai daya fara magana,ta fuskanci cikin fushi yake,ransa ne ya baci,abinda ya bata tsoro kenan,duk da cewa fuskarsa a murtuke take cike da rashin fara'ar da dama can kowa da ita ya sanshi,to amma wannan bacin ran dake kwance saman fuskarsa bai jima da samoshi ba "Ki kula,ki kuma yi a hankali,banason matsi ko takura,zaifi kyau ki kasance me nisantata akan yunqurin kusantata da kikeyi,stay away from me.....na gaya miki wata gaskiya guda daya wadda babu lallai a samu wanda ya gaya miki ita?" Yayi maganar yana dage girarsa dukka biyun,bata amsa masa ba saboda wani yanayi daya shigeta,shima bai damu ta amsa din ba ya dora mata "Bana buqatar rayuwar kowacce mace da sunan matata a cikin tawa rayuwar,already na rufe wannan babin,idan kin shirya ma kuma kutsa kanki ciki...... it's okay for me" ya qarasa fada yana dage kafadunsa,sai ya juya cikin takun nan nasa mai cike da ginshira yana barin wajen. Ko sau daya batayi yunqurin tsaidashi ba kamar dazun,sai kallo data bishi dashi qirjinta yana dukan uku uku har ya bacewa ganinta,kafin muryar jabir ta katse mata dukka hanzarinta "Are you okay?" Ya tambayeta yanason karantar yanayinta,don baisan me ja'afar yace da itaba,kasancewar akwai tazara tsakaninsu,amma yafi kowa sanin halinsa,tabbas something bad happened,akwai abinda ya gaya mata,saboda yadda fuskarta ta sauya gaba daya ta kuma birkice. Abirkicen ta girgiza kai "Akwai damuwa tabbas" batayi qasa a gwiwa ba ta gaya masa maganganun da sukayi,sosai jabir yaji babu dadi,amma a zahiri sai ya kawar da hakan daga saman fuskarsa "Karki damu,nasan J,a yanzun rashin sabo ne ya kawo yake gaya miki haka, with time zaku saba,zakiga kuma kaman bashi ba" sosai yayi qoqarin gaya mata maganganu masu kwantar da hankali,har sai daya fuskanci ta nutsu sannan ya taka mata gaban main entrance na gidan,sannan ya wuce zuwa inda suka ajjiye motarsu. Hannu yasa ya bude murfin motar idanunsa na sauka kan fuskar ja'afar,wanda ya kwantar da seat din motar ya kuma miqar da bayansa sosai a kai,jin bude motar baisa ya motsa ba,har sai da jabir ya shigo,sannan ya bude kyawawan idanunsa da suka sauya kala a hankali ya watsasu kan fuskar jabir "Kaci sa'a kaine,da saidai kazo ka samu empty din wajen" "Yanzun ma me ya hanaka tafiya?,tunda kazo kayi abinda ranka yakeso?" Ya amsa masa yana dan nuna masa bacin ransa,duk da yasan ja'afar din dole abishi a sannu,saboda wata irin zuciya da yake da ita da bata iya qaramin so ko qi ba,hakanan ba qaramin riqo shaheeda ta yiwa rayuwarsa ba adan tsukin lokacin na zaman da sukayi. Bai sake cewa jabir komai ba,sai dan qaramin tsaki da yaja yana tada seat din ya zauna sosai,tun basuyi nisa ba suna isa wani guri yace jabir din ya saukeshi qofar wani gini,kamar ya tambayeshi me zaiyi sai yaja baki ya qyaleshin,ya saukeshin ya kuma wuce da motar. ***********Dukkan tafukan hannayenta ta buda tans kallon tsakiyarsu,batasan me zata tuna ba,saidai ta samu kwanyarta fayau babu komai tun daga sanda taji ana hargowa sa hayaniyar zuwan al'ummar gombawa,ta dai tsinci kanta da matuqar sanyi da kuma faduwar gaba,wanda tunda aka fara bikin kwana hudu kenan yau cikon na biyat bataji irinsa ba sai yau,tasa ran ganin anni da amnanta cikin matan da suka iso,saidai babu daya cikinsu,kusan dukka baqin fuska ne idan ka cire anty maama wadda ita ta jagoranci tafiyar. Ko ba'a gaya mata ba tasan cewa ayau qaramar hukumar ta gembu ta karbi baquncin manyan mutane irin wanda bata taba karba ba,jiniya da qarar ababen hawa kala kala ke tashi,hayaniyar da hatta cikin dakin da take zaune bai tsira ba,dakin dake cike da 'yammatan fulanin da suke danginta ne,duk kuma cikinsu bataga gaje ko gilmawar inna furera ba,tun ranar da za'ayi mata kamu inna fureran ta iso,da tarin sharrikanta wanda ya zame mata tonuwar asiri saboda zuwan yuuma garin,wadda da ita ake gudanar da komai,batasan inda inna fureran tayi ba tun ranar da aka silleta,umarni dai na qarshe da aka bata maimunatu tayi yaqinin shine abu mafi tsauri a wajenta da zai iya sanyata batan dabo "Ki tattaro duk wata dukiyar dabbobi ta shatu da maimunatu dake hannunki ki kawo mana ita" bammmm!!!!. "Alhamdlh,aure ya dauru" muryar maroqin mai babban maqogaro ta kwararo cikin gidan,ta kuma isar da saqon nasa inda yakeson ya isa,lungu da saqo na gidan,sai kuwa mata suka dauki guda,gudar data zagwanyar da duk wani qwarin gwiwa na maimunatu,ta nannade kanta da kyau cikin mudukajenta(kayan saqi na zallar lallausar auduga na musamman da matan bappa sama'ila suka tanadar mata harda na yafawa saboda wannan ranar),take taji kamar zazzabi keson kamata saboda sanyi daya fara ratsa qashinta wanda batasan dalilinsa ba,tana jin 'yammatan na waqe waqensu na fulani suna kuma tsokanarta amma ko motsawa batai ba. Tana ji daga tsakar gida wata qanwa ga kakarsu ta wajen mahaifi tana fadin tare za'a wuce da ita da 'yan daurin aure zuwa can gombe,sunce nan da awa daya a shiryata" gabanta yayi mummunar faduwa,tana jin fargaba sosai,tana jin kamar su annin baqinta ne,duk da zuciyarta na gaya mata,bawai dasu anni zata zauna ba,zataje ne tayi rayuwa da wasu mutane na daban da batasansu ba,batasan halaye da dabi'unsu ba,bakuma tasan yadda zata fusakanci zama dasu ba. Tana jin sanda aka gama tiri tirin hada kayayyakinta tsaf,yuuma na tsaye akai,tamkar ba daga dangin ango ta fito ba,domin tace ita din a yanzun uwace ga maimunatu bawai suruka ba,ita ta riqeta ta rakata zuwa gaban baffaninta da wadanda ke a mazaunin uwayenta a yanzu,sunyi mata dukkan nasihar da akewa kowacce diya mace a al'ada sanda ta tashi tafiya gidan miji,dukkan wannan abubuwan maimunatu ganinsu take kamar a majigin film bawai a gaske ba,kamar raqumi da akala haka take biye dasu sanda suke riqe da ita zuwa jerin gwanon motocin dake jiran fitowarta,su kuma tashi dasu zuwa gombe. Shi daya ne cikin motar sai driver kamar yadda jabir ya tsara hakan ba tare dashi ya sani ba,zaman da yayi cikin motar ya yishi ne yana jiran fitowar jabir da yace yayi mantuwa a inda suka zauna,duba daya zakayi masa kasan cewa ango ne shidin zammm,yayi wani irin kyau na musamman cikin wata arniyar shadda ruwan sararin samaniya,wadda ta lashe maqudan kudade tun daga wajen siyota har ya zuwa dinkin da aka yi mata,aikin hannu me matuqar kyau tsari da kuma tsada,takalmin sauciki kalar dark blue sosai daketa daukar idanu saboda sabunta kyau da kuma tsafta yana aje gefe,qafafunsa babu komai sai sock,gefensa ya fidda babbar rigar ya ajjye,a samanta ya cire hularsa kalar dark dark blue da ratsin light mai wani irin walqiya da daukar idanu ya ajjiyr hade da babbar rigar,hatta da links din hannun rigar gold color ya cireshi,ya nade hannun rigar zuwa gwiwar hannunsa,gargasarsa dame kwance luf ta bayyana sosai. Wata magazine data wallafa sunayen fitattu kuma manyan kamfanunuwan gine gine a satin yake dubawa,kamfaninsu shine yazo a jeri na biyu,duba bayanan yake,amma can tsakiyar qirjinsa wani irin nauyi ne dake cunkushe a cikinsa,ranar ta yau gaba daya tazo masa ne kamar cikin mafarkai,tunda ya auri shaheeda kuma mutuwa ta rabasu bai taba tsammanin akwai rana irin wannan da zata zo ba,dukka wannan abun yanata qoqarin yaqi da abinda yakeji cikin zuciyarsa ne,amma a yau din,babu wadda ke ziyartar zuciya da kuma tunaninsa sai shadeedan,yana tuna rana irin ta yau cikin rayuwarsu data kafa masa tarihin da bazai gogu ba har abada. Haske ne kadan ya bayyana a motar bayan an bude murfin motar,yana shirin daga kansa ga zatonsa jabir ne,sai yaji muryar mata suna fadin "Shiga da bismillah,Allah yasa kin tafi a sa'a" wani abu ya tsaya masa a wuya sanda take shigowa motar a hankali,tana gama zama kuma aka maida murfin motar aka rufe,sai yaji driver yaja ya soma tafiya. Shuru ne ha ziyarci motar,babu wani motsi ko kadan a cikinta illa motsin injina dake aikinsu can qasa,cikin jikinta take jin sauyin waje da yanayi tabbas ya fara daga wannan lokacin,duk da bata iya ganin komai clearly amma tasan tabbas ba ita kadai bace cikin motar. Hannunsa ya zura a aljihun rigarsa ya fiddo wayarsa yanata qoqarin hadiye bacin ransa,shi jabirun zai rainama wayo?,yana nufin shi da ita zasuyi tafiya har ta wadannan awannin a mota guda don ya rainama kansa hankali?, numbers dinsa ya nema ya kuma kirashi,bugu biyu ya daga "Jabir" ya ambata da wani irin sound dake nuna zallar bacin rai,saidai kuma ba wani da qarfi yayi maganar ba Lumshe idanun ta maimunatu dake qudundune cikin yalwataccen mayafin da aka rufa mata har ka tayi,bugun zuciyarta dake qara bugu take qoqarin saitawa,sautin muryar ya doki kwanyarta,tamkar a cikin kunnuwanta aka furta sautin kalmar jabir din,saita hade jikinta waje daya sosai,tana jin takalminta ya zame daga qafarta,amma babu damar ta motsa bare ta maidashi,hakanan kawai takejin wani irin tsoro yana ratsata,tabbas wannan shine mutumin daya zama mijinta a yau. "Kada kace komai,don muna tare dasu abbi,ga motarmu nan tasowa,wataqil zamu tsaya a hanya mu kwana saboda nisan tafiyar,please i beg you, don't misbehave,ka dorar da farincikin dasu abbi suka samu a yau din" magiyar jabir ta yau ta tabashi,don haka baice komai ba,amma hakan bai hanashi jan tsaki ba bayan ya kashe wayar "Stop the car solomon" ya fada da tattausar husky voice dinsa "Okay sir" ya amsa masa cikin girmamawa,sannan ya gangara gefan hanya ya tsaya. Rigarsa da hularsa ya dauka ya bude murfin motar ya fice ya koma zuwa seat din gaba,sannan ya bashi umarnin ci gaba da tafiya bayan ya gyara zaman kujerar yadda zaiji dadin jingina ya zama comfortable sosai. 30 ASSALAM ALAIKUM DEARIES BARKAN KU DA KOKARI…. KAMAR KODA YAUSHE. WANNAN KARON MA MUNA BARAR ROKON KU WAJEN TEMAKAWA CHANNEL DIN SUDEIS DAKE MANHAJAR YOUTUBE YARO NE DAYA TASHI DA SON KARATUN ALQURANI ME GIRMA. YA KE KUMA KWADAYIN GADON ME SUNAN SA SHEIKH SUDEIS. DAN ALLAH A TEMAKA A DANNA MASA SUBSCRIBE. A KUMA YI VIEWING DA LIKING. A TEMAKA DA SHARING MA... JAZAKUM ALLAH KHAIRAN AS YOU DO... " Assalamualaikum dear sisters and brothers. Welcome to ummu sudais YouTube channels? A channel where the Holv Quran is been recited from different Angles. Click on this link and listen to the Beautiful recitation that will melt your heart https://youtu.be/Lafgc749sK8 Your subscription to our channel is of Great important. Please help us grow our channel by subscribing and likitoci 30 Ko sau daya bacci ko gyangyadi basuyi nasarar fusgarta ba,hakanan ko qwaqwaran motsi batayi tsahon a wannin da suka dauka suna tafiya,hakazalika motar haka ta kasance shuru,ba zata ce ga ainihin abinda yake faruwa cikin motar ba,sai daga bisani ne tadan janye mayafin dake kanta kadan saboda ta samu damar kallon gefan hanyoyin da suke wucewa da mugun gudu. Taraba suka wuce kai tsaye saboda su raba tsahon tafiyar,uwa uba kuma yammaci tayi lis,babu security ace sunyi tafiyar dare,don haka suka yanke sauka a wani hotel dake kan babbar hanyar da zata sadasu da gombe,kafin su iso ma tuni jabir yayi booking dakuna,don haka suna isa kowa key na dakinsu aka bashi. Itakam tana zaune cikin motar,har zuwa sanda anty maama ta qaraso ta fiddota,ran anty maaman cike da haushin ja'afar din,ta yaya sunsha wannan doguwar tafiyar xai fita yabar diyar mutane cikin mota?. Yana tsaye a tsakiyar dakin yana amsa waya sanda anty maama tayi knocking,ya qarasa bakin qofar ya murza handle din ya bude mata ba tare da ya tsaya tambayar waye ba,kana yaja da baya yana ci gaba da amsa wayar. Bakin madaidaicin gadon dake shimfide da farin lallausan bedsheet,tadan duqa kadan dai dai kunnuwan maimunatun,ta yadda ita kadai zataji abinda take gaya mata "Ki saki jikinki da mijinki,ki samu kiyi wanka da brush kafin ki kwanta,zan ciro miki wasu kayayyaki cikin akwatinki za'a miqo miki,ki saki jiki kinji ko?" A hankali maimunatu da kanta yake a duqe ta gyada kan nata,tana jin zuciyarta na wani irin bugawa,a tsahon shekarunta na goma sha shida tunda take bata taba kebewa da wani d'a namiji ba a daki daya kamar haka,balle har ta kaisu da kwana kamar haka,yau gashi za'a fita a barta da wani,wanda yake amsa sunan miji a gareta. Juyawa anty maama tayi ga ja'afar wanda har yanzu bai gama wayar ba,sai ta kada kanta ta fice a dakin,qarar rufe qofar dakin ya sanyashi waiwayowa,don bai lura dawa suka shigo ba,ya zaci tazo wajenshi ne zasuyi wata maganar,kuma sai yaji ta fice ba tare da tace komai ba,abinda ya sanyashi juyowa kenan. Cikin mamaki idanuwansa suka sauka ga maimunatun,kawo masa ita sukayi kenan?,lallai dai sai sun qure haqurinsa da juriyar da yaketa azawa ransa?,sai ya dauke idanunsa yana sallama da wanda suke wayar dashi,ya yanke kiran yana neman number jabir. Bugu daya ya daga,muryarsa cike da wani irin nauyi yace "Baku da wani extra dakin?" "For who?" Ya tambayeshi kai tsaye,don dama yasan dole ko yaya sai ya nuna turjiya "Ban sani ba,am asking you ne,it's simple question,just answer me bawai ka tsaya tuhuma na ba" "Oh...oh sorry, let me ask abbi first,but dakin kadan ya muku ne?" Ya tambaya cikin zolaya izgili da neman fada,haushi da takaici ya sanya ja'afar jan dogon tsaki kana ya tsinke kiran,wai dole sai jabir ya sanyashi dogon magana ne?,baisan abinda yakeji bane?. Sai ya cilla wayar saman madubu,sannan ya jawo kujerar gaban mudubi ya zauna a kai. A hankali ya duqa yana zare takalmin qafarsa,idanunsa suka kan farar qafarta dake dauke da dogayen yatsu da suka sha jan lalle wanda ya sake qawata qafan,ya kuma zame mata ado sosai,sai ya janye idanuwansa,qafafun are tiny,abinda yake alamta masa tana da qarancin shekaru kenan?,haka kawai sai yaji zuciyarsa na darsa masa son ganinta da tantance wacece ita?,ta yaya zasu dubi kamarsa suce zasu aura masa yarinya kamar haka?,sakanni qalilan zuciyarsa ta kacame da wasuwasin yarinyar ce ko kuma hasashe ne irin nasa?. Miqewa yayi yana sake jan tsaki duk a qoqarinsa nason mantawa da wannan wasuwasin da yake azalzalarsa a rai,ya taka zuwa qofar bandaki bayan ya kalli agogo yaga lokacin sallar magrib yadan gota kadan,ya daura alwala,ya sake fitowa yana sauke hannun rigarsa daya nannade kafin fara alwalar,yana son ce mata taje tayi alwala suyi sallah amma kuma ya rasa ta yadda zai gaya mata,bawai kuma baisan yadda zaice mata bane,a'ah,kawai qyashin maganar yakeji,har ya fidda abun sallah ya shinfida tana zaune,sai daya sake jan tsakin nan nasa dai,wanda ya kuma sanya maimunatu faduwar gaba ta kuma rintse idanunta kamar kowanne lokaci idan yayi tsakin,don tana jin tsakin ne har tsakiyar kwanyarta,faduwar gabanta kuma nada nasaba da muryar dake mata kama da wata firgitacciyar murya data taba ji shekarun baya da suka wuce "Kiyi alwala kizo" ya fadi mata yana jona qaraman kettle dake a gefansa. A hankali ta miqe,ta kuma dan ja mayafin nata baya kadan,sannan ta wuce zuwa bandakin. Gaban madubi ta tsaya bayan ta yaye lullubin kanta gaba daya,tana sakin wata ajiyar zuciya me nauyi gami da kallon fuskarta,wadda lallausan gashinta me azabar santsi da yasha gyara daga wajen yakumbo saratu ya fito kadan ta gaban dankwalin nata,saita debe ruwan dake zuba daga famfo ta fara alwalar,tana yi tana kallon fuskarta a madubi,zuciyarta nata mata saqa abubuwa masu yawa harta gama,ta maida dankwalinta da mayafinta ta fito,ta kuma tsaya a inda ya mata nuni suka tada sallar. Yadda yake sallar cike da nutsuwa yayi matuqar burgeta,ko banza alamune dake nuni da sanin addininsa. A hankali ya sallame,idanunsa suka sake sauka akan dogayen hannayenta suma da suka jiqu da jan lallae cikin ado me ban sha'awa,hakanan ya samu kansa da juyowa gaba daya yana fuskantarta,idanunsa suka sauka gaba daya a kanta,ta tanqwashe qafafunta sosai tana zaune,sai ya ganta 'yar qarama a gabansa,tazarar dake tsakaninsu ba mai yawa bace Shuru ne ya baquncin dakin,numfashin kowannensu yana fita tare sa tulin tunanin dake zuciyar kowannensu,yaci gaba da zama a haka yana fuskantarta tare da wassafa me zayace da ita?,duk sanda yadan dubi sashen da take zaune sai yaji wani abu ya tokare masa wuya,yanzun haka bayan ita akwai wata daban dake gombe tana jiransa?,for god sake anni zatayi masa haka ne wai?. Kamar wadanda aka umarta daga shi har ita kowanne ya daga kanshi zuwa ga dan uwansa,take fuskarsu ta hade waje daya kamar yadda idanuwansu suka cudanya da juna,fari qal din idanuwan nan nata da baqaqen qwayar idanunta masu digon zaiba jiki,kyakkyawan idanunwansa dake da wani irin shape,tare da wani irin maganadisu dake cike da zallar kwarjini. Kusan lokaci daya wani abu ya daki zuciyar kowannensu,wanda ta bangaren maimunatu ba komai bane face wani irin tsoro razani da kuma firgici da ya kusa tafiya da numfashinta,cak ta tsaya da zuqar iska zuwa huhunta na wucin gadi,hatta da ja'afar din ya karanci hakan,yayin da shi kuma zallar mamakin qananun shekarun da take dashi hadi da kamanni da tayi masa da wata suka ratsashi. Cikin jarumta ta zuqi wani dogon numfashi ta kaiwa hunhunta cikin wasu sakanni masu mugun sauri,abinda ya tallafa mata numfashinta ya dawo da aiki,saita lumshe idanunta da kyau tana shaqar numfashin da qyar,tana kuma jin yadda zuciyarta ke mugun bugawa da sauri kamar zata tsinke daga inda take ta fito. "Hey" ya fadi cikin mamakin yadda take wasu abubuwa kamar wadda taga giftawar mutuwarta a gabanta,maimakon maganar tasa ta taimaka wajen bude idanuwanta ko samun nutsuwarta......a'ah,sai ta sake razana,saboda muryar ta sake tabbatar mata da shi dinne dai,shine dai wannan mutumin,take jikinta ya dauki rawa,zuciyarta taci gaba da kadawa a tsakanin qirjinta,sai tayi wuf zata tashi jikinta na kakkarwa kamar wadda azababben zazzabi ya rufe. Caraf ya damqi tsintsiyar hannunsa cike da haushinta da mamakin firgitar da tayi,riqon da yayi mata ya sanyata sakin kuka babu shiri tana dubansa,mamaki ya cikashi qwarai,sai ya janyota ta koma ta zauna a inda ta tashi. Sosai hankalinta ya kuma tashi,ta hade jikinta waje daya hawaye naci gaba da bin kuncinta,ta yaya zata manta da wannan fuskar?,yaya zata manta dashi,mutumin da ya kusan sanadin cirewar qwayar idanunta saboda marin da ya zabga mata duka akan dabbobinta?,mutumin da ya mata barazana da kakkausar murya,wanda tun daga ranar bata sake ganinsa ba,saidai duk sanda taga mota,ko taga wani abu da yayi kama da mari saita tunda da abinda yayi mata,sau tari takan shafa kuncinta idan ta tuna da wancan lokacin,mutumin da razanata matuqa,ta tsani taba,ta kuma tsani me shanta,sai gashi ya fesar da hayaqinta saman fuskarta,abinda ya kusan haddasa mata daukewar numfashi,wanda ya aikata mata wannan duka shine zaune yanzu a gabanta,shine kuma mijinta?. Samun kansa yayi da zuba mata idanu,abinda ba al'adarsa bace,yana dubanta tare da son tuna inda ya santa,tsahon wasu daqiqu kwanyarsa ta dauko masa komai,bafullatanar yarinyar nan,daya jima yana tunawa bayan marin da ya dauke fuskarta dashi,ya jima yana murza hannunsa a lokacin cikin fushi da jin haushinta na yadda ta qarasa tunzura fusatacciyar zuciyarsa ya aikata mata abinda ba halayyarsa bane,fuskar da yakan tunata lokaci bayan lokaci saboda qarfin halinta da kuma yadda ta bashi haushi a sannan. Ga mamakinsa sai yaji duk wani temper na zuciyarsa ya sauka daga kaso casa'in cikin dari,zuwa kaso arba'in ciki dari,ta yaya zai zauna da wannan yarinyar?,wadda gaba dayanta baifi ya haifeta ba inda ace auren qauye akayi masa?,ta yaya zai zauna da wannan bafulatanar rugar?,wadda ya tabbatar babu abinda ta sani,babu kuma abinda ta iya?,ya aureta yace ya auri me?,ta yaya ma duniya zata kalleta a matsayin matarsa?,wanne irin rigima ce wannan ta anni?, take kwanyaraa ta hasaso masa unaisa,yayi comparing nata da wannan,sam babu hadi,ko ita unaisar bata cika mizani da ma'auni ba,tayi masa girma da yawa,don shaheeda bata kai wadan nan shekarun ba har ta rasu,barema tun halittarsa shi mace bata taba burgeshi ba,shaheeda ce mace qwaya daya tallin tal da ya taba daga kai ya dubeta da wata ma'ana ta daban,itace macen data fara bude rayuwarsa,kuma sanda ta tashi tafiya.....yanajin ta hada da muqullin komai nashi tayi gaba dashi. Cikin rai da zuciyarsa ya dinga jin yanzu zaiyi solving daya daga cikin matsalolin kamar yadda yake kallon maimuntu da unaisa a natsayin MATSALA kuma GURBIN IDANU ne kawai,wadanda baijin zasuyi ko suna da amfani ko wata rana ga mamallakinsu,wanda dasu da babu duk daya "Relax" ya fada idanunsa a lumshe,yana zagaya lips dinsa da yatsun hannayensa "Yamin shuru!" Ya sake fada a karo na biyu,ganin taci gaba da rera kukanta kamar ma bataji abinda yace ba,yadda ya buqata kuwa a wannan karon....sai ta fara hadiye kukan sannu sannu har ta samu nasarar tsaidashi. Shuru ya sake ratsa dakin,tamkar bazaiyi magana ba,kafin daga bisani ya bude dukkanin idanunsa ya watsasu a kanta "Kinsan menene aure?" Yayi tambayar with husky voice,wani irin abu ya ratsa mata tun daga saman kanta zuwa tafin qafafuwan maimunatu,saboda girma da nauyin da tambayar tayi mata,me zata ce masa? "Kinsan me aure yake nufi?" Ba tare da tayi dogon nazari ba ta gyada kanta alamun eh,kasancewar ba mutum ce ita wadda ta iya qarya ba. Wani miskilin qaramin murmushi ya sake "Okay......yayi kyau,tell me menene aure?" Ya fada yana yin qasa da muyarsa,hadi da tsareta da idanunsa nasu nauyin kallo,duk da bashi take kallo ba amma sai da taji gaba daya ta rude ta kuma daburce "Ehhnnnnn" ya fada da madaukakin sauti,sai ta shiga girgiza kai alamun a'ah,bata sani ba "Qarya kike kenan da farko..... okay let me show you the real definition of marriage" ya fada with confidence,zuciyarsa na gaya masa that's the only way da zai cimna gaci na abinda yakeson aiwatarwa,ba tare da yasan maimunatun was simple and peace maker ba,sai ya miqa hannu ya janyota cikin zafin nama daya sake tsoratata zuciyarsa na ingizashi,ya sanyata tsakiyar qirjinsa duk da yadda zuciyarsa ke qin hakan. Fara yamutsata yayi,abinda yayi matuqar dukan hankalin maimunatu ya kuma kadata sosai,abinda tunda take makamancinsa bai taba faruwa da ita ba,mugun gigicewa tayi cikin tsoro da razani,ta sake sakin kuka tana riqe masa hannayensa da yakeson fara yawo dasu cikin sassan jikinta,sai ya tsaya cak numfashinsa na wani irin gudu,yana duban yadda ta riqe dukka hannayensa biyu cikin siraran tafin hannunta,jikinta na wani irin rawa kamar an kada mata gangi "Bai kamata ba,baka kyauta ba" yaji can tsakiyar kansa zuciyarsa na gaya masa,bai musa ba,take zuciyarsa ta gamsu da cewa bai kyauta din ba,saidai kuma wannan ce hanya guda daya da zaiwa tufkar hanci,tunda baisan irinta ba yarinyar,abu daya ya sani game da ita,tsiwarsa da har ta iya buda baki tace masa Allah ya isar mata a wancan lokacin,yana jin this the only way out da zai dorata kan duk abinda ya tsarama zuciyarsa. Saidai kash,yana shirin sakinta anty maama ta turo qofar riqe da jakar kayanta,abinda ta gani ya sanyata fadin "Subhanallah" da sauri tana komawa da baya,abinda yaja hankalinsa,yayi hanzarin sakinta ya kuma miqe a nutse,ya isa bakin qofar dakin ya sake bude mata ita sosai,sannan ya juya zuwa bandaki bacin rai yana cinsa kan yadda ta gansu,yayi yaqinin abinda zaizo ranta daban,abinda zata rayama ranta yasha banban da abinda yake faruwa,ya tura qofar toilet din ya shige. Gaban madubi ya tsaya yana duban fuskarsa,hannunsa yasa yana yamutsa sumarsa zuwa bayan kansa,yadan riqeta da qarfi yana jin haushin kansa da kansa,ta yaya zai riqe yarinyar cikin jikinsa har kamar haka?,sai yaja wani irin tsaki kamar zai cire harshensa,yana jin tsantsamin jikinsa dama hannayensa,duk da cewa babu abinda ke fita a jikinta sai lallausan qamshin turaren firdaus. Wayarsa ya ciro ya turawa jabir tex kan ya shigo masa da kayan sawarsa,sannan ya ajjiye wayar,ya soma fidda kayan jikinsa yana jefarwa,ya daidaita ruwa me dumi sosai daga shower ya shiga ciki yana sabe jikinsa kamar zai cire fatar wajen. Da wani irin nutsuwa dakiya da kuma tsare gida ya dawo dakin,bayan ya shirya cikin wata lallausar jallabiyya da aka yiwa aiki d wani gold zare mai kauri,idanunsa suka sauka a kanta,tana lafe a wani lungu dake daura da gadon,sai ya sake jan tsaki can qasan ransa,yana jin takaici na sake kamashi,baisan me anni ma ta dauki aure totally ba data hadashi da wannan. Bai tsawaita magana da ita ba,cikin taqaitattun mintuna ya gama tsara mata dukkan wasu qa'idoji da dokoki da yakeso tabi da kuma zauna akai,ya riga daya sani a yanzun bai isa yace ya rabu da daya daga cikinsu ba ko ta yaya kuwa sukazo masa indai bada wani qwaqwaran dalili ba,sai ya sauke boyayyar ajiyar zuciya,yana jin yayi maganin rabin matsalarsa,ya tabbatar a yanzun bashi da wani sauran case da ita wannan yarinyar,saura dayar,ya fuskanci itakam waccar kanta yana rawa sosai,zai kuma shata mata layi tsakaninta da rayuwarsa. Fita yayi ya barta a dakin,bai dawo ba sai da bacci suka kama idanunsa,duvet din ya yayima ya koma saman kujera yayi kwanciyarsa,bayan ya kashe hasken dakin,bai wani jima sosai ba bacci ya daukeshi,don tunani da damuwar dake kansa a yanzun ta ragu sosai. Kasa sakewa tayi cikin dakin,motsi kadan saita tuna abinda yayi mata dazun,abinda ke sake bata tsoro kenan,duk da maganganun da yayi mata dazun sun sake nuni da girman tazarar dake tsakaninsu,wanda zuciyarta tafi raya mata cewa gargadine ya sanya ya aikata mata hakan,bawai don ta isa ko tana da wani abu ba,babban shinge da layin daya gindaya tsakaninsu kawai ya sake tabbatar mata da cewa da gasken gangancin aka aikata na hadata aure dashi kamar yadda ya gaya matan,ita kanta daga dazu zuwa yanzu da kuma sanin data yi masa a baya ta sake tabbatarwa kanta tako ina yafi qarfinta,ya kuma yi mata fintikau,tun tana takure har gajiya tasa gabbanta suka saki,ta kuma zame da jikinta a nan qasa daura gadon,bacci mai nauyi ya fara fusgarta,zuciyarta cike fal da tsoronsa daya dasa mata a wannan rana. 31 Ya samu nasarar dasa tsoronsa sosai cikin zuciyar maimunatu har ma fiye da yadda yakeso,washegari da suka fito tafiya kasa hada idanu tayi da anty maama,wani irin kunya da nauyinta ta dinga ji,cikin motar kuwa tana cure waje daya,kamar xaka ce ket! Ta zura da gudu,wannan karon a bayan ya zauna,ya kame owners corner abinsa,duk wani motsinsa tana ankare dashi,saidai da kunnuwanta don tuni ta saye idanuwanta cikin mayafi. Duk tsahon awannin da suka diba suna tafiya aiki yake da na'ura,daga system zuwa wayar hannunsa,tsahon wadan nan awannin ko daya baiji tayi wani qwaqqwaran motsi ba,abinda ya sanyashi daga kai suna dab da shiga garin gombe ya dubeta. Ko ta cikin yalwatacce mayafin data lulluba har saman kanta yana iya hangen zallar quruciua da kuma qanqantar data yi masa,wani takaici na sake kamashi kan anni,sam ita babu ruwanta da duba da cancanta ne ko kuma dacewa?,gwara unaisa ta cika shekarun da zai kirata da mace,saidai ko ita din ma bata burgeshi ba ballantana wannan rabin macen,ta yaya ma idanuwansa zasuji wata diya mace ta burgeshi?,baya zaton zuwan wannan ranar,wannan duka shaheeda ta tafi dashi,tabar masa fankon zuciyar,ta yaya fankon zuciya kuwa zata san dai dai daba dai dai ba?,sai yaja dan qaramin tsaki acan ciki,yana maida dubansa ga allon computer,yana karanta saqon rubutun da ya mamayr fuskarta. Katafaren wuni ake cikin gidan dr marwan,don sanda duka isa gidan a cike yake maqil,abinda ya sanya ammi ta bada maqullin wani kebantaccen waje dake gidan aka sauki maimunatu da danginta,aka kuma cikasu da cimaka kala kala,kafin yammaci inda suka hau shirya maimunatun bisa jagorancin anty maama,don Allah ya sanya mata matuqar qaunar maimunatu,tana burgeta ainun. Sanda suka kammala sunso su kaita cikin gidan wajensu anni da amma,amma sai annin tace a wuce da ita gidanta kawai,maimunatu tasu ce,babu wani abu sabo da zasu gaya mata,don haka direct aka fito da ita zuwa jerin gwanon motocin da aka aje domin miqata gidan captain ja'afar marwan khalid akko. Duk abin nan da ake tana jin komai ne tamkar a mafarki,wasu hawaye masu dumi suka zubo mata sanda taji.motocin sun fara motsawa zasu bar gidan dr marwan,babu abinda ya fado mata a sannan sai "Allah ya nunan ranar aurenki,ya baki miji na gari" sai gata yau a bigiren zuwa gidan mijin da batasan yadda zasu rayu dashi ba,a lokacin da qasa ta jima da rufe idanun mahaifiyar tata "Allah ya jiqanki daada"ta fada cikin ranta,wannan din addu'a ce da kullum rana batasan sau nawa take yinta a ranta da kuma sarari ba. Tana jin sanda 'yan uwanta da sauran 'yan rakiya ke yaba kyau da kuma tsarin gidan,kowanne bakinsa na furta addu'o'i a kanta,abinda ita ta rasa gane kansa har yanxu,Allah ya zaunar da ita yakuma dawwamar da ita a gidan mutumin nan?. A hankali yake takawa zuwa sassan ammansa,sanye da wani irin sassalkan yadi ruwan hanta,wani irin dinki aka masa me kyau wanda yake nuni da zallar zamani da kuma wayewa,takalmin fata ne a qafarsa budadde wanda ya dace da kayan jikinsa,kamar yadda saman kansa yake sanye da hular da itama ta dace da kalar takalmin qafarsa. Wata irin tafiya yake,sam jikinsa babu kuzari hakanan Babu karsashi a tattare dashi,ya tura qofar falon amman,akwai sauran baqi da suka rage cikin gidan,umma ce qanwa ga ammansa ita da wasu mutum uku,su suka gaya masa amman tana bedroom dinta,sai ya wuce kansa tsaye. Sai da yayi knocking ta bashi izini sannan ya tura ya shiga bakinsa dauke da sallama,luf luf dakin yake a tsaftace gana fidda wani irin qamshi me dadi,kai baka ce ba biki akeyi cikin gidan ba,tana saman gado tana gyarawa amna kwanciya,sai ya matsa ya rusuna gabanta yana gaidata,ta amsa kana shuru na sakanni ya biyo baya,ta gama gyarawa amnan ta saka mata pillow sannan ta waiwayo ga ja'afar "Zaku wuce kenan?" Kai ya jinjina mata,yana zare hular dake kansa,can qasan zuciyarsa kuwa wata nannauyan ajiyar zuciya ya sauke,yana jin komai har yanzu kamar a mafarki "Ma sha Allah,Allah ya tsare,ubangiji yasa a shiga a sa'a,Allah ya kauda dukkana abunqi,ya albarkaci tarayyarku,kayi qoqari ka riqe amanar yaran mutane,ka kuma ji tsoron Allah a zamantakewarku,ka sauke nauyin da duka Allah ya dora a kanka,na horeka ka zama adali,ka kiyaye haqqin kowacce akan 'yar uwarta,karka yi zalunci,kada kuma ka bari a zalunci kowa,Allah ya shige muku gaba" "Ameen ya rahman,na gode amma" ya fadi yana jin jikinsa yana yin sanyi,wannan daren yana tuna masa da daren aurensa na fari ne da shaheeda,wanda akwai tarin bambance bambance masu yawa. Matsawa yayi gaban gadon ya dora hannunsa saman kan amna ya shafa,sannan ya duqa yayi kissing kuncinta,ya maida mata abun rufar ya miqe tsaye yana zuba hannayensa cikin aljihunsa "Sai da safe" yace da amma yana takawa zai fice "Allah ya bamu alkhairi" ta fada tana bin.bayansa da kallo,duk yadda yake qoqarin boye damuwar dake saman fuskarsa ita ta karanci hakan,saita rakashi da addu'a "Wannan hadin ubangiji kasa ya zama silar waraka a rayuwarka". Motarsa ya wuce kai tsaye kamar yadda ya zaba tafiya shi kadai babu dan rakiya ko daya,don zuwa yanzun ma yasan abokansu sun tsufa gidan jabir koma suna shirin juyowa,yace baya buqata,shi din ai ba auren fari xaiyi ba. Yana shirin bude motar yaji sallamar khadim a bayansa,sai ya waiwaya yana amsawa,cikin girmamawa ya miqa masa wasu ledoji dake hannunsa "Gashi inji ammi" jim yayi na sakanni yana bin ledar da kallo,sai kuma ya bude masa back seat bau tare da yace komai ba,khadim din ya fahimta abinda yake nufi,don haka ya qarasa ya saka musu su a baya,har ya juya zai tafi yace masa "Kace mata na gode" yayi maganar ne sanda yake shigewa cikin motar,ya maida.murfin ya rufe ba tare daya jira cewar khadim ba. A hankali yake tuqin kamar wanda baison isa gidan,tafiyar data daukeshi mintuna masu tsaho fiye da mintunan da zasu isheshi a al'adance,horn daya mai gadin gidan ga dage masa gate din,sai a sannan yadan ja motar da gudu ya shige da ita farfajiyar gidan,sannan ya faka ta a parking lot idanunsa na sauka kan wata qaramar sabuwar mota ruwan zuma,ya dauke kansa yana kashe tasa motar. Har ya fito ya tuna da ledojin da ya bari cikin motar,sai ya koma ya debosu,tun kafin ya bude ma ya fuskanci meye a ciki,sai ya riqesu a hanauyensa,dai dai sanda me gadin gidan ya iso cikin rusunawa ya fara gaidashi,amsa masa yayi cikin kulawa,saboda yana daga cikin dabi'arsa girmama duk wanda yake aiki a qasansa,barshi dai da zafinsa miskilanci rashin daukan raini da rashin son wasa da aiki,hannunsa ya sanya cikin aljihunsa ya fiddo 'yan dari biyar biyar sababbi guda shida ya miqa masa,hannu biyu ya sanya ya karba yana ta zabga godiya,yayin da shi kuma yayi gaba abinsa ba tare da yace tak ba. Sai da yayi addu'ar shiga gida sannan ya kutsa kai cikin babban falo,shuru yake babu alamun motsin me rai cikin gidan,cikin nutsuwa ya fara takawa zuwa stairs,sai kuma ya tsaya cak saboda maganar da abbi da kuma amma suka gaya masa a daren jiya da yau,ledojin hannunsa ya kalla,a hankali sai yayo baya,ya kuma nufi qofar dake hannun dama na falon. A hankali ya tura qofar,falo ya bayyana,wanda aka qawata da kalolin kujeru da curtains masu azabar kyau,royal blue da golden,komai na falon,a tsaftace yake cikin qamshi da sanyi daya gauraye da sabunta,ci gaba yayi da tafiya har ya isa qofar bedroom din,itama ya turata ya shige. Dai dai lokacin da take zaune saman abun sallah,saboda ganin yadda lokaci yaketa tafiya,an doshi sha biyu na dare,kuma ana binta sallar isha'i da kuma shafa'i da wuturin da batayi ba. Can qasan maqoshinsa yayi sallama idanuwansa suna sauka a kanta,gabanta ya buga fat,don bata tsammaci shogowarsa din ba,saboda dukkan wata magana daya gaya mata a jalingo ta haddacesu tsaf a kanta, janye kansa daga wajen da take yayi,ya isa gaban madubi ya ajjiye ledar a kai,sai ya tsaya yana goye da hannayensa a qirjinsa. Raka'ar qarshe take amma kawai sai ta miqe taci gaba da kawo wasu raka'o'in,abinda ya sanyashi sakin hannayensa kenan,ya kuma juya a hankali ya fice a dakin bayan yaja qofar kamar yadda ya ganta. Sallamewar sallarta ta fito ne hade da ajiyar zuciya,ta danyi shuru tana karanta la'ilaha illa anta subhanaka inni kuntu minazzalimin,tana kuma jin yadda zuciyarta take bugawa,lumshe idanunta ta sakeyi,ba shakka tana tsananin tsoronsa,tana tsoronsa bilhaqqi da gaske,hoton sanda ya zuba mata lafiyayyen marin nan ya gilma a idanunta,sai kuma sanda yake zuqar hayaqin taba yana bulbular da ita daga bakinsa zuwa hancinsa,sai ta girgiza kai,tana jin wani bala'in haushinsa yana ratsata. Yaya akayi ya kasance mashayin taba?,bayan shi din ya fito ne daga gidan tarbiyya kamar haka?,mutane masu karamci dattako da sanin darajar dan adam?,bata tunanin akwai wanda yasan yana sha din cikin gidan,don ko da wasa bata tabs jin anyi magana makamanciyar wannan ba. Tunanin ta ture gefe,ta fara karanto azkar dinta da bata samu tayi ba a yau din,gefe na zuciyarta kuma cike taf da kewar amna,tana jin cewa zaiyi wuya bata nemi su anni su bata yarinyar ba,don ko a yau ma sai da akayi wayon janyeta sannan suka tahi,wanda ita bata kawo hakan ba,ta tsammaci zasu taho ne da ita,amma sai taga akasin hakan,to me zata zauna ne tayi a gidan?,gwara gwara ma ace da amnan,zata taimaka mata wajen debe kewa. Kamar yadda ya shiga sasssan maimunatu haka ya shiga na unaisa,saidai ita ya sameta tsaye ne a gaban mudubi tana kallon kanta bayan ta gama sake feshe jikinta da turare tana gyara zaman rigar jikinta. Sallamarsa hade da turo qofar ya sanyata saurin maida mayafinta saman kanta, ta rufe ruf,saidai tana iya hangensa ta cikin mudubin,wani sassanyan abu ya ratsa zuciyarta ya kuma haifar mata da yalwataccen murmushi akan fuskarta,a fakaice taci gaba da binsa da kallo,tana jin wani farinciki yana ratsata,burinta ne na tsahon wasu shekaru Allah ya cika mata shi,duk da cewa ranta ya baci a dazun da ganin irin gidan daya zaba a jjiyeta kuma tare da wata,saidai anty talatu ta kwantar mata da hankali "Kinsan baso yake ba,ta yiwu yayi hakanne don ya baki haushin dama harkiyi wani abu da zai janyo a fasa gaba daya,dole fa saikin anjiye rashin haqurin nan,kin janyo hankalinsa a hankali a hankali,sanda zai canza miki gida ko ya rabaki da qasar ma gaba daya bai sani ba" qwarai ta gamsu da maganganunta,don haka ta ajjiye komai gefe a ranta. Cikin salo ta amsa sallamar tasa cikakkiyar amsawa,bai sake cewa komai ba itama ya ajjiye mata ledar,ga zatonta zai qaraso koda gefanta ne yace wani abu da ita,saidai gani tayi yana shirin ficewa,muryarsa can qasa ya furta "Gudnyt" ya tursasa zuciyarsa ta fada,duk don son ganin yayi abinda ya dace bakin gwargwado. Gabanta ne ya fadi sanda yake gab da fita,ta daga kai tana dubansa ta madubin,zuciyarta tana bata shawarar tsaidashi,yayin da wata zuciyar ke hanata,tana gaya mata girman wannan rana a wajenta,ita yafi kamata ace an tsaida,an kuma nema kasancewarta cikin dakin,tana wannan shawarar da tattaunawar da zuciyarta har ya fice. Kasa zaune tayi,ranta ya baci sosai,ta dinga kai kawo tana tunani a ranta,shin sassansa ya tafi ko kuwa na maimunatu?,sai taji zuciyarta taqi aminta da hasashen daketa mata yawo,don bai kamata ace sassan maimunatun ya fara sauka ba,tunda a qa'ida itace babba,ta girmewa maimunatu,ita ya kamata ta fara karbar baquncinsa,tafi maimunatu sanin rayuwa dama komai da komai da za'a tarairayi mutumin da ya jima babu mata a gefansa kamarsa,don haka ta gyara rufin mayafinta,ta kuma bude qofar ta fito. Bata ma isa sassan maimunatun ba taji motsinsa daga sama,don haka taja birki,ta kuma koma nata sassan,girman kai yana sauko mata,tana jin ba zata iya nemansa a yau ba itama. Yana shiga dakin ya sauke ajiyr zuciya mai qarfi kamar zai tofar harda qirjinsa,ya soma bin dakin da kallo,an qawata masa shi yadda yakeso ya kasance,idanunsa daya bayan daya suna sauka kan hotunan shaheeda da amna da amra wanda aka musu tare yasa aka gyarasu aka shiryasu a falon gwanin burgewa,kai kace idan ka kirayesu zasu amsa,zakayi tsammanin har yanzu sune ke rayuwa cikin gidan,addu'ar da baya gajiya dayi musu yayi wani abu na motsa ransa,ya wuce zuwa bedroom dinsa. Sai daya gama duba komai daya ce a sanya masa a dakin,wanda yake buqatar ya canza masa waje ya canza masan ya ajjiyeshi inda yakeso,sannan ya fidda kayan jikinsa ya zubasu a laundry basket,sai ya wuce toilet kai tsaye,ya daura alwala sannan ya fito ya kuma bude walking wardrobe dake manne da bedroom dinsa ya shiga ya duba wasu navy silk pyjamas Natalya's company,ya shirya kansa wadata jikinsa da turaren da yake amfani dashi duk dare,sannan ya feshe kansa da BB hair spray. Abun sallarsa ya shimfida sannan ya tattara dukkan hankalinsa da nutsuwarsa ga alqibla. Unaisa kuwa kusan raba dare sukayi suna waya da anty talatu qanwa ga mahaifiyarta haj Aayah,tana gaya mata abinda yafaru,ita kuma tana shirya mata yadda zata aiwatar da komai,sun jima sosai suna tattaunawa kafin suyi sallama "Amma dai lafiya ko?" Haj Aayah da suke kwance daki daya da qanwarta wadda bata kai ga komawa gida ba ta tambayeta "Eh to,lafiya amma ba lau ba" abinda ya farun ta gaya mata,sai ta sauke ajiyar zuciya "Yaron nan fa ba lafiyar kwanya ya cika ba,idan anyi magana sai kuce depression ne ya kamashi bawai ciwon hauka ba,ni tsorona ma kada ya kama min diya ya jibga,don banjin zanyi kawaici,babu yadda banyi da unaisa ta haqura dashi ba amma ta kasa haqura" murmushi talatu tayi "Banda abinki yaaya,ta yaya yana da ciwon hauka zan goya ma unaisa baya ta aureshi,an gaya miki ciwon damuwa ne,kuma a yanzunma komai yana wucewa tunda gashi ya amshi mata har biyu,mudai burinmu kawai diyarmu tayi zarra ta zama star dinsa,don kishi da bafulatana sai an kula,shegen surkulle garesu" haka suka yita tattauna maganar a tsakaninsu a daren. Itako maimunatu wani nutsuwa ta sauko mata bayan ta gama dukka addu'o'inta ta isa ga gadonta ta kwanta,gadon data dinga ji kamar ba nata ba,dakinma kansa jinsa take kamar an bata aronsa ne,kewa da kadaici suka dinga damunta,sosai ta dinga ji cikin ranta inama ace an bata amna,sannu a hankali idanuwanta suka dinga nauyi,bacci kuma me qarfi ya fusgeta. *Follow my arewabooks account for more latest pages* *Arewabooks:HUGUMA* ______________________________ *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 32 *WASHEGARI* Tun sanda ta idar da sallar asuba bata koma bacci ba kamar yadda ta saba,tana ta azkar dinta,yayin da rabi da rabi na hankalinta ke kan tunanin yadda rayuwa zata kaya mata cikin gidan. A hankali taji idanunta suna mata nauyi,gajiyar zaman mota daga gembu zuwa gombe ya sanya bata kai ga qarasawa ba bacci yayi awon gaba da ita,ba kuma ta farka ba sai wajen qarfe tara saura na safe. "Hasbunallahu wani'imal wakil" fa fada s sauri hamma na qwace mata,ta miqe tana linke abun sallar data tashi akai,daga nan kuma fa zarce sa bubbuge bubbugen qura duk da dakin babu abinda yayi,ta kauda abinda yake zaune ba'a kan tsari ba,daga nan ta wuce toilet kai tsaye,ta hada ruwa tayi wanka. Sanda ta fito hudubar anty maama da yadikko matar kawu sulaiman akan tsafta da kula da kanta,duk da cewa kwatakwata qazanta ba dabi'ar ta bace. Cikin mayukan dake jere saman madubinta ta bude wasu ta shafa,sannan ta duba makekiyar wardrobe dinta ta jikin bango. Tsaiwa kawai tayi tana kallon tarin uban suturun da a yanzu suke mallakinta,sai takejin kamar ta zurawa rayuwa jikinta da yawa,banda haka ina ita ina wadan nan kayan da batasan ranar da zata gama sanyasu ba?,haka ta dinga dubawa har zuwa lokacin da hannunta yakai kan wata atamfa,kalarta ce ta dauki idanun maimunatu,data gwada sanyawa kuwa saita amsheta,tayi mata kyau matuqa da gaske,batayi amfani da dankwalinta ba,a maimakon hakan sai ta nema qaramin hijab ta maqala a kanta. Bakin gado ta koma ta zauna,ta rasa abinda zatayi,sai kuma ta fada tunane tunane,abubuwan da suka faru a rayuwarta,suke ma kan faruwar,tsakiyar haka taji kamar qararrawar falon nata neman dauki,hade da knocking,tayi kamar kada ta fita,amma jin baa fasa knocking din ba ya sanyata miqewa. Cikin nutsuwa ta fita,qafafunta suna nutsewa cikin lallausan carpet dake malale a wajen har ta iso falon ta doshi qofa,dai dai sanda yake saukowa daga samansa,sanye da wata jallabiya saqar qasar morocco,ruwan a qasa da aka yiwa ado da wani zare mai dan kauri ruwan madara,yankakken hannu gareta,don haka dukka singalalinsa dake lullube da gargasa waje yake,sumarsa tadan hargitse kadan,haka nan fuskarsa na nuna alamu na jin bacci. Idanunsa a kanta sanda ta bude qofar yana step na qarshe,ta gane fuskar matashin saurayin dake miqo mata kwanduna dauke da fulasai masu azabar kyau "Daga gidan dr,amma ce tace a kawo muku" sosai taji dadin karamcin amman har cikin ranta,tasa hannu ta karba tana cewa "Kayi mata godiya,Allah ya saka da alkhairi" sai ta maida qofar ta tura ta yadda take,ta kuma waiwayo don komawa ciki ta sama musu mazauni. Karaf idanunta ya sauka a kansa sanda yake isa gaban babban freezer dake falon tamkar ma bai ganta ba,budeta yayi ya ciro babbar gorar ruwa guda daya,gabanta ke wani irin faduwa,tsoronsa dake shaqe a zuciyarta ya motsa "Ina kwana" ta fada bakinta yana dan rawa kadan,tana jin kamar zai mata wani mummunan abu ne,banda alamun sauti da taji da sai tace bai amsa gaisuwar tata ba,kunnuwanta na biye da takunsa sanda yake shirin komawa saman,sai tayi ta maza tace "Ga abinci amma ta aiko dashi" shuru na wasu sakanni suka ratsa yana ci gaba da tafiyarsa,kamar bazai ce komai ba sannan tayi yace "Madalla,an gode" yaci gaba da hayewa saman,kunnuwanta dai na biye da sautin takunsa,takun da ake yinsa cikin wani irin salo da kuma tafiya wadda jinin sarauta ke yawo a cikinta. Sai data daina jin motsinsa sannan ta daga kanta tana duban kwandon hannunta tare dason gane me madalla da yace take nufi?,ita yanzu ya zatayi da wannan abincin?,sai ta maida dubanta ga sassan unaisa dake a rufe,zuwa zatayi ta mata magana ko kuwa ta qyaleta?,kai ta girgixa,zuciyarta tafi karkata da ta qyalesu gaba daya,don haka tayi kitchen da abincin,ta ajjiye acan,bayan ta bude ta diba iya abinda cikinta zai iya dauka,wanda duka duka cikin plate daya ta xuba komai. Tunda ta koma daki bata sake jin motsin kowa ba,don ko data gama cin abincin sake kwanciya tayi,ita ba gwanar kallo bace bare ta dawo falonta tayi,sai bayan kusan awa biyu taji tashin mota daga farfajiyar gidan,wadda batasan ta waye ba,saidai tana kyautata zaton tame gidan ce. Qarfe daya da ashirin na rana tana fitowa daga alwalar sallar azahar taji knocking da 'yar hayaniya,sake fitowa tayi falon,har yanzun kamar dazun dai babu kowa ba kuma motsin kowa. Murmushi ya subuce mata sanda ta bude qofar,laila ce ita dasu hanne da hauwa,sai fa'iza da safina harda khadija,kusan dukkaninsu mutanenta ne,akwai sabo tsakaninsu sosai,abinda yasa ta sake jikinta ta kuma ji dadin zuwan nasu "Ina fatan dai yaa ja'afar bai nan?" Fa'iza ta fada tana dan fidda idanu gami da watsa idanunta a babban falon gidan hadi da kallon stairs din,qaramin murmushi maimunatu tayi tana kada kai "Ya fita" ta amsa musu kai tsaye,don motsin fitar motar dazun ranta yana gaya mata shine "Na baroshi wajen amma ma fa sanda muke fitowa" safina ta fada tana zare mayafinta daga kanta "Au to,dama wai don mufi sakewa ne" ta fadi tana dariya,ita dai maimunatu jagora ta musu zuwa sassansu,suna tafe suna gaya mata ba dadewa zasuyi ba,amma tace au dawo da wuri,kuma su hauwa da qyar idan ba anjima zasu wuce ba,zasu biya ta jalingo ne,akwai gaisuwar mutuwa da akayi da zasu fara zuwa sannan su wuce gembu. Awa biyu kawai sukayi,amma sai taji kamar sunyi awa biyar,saboda yadda hirarsu ta dinga debe mata kewa,kowacce na qoqarin koya mata yadda zata zaun a gidan,ta kuma kama hankalin mijinta sannan ta tserewa kishiyarta,kasancewar dukansu sun girme mata,ita dai jinsu kawai take da kunne,hausawa sukace me daki shi yasan inda yake masa yoyo. Da suka tashi tafiya sukace zasu leqa wajen unaisan su gaisa,cogewa maimunatu tayi har suka shiga suka fito,sannan tayi musu tattaki zuwa farfajiyar gidan,karon farko kenan da taga yadda harabar gidan yake,salmanu drivern abbi ne ya kawosu,tana tsaye tana binsu da kallo har suka fice daga gidan,sai ta sauke ajiyar zuciya tana jin tamkar ta bisu,cikin matuqar sanyin jiki ta dawo cikin gidan. Tunda ta koma din bata sake jin motsin kowa ba,gaba daya gidan sai take jinsa wani iri,babu armashi babu kuma dadi,tana jin inama za'a maidata gidan abbi?,inama zaa maidata wajen anni,rayuwar can tafi mata dadi dari bisa dari. UNAISA tun bayan tafiyar 'yan uwanta da sukazo mata bayan sallar magrib ta shiga toilet dinta ta sheqa wanka,sunyi maganganu masu tarin yawa da anty talatu,wanda ta dinga qoqarin ganin tabi kowacce shawara da umarni da anty talatun ta dorata akai. Cikin wasu azababbun English wears ta shirya kanta, straight leg jeans da rigarsa wadda tsahonta iyakarta cinya,ta zuba turare sosai a jikinta,ta kuma wadata fuskarta da powder da lip gloss da ya qarawa lips dinta sheqi,nails polish remover ta saka ta cire tsohon nail polish din,ta sabunta da wani da yaketa glittering. Sai data tabbatar komai yayi,ta juya gaba da baya sannan ta dauki wayarta,already tana da number dinsa,saidai bata taba gigin kira ba,ta zauna gaban dressing mirror dinta ta kara wayar a kunne sanda take ringing,tana kuma kallan fuskarta,gabanta yana dukan uku uku,don batasan da wacce fuska zai tarbi kiran nata ba. Dai dai lokacin da yake kashingide bayan motarsa suna magana da mr husain daya daga cikin manyan ma'aikatansa,kallo daya ya yiwa wayar ya dauke kansa ya maida ga maganar da sukeyi dashi cikin ma'ajiyar motoci ta kamfanin nasa,wanda ya budewa wuta yakeson ya dawo dashi.hayyacinsa,ya kuma ci gaba da aiki fiye da yadda yakeyi a yanzu. Al'adarsa ce haka,ba kasafai yake daga baquwar number ba,don haka da ring din ya isheshi saiya maidata silent yaci gaba da uzurin gabansa. Da matuqar sarewa ta sauke wayar daga kunnenta,kira uku kenan bai dauka ba,sai ta yanke ta tura masa gajeran saqo kawai,don haka ta batayi qasa a gwiwa ba ta senda masa _hello hottie,it's your wife calling you,i missed you so much today,please come back as early as possible,akwai abubuwa masu dadi dana tanadar maka....am waiting for you,urs.....unaisa_ Sanda saqon ya shigo wayar tana hannunsa yana duba wani verification code da wani company suka turo masa,zai bawa mr hussain,tsaki yaja wanda sai daya fito a fili,har sai da mr hussain ya daga kai ya kalleshi,saidai bai tambayeshi ba,shi sam yama mance dasu,tunda yasa qafa ya fice yau din duka aiki ya riqeshi,gaba daya hidimar company dinsa ne a gabansa,ko gidama da yaje amma kawai ya samu ya gaisar ya wuce,bai samu ganin abbi ba bare anni,saboda akwai sauran baqi,shi kuma bayason wannan wasan banzan da akema mutum da sunan abokan wasa. Sai daya bawa mr hussain duk abinda zai bashin sukayi sallama sannan ya yiwa driver dinsa sign da ya shigo su tafi,sai daya tada motar suka fice a company din sannan ya tambayeshi "where are we going sir?" "Take me to the nearest restaurant" ya bashi amsa yana kara wayarsa a kunne,jabir ya kira,don tun dazun yaga miscalls dinsa,a sannan yayi calling urgent meeting da ma'aikatansa,daya fito kuma ya manta sai yanzu ya tuna. Sai data kusa tsinkewa ya daga,cikin wata irin raunanniyar murya me cike da sanyi jabir din ya masa sallama,muryar data sanya ja'afar din tuno abubuwa masu yawa a shekarun baya wadanda suka shude masa,kamar shi a irin wannan lokacin da jabir din ya kirashi,da qyar ya samu ya daga,a sanda yake rayuwa da muradin zuciyarsa shaheeda. Yayi kamar zai katse kiran,sai kuma ya dake,suka gaisa ya gaya masa uzurin da yasa ya kirashin "Am sorry J,amma if possible please kayi postponing schedule din zuwa upper month mana,saboda ina tunanin tafiya honey moon ni da my fa'eem" wani dogon tsaki ja'afar ya sake a kunnen jabir,yana jin kamar ya raina masa wayau ne "What nonsense are you talking about?,ina maka magana ne akan abinda ya shafi company kana min maganar honeymoon,if u r not ready to accept your vacancy shikenan fine,i can I can manage the company" daga haka ya katsr kiran cikin fusata,tamkar wani gagarumin abu jabir din ya gaya masa,yana furzar da wata zazzafar iska daga bakinsa. Ko da yaje eatery din da drivern ya kaishi,ya kuma zaba abinda zaa kawo masan sai ya kasa ci,daga qarshe haka ya miqe ya biya abinda aka cajeshi duk da tsadar abinci a wajen ba tare daya ci wani abun kirki ba,yace su wuce gida kawai. 33 A hankali yake takawa zuwa cikin gidan,duka hannayensa cikin aljihun rigarsa,duk da yadda ya gaji amma sai daya daure ya biya ta store din gidan,ya duba kayayyakin amfanin da yace a zuba a ciki,ya tabbatar a saka komai da komai na amfanin gida na yau da kullum,sannan ya rufe,ya bulla ta qofar kitchen. Dai dai lokacin da maimunatu ke cikin kitchen din,tana tunanin yadda za'ayi da abinciccikan da aka kawo na safe rana dana dare,tunda bai cinyu ba,daga qarshe kamar yadda taga acan gidan sunayi,saita kwashesu ta zuba a freezer. Hannunta take daurayewa a bakin famfon dake cikin kitchen din,tana gamawa ta kashe ta juyo tana yarfe ruwan dake jiki,dai dai sanda yake fitowa daga store din,idanunsa suka sauka a kanta,cikin lausasan kayan bacci,doguwar riga baby pink da baby hijab light blue,kalar datayi masifar haskata,ta kuma fidda gewayayyar fuskarta dake nuna qarancin shekarunta,sam bata lura dashi ba,saboda idanunta yana kan hannayenta,har sai data zo gab sannan ta ankara da inuwarsa,taja baya kuwa da sauri gabanta yana faduwa,idanuwanta suka fada cikin nashi,zallar tsoron dake zuciyarta ya bayyana qarara cikin idanuwa da fuskarta. Wani kallo yayi mata fuskar nan a dinke babu ko digon annuri,jinta tayi tamkar nutumin da zaki ya ritsa a tsakiyar jeji babu gurin kubuta,sai ta rasa me ya kamata tayi,cikin juriya da qarfin hali jajayen lips dinta suka motsa "Sannu.....da zuwa" ta fadi a rarrabe,dauke idonsa yayi daga kan labban nata yana jan qaramin tsaki qasan ransa,yadda tayi maganar ma kawai zai gaya maka shes very young,ta yaya wai ma anni zata ce ya ajjiye kamar wannan a matsayin matar aure koda ya tashi yin auren?,wannan ba saidai a dauki buzunta ba duk sanda yace zai kaara jikinsa a nata?. "Ungo nan" taji ya fada a maimakon amsa sannu da zuwan data yi masa,daga kai tayi a hankali tana duban abinda yake miqo matan,kafin ta saka hannu ta dauka a saman fridge din dake daura dasu,inda anan ya aje mata kafin takai ga karbar,sababbin kudi ne a daure a kyauro masu yawa,don ko da batasan adadinsu ba amma tasan cewa suna da yawa qwarai "Idan kina da buqatar wani abu kiyi amfani dasu,banason ki nemeni,don banason damuwa da takura,take care" gyada kai tayi a hankali,sannan tace dashi sanda yake fita a kitchen din "Allah ya saka da alkhairi" bata iya jin ya amsa ko bai amsa ba,itadai tabi bayansa itama ta fita bayan ta tabbatar yayi nesa da wajen,kudin na rungume a hannunta,saidai tana tsananin jin qyamar kudin har cikin ranta,itafa...daga randa ta ganshi yana zuqat taba shikenan kuma,bata masa kallon komai sai dan iska,mugu kuma azzalumi,biyo bayan abinda yayi mata,zuciyarta cike fal da tunanin mema zatayi da kudade haka?,me zafa buqata dasu?,da wannan tunanin ta fada dakinta ta kulle,ta isa gefan gadonta ta jawo side drawer ta jefa kudin ta mayar ta rufe. Tunda taji motsi a sama ta tabbatar shine ya dawo,don haka ta sake duba kanta da kyau,sannan ta bude freezer dinta ta dauki sassanyan ruwa da lemo ta aza saman wani set din tray me hade da cups,ta yane kanta da wani dan yalolon mayafi,sannan ta fito. Wani abu ya mintsini mai kama da kishi sanda idanunta suka sauka a sassan maimunatu,basu taba haduwa da yarinyar ba,basu taba gamuwa ba,ko yaya take?,tana ina yanzu oho?,taja wata qwafa kamar zata cire harshenta sanda zuciyata ta raya mata ace dai taje ta sameta tare dashi. Har tsakiyar zuciyarta falon nasa ya tafi da ita,akwai wani yanayi na musamma tattare dashi,taci gaba da takawa a hankali ta nufi bedroom dinsa kai tsaye,saidai kuma kamar yasan wani zaya shigo masa,yana shiga kafin ya shiga wanka ya murza key,tana taba handle din ta gane hakan,dole ta koma saman kujerun alfarma dake falon,ta zauna ta dora qafa daya saman daya bayan ta kunna tafkekiyar tv dake falon,takuma canza tasha zuwa mbc Bollywood,ta samu kuwa suna wani film me kyau,saita maida hankalinta a kai,yayin da wani sashe na zuciyarta kuma yaketa wassafa mata yadda zai tarbeta,duk da tasa a ranta ba zata samu tarba me kyau dari bisa dari ba. Cikin jallabiyya Morocco's male abaya me ruwan gold mai gajera hannu ya shirya bayan ya fito daga wankan,duk da baici abinci ba amma sam baya jin yunwa,muryar amna yakeson ji,yayin da wani sashe na zuciyarsa kuma a yau yake cike da kewar shaheedansa,ya feshe jikinsa da lallausan turaransa bayan ya gama gyara sumarsa dake samun gyara na musamman,ya dauki wayarsa ya danna kiran number ammansa. Bugu biyu aka daga,salma ce,ta shaida masa amman tana wajen abbi,sai ya nema ta hadashi da amna,ta kuwa hadasun,yarinyar ta dinga masa hira sosai,abinda yasa ya samu relief daga abinda yakeji kenan,yadan sake shima yana tayata. Ya kusa minti talatin tare da ita,ya samu sauqi sosai cikin ransa,harma ya samu qwarin gwiwan jin son shan coffee,don haka ya diba takardun da zai duba da system dinsa ya nufi falon. Janye idanunta tayi daga fuskar tv din tana sakin murmushi,jarumin film din yana mata mugun yanayi da J dinta,yadda ya iya soyayya ta tabbatar J zai iya finsa,saidai shawo kansa da qwato hankalinsa abune mai wahala ta sani kuma,dai dai sanda take shirin sake maida idanunta ga film din,sai suka sauka ga babban hoton shaheeda dake rataye cikin falon,zuba ma kyakkyawar fuskarta idanu tayi,murmushin da take a cikin hoton tajiyana tabata,sake waiwaya tayi wani sashe still hotonta ne ita da twins dinta amna da amra,daga daha bangaren kuma shi da ita ne,sunyi masifar kyau cikin qananun kaya,karon farko data fara ganin wani abu me kama da murmushi saman fuskarsa,yana rungume da ita ta baya,da gani ba'a qasar nan aka dauko hoton ba,yana sanye da uniform da matuqan jirgin sama,kyau iya kyau yayishi,uniform din sun karbeshi matuqa da gaske,hoton ya fusgi hankalinta,ya kuma saka kishin shaheeda mai yawa cikin ranta,har sai data miqe ta isa ga hoton dake can wani kusurwa na falon,ta tsaya a gabansa tana sake qare musu kallo. Da farko daya fito bai lura da ita ba,sai daya kusa isa inda ya ajjiye na'urar hada coffe dinsa take,yadan tsaya kadan,kamar zai magana sai ya fasa,ya isa inda coffee maker din yake,ya soma hada abinsa,saidai abun mamakin har ya hada ya dawo ya zauna saman kujera bata ankara da wanzuwarsa,abunda yayi masifar bashi haushi,saidai zaiga iya gudun ruwanta da nata qwaqwqwafin da kuma sanya idon. Hannu ta sanya zata daga hoton don ganin date din jiki sosai "Don't dare touch it" ya fada da kakkausar muryar data ankarar da ita yana wajen,tadan zabura kadan tana juyowa,idanunta suka sauka akansa, sipping coffee dinsa yake hankali kwance,idanunsa kan tv din daya sauya tasha zuwa ta news,kai baka ce da ita yake magana ba. Wani mugun kyau yayi mata,sai ta dinga jin inama ace zai rungumeta,ko ita ya bata wannan damar?,qoqarin dai daita kanta tayi,sannan ta fara takowa cikin salo na canjin tafiya zuwa inda yake zaune "Welcome home" ta fada tana sakar masa murmushi,saidai kuma abun haushin,baiko kalleta ba bare ya fahimci kwainanen da takeyi,hasalima tambaya ce ta biyo baya "Who gave you permission to enter my room?" Tambayar data sanyata yin sak,kafin kuma ta saki murmushi tana ci gaba da takowa "am your spouse fa,mene ne a ciki?" ta fada tana isowa dab dashi,shirinta shine ta zauna daura dashi din. Idanun nan nasa masu matuqar nauyi da kwarjini ya daga ya watsa mata su,abinda ya sanyata tsaiwa ta kuma kama kanta,bata sake gigin yunqurin zama kusa dashi ba yadda taso a baya,kamar bai shirya yin magana ba,saidai zuciyarsa tana gaya masa,ita kadai ce a yanzu zata zame masa damuwa cikin gidan baiyi wasa ba,itakam waccan bashi da damuwa da ita ya tabbatar,don ya gama da babinta,unaisan ke kallon kanta a ta cika macen da zata kutso kai tayi tarayya dashi cikin rayuwarsa,abu mafi wahala da tsada da diya mace ke nema ko ta samu daga wajensa,yana jin komai nasa kebantacce ne na musamman "Am warning you for the second time,stay away from me,banason kutse cikin al'amurana,Live your life,I live mine,banason kutse cikin al'amurana,ki kiyaye" ya fada da sautin dake nuna gargadi mai qarfin gaske. Har cikin zuciyarta maganganunsa suka soketa,tanason ta maida masa raddi amma kuma ya mata kwarjinin da ko bakinta ta kasa motsawa "Am saying in respect, get out of my room" ya fada with his husky voice. Jikinta a sanyaye ta fara takawa zuwa bakin qofa,gefan ranta a quntace,sai ya ajjiye cup din idanunsa na sauka kan tray din data ajjiye,ya janyo wata qaramar dawer daga jikin kujerarsa,wadda ba kowa ne zai kula da ita ba,ya ciro kudi kusan adadin wanda ya baiwa maimunatu ya dora mata a kai,sannan yace "Dawo ki dauke kayanki" cak ta tsaya,kamar ba zata dawo din ba saboda yadda qwalla ke neman cika mata ido,to amma ba zata iya tafiyar ba,saboda yadda muryarsa ke iya canza duk wani nufi naki,ta dawo ta dauka din kamar yadda yace sannan ta fice. Cup din ya dangwarar a wajen,yana furzar da iska daga bakinsa,shi kansa yana jin baiyi dai dai ba,amma kuma hakan shine dai dai a wajensa,gwara tun wuri kowacce a cikinsu tasan cewa bata da gurbin zama cikin rayuwarsa,yafi kyau ya nesanta kansa dasu akan ya sake musu su sanya ransu a kansa. Tun a falonta ta watsar da komai suka tarwatse sukayi nasu waje,ita kuma tayi daki da sauri tana sakin kuka,wayarta ta laluba,ta kuma kira anty talatu,kukantanya daga mata hankali sosai,don da qyar ta iya ta mata bayanin abinda ya faru. Murmushi anty talatun ta sake,alamun hankalinta a kwance yake "Hmmmm,yaro man kaza,ke haka kike unaisa?,baki da haquri?,ga shegen gaggawa?,daga fara wasan saiki saare?,waya gaya miki abu mai daraja da tsada yana samuwa ta sauqi haka?,in just a minutes amma kin gaza?,haka zaki nunawa kishiyar taki har ta fuskanci kema kin kasa?,to kiyita kukan,idan kin gama kya kirani na fada miki abinda zan gaya miki" sai ta kashe wayarta,itama bata sake kiran nata ba,sai data gama kukan nata,ta kuma huce sannan tayi kiran nata. ********Cikin kwanakin ya maida kansa busy qwarai da gaske,duk wani tunani nasa da kulawarsa na ga companies dinsa dake nan gombe kano da kuma lagos,kusan tun daga ranar yama mance dasu cikin lissafin rayuwarsa,basu kuma sake haduwa da kowacce a cikinsu ba,kamar yadda suma kowacce rayuwa take a sassanta ba tare da 'yar uwarta ba,duk da cewa sau tari maimunatu takanyi kamar ta leqa su gaisa da unaisan,amma kuma sai taji tsoron yin hakan,musamman idan ta tuna da me gidan kansa "Qila itama irin halinsa ne da ita" abinda zuciyarta take raya mata kenan,saita juya ta koma. Daga gidan dr marwan ake kawo musu abinci kullum,safe rana dare babu gajiyawa,kullum maimunatun ke amsa,ta kuma barshi saman dining na main parlor na gidan idan ta diba yadda zai mata,wanda yawanci ma idan ta diba na rana ita shike kai mata har dare,bata sake neman wani kalar abincin. Ba kasafai yake dawowa gidan da wuri ba,yakan kai tara ko goma,kuma daya dawo ya haye samansa yake rufewa,idan ba wani babban uzuri ba baya saukowa sai washegari,takwas na safe ya fice sabgoginsa,saidai lokaci lokaci yakan sauko ya duba cikin gidan ko akwai wata matsala,sai ya tabbatar da babu wani abu da ake buqata sannan ya sake komawa,a hakan suka kwashi sati biyu cur,a ranar suka tashi shuru babu saqon abinci,dama kuma maimunatu ta tsammaci hakan,don haka qarfe sha daya saura bayan tayi wanka,ta danyi gyare gyarenta cikin daki wanda basu da yawa,tayi wanka ta shirya kanta cikin wata army green din atamfa me maroon din ado saita fita zuwa kitchen don samawa kanta abinda zata saka a bakinta. Ruwan tea ta dora,ta kuma hada kayan qamshi kamar yadda ta koya daga wajen baba tabawa,sannan ta juya ta laluba dankali ta debo bayan ta kwashe wadanda suka lalace saboda kwanakin da suka dan dauka ba'ayi amfani dasu ba,ta dauko qwai guda biyu ta fara aikinsu. Tana aikin tana kuma tunane tunane,abinda ya zame mata jiki,a zaman kwanakin da tayi cikin gidan,zaman kadaici,da za'a irga adadin tunanin da tayi zata tashi wani dan qaramin littafi,ta saqa burika masu yawa da takeson cimmawa a rayuwarta,wadanda bata da tabbas din wanzuwarsu,tunda dai bataga hanya ko qofar da hakan zata kasance ba,nan din tana wani zama ne kwatankwacin zaman mutumin da aka kai prison. Bata dauki lokaci ba,ta gama komai,tuntuni ta juyr tea din a flask,dankalin kuma ta zuba akwando don ya tsane,ta matsa gaba tana neman plate da zata xuba,tana ta kokwanton ma zata iya cinyeshi kuwa. A dan hanzarce ta turo qofar kitchen din saboda wata mahaukaciyar yunwa dake sakadar cikinta,ta duba saman dining inda kullum take tadda abinci ta diba ba tare data damu da wanda ke girkawa ba. Motsinta ya sanya maimunatu dake dauko plate dakatawa ta waiwayo,idanunsu suka hadu waje guda lokaci guda,lokaci na farko kenan da kowacce taga 'yar uwarta,kuma kowacce a cikinsu jikinta ya bata. *HUGUMA* 34 *Arewabooks chapter 39* https://arewabooks.com/chapter?id=63637876d52c9563f3289fda _______________________________ Wani kallon qurilla me dauke da mamaki da kuma fargaba unaisa ke bin maimunatu dashi,zuciyarta na qiyasta mata wannan ce maimunatun?,wannan itace kishiyar tata?,yarinyar da duka duka bata wuce qanwarta ta uku biyu ba?,a qalla zata iya bata good five years,wannan zata kalla a matsayin kishiya?,no saidai ta dauketa tamkar 'yar aiki,amma kuma...... she's very beautiful,tana da wani irin kyau daya daki zuciyar unaisan,kyan da idan tace maimunatun ma 'yar aikinta ce ba shakka babu wanda zai yarda,don yarinta kam yarinya ce,amma batun tace 'yar aikinta ce ma bata taso ba,kyan yarinyar ya daketa,ya kuma tsole mata idanu tun daga kallon farko,abinda ya hanata sukuni,ko bayan data qarasa kitchen din tayi abinda zatayi ta fito,wanda gaba daya ruwan zafi ta iya dafawa ta juye a cup ta hada tea ta dauki five slices of bread ta hada dashi ta fita. Ji tayi sam bata jin taste na tea din,sai ta aje ta dauki waya ta kira anty talatu,ta kuma rattaba mata komai "Keba macace bace?,meye na daga hankalinki?" Ajiyar zuciya unaisa ta saki "Ba zaki gane bane anty,ni da nake mace ma kyanta ya tabani,ina ga da namiji?" Murmushi me sauti ta sake "Bakisan namiji ba kenan,shi kam idan zuciyarsa ta qyasa da abu babu ruwansa da kyansa ko muninsa,abu daya ne da zakiyi shine ki kama zuciyarsa da kyau ta duka hanyoyin da suka dace,ba da bakinki kike gayan tafi marigayiyar matarsa kyau ba?" Kai ta gyada kafin tace "Haka ne anty" "To amma me yasa wannan kyan bai sanya ya sota ba har yanzun zuciyarsa naga marigayiyar?" Tambayar da tun kafin ta amsawa kanta ita taji gamsuwa "Exactly" "Da kyau,abu daya ne yanzun zakiyi,ki tabbatar kawai yarinyar bata sake cikin gidan ba,duk yadda zakiyi ki nuna mata a qasanki take,matsayinku kuma ba daya bane,wanna zaisa ta kasa kallon kanta a matsayin cikakkiyar mace da har zata maida hankali wajen ganin tayi tarayya dake akan mijinku,sannan kinfinkowa sanin daga inda ta fito,bata da cikakkiyar wayewar da zaki kasa juyata yadda kikeso,cikin ruwan sanyi zata zame miki kamar qasqantacciyar 'yar aikin ba tare da ta ankara ba" dukka wadan nan maganganun na anty talatu dama wadanda suka biyo baya sunwa unaisa dadi,sai ta saki jikinta suka sha hirarsu,tana sake bata haske game da wasu abubuwan. Cikin zuwan da yakanyi gida wasu lokutan idan ya tashi a aiki da wuri anni tace ya kawo unaisa da maimunatu su gaida surukansu,hikimar hakan kuwa,tayi ne don taga kamun ludayinsa da kuma yadda su din suke zaune,don tun daga washegarin randa aka kaisu ba wani dan gidan daya sake komawa gidan nasa. Baya buqatar magana da kowacce a cikinsu,baisan ta yadda zai sanar musu su shirya ba,don haka sai kawai ya sanya driver ya dauki laila yace ya kaita gidan su taho tare,shi kuma ya wuce aikinsa abinsa. Kamar a mafarki maimunatu taga lailan,ta saki ihun murna ta rungume lailan duk da baqunta da rashin sakin jiki irin na maimunatun,sanda ko ta gaya mata inda zasun ji tayi kamar anyi mata bushara,sati na uku nason cikewa ko farfajiyar gidan bata qara leqawa ba tun randa sukazo tayi musu rakiya,nan da nan ta hau shiri,kafin ma unaisa ta gama laqai laqai dinta ita ta gama shiryawa,cikin wata jar atamfa data haskata sosai. Duk inda maimunatun ta motsa laila na binta ne da ido,tayi wani fresh sosai,fatarta kamar babu abinda yake hawa,saidai kuma babu wata qiba ko murmurewa da tayi,kuma tana da tabbacin inda maimunatun ta qara qiba lallai zama zatayi abar kallo,don komai na jikinta ya soma cika da alamun girma da budurci tare da kwarjini na aure. Sanda suka fito zasu wuce laila ta leqa yiwa unaisa magana,sai ta sameta bata ma shirya ba "Kaina kemin ciwo,kice ina gaishesu,zan sanya lokaci sai mu shigo ji dashi" amsar data bawa laila haushi matuqa,ta kuma fito tana mita,wannan ai tsabar rainin wayo ne,ita dai mainunatu batace komai ba,daga bisani ma sai ta janyo mata hirar islamiyya,wadda takejin kewarta qwarai da gaske,tana jin inama za'a barta taci gaba da zuwa,tana jin rashin dadi kan yadda haddarta ta tsaya cak,duk da tana tilawa a gida. Tsaki unaisa taja bayan jin tashin motarsu,me suka maidata ne?,ko sun manta matsayin ubanta a qasar nan,banda soyayyar da takewa J da ta yaya ma zata zauna a inda take yanzu?,ta yaya zata yarda ta hada kishi da wata bafulatanar ruga?,idan gaisuwar surukai ne ai basai ta hada kafada da 'yar qauyen yarinyar ba,cikin motocinta zata ja daya takai kanta gidan idan fa shirya gaishesun basai an mata jagora ko an tusata a gaba ba. Sai data shiga ta gaida amma da ammi sannan ta yada zango wajen anni,annin na karance da maimunatun sarai duk da ita bata fahimta ba,ta kuma samu gamsuwar gabatarwa da ja'afar qudurinta,don haka sanda yazo washegari gidan,akaci sa'a safiya ce,saboda yau din da yunwa ya tashi,don jiya bai samu tsaiwa yaci abinci a inda ya saba tsaiwa cin abincin ba "Makaranta nakeso ka dauki maimunatu da kanka ka sanyata" ta bashi umarni nakai tsaye idanunta a kansa sanda yake zaune gabanta amna na saman cinyarsa yana bare mata chocolate. A hankali ya daga kansa zai kalleta,sai ya samu itama shi take kallo,ba tun yau ba,yasan anni sarai,yasan kuma tunda ta tada zancan nan akwai abinda ta taaka,kamar zaice wani abu sai kuma yace "Ba damuwa" a taqaice,yadda yayi saurin amsawar ya bawa anni mamaki,ya kuma tabbatar mata akwai wata a qasa,kuma ruwa baya tsami banza,amma kuma zata zanya idanu taga me zai aikata "Idan ka tashi ka hada mata da waya,don ya kamata ace tana waya da 'yan uwanta,bawai don ta taho ta taho kenan ba" "To" ya sake cewa da ita "Kiyi picking ledojin chocolates din ki biyoni mota zaki rakani unguwa" yace da amna bayan ya sauketa daga kan cinyarsa ya kuma miqe,ta sauka kuwa da sauri tana murna,ta hau tsincewar tana ta yiwa anni da ta bishi da kallo surutu,hankalinta bai kwanta ba,tasan halin ja'afar itama,wannan saurin amsawar da yayi ba'a banza ba,amma koma meye ya shirya yi,indai cutuwa ne ga maimunatun ba zata bari ba. Shegen miskilanci gami da zurfin cikinsa yana nan har yanzu,yana da wannan nuna shakulaton bangaron kan abubuwan da yana sane dasu sarai,suna kuma cikin ruhi da zuciyarsa,amma sai yayi kamar bai damu ba,kamar baya ankare da abun,kuma kamar baya gani,saidai duk randa ya magantu ko ya dauki wani action akai kowa zaiyi mamakin hakan,wannan ya sanya anni ta sake sanyama ranta zata kula da komai da irin abinda zai biyo baya,ta sauke ajiyar zuciya tana hade hannayenta waje daya,fuskantar ja'afar ko yin gaba da gaba wajen saukeshi daga ra'ayinsa ya zuwa wani babban aiki ne da ba kowa zai iya shi ba,fatanta ubangiji ya dubesu,rayuwarsa ta sai saita,ya kuma riqe amanar yaran mutane kada suji kunya. *********Kwanaki anni tayita qirgawa tana jiran taji yace wani abu,ko kuma ya tanka game da maganar da sukayi da ita,saida har ta gama irga kwanaki bakwai baice komai akan maganar ba. A daren ranar ya koma gida da wuri kai tsaye daga wani gidan saukar baqi,inda suka tattauna da wani babban mutum da ya bawa company dinsa kwangilar ginin wata university da zai bude. A gajiye ya shigo gidan,ya wuce sassansa kai tsaye ya fidda kayan jikinsa ya watsa ruwa,duk da gajiyar da yayi amma yanason yaje gida wajen anni,don haka sai ya shirya cikin wani irin straight leg jeans da shirt masu azaban kyau,ya kuma sakaya qafarsa cikin wani rufaffen sneakers daya dace da kayan jikinsa,ya sake gyara sumarsa tsaf,kai bakace dare bane,ya dauki maqullansa da wayarsa guda daya a gurguje ya sauko,yana so yaje yayi ya gama ya dawo ya kwanta,don gobe yake sanya ran zai wuce lagos. A nutse yake tuqinsa,yana kuma amsa wayar da suke da jabir ta speaker din motar har ya isa gidan,sai daya tura hancin motar zuwa farfajiyar gidan sannan sukayi sallama dashi,ya dai daita tsaiwar motar a parking lot na gidan yana duban inda masu gidan ke ajiye motocinsu,akwai kotar hisham data abbi duka a wajen,da alama suna gida,sai ya balle murfin motar ya fito zuwa cikin gidan,cikin takun nan nasa dake nuni da qasaitarsa da kuma aji da yake dashi cikin jininsa,duk inda ya gifta sai ya bada ajiyar qamshinsa a wajen,wani qamshi na musamman da zaiyi wahala ka jishi jikin wani,turare na musamman yake amfani dashi,na jiki kuma ya banbamta dana kaya,hakanan na gashin kansa daban da wanda yake shafawa qirjinsa,dama can haka yake,dan gayu ne daya zarta kowa cikin gidan dama familyn khalid akko. Jifa jifa ma'aikatan gidan ke kawo masa gaisuwa har ya dangana da sassan ammansa,wanda kusan ko da yaushe yazo gidan wajenta yake fara zuwa,ya sameta zaune a falon gidan,sanye da hijab,yatsarta kuma sarqafe da da tasbah counter,idanuwanta na kan tv. Fuskarta fadade da fara'a ta gyara zamanta tana masa maraba "Kaine a daren nan?" Ta fada tana ajjiye masa ruwan data dauko masa da kanta,sai yasa hannu ya karba,duk da baya jin qishi amma kuma bazai iya wucewa tayinta ba,saboda kima da martabar da take dashi a wajensa,ya gaidata cikin girmamawa "Lafiya qalau,yasu maimunatu?" Sunan yajishi tamkar baqo a wajensa,don bai gama tantance wacece maimunatun ba,wadda ya lura duk zuwa shine suna na farko da take fara tambayarsa "Lafiya qalau" ya amsa mata,yana zarcewa da shan ruwan daya tsiyaya din,sai daya ajjiye cup din sannan ya dubi amma "Amna fa?" "Ina zaton tana wajen ammi,suna can sassan babanku da ita,yau rigima takeji tun yamma,wai sai an kaita gurin adda maimunatu" bai fahimci gundarin abinda maganar ta amma ke nufi ba,yadai dauka key dinsa ya maqala a yatsan hannunsa yana shirin tashi,dai dai lokacin da salma ta fito daga dakinsu,ta kuma ratso cikin falon cikin kwalliya,tana baza qamshin turare. Kafin ta qaraso ta ankara dashi,sai duka karsashinta ya zagwanye,ta sake saita kanta da kyau don kada tayi wani laifin,ta qaraso ta rusuna tana cewa "Barka da dare yaaya" "Yauwa barkanki dai" sum sum tafara takawa zuwa gaba,sai a sannan ya waiwaya zuwa inda take "Ke!" Ya kirata da nannauyan muryan nan tasa da take sanyasu cikin rudani da tsoro "Na'am yaaya" "Zo nan" ya fada yana mata sign da hannu ba tare daya sake dubanta ba,gabanta nata dukan uku uku ta dawo,ta sulale saman carpet din ta zauna tana dubansa yana danna wayarsa,sannan ya karata a kunne,second uku kacal yace "Ka bude ka shigarmin dasu sassan anni" iya abinda ya fada kenan ya katse wayar,sannan ya maida dubansa ga salma,sai tayi qas da kanta,yana da wani irin kwarjini wanda ba kowa ke iya sanya idanunsa cikin nasa ba "Ina zakije?" Dan muskutawa kadan tayi,duk sanda ya sanyata gaba da wata tambayar komai qwace mata yakeyi,kamar ba ita salman ba,'ya gayu me aji,wadda take kadawa maza ganye,'yar jami'ar dake gab da kammala degree dinta "Yaa..... Ahmad ne yaxo" wani kallo ya watsa mata,wanda yasa tayi dana sanin bashi wannan amsar "Koma ciki ki saka hijab dinki" iya abinda yace da ita a taqaice kenan,ya maida dubansa ga wayarsa,bata da iko ko qwarin gwiwar musu dashi,don dole ta miqe ranta a bace kan yadda zai bata maka kwalliya ta koma dakinsu,ahmad din nan ba baqo bane,koshi kansa yasan da zamansa,tunda sai da iyayensa sukazo nema masa izinin fara zuwa wajenta,amma shi da yake wani irin mutum ne mai shegen tsari da qa'ida,ji yadda yayi kamar bai ganeshi ba. Da sallama ya shiga sassan annin,tana zaune a qasa,ta dora qafafunta saman tuntum,daya daga cikin masu aikinta na mata yankan farce,fa'iza khadija da laila na zaune daga gefe suna kallo duka harda annin. Sallamarsa tasa dukkansu suka gyara zamansu,hadi da hada baki wajen amsa sallamar tasa,anni ta waiwaya ta zuba musu harara "Ya'yan nema marasa kunyar Allah,ni da yake marainiyar wayonku ce magana nayi muku har babu adadi amma ba wadda na samu ta tankani,amma da yake dodon naku ke magana har hada baki kuke wajen amsa sallama kamar na Allah....." Laila daketa motsi tana yiwa anni sign na tayi shuru don Allah amma tayi kamar bata gani ba takasa shuru "Amma anni don Allah ba cewa nayi bari mu qarasa ganin wannan ba?" Da yatsa annin ta nunata "Ke arcan,kiyi ta kanki yarinya,ni zaki yiwa sanabe?" "Barka da dare" mai rahila me aikin ta gaidashi kanta a sunkuye "Kina lafiya" ya maida mata yana daga tsaye "Alhmdlh yallabai" "Ajjiye ki tafi" ya fada mata kansa tsaye,da hanzarinta ta miqe bayan ta ajjiyr nail cutter din,sai data bace a falon sannan ya waiwaya ya dubesu duka su ukun,ya sauke kallonsa ga fa'iza babbar cikinsu "Xoki dauka ki qarasa mata" cikin sauri ta taso ta zauna inda rahila ta tashi "Nidai ki bini a hankali,kada garin rawar jiki ki yankemin jiki ina lallaba rayuwata". "Tashi kije ka karbomin abinci wajen amma,idan kinso ki xauna ko kiyi mistake" ya fada cikin gatse,yana zama a qasan carpet daura da anni tare da duba agogon hannunsa,saura minti daya a fara haska wasan tseren dokuna, favourite thing nasa kenan,ya yiwa khadija umarni da ta bashi remote,tana miqa masa ta samu ta sulale daga falon,ya canza tashar yana jin anni na mitar me zasu kalla a nan?,shi dai baice da ita komai ba ya maida kansa ga kallonsa,har zuwa sanda laila ta dawo da wani qaramin kwando kamar na kaba,saidai an saqa wannan ne da wata irin roba me kyau,ta ajjiye masa a gabansa,sannan ta duqa ta fara shirin serving dinsa. "Stop" ya fada da sauri,a dan tsorace ta daga kanta,sai ya sauke dubansa ga yatsunta ba tare da yace komai ba. A tsorace ya dunqulesu cikin tafin hannunta,sai a sannan ta tuna,babu abinda yafi tsana irin tara farce "Na baki minti biyar ki tabbatar sun koma kamar na hannun kowa" abinda yace da ita kenan,ta gyada kanta tana miqewa,bataso ya gani ba,saboda bikin rumaisa za'ayi,cousin dinsu,diyar uncle umar,mai bin dr marwan. *Ku bibiyi shafina na arewabooks don samun sabbin shafuka* *AREWABOOKS:HUGUMA* INAYA(Riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 35 _INA MASOYA KUMA MA'ABOTA KAMSHI MA SU KAUNAR KAMSASAWA A KODA YAUSHE? DOMIN KAMSHI RAHAMA NE.._ _TO KU MATSO, DOMIN WANNAN KARON MA ZAFAFA BIYAR SUN ZO MU KU DA TALLAN MASARAUTAR KAMSHI NA KAMFANIN TURAREN *YERWA INCENSE AND MORE*_ _A *YERWA INCENSE AND MORE* ZA KU SAMU TURARUKAN WUTA NA *GIDAH, NA KAYA, NA TSUGUNNO* BA A NAN KADAI SUKA TSAYA BA. AKWAI *KHUMRAHS* MASU KAMSHIN LARABAWA DANA FRUITS KAI DAMA KAMSHIN TURAWA. AKWAI KHUMRAHS TA MATAN AURE DA TA YAMMATA_ _SANNAN SU NA DA *TURAREN WANKA DANA SHAFAWA BAYAN AN KAMMALA WANKA.* BA ANAN TURARUKAN NA SU SUKA TSAYA BA. AKWAI *KULACCAM* MAI MATUKAR KAMSHI DA SANYAYA ZUCIYA, SANNAN SU NA DA *MADARORIN TURARUKA NA JIKI DA NA KAYA*_ _AKWAI TURAREN *AL'AJABU NA TSUGUNNO DA KHUMRAH* DIN SA_ _SANNAN SU NA DA *TURAREN GASHI NA CREAM DA KUMA SPRAY DIN SA NA FESAWA*_ _BA ANAN SUKA TSAYA BA. SU NA DA *TURAREN MOPPING, DA NA BANDAKI AKWAI NA RUWAN WANKI DA NA FESAWA A DRAWER KO AKWATI*_ _AKWAI KAYAN GYARARRAKI NA FATA. KUJERAR TSUGUNNO, KASAKE NA WUTA, COAL IGNITER TA KUNNA GARWASHI, ELECTRIC BURNERS DA ENGLISH COAL_ _AKWAI LAFFAYAS DA SAURAN TURARUKA NA KAMSHI KALA KALA_ _SU NA BADA KAYAYYAKIN SU AKAN FARASHIN SARI KO SAYA AKAN DAYA DAYA. SANNAN SUNA TURA KAYAYYAKIN SU KO'INA A FADIN NAJERIYA DA KETARE. KAYAN SU YAN CHADI NE DA SUDAN DA KUMA YERWA WATO MAIDUGURI._ _KYAU, INGANCI DA RAHUSA SAI KAYAYYAKIN KAMFAMIN YERWA INCENSE AND MORE. SAI KUN GWADA ZAKU BAMU LABARI_ _NAMBAR TARHON SU DA ZAA KIRA KO MUSU MAGANA TA WHATSAPP ITACE: 08095215215_ _INSTAGRAM HANDLE DIN SU: @yerwaincense_and_more_ _YERWA INCENSE AND MORE: A NUMBER ONE STOP SHOP FOR HEAVENLY EXOTIC SCENTS AND MORE_ _________________________________ Ficewarsu sai falon ya zamana daga shi sai annin,yaja kwanukan yayi serving kansa da kansa,ya dauki plate din ya dora saman qafafunsa ya fara ci. Duka anni na karantarsa ba tare da tace komai ba,yadda yake cin abincin nasa ya sake tuna mata da ja'afar din,har yanxu qasaitarsa da jan girman nan nasa yana nan,rashin daukan wasa qarancin magana da rashin walwala,saidai kuma baya wasa da cikinsa,har yanzunma haka abun yake,yadda taga yana cin abincin ya tabbatar mata babu komai a cikinsa "Ni na rasa wanne irin wayo da dabara ne wannan,ka baro abincin mata har biyu a gidanka kazo kana cinyewa bayin Allah abinci?" Idanunsa ya sauke ka fuskar anni,da gangan take musu gorin abinci,duk sanda kaji tana gorin abinci to 'yan rigimar nata ne a kusa,batasan cewa shima yau da tasa rigimar yaxo ba,don haka baice mata ta tafas ba,sai daya gama yana goge hannunsa da tissue,duk da ba da hannun yaci ba,ya janyo takardun da yasa a shigo masa dasu ya ajjiye a gabanta. Kallon takardun tayi sannan ta maida dubanta gareshi tana bata fuska "Meye wannan din?,kasan dai ba wani bokonku nayi ba da zaka turon takardu gaba ko kana wani cushe fuska kamar tsohon kashi" can qasan ransa ya murmusa,amma ko days ba alamun murmushin a saman fuskarsa,yasan zata fadi sama da haka ma idan tana jin rigimarta "Takardun makaranta ne da kika nema a samar mata" fuska ta yatsine "A samarma wa?" Ta fada tana jifansa da kallo "Kin manta maganar da mukayi kenan?" "Na manta,saika tunamin" hannu ya miqa ziwa gabanta zai janye takardun nasa yana fadin "Duk randa kk tuna zan dawo saimu qarasa tattaunawar" "Kaniyarka.....kaniyarka nace" ta fada bayan ta danqe hannunsa "Ka kirata da maimunatun kake ganin asara?,manya....manya ka kiyayeni" sakar mata takardun yayi,ya koma baya yayi relaxing yana dubanta cikin calmness din nan nasa,har ta gama fadanta,sannan don kanta tace "Ina jinka,wacce makaranta ce?" "Pen resources academy" ya amsa mata a taqaice,shuru ta danyi don makaratar ta kwanta mata,kafin ta sake cewa wani abu hisham yayi sallama falon,saita diba takardun ta miqa masa tana cewa "Dubamin da Allah,wacce makaranta ce wannan?,tana da kyau ko kuwa lullubin biri ce?" Qunshe dariyarsa yayi,da alama yayan nasa ya yiwa anni halin nasa,sabgarsu shida annin babu me shiga,idan ka shiga kunya zakaji wajen anni,saidai kuma idan suka tashi al'amarinsu saisu. Duba biyu ya yiwa takardun ya gama fahimtar komai,me yasa yayan nasa zai dauki maimunatun ya kaita boarding school,duk da cewa ba nisa bane a tsakaninsu,amma koma meye ita din a yanxu ai matar aure ce,eh makarantar nada kyau da kuma tsari me kyau,saboda private ce da ake biyan maqudan kudaden da sai dan wane da wan ke yinta,to amma ya manta igiyar aurensa dake kanta?. "Ya ka tsaya?,tana da kyau?" "Sosai ma anni,makaranta kwana ce,tana gombe bauchi road" da fari a zafafe ta daga kai ta dubi ja'afar din da niyyar qare masa tatas,saidai kuma yadda ya kashingida hankali kwance kamar baisan abinda ke faruwa ba ya tabbatar mata da biyu ya aikata hakan,saita jinjina kai,ta kuma maida dukka wani fadanta data debo niyyar yi masa,zata bishi ta yadda ya biyo,amma kuma tabbas yaci bashi ne,zai kuma gane ta yaro kyau take bata qarko. **********washegari******* Daya idar da sallar asuba bai koma ba,saboda tafiyan dake gabansa,zaibi flight ne da zai tashi qarfe goma na safe,waya ya amsa me dan tsaho da CEO na wani company da yakeson zuba hannun jarinsa a kamfaninsu,yaci a qalla awa daya cikin wayar,har sai daya fara murza goshinsa saboda maganar ta fara hawan masa ka,bai fiya jurewa doguwar magana ba,ya bashi excuse kan cewa idan ya gama abinda yake bayan ya shigo lagos din zai nemeshi,da haka sukayi sallama. Ajiye wayar yayi yana lanqwasa yatsun hannunsa da yaji sun sage masa,ya kalli agogo,qarfe takwas da ashirin,yana son shiga gym room amma lokaci bazai bashi dama ba,don haka ya miqe yana nufar falonsa don ya hada koda coffee yasha ne ya dumama cikinsa. Coffee powder din ya duba yaga ya qare,dole kenan sai ya sauka kitchen dinsu ko zai samu wani,sai ya zura slippers dinsa masu taushi,ya nufi qofa yana gyara maballin pyjamas din dake jikinsa. A hankali yake saukowa daga stairs din,falon shuru yake kamar kowanne lokaci,ya ratsa ta cikinsa ya wuce dining area ya wuce kitchen,hankalinsa da tunaninsa yana can ta wani waje daban. Dai dai lokacin da take kwashe gasashen dankalin data hada masa wata 'yar source data wadata da albasa da koren tattasai da nama da aka yiwa yankan cube shape,tana sanye da wata night gown mai taushi,me dogon hannu ce data sauka mata har qasa,ta sanya baby hijab dinta shima kalar rigar,abinda yasa baby face dinta sake fitowa sosai,quruciyar dake tattare da ita na sake fitowa. Kusan a tare suka daga kai suka kalli juna,saura kadan ta saki frying pan din dake hannunta,tayi hanzarin ajjiyeshi,sannan ta duqa har qasa ta fara gaidashi kamar yadda take masa. Ciki ciki ya amsa idanunsa na sauka kan dankalin,ya mishi wani kallon qyanqyami yana matsawa gaba ya fara duba kayan da suka kawoshi kitchen din,ci gaba tayi da tsugunnawa a wajen,turarensa na cike ilahirin kitchen din,kamar a yanzun ya fesa shi a jikinsa,ya gama daukan abinda zai dauka,ya nufi qofa. Har ya kusa fita ya tsaya,yadan tako baya kadan yana cewa "Ki shirya anjima kadan hisham zaizo ya daukeki,zai kaikai makaranta zasuyi miki interview,next week zaki fara zuwa,ko ince za'a kaiki keda kayanki,after every Three month zaki dinga dawowa hutu kafin ki koma" ya mata maganar gwari gwari,saboda gani yake babu abinda ta sani,babu kuma abinda take ganewa,idan ma yace mata boarding school ba lallai ta fahimceshi ba. A ba zata albishir din yazo mata,don ko a mafarki bata taba kawo hakan ba,bata taba tsammanin haka ba,tunda a society din data tashi bata ga ana hakan ba,cikin ruhinta ta dinga jin wani farinciki da bashi da misali yana kutsawa,ashe dai tana da rabo,ashe dai burinta zai cika?,tana shirin buda baki tayi masa godiya ya fice abinsa,yana fitar ta miqe cikin farinciki,tayi wani dan tsalle,ta qanqame jikinta waje guda tana fadin "Alhamdulillahi,miyatti Allah" cikin walwala karsashi da kuma kuzari taci gaba da aikin nata,Allah Allah take ta gama ta shirya,batason yaa hisham din yazonya jirayeta,tunda bai gaya mata qarfe nawa zaizo din ba. Sanda ta kammala girkin unaisa ta shigo,kamar ko yaushe cikin takun taqama isa da jin cewa NA FIKI FA,ta qarasa inda maimunatu ta adana warmers din,tasa hannu tana budewa,kafin ta zaqulo faranti cikin nata kayan kitchen din tasa serving spoon ta fara diba ba tare data ce da maimunatun kanzil ba. Bata daga kai maimunatun ta kalleta b,don kusan ta saba da hakan,ita ke girkin safe da kuma na dare amma unaisan tana rigata ci,da farko iya cikinta take,ganin unaisan tana diba ya tabbatar mata itama tana buqata,duk da bata taba budar baki ta gaya mata hakan ba,shi yasa idan ta tashi yi takeyi harda ita "Ina kwana?" Ta gaidata kamar yadda kowanne lokaci take mata,ganin cewa ya girme mata,ita kuma tana mata kallon yaya ne a wajenta,tunda shekaru da tazarar dake tsakaninsu tana da yawa. Bata amsa mata ba,saima dawowa da tayi ta dubeta "Daga yau idan kin gama girki,a cikin warmers dina nakeso a dinga xubashi,banason amfani da kayan kowa" ta fadi tamkar me magana dame aikinta. Maimunatun bata kawo komai cikin ranta ba,hakanan ranta bai wani baci ba,cikin girmamawa ta amsa mata da to,sai tasa kai cikin izza tana fita daga kitchen din. A kan lokaci maimunatun ta gama komai,ta gyara wajen ta wuce dakinta,daga nan toilet ta fada ta soma wanka. Yana gaban madubi yana amsa wayar muzaffar, cousin dinsa,kuma daya daga cikin ma'aikatansa dake aiki companynsa na lagos,gyara tie din suit dinsa yake,yana dai daita wuyanta yadda ba zata dameshi ba,ya gama ya dauki comb yana sake gyara qawatacciyar sumar kansa wadda take fidda sassanyan qamshi tare da wani sheqi na musamman da takeyi. "Okay,zan kiraka idan na iso,ka zama ready,banason jira" ya fada yana jefa comb din inda ya daukoshi tare da gyara hannun suit din nasa wanda aka yiwa wani ratsi daya sake qawata ta tare da nuna ainihin tsadar da take dashi,jikinsa sai fidda qamshin turaren bad boy yake na kamfanin carolina Herrera yakeyi,nan gaban madubin ya zauna,ya janyo sock dinsa ya sanya,sannan ya dauko takalminsa qirar qasar Italy dake daura da inda yake ya saka,sai ya miqe daga durquson da yayi yana furzar da iska cakude da ajiyar zuciya daga bakinsa,hadi da lumshe idanunsa yana tuna shaheeda,baisan dukka irin wadan nan wahalhalun ba muddin suna tare,komawa yake dan lelenta,bata barinsa yayi komai. Karar da yaji cikin wayarsa ya sanyashi hanzarin duba fuskar wayar,sai ya miqe yana daukan wayarsa,ya kuma janyo trolly dinsa zuwa qofar dakin,yana dora handle dinsa a bakin qofar unaisa tana turowa itama. Da kallo kadan ya bita dashi bayan ya janye mata baya,tana sanye da wata doguwar riga mai budadden hannu silk material butter color,tayi ado sosai wanda ya bayyanar da zallar hutu da jin dadin data samu tun daga gidan mahaifanta,saboda yadda farar fatarta take a kwance very smooth,bakinta sai qyallin lip gloss yake,tana tauna chewing gum a hankali. "Gud morning dear" ta furta tana murmushi tare da sake takowa gabansa,sai ya dan goce kadan yana amsa mata can qasan maqoshinsa "Morning" idanunta ta sauke kan akwatin hannunsa,da alama tafiya zaiyi,wanda ko alama itakam batasan da zamanta ba,tadan bishi da kallo sanda ya sanya hannu ya bude aljihun gaban trolly dinsa,kudade ya ciro,ya matso daura da ita kadan ya ajjiye yana cewa "am going to travel somewhere,zaku iya kiran number dake jikin nan whenever you need something" binsa tayi da kallo sanda ya gama jawabinsa,ya kuma taka cikin cikakkiyar nutsuwarsa ya soma barin falon "Ba wannan nake buqata,ba kudi nake so ba,ba kuma shine ya kawoni ba" cak ya tsaya daga tafiyar da yake,hannunsa daya na soke a aljihun wandon suit dinsa yana kallon qofa ba tare daya juyo ba,kamar kuma bazai juyo din ba,kamar yadda kuma yanayinsa ya nuna baida niyyan yin magana,saidai kuma faaida trolley din yayi,ya waiwayo ya kuma fara dawowa,cikin wani irin yanayinsa dake saurin sanya karaya da karyar da duk wata zarra jin kai da jin isa na 'ya mace ya aza mata idanunsa,a gabanta ya tsaya yana dubanta,ya sake sakaya daya.hannun nasa dake waje cikin aljihun wandon nasa,yadan raba qafafunsa kadan "Me kike da buqata?" Ya furta with husky voice,wadda bata sauka ko ina ba sai tsakiyar zuciyarta,ta kuma nada ajiyar wani yanayi mai tsauri ga zukata. Nata idanun ta daga da niyyar gaya masa abinda yake ranta quru quru,saidai inaaa,zarrar ba daya bace,don kuwa kasa qarasar da kallonta tayi izuwa fuskarsa,saita zube idanunsa a qirjinta,wanda iya nata tsahon kenan "Iya abinda zaki samu shi nake baki,indai wannan jikin kikeso,to a shawarce ki koma gida,don abune da bazai taba samuwa ba wajen wata har abada....." Daga haka ya juya abinda hankali kwance,ya riqe trolley dinsa ya fara turata waje,sai a sannan yace mata "Idan kin gama abinda zakiyi kina iya ki rufemin dakina" sai ya qarasa tura akwatinsa ya fice. Wani wawan kuka ga saki sannan ta sulale a waje ta zauna,ya Allah,itakam wanne irin abune J yakeso tayi?,wanne abu zatayi taja hankalin ja'afar,saita kifa kanta saman kujerarsa tana sheshsheqa. A shirye tsaf cikin Egyptian hijab ta fito ruwan golden yellow,tayi matuqar kyau qwarai,kyakkyawan fuskartan nan me dauke da wani lafiyayye kuma boyayyen kyau tayi fayau tsakiyar fuskar hijabin. Yana zaune cikin motar w farfajiyar gidan,don bai shiga ciki ba tunda yasa daya daga cikin masu gyaran farfajiyar yayi mata sallama,wayarsa na a hannunsa yana chart,ya bude qofar mazaunun gaba dake daura dashi,takun tafiya ya sanyashi daga kansa,ya sauke su ga madubin dake gefan murfin motar,fes ta fito a ciki,tana takawa cikin nutsuwa inda yake tsimayinta din. Gabansa yadan fadi,ya lumshe idanunsa yana sauke ajiyar zuciya,kana ya kauda dubansa daga gareta,kasancewar yasan haramcin aikata hakan a yanzu,har yau yana jinta a ransa,kuma har yau yana jin zafin rasata,tun daga randa zai shiga dakin anni yaji tana masa tayin auren yayan nasa yakejin wani abu ya tsaye masa a wuya,saboda tabbacin rasatan da yayi,amma yayi namijin qoqarin ganij ya fidda komai daga ransa,tunda yana da tabbacin ya rasata rashi na har abada. Baisan me yahau kan yayanshi ba daya kasa gane baiwar da Allah yayi masa,ya kuma yi masa musaya na abinda ya rasa,duk da baisan gaibu ba,amma yana da yaqinin idan maimunatu batafi marigayiya quality ba,to tabbas marigayiya ba zata fita ba,ko yanzun driver yaji yana zancan ya kaits makarantar,sai yaga rashin dacewar hakan yace zaije. Sauke qafafunsa yayi ya gyara zamansa gami da ajjiye wayar sanda ta iso dab da motar,ya sanya hannu yana laluba maqullin tare da amsa sallamarta sanda take yunqurin shigowa cikin motar cikin nutsuwa da kamewa "Ina kwana ya hisham?" Murmushi ya sakar mata "Haba anty moon,ai kya bari na fara gaidaki dai ko?,matar babban wa yayace itama" kunya ce sosai ta kamata,tayi qasa da kanta tana yaba karamci da kirkinsa,shi kam halinsa yasha banban dana dan uwansa,tasan hakan tun ba yau ba,tun tana gidan dr. Motar ya kunna suka fito daga unguwar gaba daya suka hau main titi da zai kaisu pen resources,rashin sabo ya haifar da shuru a tsakaninsu,duk da yaso yadan jata da hira ko zata sake amma sai ya fasa,sabon album na wani waqar hausa ya sanya musu,duka sai sukayi shuru kowa yana saurare,musamman maimunatu da batasan waqoqin ko kuma mawaqin ba,ta dinga bin duka baitukan cikin zuciyarta tana nazartarsu,sai taji waqoqin sun mata,suna kuma motsa mata wani da wani abu ckin zuciyarta,duka baituka ne da suka shafi soyayya da qauna,masu taba zuciyar duk wanda yake cikin soyayya. Sanda suka isa makarantar ayi mata dukka abinda ya dace,an kuma ce next week ne zasu fara daukan sabbin dalibai kamar yadda ja'afar ya gaya mata,sosai farincikinta ya nuna,har hisham yana tsokanarta,ya zaci hukuncin da yayan nasa ya yanke bazai mata dadi ba,sai kuma yaga akasin hakan,tabbacin mutum ce ita mai tsananin son karatu. Kasancewar batasan hanya ba yasa bata gane inda ya nufa da ita ba sai da suka je,gidan anty maama,abinda ya yiwa maimunatu dadi qwarai,ko babu komai zata miqe qafarta ba zata koma waccan kurkukun da wuri ba,karon farko data soma zuwa,qawataccen gida mai bala'in daukan hankali da nuna gayu da kuma dukiya,cikin tafkeken falonta na alfarma ta saukesu,farinciki fal zuciyarta,ta rasa wacce irin sauka zatayi musu,take tasa masu aikinta suka cika musu gabansu da kayan ciye ciye har babu adadi "Amma dai ba daga gida kuke ba,don nasan J bazai barku ba" anty maama ta tambayi jabir sanda maimunatu ta shiga toilet don tayi futsari ta kuma hado da alwalar sallar azahar,saboda mukhtarinta ya shiga,yana bare ayaba mutuniyar tasa ya amsa mata "Daga makaranta,na kaita sun mata interview" "Makaranta?,wacce?" "Pen resources boarding" "What?" Anty maama ta fada cikin mamaki tana kallon hisham,kai kace shine ja'afar din "Bama day din ba?" Ta sake tambaya "Yadda dai kikaji haka ne" ya amsa mata yana tauna ayabar,don shima bashi data cewa akan al'amarin J din "Meye hakan yayi kenan?,mtseew lemme call him,wannan sam bai dace ba,yana son yayi avoiding nata ne akwai a fakaice,ya Allah.....wanne irin mutum ne J din?,kuma anni ta sani ta barshi?" "To ya zata masa,badai matarsa bace?" Wayarta ta janyo ta fara laluban layin jaafar din,wanda a dai dai lokacin yana kwanye bayan lafiyayyar motar company dinsa datazo daukansa,a nutse ya daga wayar yana duba me kiran,sai ya daga ya kara a kunnensa. *GURBIN IDO* 36 *Arewabooks:HUGUMA* https://arewabooks.com/chapter?id=6364b7c12730d61e09816f8b __________________________________ "barka da warhaka" anty maama ta fada,yadan saki muryarsa kadan,duk da haka akwai heaviness din nan a cikinta dake qara masa kwarjini ya amsa mata "Barka kadai,yasu hamood" "Kowa yana nan lafiya qalau" "Ma sha Allah" ya amsata a taqaice,sai ta danyi shuru kuma,ita kanta wani lokaci kwarjini yake mata,duk kuwa da cewa duk irin miskilanci da zafin kai irin nasa bai taba qin bata girmanta ba,saidai babu wani dogon magana me yawa tun dacan a tsakaninsu,shi yasa lokuta da yawa hisham dinne abokin maganarta,amma tuna wannan attitude din nasa na respect ya bata nutsuwar cewa "Muna tare ne da hisham,yanzun yake gayamin wai kaine kace akai maimunatu boarding school?" "Maimunatu?"ya dan maimaita sunan,sai kuma yace "Oh.....eh,hakane,abinda anni ta buqata kenan,komawarta makaranta" "Amma sai nakega anni bawai tana nufin a kaita makarantar kwana ba ko?" Ta fada cikin kwantar da murya "Ban sani ba gsky,na duba kawai makarantar dake da kyau ne,kuma sai naga kamar abun arziqi nayi" shuru tayi ta jinjina kai "Shikenan,Allah ya rufa asiri" "Qarata ya kawo kenan?" Ya jefa mata tambayar,saita gyada kanta da sauri "A'ah sun dai biyo ne shi da ita mu gaisa" "Ok,yayi" ya fada kana ya sauke wayar yana kashewa ba tare da yabi ba:asin me yasa suka biyo din ba,tunda basu gaya masan xasu biyo ba. Gefe ya aje wayar yana duban titin lagos da suke ratsawa cikin sa'a yau babu cinkoso da yawa,sai yake jinsa sakayau,ya rufe case din wannan,saura dayar,ita dinma da bata wuce lavel don boarding din ba hadasu zaiyi ko xai samuu peace of mind,haka kawai ya samu yana lallaba rayuwarshi annin ta hadashi da aiki. **********Bakwai da rabi na safiyar litinin a pen resources academy tayi musu ita da hisham wanda shine ya kawota da kanshi,sanye take da uniform dinta da duk wani abu da sabon dalibin boarding na private school zai buqata,ba wasu kaya bane masu yawa,saboda makarantar suna da tsari ba kamar government boarding school ba,makaranta ce ta wadanda sukaci suka tada kai,saboda haka duk wanda ka gani a cikinta ba dan kuci ku bamu bane. Tunda suka shiga makarantar ta tabbatar da haka,duba da irin motocin da suke sauke daliban da a yau suka dawo daga hutun zangon qarshe na shekara. Sai da aka kammala komai hatta daki aka bata hisham yana zaune,bayan ya tabbatar komai yayi settling ya dubeta,murmushi yadan qwace masa ganin yadda idanunta suka tara qwalla "Zan koma matar babban yaaya,Allah ya bada sa'a,yasa a fara a sa'a" hakanan sai taji zuciyarta ta karye,kamar wadda aka kai nisan duniya,tana qoqarin maida qwallarta ta amsa da amin,tana nan a tsaye har ya isa motarsa ya budeta ya shiga,har ya tadata sai kuma ya kashe ya sake fitowa,hannunsa dauke da madaidaicin kwali ya miqa mata "Na manta,ga waya koda zaki buqaci communicating da mutanen gida" wayar ta kalla sannan ta maida dubanta gareshi,wannan shine karo na farko da aka soma malllaka mata waya a rayuwarta,sai tasa hannu bibbiyu ta karba tana masa godiya "Babu komai fa" ya sake amsa mata yana murmushi,har zuciyarsa yana jin tausayinta,tun dava randa laila ta bashi labarin wacece ita,sai data ga fitarsa a makarantar,sannan ta juya jiki a sanyaye,saita duba agogon dake daure tintsiyar hannunta,lokacin shiga aji yayi,don haka ta ciro school bag dinta dake saqale a bayanta ta cusa wayar a ciki sannan ta kama hanyar da classes dinsu yake. Da sallama ta shiga ajin,sai ta dan tsaya tana dawurwura,don ajin adan hargitse yake da hayaniyar dalibai,wanda basu ma lura da wanda ya shigo din Ta gefanta taji alamun shigowa,saita waiwaya kadan,daliba ce kamarta take shigowa ajin,hannunta dauke da water marker da kuma wasu litattafai,suka hada idanu saita dauke kanta,ta isa gaban allo ta zube marker din,sannan tazo zata giftata,har tadan gota ta waiwayo ta dubeta "Sabuwar daliba?" A hankali maimunatun ta gyada mata kai,sai ta waiwaya tana duban cikin class din sannan ta sake maido dubanta gareta "Ga seat din muje ciki" hakan ya bata damar bin bayanta,har suka isa gaban wani seat,sai taga ta zauna daga gefe,kamar yadda ta karanci duk set daya yana daukan mutum biyu ne "Zauna a nan,akwai abokiyar zamana,amma dawowarmu wannan hutun ashe ba zata dawo ba,an canza mata makaranta,saiki maye gurbin wajenta" tace da maimunatu tana dauko jakarta gami da zugeea tana fiddo da sabin exercise tana dorsawa saman desk din "Na gode" ta amsa mata a taqaice,cike da tsarguwan kallon qurillar da daliban ke binta da shi. Tun zamansu a wajen ta fuskanci lokaci bayan lokaci sukan hada idanu da class captain din,wadda taji suna kira da afrah Ateeq Muhammad,tana taqaitawa da afrah A muhammad,duk sanda suka hada idanun sai ta dan sake mata murmushi kawai taci gaba da abinda takeyi,itama maida mata martani take,sai taji kallon bai dameta ba. Lokacin break har tayi gaba sai ta dawo ganin maimunatu a zaune "Zamuje dakin cin abinci,ko kinsan hanya?" Kai ta girgiza "Okay,kina iya tasowa mu tafi" "Na gode" ta fada tana miqewa,ta ajjiye jakarta tabi baya afran. Abinda ta lura afra nada kirki,tana kuma da kyakkyawar mu'amala da jama'a,hakanan tana da mutane sosai,a nutse take,bata da tarin hayaniya ko rawar kai,tare suka gama cin abincin sannan suka dawo aji. Karfe biyu aka tashi daga makaranta,masallacin cikin makaranta taga yawancin daliban suna tafiya,bataga afran ba,don gab da zaa tashi ta fita a class din,tana buqatar koyon wasu abubuwan da kanta,don haka sai kawai tabi sahun daliban itama ta wuce zuwa masallacin. Batayi gaggawar barin masallacin ba sai data fuskanci lokacine na komawa daki kowa ya huta,ta dauki jakarta ta nufi inda dakunan kwanan dalibai mata yake,tana tafiya ne a hankali don kada ta bace a dakin,jifa jifa tana cin karo da dalibai a verender,duk wadda tazo giftatan kuma sai ta bita da kallo,a haka ta isa dakinsu,ta murza handle din sai taji qofar a bude take,ta tura da sallama tana shiga. Madaidaicin daki ne,mai dauke da gadon kwanan dalibai guda hudu,shimfidadden tiles qaramin toilet da kuma locker ajiyar kaya da aka bawa kowanne dalibai,wutar na'urar solar da fankar sama dake juyawa a hankali,fes dakin yake sai qamshin freshener da yake fiddawa. Gadon da yake qasan nata gadon tunda a sama take taga mutum a kwance,ta motsa sannan ta dago tana amsa sallamar tata,suka hada idanu,sai taga afra dince,murmushi tayi mata tana miqewa daga kwanciyar da tayi "Ah,baquwa,ashe dakinmu daya?" Murmushin itama maimunatu ta maida mata "Ban sani ba nima sai yanzu,dazun da nazo ajjiye kayana babu kowa a dakin" "Yanzun ma saini kadai,su feena basu shigo ba,sun tsaya karbomin magani a pharmacy" afra ta fada tana dan yatsina fuska "Ayyah,baki da lafiya ashe?" "Wlh,yau duka daurewa kawai nakeyi,da ciwon mara na tashi" ta fada tana cije labbanta,da alama ciwon ya motsa mata ne "Sannu,Allah ya sawwaqe" "Ameen na gode" ta fada tana kwantar da kanta saman qafarta,maimunatu kuma ta matsa gaba kadan,ta taka gajerun steps din da suka sadata da gadonta,ta ajjiye jakarta ta kuma canza uniform din jikinta zuwa kayan gida a dan wajen da suka kebe saboda sauya kaya. Leqawa ta sakeyi tana yiwa afra sannu,dai dai lokacin da wasu 'yammatan guda biyu suka shigo dakin bakunansu dauke da hira cai cai,da alama wata gulmar suka qunso daga waje suka shigo da ita. Bin maimunatu sukayi da kallo,duk da a dazun sun ganta a aji,da alama suma suna mamakin ganinta a dakinsu,duk da dama sunsan akwai sauran space na abokiyar karatunsu data canza makaranta. Itama dan bin nasu tayi da kallo,dukkansu kana dubansu zakasan cewa kowacce daga gidan gata ta fito basai an gaya maka ba,ta amsa sallamarsu tana debe idanunta daga kallonsu,suka qaraso kusa da afra,kusan a tare suka ce da maimunatu "Sannu New roommate" murmushi tayi musu "Sannunku" "Sunana fatima baqo" sai dayar ma ta kama "Ni kuma ummu ayman buhari" ta qarashe maganar tana miqa mata hannu "Maimunatu Abubakar muhammad" ta amsa musu tana miqa musu nata hannun itama "Nice meeting you" suka amsa fuska sake kaman sun saba da ita dama can. To hausawa sukace juma'ar da zatayi kyau tun daga laraba ake ganeta,dukkan alamu sun nunawa maimunatu zataji dadin zama da abokan karatun nata ainun tun a waninsu na farko,wasu irin mutane ne masu sauqin kai da kuma dadin zama ainun,yadda suke nan nan da ita da kuma haba haba sai ka zaci an jima da haduwa tare. Takeaway mai yawan gaske suka zube musu sukaci,sunayi suna duba jikin afrah,duk da cewa da sauqi saboda maganin data sha,har sukayi sallar la'asar,sannan suka fara shirin tafiya islamiyyar cikin makarantar,wadda suke shiga hudu na yammaci "Inaga tunda ku kun saba zuwa,kuje kada ku rasa karatunku na yau,ni zan zauna da sister afra(ta fadi kamar yadda taji suna kiran juna),idan yaso ko zuwa gobe sai na fara zuwa"abunda ya yiwa afran dadi qwarai,ta kuma sake jin maimunatun cikin ranta fiye da daxun farkon zuwanta,bayan fitarsun kuwa hira suka dinga yi sosai da afran,a nan ta fahimci dukkansu 'ya'yan manya ne,sai maimunatun taji a ranta ya kamata ta kama kanta,tunda ita din ba 'yar kowan kowa bace,amma duk da hakan sai ta saki jikinta,ta dinga dan tambayar afran game da wasu abubuwa na makarantar,ta samu haske kuwa sosai,don su tun daga js one suka fara,ba kamar ita ba data datsi ss one. Ta fahimci team ne na masu son karatu aka hada daki guda,afra ayman da fatima,wannan yasa itama ta sake jaddada niyyarta na zage damtse tare da yin karatu tuquru haiqan,son karatunsu ne ya sanya a aji suka raba set,don kada suje kasa maida hankali,kowacce a cikinsu akwai babban alqawarin da aka yi mata daga gida na idan ta gama ta fita da sakamako me kyau a dukka record nata,to zata zabi duk abinda takeso kuma shi za'a bata,wannan yasa a tsakaninsu duk term ake samun first second and third position,saidai sukanyi exchange a tsakaninsu wata ta karbe position din wata. Fadan me uwa inji hausawa sukace,idan ana masa mara uwa labewa yakeyi ya saurara ya kuma yi aiki dashi,dama da niyyar karatun ta shigo,haduwarta dasu afra yasa ta sake ninka qudurinta. Kusan abinda ya tashi hirar qarar wayar afran dake daman katifarta,ayman ce ta miqo mata,tana duba number ta miqe ta haye gadonta basu sake jin motsinta ba,maimunatu dai na jinsu suna mata tsiya amma bata fahimta akan meye ba,don tayi nisa a tunanin yadda zata tafi da tata rayuwar,qarar wayar ya sanyata tunowa da tata wayar da yaa hisham ya bata,ta miqe ta haura,ta dauko tata jakar ta bude ta ciro wayar ta bude kwalin. Ido da baki ta saka tana kallon kyan wayar,sai takega wayar tafi qarfinta,ko ba's gaya mata ba tasan mai tsada ce ainun,don haka ta bude cikin locker dinta ta turata ciki ta mayar ta rufe. ********Cikin kwanaki qalilan sabo mai qarfi ya shiga tsakaninsu,musamman tsakaninta da afra,irin sabon da ita kanta maimunatu tayi mamaki,saboda sabo ne da tun zuwanta duniya batayishi da kowacce halitta ba idan ba mahaifiyarta ba,tunda kusan a tsangwame ta tashi,batasan dangin mahaifinta ba,dangin mahaifiya kuwa babu wannan fuskar,wajen inna furera ma kam ba'a wannan maganar,bata jima sosai tare dasu anni ba bare ta gama tantance wannan,duk da dai alhmdlh,ta samu sakewa sosai dasu,don ma ta gaza sakin jiki dasu,wala'alla don tana musu kallon iyaye,su laila kuwa sun dan girme mata kadan,fa'iza da khadija ne kusan sa'anninta. Yadda suke rayuwa basa boyewa junansu komai,infact tama lura kusan kowa yasan family din kowa,don ko waya daya tayi da gida zatace wance tana gaidaku,kusan tasan labarin kowa a cikinsu,har da na mahaifin afra da bashi da lafiya,wannan yasa itama bata boye musu ko wacece ita ba,ta shaida musu,saidai bata gaya musu tana da aure ba. Zamansu tare ta fara koyon abubuwa daga garesu,kowacce nada tarbiyya gwagwadon iko,hakanan itama sun fara koyon nata dabi'un,ada basu wani damu da islamiyya ba,bata dadasu da qasa ba,suna zuwa,amma suna mata asha ruwan tuntsaye,zuwan maimunatu da yadda sukaga ta maida hankalinta ga zuwan,shine yaja hankalinsu,ita da kanta data fuskanci yadda malamin yake da sauqin kai fahimta da kuma iya koyarwa ya sanya ta roqeshi da kanta ya sanya musu wasu litattafan,hakan yayi masa dadi shima,saboda kusan itace daliba ta farko data fara mai da hankali kan karatun,harta nema a sanya musu wasu litattafan bayan qur'ani da ake musu,ba bata lokaci kuwa ya laluba litattafan da suka shafi fiqhu hadis da sira ya saka musu,tun dalibai da dama basu wani damu da karatun ba,sai gashi sannu sannu abun yana jan hankalinsu,ba'a wani bata lokaci ba islamiyya ta cika da dalibai,abun da ya fara tambara sunan maimunatu a makarantar,haziqa ce sosai musamman ta fannin islamiyya,bangaren boko ne yake dan bata kashi,saboda kusan jumping tayi,a sannan taga amfanin lesson din da anni tasa aka dinga yi mata lokacin da tana gida,ya taimaka mata matuqa da gaske,da batasan yadda zatayi da karatun makarantar ba. *GURBIN IDO* 37 *AREWABOOKS:HUGUMA* https://arewabooks.com/chapter?id=6364b8542730d61e0981706d ______________ Sanda sukai jarabawar first semester ta goma sha biyar tazo cikin su arba'in,ko kadan hakan bai mata dadi ba,saboda ta saba,har ta gama rayuwar primary dinta bata wuce ta biyar,bata nunama kowa ba sai aminanta kuma roommates dinta,afra ce tace "Naga qoqarinki ma maimoon(sunan da suka koma ce mata kenan),a wata uku kacal kin doke mutum ashirin da biyar?" Kai ya girgiza sanda take hada kayanta,don a gobe kowa zai wuce gida hutu "Ina qoqari a nan afreen(sunan da ita dinma take kiranta dashi),bazan iya nunawa kowa result dina ba" "Zaki iya maimoon,i trust you,duk wanda ya iya arabic,boko bazai bashi wahala ba sam sam sam,boko minor abune akan arabic" "Next time I will try my best in sha Allah" ta amsa mata tana sakar mata murmushi,tare da jin dadin irin qwarin gwiwar da ko yaushe afra take bata. Washegari tana ta zuba idanun ganin wanda zayazo daukarta saiga yaa hisham,ya fito suka gaisa dasu afra,ya kuma gabatar musu da kansa da kansa a matsayin yayan maimunatu,sosai abun ya mata dadi,ya girmamasu ya kuma mutuntasu a mazauninsu na aminanta,su kansu sun nuna jin dadin hakan,afra taso su gaisa da 'yan gidansu,suga kuma sabuwar aminiyarta,to amma ya hisham din ya bada uzurin yana da patient da zai gani,dole sukayi sallama suka shiga mota. Yana qoqarin tada motar ya lura da envelope din hannunta,wadda ke dauke da tambarin makarantar,sai ya miqa hannu "Duk da ba'ayimin tayin ganin result din ba,nayi shishshigi,a bani na gani" idanu tadan zaro,ta yima kanta alqawarin babu wanda zai gani,har sai tayi abun arziqi,amma tana jin nauyin hisham din "Ya hisham,don Allah.....ka bari sai next term saina hada maka da wannan din duka ka gani gaba daya" ta fada tana marairaice masa,wanda har ga Allah ita din batasan tayi ba,kamar yadda batasan mugun kyan da hakan ya qara mata ba,har sai daya janye idanunsa da sauri daga fuskarta yana fadin "Subhanallah" cikin ransa ya furtata a hankali "Ba matsala,Allah ya nuna mana" yadda taga yayi maganar yana tada motar ba tare da ya sake waiwayowa ba yasa taji babu dadi cikin ranta,sai taji kamar bata kyauta masa ba,don haka ta zaro ta miqa masa,sannan tayi qas da kanta tana jiran jin maganar da zai fada mata "Kinyi qoqari sosai,ma sha Allah,wannan ne karonki na farko fa?" Ya fada cikin nuna qwarin gwiwa da kuma qarfafata,maganar tazo mata a ba zata,ta kuma bata mamaki,sannan kuma taji dadi gaki da sake samun qwarin gwiwa. Ta zaci gidan abbi zai kaita,sai taga ya wuce da ita gidanta,bata tambayi dalili ba,bayan ya aje ta tayi masa godiya,ta kuma bashi saqon gaisuwa wajensu anni,tare da roqonsa a kawo mata amna. Gyare gyare ta shiga yi,irin na mutumin da ya kwan biyu baya waje,sai data gama komai sannan ta sake wanka,ta kuma wuce kitchen ganin azahar har ta gota don ta samawa kanta abinda zataci. Har zata shiga ta tuna da unaisa,sai taga bai dace tana cikin gida ba amma batasan da dawowarta ba,ko banza ta girme meta a shekaru,wannan tunanin yasa ta karkata akalarta zuwa sashen unaisan. Knocking biyu aka tambayi waye,kai tsaye ta amsa da itace maimunatu,sai da aka dauki mintuna sannan ta bata izinin shigowa. Zaune take saman doguwar kujerar falon nata,ta miqe qafafunta akai tana shan lemon fata,da alama tun dazun a hakan take a zaune,kawai dai batayi niyyar bata izinin shigowar bane,kallo daya tayi mata ta canza fuska ta kuma kau da kanta taci gaba da kallonta ga tv. Koda ta gaisheta sama sama ta amsa "Na dawo,nace bari na shigo na sanar miki" wata dariya ce ta zowa unaisa,ya tabbata ja'afar din mugun dan rainin hankali ne,hakazalika da biyu ya dauki yarinyar ya kaita makarantar kwana saboda ya raina ajinta da kwanyarta,to amma hakan yayi mata ita din,tunda ko banza kawo yanzun tana dan samun wasu sauye sauyen,duk da cewa ko sau daya bau taba hada dakin kwana da ita ba "To yayi" tace mata kawai taci gaba da shan lemonta tana kada qafa gami da ci gaba da kallonta,ganin babu wani magana data sake hadasu sai maimunatun ta miqe zata fita "Agwai" ta kirayeta da sunan da maimunatun tafita sanin me sunan yake nufi,sunan yadan sosa ranta,amma bata nuna ba ta waiwayo tana dubanta "Am please idan kin tashi girkinki,ki dinga yi iya cikinki,wanda naci a baya ma shahada nayi,don ba abinci kowanne irin mutum nake ci ba,so ina da masu aiki,zasu dinga yin komai" kai ta gyada sannan tayo gaba tana bar mata dakinta. Ga mamakinta sai taji maganganun unaisa sun dan sosa ranta kadan,abinda tun tasowarta da irin cin zarafin data gamu dashi a rayuwa bata taba jinsa akan kowa ba,ko hakan yana da nasaba da zama dasu afra?,hakan na nufin ta fara sanin kanta da kuma sanin mene ne rayuwa?. Muje zuwa dai. Tunda ta dawo gidan bataga koda gilmawar J ba,abinda ko sau daya bai ɗaɗata da ƙasa ba,sau tari mancewa take dashi kwata kwata cikin rayuwarta,tasa litattafanta a gaba tana ta haddar hadisan data daukarwa malamin islamiyyarsu alqawarin zata kawo masa su kafin a koma hutu,da kuma izifin data diba shima zata daw da haddarsa,don hatta haddar qur'aninta bata bari ta tsaya ba,tana ganin wannan damar ta roqa alfarma,yake mata qari kuma tana kawo masa. Ta fannin boko ma litattafan da zasu sake inganta mata koyo da gane turancinta ta karba aro masu yawa daga library din makaranta ta taho dasu,wadan nan abubuwa sune abokan hirarta,kewar da tayi fama da ita zamanta na baya a gidan yanzu duka babu,mantawa ma take da inda take,wani lokaci ma idan tayi breakfast bata sake neman abinci saina dare,batajin yunwa sam idan ta duqufa karatunta,bare kuma ba wani motsi zatayi me yawa ba bare ya zazzage mata cikinta ya jawo mata yunwar ba,tana daki kwance,saman gado idan ta gaji ta dawo falo saman kujera,ba kasafai take shiga kitchen din ba,dalilin da yasa har zuwa sannan batasan ma kalar 'yan aikin da unaisa ke maganar ta kawo ba,don sanda zata shiga da safe basu soma nasu aikin ba,lokacin da zata sake komawa kuma dare yayi sun gama nasu aikin sun bar kitchen din. To da wannan damar data samu yasa tayi karatu me yawan gaske,wanda ita kanta batasan ta yishi ba,hutun da akazo gida don yinsa nata hutun kadanne. Randa tayi sati a gidan,tana daga bakin window dinta ne taji cewa ja'afar din tafiya yayi ashe,ta bakin unaisan sanda tayi baqi take rakasu zuwa parking lot na gidan xasu shiga motarsu,saita janye zuwa ciki,ta bude shafin gaba na littafinta taci gaba da karatunta. Sai da tayi kwana takwas da dawowa sannan su fa'iza suka zo mata,harda amnanta,ranar kamar sallah haka ta jita,sun sameta anata sana'ar wato karatu,amna na jikinta ta dauketa zuwa kitchen don ta sama musu abun sha,kafin tayi tunanin me zata girka musu. Sanda suka shiga amnan nata mata tambayoyi da zuba mata surutu,tabbacin yarinyar tayi kewarta matuqa,bata lura da unaisa dake tsaye riqe da cup da yoghurt a hannunta ba har sai data kirayi sunan yarinyar,tare suka waiwaya zuwa gareta ita da maimunatun,maimunatun ta dubi yarinyar data zubawa unaisa idanu tana kallonta,duba na rashin sani da kuma rashin sabo "come-on baby,new mom dinki ce" unaisa ta fada tana murmushi gami da miqawa yarinyar hannu,karon farko da yaro ya burgeta,kasancewarta ba ma'abociyar son yara ba,tsantsar kamanninta da silly mahaifinta din nan ya bayyana,tana fatan batayo miskilanci irin nasa ba. Kamar kuwa yarinyar tasan me take rayawa a zuciyarta,sai ta noqe kafada tana ci gaba da kallonta "Zo mu gaisa mana,haba amna,nace miki new mon dinki ce" ta sake maimaitawa dai,sai ta sake maqale mata kafada,wannan karon kallon fuskar maimunatu dake duba lemon da zata dauko musu tayi "Wannan ce new mom dina,ke ban sanki ba" ba unaisa da yarinyar ta fadawa maganar ba,ita kanta maimunatu taji mamakin maganar,ta dago kanta tana duban fuskarta,waye ya gaya mata itace new mom dinta?,ya akayi ta fahimci haka?,duk da dai yarinyar nada wata muguwar kwanya da kaifin basira,wanda maimunatu tafi tsammanin daga wajen mahaifinta ta gajeta. Sauke amnan tayi qasa tana dubanta "Itama new momma ce,kije ki gaisheta kinji" saita gyada kai,duk da bata sake jikinta ba amma haka ta nufi unaisan,abun ya yuma unaisan ciwo sosai,yarinyar ma ba zata zo wajenta ba sai wannan agwai din ta yarje mata,ta kuma yi mata umarni?,ta zabgawa maimunatu harara sanda ta riqe hannun amna,hararar da maimunatun bata ma san tana yinta ba,da hilata ta samu ta janye amnan zuwa part dinta,saidai suna tsaka da hira sai ga daya daga cikin masu aikin unaisan sun dawo da amnan,idanu fici fici da alama rigima ko ma kuka tayi musu. To hutun kwata kwata na sati hudu ne,suna gama satittikansu suka sake diba suka koma makaranta,maimunatu ta sake dasa yaqin neman karatu,babu ji babu gani,bakin rai bakin fama,su kansu su afrah sunyi mamakin yadda qwaqwalwar maimunatun ta sake budewa daga zuwanta hutu zuwa dawowarta,ta dings musu dariya ganin yadda dukka suke mata duban mamaki,a wani yammaci suna hanyar zuwa islamiyya,bayan ta bada amsar wata tambaya cikin subject din math,shi kansa malamin sai data burgeshi yadda ta amsa question din a gaban allo. To bata qarasa basu mamaki ba sai da sukaje islamiyyan,duka ta zubewa malaminsu haddar hadisan data yo,a washegari kuma zai karba na qur'ani,wannan yana daya daga cikin abinda ya sake zaburar dasu suma,sannan kuma farat daya sunan maimunatun ya fara tambari cikin makarantar,tun daga juniors dinsu zuwa seniors,cikin watanni shida kacal ta fara zama sananniya,duk wanda kacewa maimunatu abubakar muhammad zaiyi wuya yace maka bai santa ba,dalibai maza da kuma mata,saboda zuwan da tayi da tarin baiwarwarki a lokaci qalilan,kyakkyawar bafulatar usul,wadda ke dauke da wani irin kyau mejan hankali,musamman da a yanzun take zaman makarata,daga dakunan kwanansu sai ajujuwansu na boko sai kuma masallacin makarantar inda a nan suke gudanar da islamiyyarsu,fatarta ta sake wani irin haske,kamar zata tabata jini ya fito,jajayen labbanta da bata sanya musu komai sun sake ja,hakanan idanunta masu wani irin kyau da suke dauke da golden din qwayar idanu,ita kanta takan jima gaban mudubi tana kallon kanta,tare da tambayar kanta ita dince kuwa?,itace maimunatun rugar ummaru?,itace maimunatun inna furera?tabbas ta canza,canji me nisan tazara kuwa. Duk da cewa gayu da wasu dabi'u nasu afrah sun ratsata,har sun zame mata jiki itama ba tare data sani ba,amma hakan bai hanata yin takatsantsan da kanta ba,qwarai ta sani cewa ba daya suke dasu ba,ita din akwai auren wani a kanta,zuwa yanxu ta sake samun ilimi sani da kuma wayewa kan muhimmancin aure da girman matsayinsa saman kan kowacce diya mace,duk da cewa takan manta sosai da cewa ita din matar wani ce,don shi kansa wanda aka daura mata igiyar ta sanadinsa ba ganinsa take ba,wani lokaci sai taje hutunta har ta dawo baifi su hadu sau daya cikinn gidan ba,idan an samu akasi ne suke haduwa biyu,gaisuwa kusan itace maganar da take gilmawa tsakaninsu,har yau har gobe basu taba wata magana data gota babin gaisuwa da amsa ba. Tana qoqarin tunawa kanta cewa ita din me aure ce,bawai don damuwa ko soyayya ba,haka kawai cikin ranta takeji bai kwanta mata ba ko kadan,me yasa bai dauko halin hisham ba?,hisham din mutum ne da take matuqar ganin kima mutunci da kuma martabarsa,bata ga alama koda ta kuskure da zata nuna maka yana mu'amala da wani abun maye ko shaye shaye ba,sabanin shi da tun ranar data fara ganinsa tasan cewa mazuqin taba sigari ne,sauran abinda kuma yake sha wannann Allah ne kadai ya barwa kansa sani,tunda ita a nata hasashen,duk wanda yake shan sigari to yana shan komai ma na kayan maye. Abu na biyu hisham din mutum ne me kimanta dan adam da darajtashi,koda yaushe yana faran faran da ita dama sauran qannansa,a gu daya take ganin kamewarshi da nashi salon miskilancin shima,idan ya fita cikin mutanen da suke ba ahali a garesa ba,ko kuma baqin fuska,a duk sanda zai dawo da ita makaranta ko kuma zai maidata,hira ce me tsafta take wanzuwa a tsakaninsu,yakan bata shawarwari da qarin haske akan karatunta,labarai da suke da nasaba da karatu,kamar labarin lokacin da yake dalibin secondary kamar ta,takan iya sakin jiki dashi kadan yanxu,wannan baquntar da take masa a da yanzu ta ragu sosai,yayin da shi kuma yake girmamata kamar yadda zai girmama dan uwansa,har wani lokaci yakan bata kunya ainun,ganin cewa ya girme mata nesa ba kusa ba,ita yafi cancanta ta bashi wannan girman. 38 *************Karfe biyar da rabi ne na yammacin ranar lahadi,cikin dakin kwanan dalibai na makarantar,maimunatu ce zaune saman gadon afrah,ta baje litattafai kai kace duka litattafan data mallaka ne a gadon. Sanye take da chiffon fabric,material ne da aka yiwa dinkin simple gown brown color da ratsin coffe,sai milk color da akayi adon flower din jiki,dinkin dogon hannu ne,amma daga tsintsiyar hannun an sanya masa roba,abinda ya rage fadin hannun kenan ya zama tattara,abinda ya zama kamar wani ado na musamman,saman kanta wani silk v-shape vail ne data yafashi ta kuma daureshi qasan habarta,fuskarta da labbanta sai glowing suke tamkar ta shafa musu wani abun,saidai kuma ba abinda ta shafa din,nutsuwa da hutu data samu ne koda yaushe yake qara bayyana sirrin kyanta. Tsaki taja ta ajjiye pen din hannunta tana lanqwasa yatsunta,karatun exams take,saboda rana ita yau zasu zana jarabawar da daga ita sai ss two,ta riga taci alwashin wannan karon sai ta kawo first position da izinin ubangiji,tunda jarabawar farko tazo ta sha biyar,ta second term tazo ta uku,wannan karon ta daya take buqata. Kanta tadan daga sama kadan,inda afrah tun dazun ta haye gadonta tana waya,abinda yasa sukayi exchanging gado kenan,a boye take wayar,saboda duk lokaci irin wannan ana karbar wayoyinsu ne sai sun kammala jarabawa kuma. Har ta bude baki zatayi magana afran kamar ta sani sai gata ta motsa tana saukowa,harara maimunatu ta bita da ita,sai ta bushe da dariya tana fadin "Am sorry moon,afwan,bazan iya skipping amsa wayar nan bane" "Bansan me yake damunku ba afrah,exam around the corner amma ta waya kike?" "Ke kuwa kinsan dadin soyayya?" Tambayar ta tuna mata da himunta,sai kuma tayi hanzarin yin ta'awizi "Ban sani ba" ta amsa mata kai tsaye saidai cikin gatse,tana kuma miqewa tare da zura slippers dinta,dariya afrah ta saki,duk da ta fahimci gatsen ne "Naga alama ai,tunda duka tarin English novels din dana baki wancan hutun haka kika dawomin dasu,banga alamar kin karanta kowanne a ciki ba" "Kanki akeji,don na karanta kuma sai nazo na zauna ina baki labarin abinda na tabbatar kema kin sanshi" ta qarashe maganar tana shigewa toilet dinsu,saidai a zuciyarta afran ta motsa mata tasirin da labaran sukayi mata,kuma har yau idan ta tuna sai taji shauqin,saidai kuma bata son abinda zai shiga karatunta,shi yasa bata sake neman wani ba,tana jiyo afran tana mata shaqiyanci "To ban taba jin sunan kowa a bakinki ba idan ba ya hisham ba,ga waya kina da ita amma kinja kin aje,ke bakya zancan kowa fa a rayuwarki,dole nace bakisan dadinta ba" koda a dakin take ma ba zata tanka mata ba bare tana bandaki,don tana da attitude na qyaliya sometimes,ita afra ta saba da wannan,tace ta saba zama miskilai irinta,haka sister dinta take,da itace zamansu zai bada kala sosai. Har ta gama fitsarin data shiga yi ta dauro alwala bata sake jin afra tace komai ba,don haka ta bada a ranta ta fita ne a dakin,don indai ta fara dauko yi mata shaqiyanci irin wannan.....duk da itama gwanar miskilanci ce idan taso,amma bata shuru da wuri,wani lokaci har sai su fatima sun shiga maganar take barta ta sarara. Ga mamakinta sanda ta fito afran na dakin,tana zaune inda maimunatun ta tashi,wani littafi ne a hannunta,amma kuma ba shi take karantawa ba,wata takarda ce riqe a daya hannun hagun nata,ta tattara hankalinta kacokam a kanta,kamar zata koma cikinta,yadda taga afran ta nutsu yaja hankalin maimunatun,sai ta fara takowa a hankali itama tana duban hannun afran. Tana sake matsowa tana kuma sake fahimtar meye a hannun afran,invitation ne,invitation din kuma bana kowa ba face nata,na daurin aurenta,gabanta ya fadi sosai,tsoro kuma ya tsarga mata,ya akayi IV din ya shigo cikin kayanta?,litattafanta na karatu?,bayan kusan gaba daya a gembu tabarsu tun randa kawu sama'ila ya bata ta danqawa inna saratu bata taho dasu ba. Cikin matuqar dakiya maimunatu ta miqa hannu zata karba IV din tana cewa "Ba wannan aka ce ki karanta ba,litattafan makaranta zaki duba" gocewa tayi da katin yadda maimunatu ta gaza kamashi,sannan ta watsa mata harara "Anqi ayi karatun,sai aukin cewa mutum yayi karatu amma ashe bada zuciya daya kika daukeni ba moon?" Afra ta fada kamar idanunta zasu fado "Me kuma ya faru?" Tayi tambayar kamar batasan komai ba "Indai masu irin dabi'arki ne ai zasuyi fiye da hakan,wannan katin daurin auren waye?" Tambayace takai tsaye,wadda babu hanyar da zata kauce mata,suna dai gashinan ya fito baro baro a jiki full name nata,tace sunan waye kenan?. "Yanzu har a miki aure cikin hutun nan amma koni ki kasa gayamin moon?,ashe yadda na daukeki daban yadda kika daukeni daban,na gode,na gode sosai" ta fadi tana miqewa daga gadon bayan ta ajjiye mata katinta. Da hanzari ta kamota tana dubanta "Ni ba cikin hutun aka dauramin aure ba,da aurena na shigo school din nan" amsar tata ta bawa afra mamaki matuqa,ta kuma taimaka wajen sauke fushinta,mamaki ya maye gurbin hakan. Janta tayi suka zauna tare,sannan ta dubi afran "Sai da nayi watanni da aure sannan na fara zuwa nan" a nutse ta warware ma afrah komai,babu wani abu data boye mata,don itama tana jinta da gasken gaske har cikin zuciyarta,asali ita bamai yawan magana da dogon surutu bane,kuma tun zamansu tare suka fuskanci ba kasafai hirar samari data aure take burgeta ba yasa basu fiya irin wannan hirar ba muddin tana cikinsu,hakan yasa babu wani abu da ya tado maganar bare su sani. "Captain ja'afar marwan akko?,shi na gani a rubuce,da gaske shine mijinki?" Afra ta fada wani murmushi na fita saman fuskarta,kai maimunatu ta jinjina mata "Dama ance yayi aure,mata biyu,ashe harda aminiyata ta gobe a ciki, congratulations.....congratulations once again sister,kin ciri tuta,ke dashi kun tsinci dami a kala" ta qarashe maganar tana duban idanun maimunatu,fuskarta fal da murmushi,maganar ta bawa maimunatun mamaki,ta waro idanu tana duba afrah ba tare da tace komai ba,ita kuwa batayi qasa a gwiwa ba ta dora da "Duk yadda zan fasalta miki kyanki haduwarki da kuma nutsuwarki ba zaki fahimta ba maimunatu,tunda a kanki ake magana,kina da dukkan wani qualities da nake da tabbacin babu namijin da zaisan kina dasu ya iya dauke kansa a gareki ki wucess,infact.......ba namiji ba,koni macen na gama yiwa brother na kamu,ashe J ya riga dsya qwamshe wannan rabon" takai qarshen maganar murmushinta na sake yawa zuwa dariya dariya,dole kuma ta dora murmushi kan fuskar maimunatun,tasan halin afrah sarai,duk da cews ba wai yaune ranar farko da ta fara ko suka fara kodata ba ita dasu ayman "Well......abinda yasa nace ke kuma kin tsinci dami a kala?.....hmmmm..... captain ja'afar.......matashin da yake sanya razani da yawa a zukatan 'yammata,matashin da ya sanya idanuwan 'yammata da yawa zubda qwalla,matashin da ya sanya zukata da yawa cikin bege da qauna mai tarin yawa,ciki harda cousins dina su biyu,wanda har yau basu debe tsammani a kansa ba" ta qarashe tana sakin dariya,tare da tuna irin dambarwar da suka sha,tana cikin masu yi musu dariya kafin ta fahimci girman jarrabawar da suka fada,kafin ta fahimci waje ja'afar data fara yin hankali ta fara tausaya musu. Dubanta maimunatu takeyi kwanyarta na tafiya cikin nazari da tunani afran ta dora,saidai wannan karon cikin seriousness take maganar "Qawa,kada kiyi wasa da damarki.....kada kuma ku tsaya kallon ruwa kwado yayi miki qafa,kina da dukkan komai da zakiyi wining a kansa da zuciyarsa,karki barwa kishiyarki waje ko fili ko kadan,kada kuma ki sake wadan nan alamomin rainin daga wajenta suci gaba da fitowa a kanki,ta yaya zaki sakar mata rayuwarki tayi yadda taga dama?,mijinki rayuwarki ne ko yaya kika gai ga qinsa,wannan zaiyi amfani ne kafin ki amsa sunan matarsa,duniya ta fara kallonki da sunan,amma bayan kin amsa din kuwa,baki da wani zabi daya wuce ki gyara komai,indai bakiyi hakan ba....baki kyautawa anni ba,sannan bata cancanci wannan tukuicin daga gareki ba" maganganun afra sun ma maimunatu nauyi a ka,ta saqa abubuwa masu yawa a zuciyar maimunatu wanda suka dinga yi mata kai kawo aka,saidai tana duba abin,tana duba yadda lamarin zai kasance,ba zasu fahimta bane cewa yadda suke kallon lamarin dashi kansa mutumin ba haka abun yake ba?. To sai da tayi mugun da gaske sannan ta yakice tunani me qarfi da ya kamata daga ranta,ta koma karatunta ka'in da na'in,itama afrah bata sake ce mata komai ba,saidai a fakaice take mata karatun yadda soyayya take,sau tari a gabanta take wayoyinta yanzu,ta daina kebewa kamar yadda takeyi a baya,wani lokaci saidai ta tashi ta bata waje,idan taga dama ta qyaleta,idan kuma bata so ba ta biyota nan ma ta addabeta. *************Tsararriyan books shelve,wadda ke dauke da tarin litattafai a jere cikin tsari da tsafta da kuma sanin makamar aiki,tsaye yake a gabanta,daya daga cikin qofofinta a bude,da alama wani littafi yake nema,hannunsa daya dauke da wani littafi daya nutsu qwarai yana dubashi shafi bayan shafi,yayin da daya hannun nasa kuma ke riqe da cup dauke da matsatsen ruwan tuffa da inibi,sanye yake da wasuSlim fit suit Korean design royal blue color,shigar da a duk sanda ya yita take masifan karbarsa,kamar dama anyi suits da blazers saboda shi ne,kallo daya zaka yiwa kwantacciyar fatarsa kasan cewa hutu da jin dadi sun ratsashi,duk da cewa babu cikakken hutun ba ma'ana a ruhinsa,saboda uban tulin tarin ayyuka da kullum yake jibgama kansa,duk don yayi keeping kansa busy,ya raba kansa kuma da dukka wani tunani da kuma damuwa. Fuskarsa nan mai cika da haiba da kwarjini tana nan a yadda take,babu faraa ko walwala sam kamar bashi daya bane a cikin qawataccen office din nasa ba,sumar kansa zuwa ta fuskarsa nata sheqi tare da fidda qamshin hair mist mai kwanatar da zuciya. Taku daya yayi zuwa baya kadan da qafafunsa dake sanye cikin wasu lafiyayyun baqaqen takalma,wanda zaka rantse da Allah ba'a fita waje dasu saboda yadda suke sheqi,babu alamun saukar qura a kansu,ya dan jingina da teburinsa yana furzar da iska daga bakinsa bayan yakai shafin qarshe,yana tuna sanda shaheeda ta bashi gift na littafin,sai ya dan rufe littafin kadan yana kulle idanuwansa na wasu sakanni,kullum kwanan duniya yana jin cewa ya rasa babban bango kuma majingina a rayuwarsa,tunda ya rasata kullunm rayuwarsa sake jigata takeyi,babu wani sassauci tako ina. Idanunsa ya buda a hankali sanda akayi yaji ana scanning key din office din nasa,qofar kuma ta bada qara alamun an budeta kenan,bai wani motsa ko kuma ya damu ba,saboda yasan duk duniya mutum daya ya bawa wannan damar wato jabir,shi dinne kuwa,ya sako kai cikin office din bakinsa dauke da sallama,hannunsa dauke da file yayin da idanunsa suke kan fuskar ja'afar,yayi kyau shima cikin tashi suit din da take kamanceceniya data ja'afar,ya qara haske da kuma qiba yayi fresh,alamun duk yadda yakeso haka take samuwa a gareshi. Bakinsa ya motsa yana amsa sallamar tasa,kana ya miqe tsaye sosai saman qafafunsa,ya sanya hannu a nutse ya maida littafin inda ya daukoshi,ya rufe sannan yafara takawa zuwa kujerarsa,jabir din na biye dashi da idanuwa,yana kuma karantarsa,ransa da zuciyarsa na masa rashin dadi,don ko kowa baice komai dashi ba,yasan akwai abinda ya motsa zuciyar ja'afar din. Sai da ya zauna sosai sannan ya tura file din gaban "An gama hada komai,na gama nawa signing din,saura naka,zaka duba inda yake da gyara sai kayi,ka saka hannu mu miqa musu takardun, withing one to two weeks ya kamata a gama" ya qarshe maganar yana maida dubansa ga wayarsa daya zarota daga aljihu,saboda qarar shigowar text,murmushi ya subuce masa ya buda text din yana dubawa,yayin da hankalinsa kacokam ya koma kan wayar tasa,abinda yaja hankalin ja'afar,ya tsaya ya zuba masa ido,kana yadan bugi table din dake tsakaninsu. Daga kai jabir din yayi yana dubansa,har yanzu murmushi bai bar kan fuskarsa ba "Ina jinka" "Baka tare dani" ya amsa masa kai tsaye da tsayayyar muryar nan tasa "Yes.....gaskiya ne,hankalina bai wajen magana ta gaskiya,yanzu me ya rage?,inason naje gida lunch ana jirana" zube masa idanunsa yayi sosai kafin ya janyesu,kana yace masa "Kana iya tafiya" da wani irin low tune da ya sanya tausayinsa sauka a zuciyar jabir,yafi kowa sanin yadda shaheeda tayi tattalinsa a lokacin rayuwarsa harma fiye da haka,amma a yanzu duka yayi loosing wannan caring din,dole abubuwan su dinga tabashi,duk da cewa shi yaqi bada wannan damar,yana da hope akan maimunatu shima kamar yadda yaji anni tana fada,ya sake samun gamsuwa akan yarinyar tun ranar da suka zauna sukayi magana ne tsaho a kanta da anni amma ya tattarata ya kaita makarantar kwana,annin kuma ta hana kowa masa magana,tace su xuba masa idanu suga iya nasa gudun ruwan. A dan shurun da ya ratsa ta tsakaninsu ne tex ya shigo tasa wayar shima,sai ya jawota yana dubawa,qaramin tsaki yaja "this is nonsense" furucin ya fita can qasan maqoshinsa,idan ba kunne kasa sosai ba ba zaka ji me yake fada ba,kira yayi ya aje wayar saman table bayan ya sakata a loud speaker,bugu biyu ya daga "Me kake cewa ne?,ace duk gidan a rasa me daukota?" Yace da hisham kai tsaye,lumshe idanunsa hisham yayi daga wancan bangaren kafin ya amsa shi "Babu yaaya,drivers din duka sun fita tare da abba,yana da baqin da suke zirga zirga dasu,ni kuma nan da minti goma akwai wanda zanwa surgery,kuma emergency ne har mutum biyu,kafin na gama kuma an ja lokaci" katse kiran kawai yayi,ya fara laluban number anty maama. Itama bugu biyu ta daga suka gaisa "Driver dinki yana kusa ki bani aronshi?" "Wai.....ai kuwa yau tun sassafe ya debi yara abbansu yasa ya kaisu qauye" "Ok" yace a gaggauce "Akwai wani abu ne?" "No,ki gaida yaran, thanks " "Okay" itama ta bishi dashi,tasan halin kayanta fes,bama fadar zaiyi ba "Waye ya bawa drivers na gidan nan hutu ne gaba dayansu?" Ya jefawa jabir dake nanuqe da wayarsa yana maidawa fatimansa reply na dinta tambayar,sai a sannan ya daga kai ya dubeshi,duk nema neman drivers da yakeyi yana jinsa,ya kuma san dalilin hakan,don kusan da goyon bayansa anni tayi wannan hukuncin "Hey man,kai ne mana?,ka manta kenan ka zauna ka sani a gaba zaka fara tuhuma?" Tsaki ya sake ja yana tattare files din da suke gabansa "Bari na fito maka a mutum,duk wannan goce gocen da kake bazai maka bafa,ka tashi kaje dauko yarinyar mutane kawai,three months bata nan amma don zaka bata just thirty to fourty minutes ka daukota a school sai ya gagara saboda adalci irin naka?" Wani kallo ya masa,tunda yaji amsar daya bayar yasan da issue din kenan,sai ya dakata daga hada takardun "Idan kaji haushi me zai hana kaje kai" dariya ya sake sosai "Ba dole na bace,ga dole na can tana jirana,kuma inda itace da tuni na tsufa a school din,don bazan bari Allah ya kamani da laifin rashin sauke haqqin dake wuyana ba" yana gama sai ya miqe yana 'yar dariyarsa zai fice daga office din,har ya kusa qofa sai ya tsaya "Da zaka zo sai mu wuce gida tare ka fara yin lunch kafin ka tafi" ya fada with full caring in his voice,saidai kallo dayan da ja'afar yayi masa ya bashi amsarsa,sai ya kada kai kawai ya fice a office din yana murmushi,ya gode Allah daya bashi juriya da hikimar zama da ja'afar din,mutumin da yake jinsa tamkar cikin mahaifa guda suka kwanta dashi. Riqe da suit dinsa a hannu ya fito,kana ya sauko kai tsaye zuwa floor din qarshe ya kuma wuce parking lot na ma'aikatar,key dinsa already yana hannunsa,tunda ya sallami driver dinsa,don yau din ya tsara lokacin tashinsa,zai iya kaiwa dare,don haka ya bashi umarnin tafiya idan akai azahar,sai gashi kuma wani abun da babu shi cikin schedule dinsa na yau ya taso masa. Next Chapter Leave a comment Post Comments No Comments posted yet Contact Us Arewa Books Publishers WhatsApp: 09031774742 Email: arewabookspublishers@gmail.com Navigation HomeAboutFAQ's Legal Privacy PolicyTerms of Service Social 39 Da hannu daya yake driving din,cikin jin wata irin kasala a jikinsa,kai tsaye masallaci da yake sallah idan sallar ya riskeshi akan hanya irin haka ya nufa,ya samu jam'i,ya bada faralin sallar azahar,sannan ya sake fitowa,ya wuce eatery din da yakanci abinci time to time,yayi order din dinner,ya tsaya acan ya tsakura ya biyasu sannan ya wuce kai tsaye zuwa makarantar yana duba lokaci gami da jan tsaki,a yadda jikinsa yayi masa weak a yau,ya tabbatar komai nasa ya rushe,saidai ya barwa gobe kuma,ya fuskanci wani lalaci ne yakeson kamashi a yan satittikan nan,ko zuciyarsa na la'akari da achievements din daya samu take ganin kamar it's time for her to get some rest wanda shi kuma bai shiryawa hakan ba. Karo na uku kenan dame kula da dakunan kwanansu idan sun tafi hutu ta sake leqowa tana tambaya "Bai iso ba har yanzu" "Gashi office din principal din shima a kulle yake,duk dakunan da za'ayi kiran suma a rufe suke" cikin qarfin hali tayi murmushi "Kada ki damu mr Rebecca,nan da minti goma idan bai iso ba,saiki taimakin mu fidda kayan na samu okada na hau" kai ta jinjina "Shikenan ba damuwa,fata dai kawai Allah yasa lafiya" "Ameen" maimunatu ta amsa tana son danne rauninta da fargabarta,tunda ta fara makarantar itace ta farko da take rigasu afrah tafiya gida,ko sau daya hisham bai taba delay na zuwa daukarta ko kawota ba,dalili kenan da yasa yau din da suke mata dariyan zasu rigata tafiya gida bata damu ba,tace musu tasan yana hanya,qila ma kafin su gama ficewa a makarantar ya iso,wannan dalilin yasa suka tafi suka barta,don dukkansu sunsan himmar hisham din wajen daukota,sai gashi abun mamaki duka makarantar an fashe,sai ita daya data rage. Baya ga fargabar abinda ya riqe hisham din,harda zazzabi da tun jiya takejin somi somin alamun zuwansa,zuwa yanzu kuwa ya fara hade mata har da ciwon kai,abinda yasa ta sake laushi sosai,jimawa kadan sai ga hawaye sun fara layi saman kuncinta tana daukesu,tun ba yau ba dama tasan ita din gwanace wajen saurin kuka,sai gashi dabi'ar tata tana son dawowa,tun tana zaune sai data koma saman gadon afrah ta cure waje daya,tana jin jikinta kamar ana sassara mata shi,hakanan kanta da jikinta kamar an dora mata dutse. Sanda mr Rebecca ta turo qofar take shaida mata anzo daukarta sama sama take jinta,amma cikin qarfin hali ta amsa mata da to,wani sashe na zuciyarta tana jin ya sake,ta samu sauqin tunanin wani abu me muni ne ya samu hisham din,mr rebacca ce ta dauka wasu kayan tace bari ta fitar mata dasu,ita kuma ta lallaba ta miqe a hankali,saita koma ta zauna,saboda jinta da tayi kamar tana yawo kan iska,ta dafe kanta da hannunta tana jin kamar zai fado "Kamar yana sauri ne,zan fita miki da sauran kayan,kiyi ki fito" tafadi ba tare data lura da yanayinta ba tana daukan jakarta data rage ta fice. Agogon gaban motar ya kalla,mintuna kusan hudu kenan yana jiranta?,me ta tsaya yi ya tambayi kansa a zafafe,baya son xaman jira ko qanqani,dabi'ar da yafi tsana kenan,sai ya daga kansa don duba hanyar da zata sadaka da dakunan kwanan nasu,dai dai sanda take fitowa,tana takawa ne a hankali cike da takatsantsan saboda yadda takejin jikinta kamar ba nata ba,iska kuma nason wasa da ita daga hagu zuwa dama,fuskarta tadan tasa kadan wala'alla zafi zazzabi ya sanya hakan,lokaci bayan lokaci tana sanya tafin hannunta tana dafe kuncinta,har yanzu baby face dinta tana nan,saidai ta fara cika,ta kuma fara sauyawa,fuskar shaheeda ce ta fado masa at her age,a irin wannan lokacin datake dalibar secondary kamar haka,a wata rana da yayi mata surprise,yazo daukarta daga makaranta ranar daya samu cikar burinsa a sannan,ranar da ya zama samu shaidar zama cikakken matuqin jirgin sama me lasisi,irin murna da d'oki da ya gani saman fuskarta a sannan "Ban zaci ganinka ba,har kazo da kanka daukana?" Shine abinda shaheeda tace "Saboda me?" Ya tambayeta kai tsaye,shuru ta danyi still tana murmushi,da alama tana masa kaara ne akan abinda zata fada "Uhmmm,say it,say your mind" murmushi ta sakeyi ta girgiza kanta "Ka barshi kawai" "Saikin fada.....koni na ari bakinki naci miki albasa....mutum ne kai mai wahalar fahimta,me tsaurin ra'ayi,mara sakewa da mutane mara alqibla" baki ta rufe tana dariya,matsalarta dashi kenan,he can say her mind daga kallon qwayar idanunta kawai,yana da wannan baiwar sosai,shi yasa duk sanda ya dage saita kalleshi ido cikin ido ba kasafai ta fiya yadda ba,baya ga dafi da zai barwa gangar jiki da zuciyarta kuma sai ya karanto sirrinta "Nidai ban fada ba" "Ni kuma na fada,with all these lapses ma cancanci a bani soyayya..... I don't know what to say...mafi qarancin abinda zance shine, thank you for opening my eyes and showing me the way, thank you for loving me" kalamansa sun mata dadi sosai,kuma ta sake tabbatar da cewa lallai mahaqurci mawadaci ne. A daddafe take qarasowa cikin wata tafiya da tayi kama da takun isa ko yanga,wanda sam babu daya daga cikin abu biyun illa ciwon da takeji a dukka gabbanta,tun daga nesa idanunta ya sauka akan rolls Royce ghost din,tana da yaqinin ba motar hisham bace,ba kuma tasan me motar ba,don bata taba ganinta ba,don haka koda ta isa sai taja ta tsaya tana dan duba gefenta ko xata hangi motar hisham,wala'alla wanna motar ba ita tazo dauka ba. Idanununsa ya bude a hankali daga dogon tunanin da ya tafi jin shuru har yanzu ba ita ba alamarta,kai tsaye a kanta suka sauka sanda take dube duben,sai ya sanya hannunsa saman hon na motar ya danneshi ba tare daya dauke dubansa daga gareta ba. Wani irin firgewa tayi saboda yadda qarar ya saukar mata a bazata,baqaqen gilasai ne,bata tsammaci ma kwata kwata da mutum cikin motar ba,qafafunta ne gaba daya sukayi wani irin laushin da bazasu iya daukarta ba,tilas ta sulale a wajen tana dafe da kunnuwanta,jikinta na wani irin rawa. A hankali ya bude murfin motar ya fito,ya fara takawa zuwa inda ta sulale din,tana tsugune a wajen ta cure waje guda,yaga yadda ta tsorata din ta cikin mudubin motar "Get up" ya fada a taqaice yana duban ginin makarantar cikin yanayi na nazari,yayin da sautin muryarsa ya sake sanya maimunatun qara dimaucewa,tsoronsa ya sake shigarta. Idanunsa ya sauke akanta jin bata motsa ba,bata kuma ce komai ba kamar bata wajen,sai ya lura da yadda jikinta yake rawa,da gasken tsoratar tayi sosai?,kafin ya sake cewa komai miss rebacca dake goye da jakarta ta iso wajen "What's happening?,sir...kamar bata da lafiya sosai fa,ko jikin ne?" Ta fada tana qarasa kusa da maimunatu ta kama kafadarta tana tambayarta,sannan ta fara qoqarin dagota "Sir....jikinta da zafi sosai,clinic sun rufe suma,saidai idan kun fita ku samu wani a waje a samo mata magani" ta fada cikin girmamawa bayan ta raka maimunatu cikin mota ta zaunar da ita "Thank you" ya fada a taqaice,sannan ya taka zuwa motar ya shiga ya tada ita,saidai can deep inside him yana jin wani ba dadi a cikin ran nasa. Tunda suka fara tafiya qwaqwqwaran motsi batayi ba cikin motar,sai ma sake takurewa da tayi saboda yadda uwar ac din daya balbalawa motar take barazanar hallakata,mugun sanyi takeji kamar me,ga na zazzabi ga na sanyin ac,abinda ya sake galabaitar da ita kenan,sanda take shirin ta bude murfin motar tana shirin fitowa wani zazzafan amai ya kubce mata,duk yadda taso kada tayishi cikin motar amma yaci qarfinta,take ta wanke jikinta zuwa qasan motar,sai ya zare seatbelt dinsa yana fitowa daga cikin motar. Zagayowa yayi,yayi tsaye a inda take aman yanayin fuskarsa na sauyawa "Why J,why?" Ya samu kansa da tuhumar kansa da kansa,yadda take ta yunqurin aman ya isa gaya maka tana jin ba dadi sosai a dukka jikinta,baisan kuma yadda zai taimaka mata ba,sai ya dan tura mata murfin motar ta sake dafeshi kuwa sosai taci gaba da kelaya amanta. Ruwan roba ya fidda a motar ya miqa mata sanda ta gama aman,a galabaice ta karba,sai data kusa minti biyu sannan ta iya kuskure bakinta ta zubar,yasa hannunsa ya rufe motar,sannan ga zagaya seat dinsa ya sake shiga ya tashi motar a hankali yana yiwa mai gadi hon ya dage masa qofar suka sake ficewa daga gidan ba tare da ko ciki sun shiga ba. Ganin yadda take rawar sanyi sai yasa hannu ya kashe ac din,tuqi yake a hankali yana tunanin wanne asibiti zai kaita?,daga qarshe dai ya samu kansa da yiwa kansa jagora zuwa asibitin da marigayiya shaheeda ke ganin likita. Sun dan sha fama kafin a gano file din nata,idanunsa akan sunan dake jikin file din,sai ya janyeshi gefe yana gayawa receptionist din,su maida wannan a bude sabo da wani sunan daban. "Me sunan da za'a zaka?" Ya tambayeshi "Maimun.....maimun ja'afar" bakinsa ya subuce kawai yaji ya furta hakan,sai ya maida kansa ga wayarsa yana juya sunan a cikin ransa. Bayan likita ya gama ganinta dole yasa aka bata daki saboda yadda take sake galabaita,tana ta aman,yasa kuma aka jona mata ruwa bayan ya mata allurai,cikin lokaci qanqani bacci ya dauketa saman gadon. Idanunsa yadan kai kanta,fuskarta har tadan yi fayau akan ganin da yayi mata dazun,wani abu me kama da tausayinta ya tsarga masa,yana ganin kamar hon din daya danqara mata shi yayi silar ta'azzarar ciwon,don likitan ya fada,akwai abinda kamar ya razanata,dubansa yakai ga hijabin dake wuyanta tun dazun,wanda dashi akasha gwagwarmayar aman,akwai buqatar a cire mata shi,to amma bazai iya tabata ba,agogo ya kalla,baisan yaushe zaa sallamesu ba,uwa uba ma likitan yace sai yadda yaga jikin nata,sannan shi kansa drip din kadan kadan yake diga,bazaiyiwu yayita zama ba yabar duk aikin dake gabansa,don haka ya fidda wayarsa ya soma duba number anni. Har zai kirata ya fasa,ya duba number baba tabawa,Allah ya taimaka kuwa ya ganta,ya cilla mata kiran,ya kuma gaya mata driver ya daukota yanzu ya kawota asibitin,dai dai lokacin suna tare da anni tana hada mata kwadon zogale,sai ta dubeta "Manya ne ya kirani,wai Doma,doma hospital" cikin mamaki anni ta kalleta "Waye kuma ba lafiya?" "Baice komai ba haj anni,kinsan hali dai" "Ko shine?" Yadda annin tayi maganar cikin damuwa ma sai yadan baiwa baba tabawa dariya "Kai haba dai,shi dinne bashi da lafiya zai kirani?,kamar ma kin manta halin mutuminki?,shi da ko sanda yana matashinsa ma saidai yayi ciwonsa a daki yagama ba wanda ya sani,saidai idan anga fuskarsa ta sauya?" Kai anni ta gyada,ta tuna mata kam abinda ta sha'afa "Kamomin shi a wayar taki" bata musa ba ta koma kiran nass,dab da zata tsinke ya daga,kafin yace komai sallamar anni ta cika kunnansa "Ka kira tabawa kace tazo asibiti,sannan kuma bakayi cikakken bayani ba,waye ne ba lafiya?" Shuru ya danyi kadan,yana rarraba hankalinsa kan sunan da zaya kirayeta dashi,a hankali ya furta....... Next Chapter Leave a comment Post Comments 40 "Maimoon" "Maimoon kuma?,maimunatu?" Anni ta fadi da yadda tafi ganewa a kirata "Yeah eh" ya amsa mata a tausashe murya can qasa,don har ya qosa annin ta ajjiye waya,don yasan halinta yanzun zaa iya turkeshi da tambayoyin da wala'slla bashi da amsarsu "Mene ya sameta?" Ta fadi cikin nuna damuwa "I can't say" ya amsa mata a taqaice yana murza goshinsa da yatsun hannunsa "Kaii,kayi ta kanka malam,idan zakamin fillanci ko hausa to kayi tun wuri bai qure maka ba" "Ya salam" ya furta can qasan maqoshinsa yadda ba zata jishi ba sannan ya sake cewa "Fever.....zazzabi da amai" ya sauya harshe don yasan yanzu zata kuma complain "Ikon Allah,gata nan zuwa to" ta fada tana sauke wayar,wanda tuni ja'afar din ya rigata kashe wayar. "Kodai qaruwa muka samu ne haj anni?" Tabawa ta fada cikin zumudi,fuskarta dauke taf da murmushi,tana latse wayar ta tabe baki sannan ta miqawa tabawa tana cewa "Banjin haka gaskiya,jikina bai bani ba,amma.....koma meye ki shirya ki wuce,inason ki sakamin ido akan duk abinda yake faruwa,inason na sanin koma meye,sun doshi shekara,ya kamata zuwa yanzu musan me ake ciki,akwai ci gaba koko babu shi" "To in sha Allahu" tabawa ta fada tana yunqurawa ta wuce dakinta ta shirya,driver ya dauketa,kafin ta wuce sai data biya wajen amma ta gaya mata abinda ke faruwan,irin tunanin da ya darsu a ranta shine ya darsu a ran amman,farinciki sosai taji ya.mamayeta,tana qaunar ja'afar can qasan ranta,tana kuma qaunar duk wani abu daya danganceshi,tana boyewa ne saboda 'yan uwansa da kuma idanun mutane,tana da kara da alkunya irin wanda asalin bafulatanin mutum ke dashi. Sanda ta isa asibitin suna gaisawa ya fice a dakin,sai daya dan kalleta ta gefan idanu kafin fitar tashi,bacci take lakadan,sai ya taka a hankali yabar dakin,yana kiran waya yaji an kawo masa motar da yace a kawo masan. Sai da baba tabawa ta fidda mata hijabin jikin nata ta sake gyara mata kwanciya yadda zataji dadi kana ta zauna dab da ita kamar me gadinta,itama tana cikin masoya maimunatu,wadda Allah ya dora mata qaunar yarinyar har cikin ranta. Bayan la'asar kadan ya shiga gidan,main parlor din babu kowa,hakanan shuru yake sai na'urori daketa aikinsu,sama ya wuce kai tsaye,ya sanya key ya bude qofar dakin nasa kana ya tura yana furzar da iska daga bakinsa,da daya da daya yake duban dakin,yau dakin ya masa shirgi da yawa,baa kintse yake yadda yakeso ba,duk sai yaji ransa ya jagule,mutum ne shi da baya qaunar datti ko qanqani,don haka ya zare tie dinsa ya kuma soma fidda suit din jikinsa,ya zamana daga shi sai farar qal din singlet dinsa ta zallar auduga dake fidda wani sihirtaccen qamshi,a hankali ya fara picking duk abubuwan dake zube a qasa, yana kintsa dakin. Sam wannan ba rayuwarsa bace,dole ya koyeta,baya son kowa ya shigar masa daki,sai daya dauki good five thirty minutes sannan ya samu dakin ya masa yadda yakeso,bawai don ya gama qalqaleshi yadda ya kamata ba,yadda jikinsa yayi masa week yasa ya zame a gefan gadonsa ya kwanta,yana runtse idanunsa yana miqewa sambal,wanda tsahonsa gaba daya ya kusa cinye tsahon gadon,abinda zai tabbatar maka da baiwar tsahon da yake da ita kenan. Yadda shuru ya ratsa dakin haka yaji kwanyarsa ta dauki shurun,a hankali abinda ya faru dazun ya gifta cikin idanunsa,yadda ta tsorata sosai sanda hon dinsa yakai kunnuwanta,idanunta suka fidda wani kalar tsoro da ya sanyata durqushewa a wajen "Astagfirullah" ya fada yana maida folding hannayensa a qirjinsa,yana jin ba dadi har cikin ransa,tausayinta ya ratsashi,a sannan baisan zazzabi ne a tare da ita ba,da bai matsa mata hon din ba. Tun asalinsa mutum ne mai tausayi da kuma son kyautatawa kowa,duk da zallar miskilancinsa ya boye hakan,mutane da dama suna masa kallon bahagon mutum mai zallar rashin son jama'a da mugun hali,musamman wadanda basu mu'amalanceshi na tsahon lokaci ba. Haka yayiya kokawa da kwanyarsa da kuma tarin tunane tunanen da take saqa masa,tsahon wasu mintuna kafin a sannu a hankali bacci yazo yayi awon gaba dashi. A hankali take takowa zuwa uwar dakin nasa,gabanta yana dukan uku uku,tana kuma warning daya yanka mata sati guda baya daya wuce,saidai zuciyarta ta kasa jurewa,bata samu komai daga gareshi ba sannan kuma ace ganinsa yana gagararta alhalin suna zaune a gida daya,amma idan batayi da gaske ba sai ta shafe sati bata sanyashi a idanunta ba. Da wata nutsuwa data aro ta murza handle din sannan ta tura qofar dakin,idanunta ya sauka a kanshi sanda yake baccinsa very calmly kamar babu wani abu da yake damunsa cikin duniya,idanunta a kansa ba tare data iya daukewa ba taci gaba da takawa,duk takun da zatayi zuwa inda yake bugun zuciyarta ne yake daduwa,yayin da fuskarsan nan dake dauke da wani sassanyan kyau da kuma kwarjini na musamman wanda bai gushe ba koda ckin bacci ne take sake kusantowa gareta. Dab dashi ta isa,sannan ta zauna gefan qafarsa a hankali idanunta na sauka kan sambala sambalan qafafunsa,kai kace baya taka qasa dash,fari qal sai lallausan gashin da ya yiwa yatsunsa ado,ya kuma kwanta luf a singalalin qafarsa,hannu takai kamar zata shafo sai kuma ta janye hannunta da sauri,ta maida dubanta ga fuskarsa,zaman da tayi yadan kare mata fuskar tasa,don haka sai ta sake miqewa tayi tsaye a kansa tana morewa kallonsa,kallon data tabbatar inda idanunsa biyu bata isa ta yishi ba,wani irin sonsa ke kwarara a ranta,takai hannuna hankali zata shafi kwantaccen sajen dake gefe da gefan fuskarsa "Don't touch me" ya furta cikin kaushi cikin muryar mutumin dake bacci,sosai ta tsorata,ta janye hannunta da sauri tana fiddo idanu waje,dai dai lokacin da shima ya fara bude idanun nasa da kadan da kadan har ya zubesu fes kan fuskar unaisa. Kafeta yayi da idanu wani zallar bacin rai yana saukar masa,wannan shine karo na kusan biyar da take masa hakan,kamar bazai motsa ba sai daga bisani ya miqe daga kwanciyar a hankali,cikin zuciyarsa yana karanto addu'a,saman gadon ya zauna sosai bayan ya zubo da qafafunsa qasan gadon "Me kikemin a daki?" Ya tambayeta kai tsaye,sosai tayi qoqarin sanyawa kanta dakiya,duk da yadda jiki da kuma muryarta suke dan shaking kadan "Zuwa nayi na duba dawowarka,ga abinci can a gama" shuru yayi na second uku "How many times nake gaya miki ba kowanne jagwalgwalon masu aiki da sunan abinci nake ci ba?,take note please,kada ki sake shigomin daki ba tare da izini na ba" ranta ya sosu kamar kullum,ta kuma kasa hadiyewa "Amma dai kasan ni matarka ce ko?,sannan kuma ko yaya ne ina da hakki a kanka" qas yayi da kansa,murmushi nason kubce masa amma kuma ya hana kansa faruwar hakan,don baya son raini,daga bisani ya kuma daga kan nasa ya dubeta kai tsaye "I know,i already know, that's why na baki zabi ai tuntuni,a mutunce zan baki takardarki ki qara wuta,i assure you zaki samu dai dai dake" wani qullutun baqinciki ne ya tokare mata wuya,wanda ta kasa riqeshi,sai ta saki kuka kawai ta juya gudu gudu sauri sauri tabar dakin,yayin da shi kuma ya bi bayanta da wani kallo da tsarabar tsaki,kana ya miqe a hankali yana sanya hannunsa cikin sumarsa yana maidata baya saboda yadda ta cakude,bawai bashi da feelings ba,ko kuma feelings dinsa ya mutu ba,aah.....yana nan a yadda yake,lafiyayyen namiji,wanda wannan dalilin ya sanya ko a baya ya riga jabir aure,amma dai for now bayajin komai akan kowacce diya mace,musamman unaisar da sai a yanzu yake gano fuskarta ranar da qaddara ta fara hadasu da ita a wani club sanda yake aviation school,zuwansa club na farko kenan a rayuwarsa,shima baisan can zasuje ba,daga wajen cin abinci suke shida abokinsa kuma abokin karatunsa muslim,yace yazo ya rakashi wajen wani abokinsa,as'ad zubair,dan gida wani babbban qusan gwamnati a nijeria,acan ya gansu tare da ita,wanda shikam kallo daya ya yiwa fuskarta ya dauke kai,abinda yasa ya kasa shaida fuskarta kenan da wurwuri sai daga baya,duk da ba shigar banza ko wani abu yaga tana sha ba amma abun ya tsaye masa a rai,don yana da tabbacin cikakkiyar mace mai cikakkiyar kunya ilimin addini da tarbiyya ba zaa sameta a wannan wajen ba. Ruwa mai dumi sosai ya sakarwa kansa,bayan ya gama yayi brush ya feshe bakinsa da turaren mouth mint mai qamshin strawberry,ya dauki babban towel yana tsane jikinsa daya jiqe da lema sosai saboda yawaj gargasar da yake da ita saman lafiyayyar fatarsa. Cikin wasu lafiyayyun kaftan ya shirya kansa farare qal,duk motsin da zaiyi jikinsa na fidda wani irin qamshi mai taushi,ba kasafai ya fiya sanya hula ba,don haka ya riqeta a hannu bayan ya laluba key din motar da yake son fita da ita,ya kalli agogo yana duba lokaci,sai ya sanya wayoyinsa a aljihu bayan yayi kiran daya daga cikin drivers dinsa yaji yana kusa don qyuyar tuqi yakeji,har yanzu kasalar bata sakeshi ba,yayo waje cikin takunsan nan dake dauke da wani salo na dabam da zaka tsammaci tsabar jin kai ne ko izza. Sai da suka tsaya sukayi sallar magariba da isha'i a hanya sannan suka qarasa a asibitin,a sannan har yayi waya an musu take away na abinci awa daya kafin ya isa,qarfe takwas da wasu motsi,driver yayi parking motar tasu,ya balle murfin motar ya ficw cikin nutsuwa,iskar asibitin tana kadashi,tana kuma tuna masa wasu abubuwa sa suka shude cikin rayuwarsa. Babu yawan jama'a sosai a asibitin,hakan ya bashi damar isa qofar dakin kai tsaye,tun bai shiga ba ya tabbatar akwai mutane a ciki,sai ya tura qofan a nutse da sallama. su hudu ne 'yammatan gidan nasu,sai baba tabawa ta biyar dinsu,sallamarsa ta sanya su duka yin dif,yayin da wuta ta daukewa maimunatu dake zaune ta jingine bayanta da filo tana sauraren hirar tasu,sanye take da doguwar rigar atamfa wadda ta zauna mata sosai a madaidaicin jikinta,ta kuma fidda mata shape dinta saboda yadda breast curve din aka yishi cif da cif,ya kuma zauna mata sosai,dogon hannu aka yiwa dinkin saidai an yayyanka shi ya koma kamar spaghetti sleeve,tayi tayi sanda ta sanya kayan a bata baby hijab dinta data saba sakawa amma fa'iza tace a'ah,su da su waye a dakin da sai ta sanya hijab,baba tabawa ma tace "Ki barshi kawai maimunatu,kada kije ya dameki ma ya gotar miki da canola din" kasancewar sun cire mata ruwan da ake qara matan don ta huta. A ladabce suka gaidashi bayan baba tabawa ta miqe ta bashi kujerar da take kai ta matsar da ita gaban gadon maimunatu,maimunatun da tunda ya shigo tayi qas da kanta,ko sau daya bata dago ba,idanunta nakan Canola din hannunta. Takalmanta baba tabawa ta jawo tana sanyawa,dai dai sanda anni ke fitowa daga bandaki "Yaushe ka shigo?" Da hannu ya nuna mata yanzu yanzu "Zamu wuce,dama shirin tafiya muke" "Akwai driver?" Ya tambaya a taqaice da muryarsan nan me cike da ginshira "A'ah a'ah,salma ta tuqomu,gani nayi tafiyar babu yawa" cikin salma ya duri ruwa,ita anni me yasa ba'a sirri da ita?,kawai tace masa eh driver dinne,na meye saita bashi labari?. Qarasa dibibicewa tayi sanda ya watsa mata wani kallo na gargadin kinyi na farko kinyi na qarshe,baa baau mota su tuqa a gidan,saidai idan kinyi aure mijinki ya baki,suk inda zasu driver ke kaisu Da daya da daya suka fice a dakin suna yima maimunatu sallama tare da cewa zai gobe,murya can qasa take amsa musu,gabanta na wani irin faduwa,tana jin kamar tabi bayansu sanda suka fita,dakin ya rage daga ita saishi daya sanya waya a gaba yana dannawa 41 '"Ina yini" sassanyar muryarta da 'yammatanci suka fara cikata a maimakon quruciya ta daki kunnensa,sai ya zame wayar daga fuskarsa a hankali,karon farko da yaji muryarta a nutse kuma a wajen da babu kowa saisu,a kanta idanunsa suka sauka,kanta yana qasa bata ko qwaqwqwaran motsi,sai yaga kamar a tsorace take dashi har yanzun "Lafiya,ya jikin?" Ya amsata a taqaice "Da saugi" ta amsa masa tana jin yadda muryarsan ta saka mata ciwon kai,dama kuma tun dazun da ya shigo take jin yadda jijiyar kanta take harbawa,kallonta yayi tun daga madaidaitan farare sol don gafafunta da babu yasa ya sake maimaita tambayar tasa,ta sake masa shurun,abinda yasa ya dan fusata "Dago kanki ki kalleni nan" ya fada da dan kaushi da kuma kaurarawa,sai ta daga kan nata da sauri ta zube idanunta cikin nasa ba tare data shirya hakan ba. Wani abu me nauyi da qarfi ne ya dakeshi sanda manyan idanunta dake da haske da wani gyalli suka hadu waje guda da nasa,qarfin abun da ya sanyashi lumshe idanunsa na second biyu sannan ya sake budesu,har yanxu tana kallon nasa kamar yadda ya buqata,idanun nata sun sake wani garai garai saboda ruwan hawaye daya cikasu taf yake kuma shirin ballewa,dan bude idanun nasa yayi yana qara musu girma kadan gami da tattare girarsa,cikin kuma sigar tambaya yace "What?,meye haka?" Wannan karon ita ta gaza jurar kallon nasa,tana jin kamar zata narke a wajen,kamar ta diba qafafunta ta zura da gudu,abu daya ya rage mata ta bashi haquri ya barta ta sarara, baisan tu daxu yadda ya cika dakin ba,tana jinta kamar wadda akaje bakin jeji aka jefar aka juya aka barta ita daya "Kayi haquri" ta fada a wani salo da idan bakasan halinta ba zaja iya cewa shagwaba ce da zazzagar muryarta wadda ta fara shaking ransa,maganar ce kwata kwata baya son a yita,tayi shurun amma kuma taci gaba da qananun mitocinta har zuwa sanda yace ta wuce ya maidasu gida,da farko don tana jin haushinsa cewa tayl "Kai,kayi ta kanka kaji,ai bakai ka kawoni ba ko? kaje kaji da kamun da Allah zai maka da diyar mutane" maganar tata ma dariya ta bashi,amma a fuska ba zakaga hakan ba,yaso maida mata amsa,to amma yasan dogon magana zai jawo,qila ma indai anni ce ta barshi da ciwon kai,sai kawai ya barta a haka,tayi mitarta ta qoshi,ya ajjiyeta a gida ya wuce nasa gidan,bayan sun bar baba tabawa a asibitin zasu kwana tare. Washegari asibitin yadan cika saboda 'yan dubiya da suka dinga xuwa,har abun ya bawa maimunatu mamaki,ganin ciwon bai wani shahara ba,don ma dai likitan yaqi sallamarta ne,yace mai gidanta yace masa a barta saita warke gaba daya,tayi mamakin jin hakan,ja'afar din?,abun kuma yadan farantawa anni,tunda ko ba komai a nata ganin caring ne,a ranar harda abbi a zuwa dubiya da amma da kanta,aka kuma taho mata da amnanta,nan kuwa da dafe taqi binsu su koma,tace duk wanda yazo daga gida last zata biyoshi su dawo tare,hakanan suka tafi suka barta,amna kuwa ta bararraje abunta a gadon asibiti kusa da maimunatun,suna ta shan hirarsu,baba tabawa na daga qasa saman carpet tana tayasu,wani abun taci dariya. Sallamar anni ta sanyata daga kai da sauri tana jin dadin shigowarta a ranta,don dama neman wanda zaya shigo ya qwacetan takeyi,suna hada ido annin ta sauya fuska tana qure maimunatu da kallo "Me ya sameki kuma?" Ta jefawa maimunatu tambayar da bata shirya jinta ba,sai tayi shuru ta kasa ce mata komai,saboda batason tayi magana muryarta tayi rawa ta zargi wani abun "Me kayi mata?" Ta maida akalar tambayar ga ja'afar daya kammala wayarsa yake kuma juyowa,dan tsuke fuska kadan yayi "Ask her,gata nan ai,ki tambayeta" "Ke me yayi miki? da ganin idanuwanki kuka kikayi" kai ta girgiza "Babu komal anni" "Ko zaluntarki dama yake cikin gidan?" Kanta ta sake girgizawa alamun a'ah Shuru dakin ya dauka,sai sautin muryarsa mai cike da kwarjini dake ratso dakin a hankali,wata irin murya Allah ya bashi me dadin sauraro,ba zaka ce muryar d'a namiji bace,sake goge ragowar lemar hawayennata tayi,tana jin yadda fuskarta ta cika da tattausan qamshin turarensa "Mugu kawai,kamar mutumin kirki" ta fadi a zuciyarta,hoton sanda yake zuqar sigari ya gifta a idanunta haushinsa na cika mata zuciya "Ya boye yanata halin banzansa 'yan gidansu basu sani ba,Allah sarki abbi anni da amma" ta fada a ranta tana jin tausayinsu sosai a ranta,ita a nata ganin qarshen qurewar shaye shaye kenan,abinda yasa ta tsani buderi kenan tun farko,ashe zata tadda wannan. Sallamar anni ta sanyata daga kai da sauri tana jin dadin shigowarta a ranta,don dama neman wanda zaya shigo ya qwacetan takeyi,suna hada ido annin ta sauya fuska tana qure malmunatu da kallo "Me ya sameki kuma?" Ta jefawa maimunatu tambayar da bata shirya jinta ba,sai tayi shuru ta kasa ce mata komai,saboda batason tayi magana muryarta tayi rawa ta zargi wani abun пк want abut,stop it ya raud yana tigewa tsaye,ya matso gaba kadan yana zube hannayensa a aljihunsa,idanunsa kuma a kanta "Ya isa nace" ya kuma maimaitawa,ganin yadda shagwababbiyar muryarta ke fidda sheshsheqar kuka. Handkerchief ya zaro ya ajjiye mata agefanta bayan ya duba dakin da idanunsa baiga tissue ba "Wipe your tears" ya fada mata muryarsa can qasa,ya kuma kauda kansa gefe yana hadiye wani abu,wato ita kuma haka take kenan,babu damar fada ko tsawatarwa kai ko tambaya ma sai ta narke ma mutum?, tako ina anni ta janyo masa jagwal,ta hadashi da waccan data gama zagaye duniya yawon neman karatu,yanzu kuma ga qaramar yarinyar da inda auren qauye yayi tabbas ya haifa kamarta. Wayarsa ta sake kuka,yaja dan garamin tsakin da ya sake sanya gaban maimunatu faduwa,ya ciro wayar yana duba me kiran,sai ya koma da baya ya kuma nufi window yana amsa kiran. Shuru dakin ya dauka,sai sautin muryarsa mai cike da kwarjini dake ratso dakin a hankali, wata irin murya Allah ya bashi me dadin "Zaginki yayi?" Ta fadi duk da tasan ba dabi'arsa bace,amma ba'a shaidar dan yau,nan ma girgiza kai maimunatu tayi "Kodai ciki gareki ya nuna bayaso?" Dashi da itan gaba daya Duban anni sukayi,saboda maganar tazo musu a bazata,dauke kansa yayi yana ci gaba da matsa wayarsa,wani sashe na zuciyarsa nason jin zafin maganar,don shi bai taba musu yarinya bama bare tayi ciki,amma kuma sai wani bangare na zuciyarsa ke hango masa qani ko qanwa ga amna,madadin amra data rasa,tunanin ya goge daga kwanyarsa sanda yake deleting sagon daya tura a wayar tashi,don baya barin saqonni. Shuru anni yayi sannan ta maida dubanta garesa,wanda zaka tsammaci ma baya dakin kwata kwata tunda take maganganunta "Idan ma jan kunne kayi mata kan kada ta fada ai Allah yana nan,duk abinda mutum yake Allah yana kallonsa ko?" Ji yayi maganar ta masa nauyi sosai,ko menene za'ayi bayason mutum ya hadashi da ubangijinsa,idanu ya zubewa anni yana kallonta ba tare da yace komai ba,koda baiyi maganar ba ta karanci abinda ke ransa,maganar ce kwata kwata baya son a yita,tayi shurun amma kuma taci gaba da Kaman kana hanya Ko?' "Eh,ina ta wajen unguwarku,naje na duba patient din da na yiwa surgery jiya,sai na biyo wani suya spot" "Bakaji ko?,kai ne can gobe kaine nan,ka samu standard waje daya ka tsayar dashi duk sanda kwadayinka ya tashi,kaman ba likita ba?" Dan shafa kansa hisham yayi,ja'afar din badai aqida ba,shi kam duk inda yaji taste dinsu ya masa ko yaga abinda yakeso indai ya gamsu da tsaftar wajen zaije yaci "Am sorry" yace masa a taqaice,don yasan bazai tsaya sauraron dogon jawabinsa ba "Sorry for your self,ka biyo ta gida ka daukeni" "Okay" ya amsa shi yana murmushi sannan ya aje wayaryayan masa is very different and unique,komai nashi ya bambanta dana kowa,shi yake sarawa jabir da suke zaune lumi baka jin kansu. Next Chapter *GURBIN IDO* 42 Sai da suka tsaya masallaci sukayi sallar azahar sannan hisham ya sake daukansu wuce asibitin,gab da zasu qarasa ya soma slow da motan,jaafar dake duba wani abu a tab dinsa ya daga kai ya dubeshi "Uhmmm,ya dai?" "Naga masu fruit ne,akwai paw paw a ciki,zan siya ma maimunatu" sai ya maida kansa ga abinda yakeyi baice dashi komai ba,har ya buda motar ya fita yaje ya siyo,ya dawo ya tashi motar suka wuce. Dakin babu kowa,don duka sun yoye sun tafi,daga ita sai amnan sai baba talatu data shiga bandaki zata dauro alwala,tana zaune a saman gadon amna ta zame mata dankwalinta ala dole wai sai ta yi mata kitso,tana ta jagwalgwala mata sassalkan gashinta ta kasa kitsawa saboda sulbi da santsinsa,jikinta akwai sauran zazzabi,an yima likitan bayani yace zai shigo ya dubata,tana biyewa amna dinne kawai don kada yarinyar taji babu dadi. Batayi zato ba bare tsammani sassanyar muryarsa ta furta sautin sallama hadi da turo qofar dakin gaba daya,tashin farko kuma idanunsa suka sauka a kanta lokacin data rude ta kuma tsorata tana neman dankwalinta,wanda bata sani ba amna ta jefa mata shi qasan gadon,shi yasa ta kasa ganinsa,idanunsa ya dauke ya waiwaya baya inda hisham ke biye dashi "Wait for a while" "Okay" hisham ya amsa masa ya kuma ja baya ya tsaya ba tare da yasan dalilin ja'afar na fadin hakan ba. Koda ya shigo din gaba daya ya maida hankalinsa ga amna wadda ta diro a gadon fa kuma rugo da gudu zuwa gareshi tana kiran sunanshi,haka kawai yaji baya son ganinta haka,ya budewa yarinyar hannayensa bayan ya durqusa yana jiran qarasowarta,zuciyarsa kuma na tuna masa da lokuta irin haka a baya,lokuta mafiya farinciki a rayuwarsa,lokutan da ita da twin sister dinta amra ke rige rigen isowa gareshi,mamansi shahida na tsaye tana kallonsu tana kuma murmushi,sai gashi a yau yarinyar ita daya ta rage masa a cikin guraben farinciki guda uku da yake dasu,tana qarsowa kuwa yayi sama da itama ya cillata kan ya rungumeta cikin jikinsa. Kafij su gama ganin murnar ganin juna ta lalubo dankwalin da qyar ta yane kanta gaba daya zuwa saman qirjinta,duk da hankalinsa na kan amna amma yana ankare da ita,baisan me yasa take tsoronsa haka take kuma rudewa duk sanda yazo wajen ba,tun ranar daya tsorata tan randa suka baro gembu zuwa gombe,sauke amna yayi a hankali "Kice da uncle ya shigo yana waje" da dan gudunta ta fice,sai a sannan ya sake maida dubansa kanta,ta nutsu guri guda,wanzuwarsa a wajen tana sata jin kamar wani zazzabin zai sake qaruwar mata,kwata kwata batason ganinsa a waje idan tana nan "Ina wuni?" Ta fada da muryar nan tata dake da tsananin zaqi da sanyi,shi kansa ya yadda da hakan,idan tayi magana wani sauti take bayarwa na musamman "Ya jikin?" Ya tambayeta ba tare da ya amsa gaisuwarta ba,yana bin ledar qarin ruwa da aka cire mata da kallo "Da sauqi" ta bashi amsa dai dai da fitowar baaba tabawa daga bandaki. "Barka da zuwa,yaushe ka shigo?" "Yanzu" ya amsata yana waiwaya ga hisham dake shigowa dakin da sallama,kanta ta daga tana amsa sallamar,yadan kalleta ta gefan idanu,akwai dan qaramin murmushi saman lebanta tana dubansu shi da amna,gaisawa shima sukayi da baaba tabawa,ta tayar da sallah,sannan ya matsa inda maimunatu take "Yanzun don kada a bamu tsarabar boarding shine aka kwanta ciwo?" Shima tana jin nauyinsa sosai,amma ko kwatar na miskilin yayansa me fuskar shanu bai kai ba,akwai dan sabo haka a tsakaninsu,don haka murya can qasa ta yadda take zaton ja'afar bazaiji ba tace "Kaidai tunda sai yau kk zuwa dubiyan ai shikenan" "Am sorry.....wallahi ayyuka ne suka yimin yawa kwana biyu,ga teaching hospital da nake zuwa musu sau biyu a sati suma kyauta...." "Allah ya taimaka" ta fadi duk a darare,ita inda zai fita ya basu waje ma da sai tafijin dadin hakan,ledar gwandar ya tura mata "Nayi dubiya me kyau,tunda.na kawo miki mutuniyarki ko?" Ya fada yana dubanta yana murmushi,maganar da ta sanya ja'afar karantar fuskarta a fakaice,wanda a zahiri zaka dauka kacokam hankalinsa na ga surutun da amna ke masa,sai yaga fuskarta ta washe sosai,karo na farko da ya taba ganin irin haka tattare da ita "Na gode sosai,Allah ya saka da alkhairi,ya bada lada" maganar ta tsaya masa a rai,kwatankwacin addu'ar shaheeda kenan duk sanda aka yi mata alkhairi komai qanqantarsa. Juya gwandar kawai take,tana son sha amma dashi da hisham din duk sun cika mata waje,sanda baba tabawa ta idar da sallar likitan ya shigo,maimunatu ta daga kai a hankali gabanta yana faduwa,ta tuna maganarsa ta jiya,yace indai yazo yau ya samu da sauran zazzabin a jikinta to lallai duk qinta da allura saidai tayi haquri ayi mata ita,a duniya allura itace abu na farko data tsana ta kuma qi jini,daada tafi kowa sanin hakan,don tun kafin rasuwarta akwai sanda bata da lpy,ta takura sai anyi mata takusa shide mata,abinda yasa tun daga ranar bata qara bari anyi mata ba. "Dr hisham marwan?" Likitan ya fada yana diban hisham,da alama akwai sanayya sosai a tsakaninsu,don shima hisham din yana kallonsa ya kama sunansa,hira suka barke da ita,yana duba file din maimunatu,da treatment din da aka bata daga daren jiya zuwa yau,sai ya daga kai ya dubeta "Har yanzu da zazzabin?" Kafin ta amsa baba tabawa ta rigata "Akwai likita,ai har magana aka yo muku dazun" "Ba damuwa,zai sauka yanzun in sha Allah,qila ma idan akayi wannan allurar basai an sake wata ba" fadin haka kawai sai idanunta ya fara tara hawaye,cikin mamaki a kuma sace ja'afar ke kallonta,bawai tana nufin kiran za'a mata allura ke shirin sanyata kuka ba?,ya hangi zallar tsoro baro baro a idanunta,ta kuma kasa sukuni sanda taga yana hada ruwan allurar waje daya. Kida wayarsa ta farayi,sassanyar busa me ratsa zuciya,ya cirota ya duba me kiran,sai ya soma takawa a hankali yana ficewa a dakin yana amsa wayar. Daya daga cikin amintattun ma'aikatansa ne,suke gaya masa motocin da ya siya sun iso,suna lagos,za'a biya kudin clearance da sauransu "Ayi duk abinda ya dace" "Okay sir" ya amsa masa a ladabce,ya kashe wayar yana juyowa,dai dai sanda baba tabawa ta iso riqe da hannun amna "Manya inaji fa sai kaje maimunatu zata tsaya,taqi bari ayi mata allurar nan sam" a mamakance yake duban baba tabawa,wanne irin abune haka kamar qaramar yarinya?. "Daddy tsoro takeji wallahi,ka cewa dr ya rabu da ita" kallon amnan yayi,yadda tayi maganar har zuciyarta,hakanan itama fuskarta kamar zata saki kuka,baice mata komai ba,yadai saka hannunsa saman kanta ya shafa,sannan ya wuce zuwa ciki. Ba wanda ya lura da tsaiwarsa a bakin qofar,da gaske ne tsoro takeji,don gashi nan a bayyane baro baro saman fuskarta "Tsaya dr" ya fadi yana takowa zuwa cikin dakin,dukkansu suka waiwayo suna dubansa,sai hisham ya sulale ya fice,shigowarsa kadai ta sake sanyata jin kamar alqiyamarta ce ta tsaya,yaci gaba da takowa fuskarshin nan sam babu annuri,hannayensa zube a aljihun wandonsa. Dab da ita ya tsaya,har tana jin yadda numfashi ke zarya a qirjinsa,ya kafeta da idanuwansa wanda har cikin jininta take jinsu,abinda ya sake sakar mata da jiki kenan,qasa qasa cikin murya me kama da rada yace "Kar naga kin motsa.....if not......" Bai qarasa yadan ja qwafa "Matso kayi mata" ya fada da heavy voice dinsa dake nuni da seriousness dinsa,sannan ya waiwaya ga likitan,ya masa magana da ido kan ya taho. Kallon likitan take sanda taga da gaske matsowa yake inda take,bata manta yadda taji kamar zata mutu ba sanda aka sanya mata canular,sannan yanzun yace ta ciki zai mata allura?,ai batasan sanda ta kalleshi da shanyayyun idanunta da suka bude sosai ba,suka kuma cika taf da hawaye ba "Don Allah......dan Allah" tayi maganar tana girgiza kai muryarta tana rawa,idanu ja'afar ya zuba mata,mamakinta na sake cikashi "Tsaya" yace da likitan sanda yaga ta dunqule waje daya,hawaye na gangaro mata lokacin da yazo gab da ita ya daga allurar,wani abu me kama da tausayinta ya tsarga masa,halitta ce qin allura,ta tuna masa da marigayiya amransa,haka ake shan daga da ita idan zaa mata allurar. A hankali ya sanya hannunsa guda daya ya kamo tafin hannunta ya saka cikin nashi,tsigar jikinsa ta zuba gaba daya,tun daga tsakiyar kansa zuwa tafin qafarsa,karon farko da hannunsa ya sake taba wata mace tun bayan rasuwar shaheeda,laushi da dumin da tafin hannun ke dashi ya ratsa kowacce gaba ta jikinsa,a hankali ya soma murza tafin hannun,abinda ya daukewa maimunatu wuta kenan gaba daya,ta kuma wara dukka idanunta dake jiqe da lema akan fuskarsa dKe gab da tata,idanu ya zubawa fuskarta data yi wani kyau saboda lemar data jiqe eyelashes dinta,abinda ya basu damar yin wara wara,har yanzu da cikarsu da kuma tsahonsu "Relax....babu zafi fa,yanzu zai gama,just a few seconds" yayi maganar da wani irin sound da yasa taji zuciyarta ta sauya bugu,idanunta ta lumshe cike da kwarjinin daya ma idanun nata,tana kuma jin shigar qarfen a hannunta,saidai kuma kamar ya dauke duk wani tsoro fargaba da kuma zafi da take zaton zata ji. Batasan an gama ba,tadaiji ya danne mata wajen,likitan kuma na tsokanarta "Randa zaki haihu bansan ya zata kasance ba" murmushi gefan baki ya subucewa ja'afar,shima yayi wannan hasashen tun dazun,sai ya samu kanshi da daga kai yana kallon fuskarta,wadda ta fito clearly very close to him,jajayen lips nata suna motsawa a hankali kamar wadda ke karanto addu'a,har yanzu idanunta a kulle suke,taqi ta budesu,quruciyarta na bayyane saman fuskarta,lips dinta suka ci gaba da daukar hankalinsa,ya samu kansa da ci gaba da kallon fuskartata kallo irin na qurilla,jira yake ta bude idanuwanta yaga yadda zatayi,akwai wani irin haske da kyau da idanunta ke qarawa a duk sanda ta tsorata,abinda ya kula dashi tun a ranar,bakinta yana sake tsukewa,idanunta na dada girma da haske,abinda ke sashi cikin wani dan qaramin nishadi da gajeran tunani. Hannunsa dukka biyun ya sanya yana yafa mata mayafinta saman kanta sanda ya jiyo muryar hisham da jabir gab da dakin,da alama shigowa za suyi,kafin yace wani abu sun turo qofar sun shigo,hisham a gaba,abir din na dauke da amna,sai fatiman jabir din,sai ya janye baya a hankali,suna hada idanu da jabir din ya sauke masa wani murmushi,tuni ja'afar din ya fahimci abinda yake nufi,tsananin shaquwarsu ya sanya suke saurin karantar juna koda basuyi magana ba,murmushin da ya sanya ja'afar sake dinke fuskarsa tsaf "Allah ya taimaki boss" jabir din yafada cikin qan qan da kai,kamar yadda yaron gida ke magana da uban gidansa,amma saidai can qasan ran ja'afar yasan bawai yayi bane da gaske,akwai manufa na wannan gaisuwar,duka salon tsokana ne,don haka bai wani nuna masa ba ya bashi hannu sukayi musabaha. Jin baqin murya ya sanyata soma bude idanunta da suka sauya kala saboda rufesun da tayi gam da kuma kukan data fara a dazun,idanunta akan fatima tanason tuna inda tasan fuskar,muryar jabir data ji ya tuna mata,wannan shine haduwarsu da ita na biyu tunda sukayi aure,tayi qoqarin sakar mata murmushi duk da yadda takejin wani irin abu yana mata yawo a jikinta,uwa uba kasalar data saukar mata. Kujerar gaban gadon Fatima ta zauna suna gaisawa tana mata sannu,jabir shima ya matso yana mata sannu,sannan suka fice a dakin,abinda ya basu damar sakewa kenan gaba dayansu. Hira sosai suka sha da fatima,lokaci guda wani haduwar jini ya shiga tsakaninsu,duk da fatiman ta girme mata da kusan shekaru hudu a qalla,don zatayi shekara ashirin da biyu,kafin fatiman ta wuce har zazzabin da takeji ya sauka,alamar allurar ta fara mata aiki kenan,basu suka tafi ba sai bayan magrib ya aiko amna yace ta fito,ta sake mata sannu da jiki ta bata phone number dinta,ta nema ta maimunatun,sai taji nauyinta tace mata bata da waya,tana ganin kamar ba zata yadda da hakan ba,don haka tace da ita idan ta koma gida zata kirata,bata haddace number din ba,a zuciyarta ta yanke shawarar bude wayarta ta soma amfani da ita itama,don tun sanda hisham din ya bata ita take ajjiye bata yi komai da ita ba. Kwana biyu ta qara likita ya sallameta,zuwa sannan taji qwarin jikinta,amma sai anni tace "Tabawa,ku tafi gidan tare zuwa sanda zata sake jin qwarin jikinta,ban sani ba ko qaramin ciki ne,don namiji ba kunya gareshi ba,yana bayaso baya so,amma fa tsaf zai iya lallabawa ya dirkawa yarinyar mutane ciki" tana qarasa zancan yana turo qofa cikin dakin,hada idanu sukayi da anni,sai ta fuske kawai,sometimes ita kanta yakan mata kwarjini,kamar baiji zanca ba haka ya nuna,sai ma ya fasa shigowa dakin sanda aka kirayi wayarsa,ya juya ya fice yana qoqarin daga kiran. Sanda suke drivern ya gama sanya kayansu a mota,sai anni taja baba tabawa gefe "Tabawa,don Allah kisanya min idanu sosai akan zaman yaran nan,inaji a jikina kamar yana cutar musu da yarinya,maimunatu marainiya ce,sannan kuma amana ce a hannuna,nafi damuwa sa lamarinta akan na unaisa,saboda ita din akwai quruciya sosai ajikinta fiye da warcan,ita zata iya yaqi dashi ta qwatoshi,amma maimunatu nada buqatar kulawa" "In sha Alla haj anni,kada ki damu,koda akwai kusakurai zanyi qoqarin nusashesu tare da gyara mata" "Yauwa tabawa,na gode" "Har yau ban biyaki ba haj anni,kawai bashinki a kaina" murmushi annin tayi,tabawa tafi qarfin me aiki a wajenta,ta zama wani bangare na familyn dr marwan akko,duka gidan da wannan idanun suke kallonta,don babu wanda baiyi wasa a cinyarta ba,babu wanda bata raina ba,babu kuka wanda bataga quruciyarsa ba. Sanda maimunatu ta fuskanci tare da baba tabawa zata koma gida wani irin farinciki mara misaltuwa ya cikata,har hakan ya kasa boyuwa saman fuskarta,itama baba tabawan tafuskanci hakan,abinda yasa ta sake sanya ayar tambaya kenan,ta kuma ciwa kanta alwashin gano komai da kawo gyara dai dai iyawarta. 43 Ba wani qura sashen nata yayi sosai ba,saboda yanayin ginin gidan dama unguwar,amma duk da haka baba tabawa ta zage ta gyare mata sassan nata tas,ko ina ya dauki qamshi da qyalli,aikin da ada ita ke abunta duk sanda ta dawo hutu,abu nafarko data lura dashi,babu wani daki da maimunatun ta ware da sunan dakin maigidan,hakanan bataga wani abu ko guda daya daya danganceshi ba a sassan,koda agogo bare akai gasu hula,tsoronta daya kada dai ace fa yarinyar tana gefe suna rayuwarsu shida unaisa,kada suyi amfani da qanqantarta su cutar da ita,abinda bata sani ba duk kanwar ja ce,har gwara gwara maimunatun,yana tsayawa ya dubeta da idanunsa,yana mata kallon quruciya sometimes har yakanji abar tausayi ce a ransa (hmmmmm,ya manta duk qanqantar allura qarfe ce,mace babba da yarinya duk sunanta mace). Baaba tabawan batace dai da ita komai ba,taci gaba da sanya ido a fakaice,har zuwa sanda ta gama kintsa ko ina,sanna ta dora musu abincin dare saboda yammaci sosai yayi,sun kuma yi 'yan ciye ciyensu kafin ta gama aikin,babu kuma mejin yunwa a cikinsu,duk da maimunatun taso ta barta tadan dafa musu koda jallop ce kafin baban ta gama aikin amma ta hanata. Gab da magariban akayi knocking qofar falon,baba tabawa ta leqa,sai gata ta dawo tana gaya mata yaron gidanne da siyayyar kayan abinci,ta saba,kusan duk sanda ta dawo hutu zai aiko da cefane da kayan abinci a zuba mata a store,duk da ba rasa komai takeyi ba,hasalima kayan abincin kamar ba'a tabasu,saboda ita daya ce iya cikinta,ba kuma kasafai take wani girki ba,don idan tayi breakfast sai takai har rana bataji yunwa ba,bata sake dora girki sai na dare,ta riga data saba zama da yunwa,banda yanzun ma da cikinta yake komawa normal irin na mutane. Baba tabawa ce ta bude masa can qofar baya ta kitchen din,ya shiga ya zuba komai ya fitar da wanda zai fidda kamar yadda aka saba,sai daya tafi ta kulle wajen sannan ta dawo "Niko nace,kuna gaisawa kuwa da abokiyar zamankin nan?" Kanta maimunatu ta daga daga qoqarin jona chargy da take a wayarta "Ina shiga duk sanda na dawo a makaranta mu gaisa na gaya mata na dawo" "Amma duk xaman da kikayi asibiti ban ganta ba" ta tambaya cikin mamaki,don ko yanzun ma taji motsinta,sun kuma hadu da masu aikinta a kitchen din gidan,saidai babu wanda yace mata kanzail a cikinsu. Shuru maimunatun tayi,don itama bata da amsar da zata ce,ta kuma fuskanci kusan ita kadai dince bata zo dubata ba,tasan kuma ta sani,koda mai gidan bai gaya mata ba sanda su laila sukazo daukar mata kayan sawa sun hadu,sun kuma gaya mata abinda ya kawosu,duk yadda taso kada taji babu dadi aka abun wannan karon sai dataji ranta ya sosu,ita din batasan ciwon kanta ba kenan da take shiga har sassanta duk randa ta dawo ta gaidata ta gaya mata ta dawo,badon komai ba sai don zaman lafiya dake da dadi,bawai rashin sanin ciwon kai bane,duk mutumin da zakayi ciwo ya kasa dubaka to lallai rashin qauna yakai iyaka,a take nan taji a cikin ranta itama tabar taka sassanta. A nan waje ta watsar da batun,kamar yadda baba tabawa bata sake daga batun ba,ta wuce bedroom dinta tayi wanka,ta shirya cikin dinkin doguwar rigar atamfa A shape,ta dora baby hijab dinta saman kanta bayan tayi sallar magariba,tasha magungunanta sannan ta fito falon,tana ji a ranta zuwa yanzu wayarta ta cika da chargy. Ta samu baba tabawa ta gama shirya musu abinci "Na zuba sauran yana dumama don kada ya huce kafin yazo ci" baba tabawa tace da ita,sai ta amsa mata da to,ba tare data fuskanci ma'anar maganarta ba,tare suka zauna da ita sukaci abincin,suna ci suna hira,baba tabawa na bata labarai iri iri da suka shafi rayuwa,zamanta da kishiyoyinta da kuma mijinta,yadda mijin ke ji da ita saboda tafi duka sauran kula dashi,a fakaice take shigar mata da darasi. Sosai take jin dadin labaran,tunda take tsahon watanni sai yau ne takejin gidan a matsayin gida,sai yau ta taba jin dadin zaman gidan,sun jima sosai suna hira,harta soma jin bacci yana fusgarta,don haka ta miqe ta bada faralin sallar isha'i,ta dubi baba idanuwanta na lumshewa "Inajin akwai maganin dake sanya barci cikin magungunan da nasha" "Bacci ko?" Kai ta gyada mata "Eh wallahi,zan je na kwanta" "To Allah ya tashemu lafiya" da kallo tabi maimunatu sanda take shigewa dakinta,tana jinjina kai tare da sake tabbatarwa kanta akwai matsala,bata ga ya shigo ba,bata ga taje nemansa ba,koda kuwa ba kwananta bane,tana kuma da tabbacin zuwa yanzu ai yana gida,don ba mai yawon dare bane shi tun asali,amna zatabi komai a sannu,koda yau da gobe ba kwananta bane,dole jibi ya zamanto kwananta,jinjina kai tayi tana ci gaba da kallonta,saidai kuma gefe guda na zuciyarta tana ayyana mata yadda zata tafi da komai. ******washegari ta kunna wayarta,ta kuma dauko number afra fatima da ayman ta sanya,tayi saving number kowa,sannan ta fara kiransu daya bayan daya,duk wadda ta kira sai ta yi mamaki,cike da murna da farincikin samun number aminiyar tasu,afrah ce a qarshe,don tasan dole sufi dadewa da juna akan kowa. Da tsiya afra ta fara yi mata "Kin yiwa kanki fada kenan?" Dariya maimunatu tayi "Na gaji da kewarku ne" hira sosai suka sha da afrah din,har sai da katinta da hisham ya taba lodawa layin ya qare,afran ta biyota "Ina fata kin fara shawo mana kai captain" dan shuru tayi tana son tuna waye captain,sai kuma tadan saki fuska "Manta da wannan batun" "Seriously you are doing wrong fa maimunatu,kina nufin a haka zaki yita zama,meye ma'anar auren kenan?" "Karfa ki damu,ni dashi duka bamu damu ba" "Amma kin sauke amanar anni da amma kamar yadda suka baki?" Tambayar da ta sanya maimunatun yin shuru kenan,har sai da afrah tace "Qarshen term na ss 2 nima za'a karbi kudin aure na da farid,lalurar abba tasa uncle kamal yace a daga,amma abban da kansa yace a karba,babu wata damuwa,sannan hajja ma tace itama tafi nutsuwa nayi auren,naci gaba da karatun a dakina,tunda shima farid din yana da ra'ayin karatun" "Allah sarki,Allah ya bashi lafiya kafin lokacin bikin,Allah yasa za'ayi damu,qawata kice na fara shiri tun yanzu" hararar gefanta afrah tayi,kamar maimunatun tana kusa da ita "Nifa mun kusa raba gaari dake,muddin ba zaki tsaya kiyi abinda ya kamata ba" murmushi maimunatun tayi "Nifa baki fahimta ba,wai ta yaya kukeso na mu'amalanci mutumin da babu soyayyata ko digo a ransa sai ta marigayiyar matarsa,sannan kuma nima din babu qaunarsa ko qanqani a rai na,hasalima ni wani kallo na daban nake masa,ko inuwa daya idan muka hada Allah Allah nake yabar wajen ko kuma ni nabar wajen,infact ma kallon mugu nake masa,tunda na ganshi yana smoking,bansan ta inda zan fara sonshi ko sakashi ya soni ba" wata qaramar dariya afrah ta saki "Ban yarda dake ba,ban kuma yarda da dukka hujjojinki ba,kece number one a cikin mu hudu da kika fi kowa son kallon k-dramas na soyayya,har turkish drama kin koya kallo....." "Kin tunamin ma,akwai wani da naga talla,zanje na kalla" taka katse afran tana miqewa daga kwanciyar da tayi "Ahaf,kyaji dashi,kici gaba da zama,zaki mamaki idan kk ga wata tayi muku wuf dashi" dariya maimunatun ta saki,idan hakan ta faru batajin tana da asara,saidai unaisa,don ta fuskanci tana da damuwa sosai a kanshi. Agogo ta kalla sanda suka gama waya,sai taga lokaci yaja,abinda ya sanyata miqewa kawai ta shiga wanka,so take ta shirya ta fita su gaisa da baba tabawa. Dai dai lokacin da yake shigowa sassan nasu,cikin shirin office kamar kullum,slim fit three pieces suits ne a jikinsa Dim gray color dake da ratsin butter color,kwantacciyar fatarsa dake nuna zallar hutu da gayu tayi kyau cikin shigar,jikinsa ba abinda yake sai fidda sassanyan qamshin turaren prive rose George armani dan qasan turkey,kwantacciyar sumarsa sai fidda qyalli take kamar qura baya tabata,komai nashi me kyau tsari da kuma tsafta ne. A nutse baba tabawa dake gyara abinci saman dining hannunta kuma maqale da carbi tana ja ta waiwayo tana amsa sallamarsa "Barka da fitowa" ta fada tana sakin murmushi,taji dadin ganinsa sosai,don ya soma wanke zato da zargin dake ranta,kadan ya motsa fuskarsa,abinda ke alamta yanayin nasa murmushi ko fara'ar kenan "Barka da asuba" "Barka kadai manya,mun tashi lafiya?" "Alhmdlh,jiya na gaji sosai,kuma na dawo late,ban leqo ba" murmushi tayi "Ai babu komai,ta warware ma" agogon daure a tsintsiyar hannunsa wanda yake mix da zallar ruwan gwal ya kalla "Zan wuce office,akwai wani abu da kuke buqata?" Kai ta girgiza "Babu komai,amma ga abinci ko zaka ci" wajen ya kalla,ya sani baba tabawa is the best cook a duk gidansu,tana cikin list din mutanen da yake iya zama hankali kwance yaci abincinsu,amma yanzun sai yakejin bazai iya zaman ba,baima saba cin abinci cikin gidan ba, infact ma bai taba ba "Ina sauri ne,zan makara" "Amma akwai kunun gyada irin wanda kakeso,ka daure ko cup daya kasha" ta fada tana hada masa da sauri,bayan ta saka madara da suger madaidaita,don tasan bai cika sonsu ba "Na gode" ya fada yana karba,har cikin ransa yaji dadin hakan,yayin da baba tabawan ke karantarsa a fakaice,babu wadda ke girki a cikinsu ta bashi kenan?,abinda ya fara zuwa kanta kenan,lallai akwai aiki jazur a gidan,akwai kuma gyara. "Tana ciki,ina tsammanin ta tashi,zan shiga ciki na watsa ruwa" tayi masa tayin shiga wajen maimunatun a fakaice,tanason haifar da kyakkyawar alaqa a tsakaninsu,tanason tayi wani aiki da anni zataji dadinsa,sannan kuma ba zata manta dashi ba. Bashi da wani sauran zabi face soma takawa a hankali zuwa dakin,tunda har ta fahimci bashi da nufin shiga,bayaso ta zargi wani abu a ranta game dashi,ya kuma tabbatar kome yayin kamar yayishi ne gaban idanun anni,tunda da ita da anni duka abu daya ne,hannunsa guda daya cikin aljihun wandon suit dinsa,daya hannun kuma cup din kunun ne yana sipping a hankali,ya masa dadi qwarai,ya kuma yi masa yadda yakeso. Daure da babban towel ta fito daga bandakin,ta dora qarami saman kanta da yadan jiqe ya kuma bawa sumarta daman kwanciya a bayanta da gefan fuskarta,yau din sakayau take jinta,da alama lafiya tana sake samuwa a gareta,kai tsaye ta isa gaban mirror taja dressing chair ta zauna tana kallon fuskarta data yi wani irin haske ta kuma yi fresh har ita da kanta abun yana bata mamaki,kamar zaka taba ta jini ya fito,ta canza totally,irin canjin da ita da kanta yake bata mamaki. Towel din saman kan nata ta cire ta fara goge fuskarta dashi tana maida sumartata dake son shige mata idanu baya,bayan ta miqa hannunta ta jona hand drayer amma bata kai ga kunnata ba,tana goge gashin nata tana dan rera karatun qur'ani,haddarta ta qarshe da bata baiwa ya shaik nasu ba,saboda zazzabin da ta dinga fama dashi kafin tafiyarsu hutu,ta miqe tsaye tana ture kujerar baya,ta kunna hand drayer din ta soma busar da kanta in a low heat. Dai dai sanda ya murda qofar dakin ya kuma turo cikin cikakkiyar nutsuwa,tashin farko qamshin hair mist dinta dana hair oil da take amfani dashi wanda ya cika dakin saboda zafin hand drayer din dake kadoshi,ya kuma cakude da qamshin turarenta daya kama dakin suka buso saman fuskarsa. Wata ajiyar zuciya ce ta qwace masa ba tare daya shirya hakan ba,bai kuma san dalilin faruwar hakan ba,ajiyar zuciyar data wuce da idanunsa suka lumshe na wasu gajerun sakanni sannan ya budesu tarwai,basu sauka ko ina ba sai santala santalan qafafunta da suma fito ta qasan towel din da take daure dashi,wanda ya tsaya mata iyaka gwiwarta,soma yawo yayi da idanunsa zuwa samanta,faffadan qugunta ya fito sosai ta cikin towel din,kallo daya zaka masa kasan daya daga cikin baiwar da Allah yayi mata ne,ci gaba yayi da kallonta zuwa sama,bayanta dake dauke da farar fata me sulbi da qyalli ya bayyana muraran,da wasu daga cikin gashin kanta da suka kwanta luf a kansa. Cikin nauyin zuciya da kuma mutuwar jiki ya daga qafafunsa yaci gaba da shigowa dakin ba tare da maimunatu tasan an shigo ba,don zuwa sannan ta tattaro sumar tata zuwa fuskarta tana tajewa bayan ta kashe hand drayer din,tana kuma ci gaba da rera karatunta da qaramar muryarta mai zaqi da sanyi,karon farko ya sake sakin boyayyar ajiyar zuciya,qira'arta sak irin ta shaheeda,qira'ar malami guda suke bi,sai ya maida qofar ya rufe ya sake matsowa ciki sosai sannan yayi sallama idanunsa bisa kanta. 44 Sosai ta tsorata kamar yadda ta saba,comb din hannunta ya sulale a qass,bugun zuciyarta kuma ya sauya,zuciyarta ta fara tantama shine ko muryarsa ke mata gizo?,don gusar da tantama sai ta waiwayo cike da fatan ya zaman bashi bane. Ido hudu sukayi dashi sanda yake kurbe kununsa,wannan tsoron dake haifar da wani kyau cikin qwayar idanunta ya bayyana muraran,hakanan yadda gashin kanta ya sauko ya qawata fuskarta ya kuma yi mata ado sosai,ba tare data qara tunanin komai ba ta laluba hanyar toilet,ta manta da cewa qofar toilet din yafi kusa dashi akan inda take tsaye. A nutse ya dire cup din a saman side drower din dake gefansa idanunsa a kanta yana jiran isowarta,goye hannayensa yayi a qirji yana kallonta har xuwa sanda ta qaraso dab dashi da niyyar wucewa a rude,babu zato kuma babu tsammani taji an ruqo dukka hannayenta gaba daya,sannan kuma ya jata zuwa cikin jikinsa,ya rungumeta ta baya,hannuwansa riqe da dukka hannayenta biyu,rungumar data sanyashi cikin nadama bayan ta samu kyakkyawan masauki cikin jikinsa,gashin kanta ya musu rumfa gaba daya shi da ita,sahihin qamshin hair mist din da yake ji daga nesa bayan ya shigo dakin a yanzun yaji ainihinsa,lallausar fatarta data gama mulketa da wani body lotion mai wani irin sulbi da qamshin rose ta gogi jikinsa,saura kadan yayi missing numfashinsa na gaba,dukka gabbansa suka saki,wani irin yanayi da bai taba zata ko kawowa zaijisa daga kowacce mace ba macen ma irin maimunatu da yakejin zai iya haifar kamarta lokaci daya ya saukar ma kowanne lungu da sawo na sassan jikinsa. A jikinta ta dinga jin kamar jinin jikinta ke daskarewa saboda tsoro. Tun daga tafin qafarta zuwa hannayenta dake cikin nasa sunyi wani irin sanyi saboda tsoro da mamaki,kasantuwarta a jikinsa sai takejin kamar cikin wani mafarki take,ire iren mafarkan da suka takura mata kwanakin baya,har ta dinga tsammanin tana da wata lalura data shafi jinnu,amma kuma bayan sun karanta a fiqhu cikin alamun balagar mace da suke nuna kaiwarta munzali irin wannan mafarkin sai hankalinta ya kwanta ta kuma fuskanci abinda ke faruwa da ita. Tsigar jikinta ce tayi wani mugun zubawa,kanta kuma ya sara sanda hannunsa ya shafi wuyanta a qoqarinsa na tattare gashin nata gefe guda,bata warware ba daga wannan taji ya juyota gaba daya tana fuskartarsa cikin hanzari,tashin hankali!!....ta fada qasan ranta,ta fiddo idanunta dukka waje tana jin yadda towel dinta ya kunce daga daurin data masa,ya kuma fara warwarewa a hankali a hankali,ta kuma yi imanin nan da wasu sakanni zata iya kasancewa tsirara kenan?. Ta bangarenshi baisan me yake faruwa ba,yadda ta zare idanun nata ya sake haifar masa d wani abu ya kuma gasgata masa tsananin tsoronsa da takeyi "Why all this fear?Am I a monster?" Yayi maganar yana kafeta da ido,da mugun hanzari ta girgiza kanta,tun kafin ma yakai aya,cikin shagwabarta data zame mata jiki,shagwabar da a baya idan inna furera ta daketa ta fara bata haquri sai tace da ita ba tare da duba da cewa haka yanayinta yake ba tun usuli "Shegiya karuwa,wannan,irinku ne idan kuka kama mazan jam'a a bariki ba matarsa ba,haar uwarsa saidai ta sallama muku shi" "Kayi haquri don Allah" maganar ta fito da wata siririyar qwalla daga idanunta,saboda yadda taji towel din naci gaba da ware kansa. Idanunsa ya lumshe kadan sannan ya sake budesu,hawaye.....hawaye,he hated it,me yasa kuka baya mata wuya?,shagwaba kamar 'yar fari ko auta?,yayi qiyasin hakan a ransa ba tare da yasan ita din bace "Nooo,dole ki nunan abinda yake baki tsoro a jikina" kai ta shiga gyadawa "Babu komai" "It's a lie kuma ban yarda ba" ya fada yana tsuke fuska tare daci gaba da kallonta "Allah....wayyo Allah daadata!" Ta fadi kukanta yana qaruwa tana kuma neman durqushewa a wajen saboda jin ya fara salube mata. Dubansa yakai ga jikinta,sai a sannan shima ya karanci meke faruwa,wani mugun shock yaji sanda idanunsa suka kai kan saman rabin dukiyar fulaninta da suka fara fitowa,ba tare da tunani na biyu ba ya sakar mata hannuwanta da gaggawa ya kuma juya mata baya,sannan a hankali ya nufi inda ya aje cup dinsa ya dauka yana ficewa daga dakin ba tare da ya jira komai ba. Bai samu baba tabawa a falo ba,sai ya fice kawai daga sassan ya kuma wuce parking lot,inda ya samu drivernsa yana jiransa,bai jirashi ya bude masa qofar ba ya bude ya shiga,sannan ya bashi umarnin tafiya. Sosai yayi relaxing a bayan motar bayan ya kulle idanuwansa yana sauraren yadda bugun zuciyarsa ya sauya cike da mamakin faruwar hakan a gareshi,fuskarta da gifta duhun idanuwansa sanda take kukan,wanne irin tsoronsa take haka?,idan ta bayyana hakan gaban mutane akwai wanda zai yarda dashi kan ba wani mummunan abu yake aikata mata ba?,bude idanun nasa yayi a nutse yana duban hanya,a hankali qamshin jikinta yake yana tashi ta gaban suit dinsa da hannayensa,sai yaja dan qaramin tsaki,yana ji a ransa he's totally wrong. Ta jima a duqe a wajen tana sharar qwalla,don batasan ma ya fita a dakin ba sai da taji shurun yayi yawa,a hankali ta daga kanta,ta tabbatar baya dakin,sannan taja jikinta daga wajen,tana riqe da towel din nata gam,kamar wadda aka ce za'a qwacewa shi,saman gadonta ta nufa ta zauna,amma sai zaman ya gagareta,wani irin mutuwan jiki takeji da kasala,gaba daya kamar an samu abu an buge mata gabbanta,gefe daya kuma zuciyarta kwata kwata babu dadi,musamman idan ta tuna a yau din wani namiji ya ganta a rabin tsirara,sai wasu sabbin qwallar su sake zirto mata,saidai ta saka hannu ta shafesu. Ta kwashe awanni masu yawa a haka,ita ba me lafiya ba ita ba mara lafiya ba,bata tashi ta shirya ba hakanan bata fita a bedroom din nata ba,abu daya ne ya tsaye mata a rai yake ta mata yawo,duk juyin da zatayi sai abinda ya farun ya wulga mata a idanunta,hakanan duk motsawar da zatayi sai mayataccen qamshin da ya bar mata ya kada har qwaqwalwarta,tamkar a yanzun ne yake tsaye cikin dakin,tafukan hannuwanta gaba daya sun rune da qamshin wani dan mitsitsin oily pen perfume da yake amfani dashi,idanunta ta lumshe tana shaqar qamshin har cikin qwaqwalwarta,yana silalewa a hankali zuwa zuciyarta,sai ya tuna mata da handkerchief dinsa dake wajenta,d same qamshin da yake jiki kenan,best scent ever data taba ji me wani irin yanayi,duk da yadda zuciyarta keta qyamatar qamshin amma ta kasa daina shaqarsa,daga qarshe bayan ta gama shafe awanninta,haka ta janyo mataccen jikinta ta sauko daga gadon ta nufi toilet ta sake wanka,waiko zata samu ta raba fatarta da mayen qamshin dake qara mata kasala. Koda ta fito ma tsaiwa tayi gaban mudubi tana duban yadda fuskarta tayi jaa saboda kukan da tayin,ta sauke idanunta saman qirjinta tana tuna a yadda ya ganta,sai ta dan zame towel din tana iya dai dai yadda ya kufce mata a dazun,dukka idanunta ta qwalalo waje,indai towel din yakai haka sakkowa tabbas yaga fiye da rabin jikinta,wasu qwalla masu zafi suka sauko mata,amma kuma sai tayi hanzarin gogesu sanda taji muryar baba tabawa tana knocking qofar gami da tambayarta lafiya ta jita shuru?,ta fito ta karya kada abincin ya huce "Gani nan fitowa baba" ta amsa mata,sannan taja lotion dinta da hanzari tana sake sabon shafa. Cikin doguwan rigan wani material mara nauyi ta shirya,ta gyara sumarta ta hadeta waje daya,sannan ta yafa dankwalin kayan,har tayi gaba ta dawo ta dauki wayarta sannan ta fito. A zaune a falo ta samu baba tabawa,daga kanta tayi da niyyar cewa wani abu sai suka hada ido da maimunatun,tadan zuba mata idanu kadan saboda yadda fuskarta take nuna tayi kuka,kamar zata ce wani abu sai ta fasa,saboda ta tuna dazun,shima taga fitarsa daga dakin da wani mugun hanzari,hakan yasa taji bai kamata tace komai ba,don tsakanin miji da mata sai Allah,fatanta kawai ubangiji yasa ba wani abu mara dadi baje ya faru a tsakaninsu ba,kuma Allah ya kawo daidaito tsakaninsu nan kusa. Kadan ta zuba abinda baba tabawan ta dafa ta fara tsakura,saida kadan taci ta tashi,saboda tana jin cikinta gaba daya ya cushe,kamar babu wani sauran space na zuba abinci,data dawo saman kujera ma kwanciya tayi,yau ko hirar da sukanyi da baba tabawan jifa jifa ta dinga yinta,tans ankare da ita,lokaci lokaci sai tayi kamar ta tafi tunani,sai kuma ta sauke ajiyar zuciya taci gaba da abinda takeyi. Kafin azahar jiki da zuciyarta yayi laushi qwarai,sanda ta shiga sallar azahar mamakin kanta ta dinga yi,me yasa abinda ya farun a daxun ya tsaya mata a rai ta kuma kasa mantawa?,me yasa har yanzu take jinta kamar rungume take cikin jikinsa?,me yasa qamshinsa da kamanninsa suka kasa bace mata?,me yasa take hango idanunsan nan take jinsu da nauyi?,saita sake wata irin ajiyar zuciya me nauyi tana tabe baki kamar yaron dake shirin sakin kuka,kafin daga bisani tayi qoqarin daidaita mode dinta ta wuce bandaki don ta dauro alwala. Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana cire guda daga cikin suit dinsa ta saman,ya kuma saqaleta a suit hanger dake cikin office din,sannan yayi taku biyu ya isa rukunin kujeru masu taushi dake gefe guda a cikin office dinsa,wanda aka tsara wajen tamkar ba cikin office din yake ba. Opposite jabir dake binsa da kallo ya zauna ba tare da ya daga kai ya dubeshi ba,duk da kuwa yasan shi yake kallo sarai,ya daga qafanshi ya zame qawataccen takalmin dake qafarsa yayi wurgi gefe dashi,ya rage sai socks kawai a qafar tashi "Wai anya kuwa kasan me dame ka fada wajen meeting din nan?,abinda ka dinga fadi baiyi making sense ba......lafiyarka qalau kuwa yau?" Ya masa tambayar sanda ja'afar din ke tuttulawa cikinsa ruwan sanyi,cike da fatan abinda yakeji ya tsirga masa. Bai amsa masa ba sai daya qarar da ruwan dake cikin gorar tas yayi wurgi da ita itama,sannan ya sauke idanunsa cikin na jabir,abinda ya sanya jabir din karantarsa,ya kuma sauke boyayyen murmushi "I know......" Ya amsa masa kai tsaye "I don't think so" shima ya maida masa da amsa,janye idanunsa yayi daga kan jabir din yana lumshesu sannan ya budesu,kamar zaice wani abu sai ya fasa,ya miqe a hankali yana roller hannun rigarsa zuwa sama don ya samu daman yin alwala,ya taka sannu a hankali zuwa qofar toilet din nasa,ya turata ya shige. Madaidaicin toilet ne amma ya tsaru matuqa,hakan ya bashi damar lashe kudade masu yawa saboda toiletries da aka zuba masa masu tsada da kyau sannan kuma sabbin design,babban mudubi ne daga wani side daban da zai baka daman ganin kanka sosai,a gabansa ya tsaya yana kallon kansa yana kuma murza sumarsa da hannunsa,ta qasan zuciyarsa yake magana da kansa da kansa,he really made a mistake,ya manta wayeshi.....me ya kaishi kusanta kansa sa wata mace?,to wai hakan ma yana nufin akwai improvement kenan daga depression din da zuciya da ruhinsa ya fada?,tunda har gashi zuciyarsa da gangar jikinsa sun fara neman wani abu daban wanda a baya ko tunaninsa babu a ransa?,hannayensa ya tara a qasan famfo ya cikasu da ruwa ya watsawa fuskarsa,ya sauke ajiyar zuciya yana gaining courage daga can zuciyarsa,yana jin zuwa anjima kadan zai manta komai,komai zai wuce,da wannan ya samu ya daura alwalarsa ya fito,ya samu jabir tsaye dab da rigarsa yana duba takardun da suka gabatarma da juna wajen taron,kai ya daga ya dubeshi "dude........ina ka samo wannan turaren ne?,but......scent din nasa kamar na mata...,kamar my tee ta taba ban cigiyarsa na kasa samunsa" rasa amsar da zai bashi yayi,yace masa a jikin qaramar yarinya maimunatu ya sameshi?, Ko yace masa rungumeta yayi qamshin ya tabashi "Ka shiga kayi alwalar muyi salla,lokaci yana wucewa" tuni ya sanya masa ayar tambaya,sai ya gimtse murmushinsa,ya wuce toilet din yana addu'a cikin ransa "Ya rabb,ya rabb.....ka sanya lokacin nan ya zamo na sauyawarsa". Duk da miskilancinsa amma shurunsa yayi yawa,haka suke tafe a hanyarsu ta komawa dakin taron,taro yaci gaba kamar yadda yayo announcing business partners din da suka halarci zaman,saidai jabir yana biye dashi,gaba daya kamar ba ja'afar ba yau,ja'afar very energetic person,amma yau din yanata abu kaman mara lafiya. Biron hannunsa ya aje saman table din bayan yayi singing wata takarda,zai tura file din jabir ya karba yana duba singing din,sai ya zubewa ja'afar idanunsa "Me yake damunka yau?,kaga abinda kayi jikin takardar nan kuwa?" Ya fada masa da harshen hausa qasa qasa,duk da cewa dukka mahalarta taron babu bahaushe ko daya bare ya fahimci abinda yake fada masa "it's better to let everyone go.....ka sanya wani time and date din a qarasa abinda bamu gama ba" bai jaa da cewar jabir ba,don a jikinsa yaji yana buqatar hutu,cikin mutuntawa girmamawa da sanin ya kamata jabir ya juya yayi musu bayani gwargwadon yadda zasu fahimta ba tare da jin damuwa ba. Ko kafij jabir din ya gama sallamarsu tuni ya yima drivernsa magana,don haka ko ta office dinsa bai koma ba ya wuce parking lot driver ya tashi motar sukayo gida,yau ko ta eatery din bai biya ba bare ya samawa kansa abinda zaici. Next Chapter Leave a comment Post Comments No Comments posted yet Contact Us *GURBIN IDO* 45 Tunda ya dawo gidan baba tabawa tasan ya shigo,ta kuma gayawa maimunatu a fakaice indirectly cewan ya dawo din,ta yita zuba ido taga ta fita yi masa sannu da zuwa ko wani abu makamancin hakan amma bata gani ba,tunda tasan unaisa bata nan,dazun da ta zaga baya tana tsinkar musu lemon tsami taga fitarta,babu kuma alamun ta dawo. Abun nata cin ran baba tabawa,har zuwa lokacin da suka zauna cin abincin dare,ta dubi maimunatu "Waiku kam.....haka akewa miji?,ya fita ya wuni fafutukar nema muku abinci,ya dawo amma ko arziqin sannu da zuwa a gaya masa bai samu ba?,sa'annan ace abincin da zaici ma a gidansa ya gagaresa a kasa sammasa?,anya kuwa maimunatu?,ta yaya zaki bata dukka yardar da anni ta baki?,ta dora duk wani fatanta da burinta akanki amma kina neman bata kunya?" Qasa tayi da kanta,tana jin kunya da nauyin suna kamata tun gabanin xancan ma yaje kunnen annin,tabbas tayi kuskure da gaske,to amma kuma shi dinne.....ba irin sauran mutane bane,batasan ta yadda zata fuskanci bahagon mutum irinsa ba,yau inda ace shi din kamar hisham yake to da da sauqi sauqi,amma.....he's totally different from what they are seeing about him,ba abu bane mai sauqi tunkararsa "Kiyi haquri baba,baice yana buqata ba" "Kin taba nuna damuwa ko gwada kaiwar bare ki Fatima hakan?,bari na fito miki a mutum maimunatu" baba tabawa ta fada tana gyara zamanta,abinda ya sanya maimunatu tattara hankalinta waje daya "Gaba daya na fuskanci inda zaman aurenki ua dosa,bansan na abokiyar zamanki ya yake ba,a gajarce zan gaya miki,ba'a yankewa mutum hukunci ba tare da ka ma'amalanceshi ba,ki sauya,ki zama kamar kowacce mace a gidanta,ki sauke naki hakkin da nauyin,ko meye zai taso a gaba....ko meye zai biyo baya zaki fita a ciki,kiyimin alqawari daga yau zaki canza,inason ganinki kamar kowacce macen auren maimunatu,ina miki sha'awar hakan,na san ja'afar,yana da zuciya me kyau wani abune daban ya canzashi,kuma ina kyautata zaton duk wanda ya aro wani hali da ba nashi ba,rabashi dashi abune me sauqin gaske,zaki canza maimunatu?" Kai ta gyadawa baba tabawa a hankali,tana sake jin nauyi,saboda tana ji a ranta da gasken butulci take son tayi,tana qasan inuwar alfarmarsu,ta samu rayuwa me kyau me cike da gata,sannan ta kasa ciyar da dansu abincin da shine ya siyo shi?,bayan duka duka bata zaman wata biyu ma cikin gidan?. Da kanta baba tabawa ta shirya abincin cikin wasu sababbin warmers masu kyau "Dauka maza kikai masa,daga yau babu ruwanki da abokiyar zamanki,duk sanda kika fuskanci yana da buqatar abinci kuma bata nan,bata kuma bashi ba,koda ba ranar girkinki bane dauka ki bashi,ke Allah zai bawa ladan". Daki ta koma,ta zabo hijab cikin hijabs dinta ta sanya,ba abinda hijab din keyi sai qamsin turaren wuta na kaya,ya kuma amshi fatarta qwarai,kalar blue black,da kallo baba tabawa ta bita sanda ta fito,kamar tace mata ta canza mayafi a maimakon hijab din,amma sai kuma ta canza shawara ta qyaleta. A hankali ya sauke ajiyar zuciya,sannan ya tura hannunsa cikin sumarsa yana yamutsata,hakanan yaji kawai komai baya maaa dadi,sai yakai hannunsa guda daya ya rufe system din dake gabansa ba tare daya damu da yayi shutting down dinta ba,duk da muhimmancin hakan,sai ya koma a hankali ya jingina bayansa da kujerar da yake zaune,ya kuma hade yatsunsa waje daya yana lumshe idanuwansa. Wani irin bugu zuciyarta take sanda takai step din qarshe na benan,tana ji kamar ta koma,amma kuma idan tayi hakan bata kyauta ba,kamar ta wofantar da maganar baba tabawa ne,ci gaba tayi da takawa cikin tsoro da fargaba,tana tafiya kamar ba zata kai qofar da zata sadata da ainihin falon ba. Sanda ta isa qofar sai taja ta tsaya cak,ta runtse idanunta da qarfi,a karo na farko zata fara taka sassansa,batasan da wacce fuska zata kalleshi ba,tsoronsa yana nan fal cikin zuciyarta,tanason baiwa kanta qwarin gwiwa,ta dora hannunta saman handle din,ta runtse idanunta gami da dauke numfashinta sannan ta tura ta sanya kanta. Daga inda yake zaune miqe da qafafunsa saman table din gabansa idanunsa a rufe yaji an motsa qofar,saidai duk da haka hakan bai sanyashi motsawa ko bude idanunsa ba,a zatonsa unaisa ce,wadda ta gaza haqurin zuwa wajensa da ziyartarsa lokaci lokaci,bayan ya riga daya tabbatar mata gaskiyar abinda ke ranshi gami da bata zabi. A hankali sassanyan qamshin da ya hanashi sukuni wunin yau,ya kuma wuni dashi cikin jikinsa ya fara cika masa hanci,ya kuma gauraye da sallamarta cikin siririyar muryarta din nan mai dauke da wani amo na musamman,ba tare daya shiryama faruwar hakan ba ya soma bude idanunsa da suka sauya launi saboda mintunan da suka dauka a kulle. Fes ya sauke idanunsa a kanta,cikin shigar da yawanci shaheedansa ke yinta,shigar da yakan tsokaneta da ita zamanin da suna raye "I want to see my wife gani na haqiqa..... please madam, remove it" murmushi take jifansa dashi,sannan ta zare din tana fadin "Am all yours,and belongs to you". Haka kawai ya samu kansa da gaza dauke idanunsa daga kanta,wani abu na masa yawo tsakiyan kai kamar ana yamutsa kwanyarsa,duk da cikin hijab take amma hoton dazu ke masa yawo cikin idanunsa,ya qureta da kallon dashi kansa yasan idan da ace ita din ba halaliyarsa bace ya kauceea koyarwar addini,baisan me ya sanya masa qulafucin kallonta haka ba. cikin matuqar juriya da kuma dauriya take bawa kanta confidence,abun dazunke tabata,tana jin kakar qasa ta tsage mata ta shige,ko kuma tayi fiffike ta fice a dakin,ta iso gab dashi kana ta sulale a gabansa ta tsugunna,abinda ya bawa turarenta damar isa gareshi da kyau "Barka da dare" tayi maganar da wani irin tune,sai ya tashi ya zauna sosai yana sauke sambala sambalan qafafunsa daga saman table din zuwa qasa "Barka" ya amsata a taqaice,bata tsaya jiran cewarsa ko wani abu ba ta fara fidda warmers din,ya bude baki kaman zaiyi magana kiran jabir ya shigo wayarsa,sai ya maida hankalinsa ga amda wayar,inda ita kuma hakan ya rage mata wani mugun nauyi da takeji an aza mata tun farkon shigowarta falon,rawar da hannayenta keyi suka ragu,ta fidda koma ta kuma yi serving dinsa ta jera komai cikin nutsuwa,sai ta miqe ta fara takawa zata bar falon,cikin ranta cike da fata da addu'ar kada wani abu ya tsaidata. Dan binta yayi da kallo kadan yana karantar tafiyartata duk da amsa wayar da yakeyi,tamkar wata me tafiya saman rairayi ko yashi mai laushi,duk da bai iys ganin qafafunta saboda hijabin da ya saukar mata,amma kuma yanayin tafiyarta kawai zai gaya maka qafafunta akan tsari suke,janye idanunsa yayi yana jan dan qaramin tsaki,tsakin da ya bayyanarwa jabir ta cikin wayar "Lafiya?" Ya tambayeshi a taqaice "No... it's not a matter,ina jinka" yayi maganar yana sauke dubansa ga abincin,wanda tuni yaja ra'ayinsa,bai kuma iya gama wayar ba ya zamo a hankali daga saman kujerar,ya sanya spoon din data ajjiye masa ya diba ya fara ci. Har cikin ransa yaji nutsuwa da abincin dari bisa dari,dama baba tabawa zabinsa ce akan abinci,don haka duk wani tsohon cinsa ya tashi,yaci abincin sosai fiye da kima,ya kuma kwantar da tsohuwar yunwarsa,haka nan ya dinga jin wata nutsuwa na saukar masa,ba shakka samun abinci gamsashe ma rahama ne,duk wata gajiya da kasala da yake ji fiye da rabinta ta kama gabanta,sai ya samu kuzarin yin aikinsa fiye da dazun,ya sake kunna system dinsa,yaci gaba da nazarin meeting dinsu na dazu wanda tuni PA dinsa yayi documenting komai ya aiko masa,ya dinga cire kusakuran da yayi a dazun,lokaci lokaci yana dan jan tsaki,baisan ya akayi gaba daya dan qanqanin abu irin wannan ya dagula masa lissafi ba,saidai duk da hakan a yanxun ma idan ya tuna sai yaji tsigar jikinsa tadan zuba,yakan dan lumshe idanunsa kadan kana ya bude ya ture komai yaci gaba da aikinsa. Binta da kallo baba tabawa tayi lokacin da tayi sallama take shigowa falon,sai taci gaba da kallonta baki bude,har ta iso tana zubewa saman kujera "Wash" ta furta ba tare da tunanin komai ba,ta fadi kalmar ne saboda yadda taji kamar an bubbuge mata gabbanta,uwa uba kuma gudun zuciyarta daya qaru wanda sai a yanzu take qoqarin sai saita kanta. Hijabinta ta zare ba tare data lura da kallon da baba tabawa ke binta dashi ba,ta isa ga fridge ta bude,ta fidda ruwa me sanyi saboda yadda takejin maqoshinta ya bushe sosai,bata buqaci cup ba ta balle murfin ta fara sha a hankali,idanunta na hango mata shi cikin falon nasa da bai fiya haske ba,cikin wata abaya ta maza "A haka he's very calm and quiet,amma macijin sari ka noqe ne" ta fadawa kanta da kanta tana cire robar daga bakinta,ta dora ragowar saman fridge din sannan ta juyo. Sai a sannan ta lura da kallon da babab take mata,ta kuma tsargu,amma kafin ta tambaya ita ta rigata "Har me?,wai har kin dawo?" Kai ta gyada mata tana neman wajen zama,hannu tasa ta kama baki,sai kuma ta kada kai "Nidai nasan ba'a ajewa miji abinci a taho a barshi dashi" "Aiki yake baba,kuma waya ma yake amsawa,so yana buqatar space,may be wayar ta sirrice" ta fada har zuciyarta,saidai ita baba tabawan ta kalli hakanne da sunan bawa kai kariya kawai "To Allah ya kyauta" yadda baban tayi sai duk maimunatu taji bata ji dadi ba,saboda itama baban kamar bataji dadin yadda tayin ba,to amma kuma ta yaya zata iya zama dashi a muhalli guda?,ko abincin data kai din kawai tasan karambani tayi da kuma bin umarni,tana da yaqinin zaiyi wuya yacu,ta fahimci kamar yana da jin kansa,izza da kuma qasaita,bai taba neman wani abu daga garesu ba cikin gidan dai dai da ruwan sha kuwa,sai taja wayarta kawai ta kunna data tahau sabon Whatsapp dinta,ta kuma fara da yiwa qawayen nata guda uku sallama. Taci sa'a kuwa ta samu afrah a online,cikin mamaki take tambayar da gaske itace,sai suka zarme da hira,wadda ta daukesu lokaci mai tsaho,daga bisani sukayi sallama bayan ta bata labarin latest Korean dramas masu zafi da suka fito. Kai tsaye ta wuce Vidmate ta saukesu masu yawan gaske,saidai tana tunanin yadda zata kallesu a nutse ba tare da sun hanata bitar karatuttukanta na makaranta ba. 46 Tunda ya dawo gidan baba tabawa tasan ya shigo,ta kuma gayawa maimunatu a fakaice indirectly cewan ya dawo din,ta yita zuba ido taga ta fita yi masa sannu da zuwa ko wani abu makamancin hakan amma bata gani ba,tunda tasan unaisa bata nan,dazun da ta zaga baya tana tsinkar musu lemon tsami taga fitarta,babu kuma alamun ta dawo. Abun nata cin ran baba tabawa,har zuwa lokacin da suka zauna cin abincin dare,ta dubi maimunatu "Waiku kam.....haka akewa miji?,ya fita ya wuni fafutukar nema muku abinci,ya dawo amma ko arziqin sannu da zuwa a gaya masa bai samu ba?,sa'annan ace abincin da zaici ma a gidansa ya gagaresa a kasa sammasa?,anya kuwa maimunatu?,ta yaya zaki bata dukka yardar da anni ta baki?,ta dora duk wani fatanta da burinta akanki amma kina neman bata kunya?" Qasa tayi da kanta,tana jin kunya da nauyin suna kamata tun gabanin xancan ma yaje kunnen annin,tabbas tayi kuskure da gaske,to amma kuma shi dinne.....ba irin sauran mutane bane,batasan ta yadda zata fuskanci bahagon mutum irinsa ba,yau inda ace shi din kamar hisham yake to da da sauqi sauqi,amma.....he's totally different from what they are seeing about him,ba abu bane mai sauqi tunkararsa "Kiyi haquri baba,baice yana buqata ba" "Kin taba nuna damuwa ko gwada kaiwar bare ki Fatima hakan?,bari na fito miki a mutum maimunatu" baba tabawa ta fada tana gyara zamanta,abinda ya sanya maimunatu tattara hankalinta waje daya "Gaba daya na fuskanci inda zaman aurenki ua dosa,bansan na abokiyar zamanki ya yake ba,a gajarce zan gaya miki,ba'a yankewa mutum hukunci ba tare da ka ma'amalanceshi ba,ki sauya,ki zama kamar kowacce mace a gidanta,ki sauke naki hakkin da nauyin,ko meye zai taso a gaba....ko meye zai biyo baya zaki fita a ciki,kiyimin alqawari daga yau zaki canza,inason ganinki kamar kowacce macen auren maimunatu,ina miki sha'awar hakan,na san ja'afar,yana da zuciya me kyau wani abune daban ya canzashi,kuma ina kyautata zaton duk wanda ya aro wani hali da ba nashi ba,rabashi dashi abune me sauqin gaske,zaki canza maimunatu?" Kai ta gyadawa baba tabawa a hankali,tana sake jin nauyi,saboda tana ji a ranta da gasken butulci take son tayi,tana qasan inuwar alfarmarsu,ta samu rayuwa me kyau me cike da gata,sannan ta kasa ciyar da dansu abincin da shine ya siyo shi?,bayan duka duka bata zaman wata biyu ma cikin gidan?. Da kanta baba tabawa ta shirya abincin cikin wasu sababbin warmers masu kyau "Dauka maza kikai masa,daga yau babu ruwanki da abokiyar zamanki,duk sanda kika fuskanci yana da buqatar abinci kuma bata nan,bata kuma bashi ba,koda ba ranar girkinki bane dauka ki bashi,ke Allah zai bawa ladan". Daki ta koma,ta zabo hijab cikin hijabs dinta ta sanya,ba abinda hijab din keyi sai qamsin turaren wuta na kaya,ya kuma amshi fatarta qwarai,kalar blue black,da kallo baba tabawa ta bita sanda ta fito,kamar tace mata ta canza mayafi a maimakon hijab din,amma sai kuma ta canza shawara ta qyaleta. A hankali ya sauke ajiyar zuciya,sannan ya tura hannunsa cikin sumarsa yana yamutsata,hakanan yaji kawai komai baya maaa dadi,sai yakai hannunsa guda daya ya rufe system din dake gabansa ba tare daya damu da yayi shutting down dinta ba,duk da muhimmancin hakan,sai ya koma a hankali ya jingina bayansa da kujerar da yake zaune,ya kuma hade yatsunsa waje daya yana lumshe idanuwansa. Wani irin bugu zuciyarta take sanda takai step din qarshe na benan,tana ji kamar ta koma,amma kuma idan tayi hakan bata kyauta ba,kamar ta wofantar da maganar baba tabawa ne,ci gaba tayi da takawa cikin tsoro da fargaba,tana tafiya kamar ba zata kai qofar da zata sadata da ainihin falon ba. Sanda ta isa qofar sai taja ta tsaya cak,ta runtse idanunta da qarfi,a karo na farko zata fara taka sassansa,batasan da wacce fuska zata kalleshi ba,tsoronsa yana nan fal cikin zuciyarta,tanason baiwa kanta qwarin gwiwa,ta dora hannunta saman handle din,ta runtse idanunta gami da dauke numfashinta sannan ta tura ta sanya kanta. Daga inda yake zaune miqe da qafafunsa saman table din gabansa idanunsa a rufe yaji an motsa qofar,saidai duk da haka hakan bai sanyashi motsawa ko bude idanunsa ba,a zatonsa unaisa ce,wadda ta gaza haqurin zuwa wajensa da ziyartarsa lokaci lokaci,bayan ya riga daya tabbatar mata gaskiyar abinda ke ranshi gami da bata zabi. A hankali sassanyan qamshin da ya hanashi sukuni wunin yau,ya kuma wuni dashi cikin jikinsa ya fara cika masa hanci,ya kuma gauraye da sallamarta cikin siririyar muryarta din nan mai dauke da wani amo na musamman,ba tare daya shiryama faruwar hakan ba ya soma bude idanunsa da suka sauya launi saboda mintunan da suka dauka a kulle. Fes ya sauke idanunsa a kanta,cikin shigar da yawanci shaheedansa ke yinta,shigar da yakan tsokaneta da ita zamanin da suna raye "I want to see my wife gani na haqiqa..... please madam, remove it" murmushi take jifansa dashi,sannan ta zare din tana fadin "Am all yours,and belongs to you". Haka kawai ya samu kansa da gaza dauke idanunsa daga kanta,wani abu na masa yawo tsakiyan kai kamar ana yamutsa kwanyarsa,duk da cikin hijab take amma hoton dazu ke masa yawo cikin idanunsa,ya qureta da kallon dashi kansa yasan idan da ace ita din ba halaliyarsa bace ya kauceea koyarwar addini,baisan me ya sanya masa qulafucin kallonta haka ba. cikin matuqar juriya da kuma dauriya take bawa kanta confidence,abun dazunke tabata,tana jin kakar qasa ta tsage mata ta shige,ko kuma tayi fiffike ta fice a dakin,ta iso gab dashi kana ta sulale a gabansa ta tsugunna,abinda ya bawa turarenta damar isa gareshi da kyau "Barka da dare" tayi maganar da wani irin tune,sai ya tashi ya zauna sosai yana sauke sambala sambalan qafafunsa daga saman table din zuwa qasa "Barka" ya amsata a taqaice,bata tsaya jiran cewarsa ko wani abu ba ta fara fidda warmers din,ya bude baki kaman zaiyi magana kiran jabir ya shigo wayarsa,sai ya maida hankalinsa ga amda wayar,inda ita kuma hakan ya rage mata wani mugun nauyi da takeji an aza mata tun farkon shigowarta falon,rawar da hannayenta keyi suka ragu,ta fidda koma ta kuma yi serving dinsa ta jera komai cikin nutsuwa,sai ta miqe ta fara takawa zata bar falon,cikin ranta cike da fata da addu'ar kada wani abu ya tsaidata. Dan binta yayi da kallo kadan yana karantar tafiyartata duk da amsa wayar da yakeyi,tamkar wata me tafiya saman rairayi ko yashi mai laushi,duk da bai iys ganin qafafunta saboda hijabin da ya saukar mata,amma kuma yanayin tafiyarta kawai zai gaya maka qafafunta akan tsari suke,janye idanunsa yayi yana jan dan qaramin tsaki,tsakin da ya bayyanarwa jabir ta cikin wayar "Lafiya?" Ya tambayeshi a taqaice "No... it's not a matter,ina jinka" yayi maganar yana sauke dubansa ga abincin,wanda tuni yaja ra'ayinsa,bai kuma iya gama wayar ba ya zamo a hankali daga saman kujerar,ya sanya spoon din data ajjiye masa ya diba ya fara ci. Har cikin ransa yaji nutsuwa da abincin dari bisa dari,dama baba tabawa zabinsa ce akan abinci,don haka duk wani tsohon cinsa ya tashi,yaci abincin sosai fiye da kima,ya kuma kwantar da tsohuwar yunwarsa,haka nan ya dinga jin wata nutsuwa na saukar masa,ba shakka samun abinci gamsashe ma rahama ne,duk wata gajiya da kasala da yake ji fiye da rabinta ta kama gabanta,sai ya samu kuzarin yin aikinsa fiye da dazun,ya sake kunna system dinsa,yaci gaba da nazarin meeting dinsu na dazu wanda tuni PA dinsa yayi documenting komai ya aiko masa,ya dinga cire kusakuran da yayi a dazun,lokaci lokaci yana dan jan tsaki,baisan ya akayi gaba daya dan qanqanin abu irin wannan ya dagula masa lissafi ba,saidai duk da hakan a yanxun ma idan ya tuna sai yaji tsigar jikinsa tadan zuba,yakan dan lumshe idanunsa kadan kana ya bude ya ture komai yaci gaba da aikinsa. Binta da kallo baba tabawa tayi lokacin da tayi sallama take shigowa falon,sai taci gaba da kallonta baki bude,har ta iso tana zubewa saman kujera "Wash" ta furta ba tare da tunanin komai ba,ta fadi kalmar ne saboda yadda taji kamar an bubbuge mata gabbanta,uwa uba kuma gudun zuciyarta daya qaru wanda sai a yanzu take qoqarin sai saita kanta. Hijabinta ta zare ba tare data lura da kallon da baba tabawa ke binta dashi ba,ta isa ga fridge ta bude,ta fidda ruwa me sanyi saboda yadda takejin maqoshinta ya bushe sosai,bata buqaci cup ba ta balle murfin ta fara sha a hankali,idanunta na hango mata shi cikin falon nasa da bai fiya haske ba,cikin wata abaya ta maza "A haka he's very calm and quiet,amma macijin sari ka noqe ne" ta fadawa kanta da kanta tana cire robar daga bakinta,ta dora ragowar saman fridge din sannan ta juyo. Sai a sannan ta lura da kallon da babab take mata,ta kuma tsargu,amma kafin ta tambaya ita ta rigata "Har me?,wai har kin dawo?" Kai ta gyada mata tana neman wajen zama,hannu tasa ta kama baki,sai kuma ta kada kai "Nidai nasan ba'a ajewa miji abinci a taho a barshi dashi" "Aiki yake baba,kuma waya ma yake amsawa,so yana buqatar space,may be wayar ta sirrice" ta fada har zuciyarta,saidai ita baba tabawan ta kalli hakanne da sunan bawa kai kariya kawai "To Allah ya kyauta" yadda baban tayi sai duk maimunatu taji bata ji dadi ba,saboda itama baban kamar bataji dadin yadda tayin ba,to amma kuma ta yaya zata iya zama dashi a muhalli guda?,ko abincin data kai din kawai tasan karambani tayi da kuma bin umarni,tana da yaqinin zaiyi wuya yacu,ta fahimci kamar yana da jin kansa,izza da kuma qasaita,bai taba neman wani abu daga garesu ba cikin gidan dai dai da ruwan sha kuwa,sai taja wayarta kawai ta kunna data tahau sabon Whatsapp dinta,ta kuma fara da yiwa qawayen nata guda uku sallama. Taci sa'a kuwa ta samu afrah a online,cikin mamaki take tambayar da gaske itace,sai suka zarme da hira,wadda ta daukesu lokaci mai tsaho,daga bisani sukayi sallama bayan ta bata labarin latest Korean dramas masu zafi da suka fito. Kai tsaye ta wuce Vidmate ta saukesu masu yawan gaske,saidai tana tunanin yadda zata kallesu a nutse ba tare da sun hanata bitar karatuttukanta na makaranta ba. 47 Washegari tare suka hada breakfast da baba tabawan,suna aikin suna taba hira,sanye take da wasu kayan bacci masu taushi sosai,saidai basu da wani kauri me yawa midnight blue da torches na olive color,wandon iyakarsa saman idon sahunta,rigar kuwa tsahonta iya cinya ne,short sleeve ce,don iyaka dantsenta hannun yatsaya,daga gaba rigar ta dan lafe mata,har tana fidda shade na brazier dinta,bata damu ba sosai,tunda tasan babu kowa a sashen daga ita sai baba tabawa,hakanan babu me shigo musu,kalar kayan ta fidda hasken fatarta sosai,kanta qaramin dankwali ne mai santsi data masa Vshape ta daure sassalkan gashinta,wanda santsinsa dana dankwalin suka hadu waje daya suka sanya dankwalin qin zama sosai a kanta,duk bayan minti biyu saita janyo dankwalin ta rufe gaban kanta dake da wani irin kwantaccen suma mai santsi data zagaya har qeyarta,duk da safiya ce,amma jikinta qamshin turaren women maze alharamain yakeyi,qamshin dake cakude dana body mist datake amfani dashi. Hira suke sosai,baba tabawan tana bata labarai wadanda maimunatun take jinsu daban,saboda sun saɓa da tata rayuwar,saidai hirar tana nishadantar da ita sosai,saboda ko a saman fuskarta ya nuna hakan,kyawawan jerarrun fararen haqoranta sun bayyana. Knocking suka jiyo,maimunatu ta tsame hannunta daga ruwan da take dauraye kwanukan da suka gama amfani dasu,ta goge jikin towel na kitchen din,sannan ta fito da niyyar budewa ba tare da tunanin komai ba. A hankali ta kama handle din ta bude,abu na farko daya fara marabtarta qamshin jikinsa ne,wanda acn da aka balbalawa babban falon ke tunkudo qamshin da gaske zuwa nata falon. Saman kanta idanunsa suka fara sauka,wanda dankwalin kanta ya zame xuwa rabin kanta,abinda ya bawa gashinta damar bayyana sosai,sai ya zame idanun nasa ya janyesu gefe,tasa dukka hannayenta biyu tana dafe dankwalin dake shirin faduwa daga kanta gaba daya,ta kuma janye qafafunta da taji suna sarqewa zuwa gefe ta bashi hanyar shigowa,a sace idanunta na binsa da kallo,cike da mamakin shigarsa ta yau ta zallar bahaushe,cikin wani lallausan farin yadi me shara shara,wanda hatta fara qal din singlet din dake jikinsa sai data bayyana,ya giftata ya bar mata qamshinsa wanda batasan me yasa take samun wata nutsuwa ta musamman ba duk sanda zata shaqeshi. Kamar wata mara gaskiya ta rabe a bayansa "Ina kwana?" Ta fadi a matuqar ta kure,nadamar yadda ta fito haka gaba gadi ba tare da tambaya ko sanin waye ba tana shigarta. Gaba daya ya waiwayo zuwa inda take tsayen,hannayensa dunqule cikin aljihun rigarsa,ya zube idanunta da sukayi wani irin laushi saman qirjinta dake bayyana shatin baqar brazier dinta,yadda yake qoqarin janye idanunsa daga wajen haka zuciya da idanunsa ke ingizashi zuwa ga ci gaba da kallonta,yana jin kamar wani mayen qarfe aka dasa ma idanun nasa a wajen,yayin da wani abu me kama da tsarguwa ya saukarwa maimunatu jin shuru bai amsa ba,cike da jarumta da son tsira da mutunci ya raba idanunsa daga wajen yana lumshesu "Karki sake irin wannan gangancin,kinsan waye da kk bude qofa batare da kin tambaya ba?" Yayi maganar yana sake qarewa shigarta kallo,hatta sambala sambalan qafafunta sun fito sosai saboda rashin tsahon wandon,yana kallonta 'yar qarama a gabansa,yanayin da ya tuna masa da zamanin amarcinsa da shaheeda, she's always like this......under eighteen,sannan taci gaba da zama da dabi'antuwa kamar yadda yakeso ta kasance masa,ta ina ta kuma yaya zai maida GURBINTA?. "kayi haquri" kalaman suka sauka a kunnensa dai dai da irin yadda shaheeda take fada masa,bata kuma taba canza kalamanta da haka ba,koda shi ya bata mata,yakance "Uhnnnn.....u are killing me shaheeda,ko yaushe kayi haquri?kayi haquri,You don't want to make excuses for yourself?" Daga kai maimunatu da sauri tayi ta dubeshi jin abinda ya fada,sai shima ya maida idanunsa kanta ganin yadda take kallonsa,sai a sannan ya karanci ashe a sarari yayi maganar,saidai can qasan maqoshinsa ne,janye idanuwansa yayi yana dan tsuke fuska kadan,ya akayi maganar ta fito fili? "Shaheeda" takira sunan a ranta tana son tuno inda tasan sunan,ummin amna?,kwanyarta ta bata.....kafin ta gama tantancewa muryar baba tabawa ta yiwa falon tsinke. Sai a sannan ya dauke kansa da shanyayyun idanunsa gaba daya daga dubanta ya maida ga baba tabawa,wadda har tayi niyyar juyawa a yanayin data gansu a tsaye,cikin sakanni ta karanci wasu qananun abubuwa a fuskar kowannensu "Manya,har an fito?" Kai ya jinjina ya kuma ranqwafa yana gaidata,ta amsa cike da kulawa,ya sanya hannunsa a aljihu ya fiddo kudi ya ajjiye mata "Ah.....ai an kammala karin safe,ka jira a gabatar maka" bata saurari amsarsa ba ta juya ga maimunatu "Suna kitchen fa" ta fadi mata,kamar wadda ke jiran umarnin barin wajen tayi gaba tana qara hanzari,gaba daya kamar tayi layar zana haka take ji,da so samu ne dakinta ya kamata ta biya ta fafa dauko hijabi,to amma kuma baba tabawan fa?,hakan zai zama kamar wani rashin girmamawa ne a gareta,dole ta wuce zuwa kitchen din. Sanda ta dawo falon a tsaye ta sameshi yana saita agogon hannunsa,qarin tashin hankalin baba tabawan bata nan a falon,sau daya tak ya daga kai ya kalleta ya maida ga abinda yakeyi,saita wuce dining ta jera komai,kafin tayi magana taga yana takowa zuwa wajen,yaja kujera daya ya zauna a kai,har yanzun bai kuma dubanta ba. "Me za'a zuba maka?" Tayi tambayar tanason riqe rawar da muryarta keyi,don gaba daya ta gama rudewa,Allah Allah take ta gama serving nasa tabar wajen "Anything" ya amsata a taqaice,warmers din ta fara qoqarin budewa,saidai duk wadda takama zata bude saita kasa,saboda santsi da kuma yadda jikinta yayi weak,tako ina a jikinta takejin idanunsa na mata wayo,tayi Allah wadaran shigar da kuma yadda ta zauna haka yau din babu ko dan baby hijab din da take amfani dashi ko da yaushe,a nutse yake karantarta,kafin ya kauda idanunsa yana latsa wayarsa,ata qarshe ne ya daga hannu da niyyar karba y bude ganin ta kasa,incidentally hannunsa ya sauka saman nata hannun,abinda ya haifar masa da wani irin shock a jikinsa,yayin da ita kuma tashin farko jikinta ya dauki rawa,ta kuma zame hannun nata da sauri taja baya kadan,yi yayi kamar baisan abinda ya faru ba,a nutse ya dauki bowl da serving spoon ya fara diban farfesun kayan cikin dake cikin warmer din. Tsoronta gaba daya ta dunqule ta kuma hadiye,saboda tuna warning nata daya taba yi,ta matso a kasalance,ta jawo flask na tea data hada da kanta da wasu hadin kayan shayi na musamman data shekaran jiya tana cikin browsing ta fara zuba masa,wani irin qamshi me dadi ya gauraye wajen,har sai da yaja iskar data kwaso qamshin har cikin hunhunsa,deep inside kuma yawunsa ya fara tsinkewa,ta dauko kwalin suger ta dauki one cube ta saka,ta sake debowa zata qara sanyawa kenan yace "Enough,ya isa" gaba daya kwalin sugar din ya subuce daga hannunta don dama a tsorace take,suka fara rige rigen afkawa cikin kofin tea din,abinda ya bawa ruwan zafin damar yin fallatsi,ya dawo mata hannayenta,taja baya da sauri tana jin zafin saukar ruwan zafin na ratsata sosai har kwanyarta. Spoon din hannunsa daya fara diban farfesun ya ajjiye,ya hade yatsunsa waje guda yana kallonta,ta hada gumi tana yarfar da hannun,da alama ruwan ya tabata sosai,har ya dauki spoon din xaici gaba da cin abincinsa sai kuma ya kasa,komai tayi shige yake masa da silly attitude na shaheeda data sha yi masa farkon aurensu "seat here" yayi maganar yana jan kujerar dake daura dashi,idanunta da suka tara hawaye ta daga ta dubeshi dasu,kamar wadda ke shirin sakin kuka,sai ta tako a hankali kamar kazar da qwai ya fashewa a ciki,ta zauna a darare saman kujerar tana dubansa "Let me see" ya fada yana miqa mata hannunsa,idanunsa cikin nata yana kallon yadda ta narke gaba daya,gumi kuma ya tsatstsafo saman goshinta. Sai data maida dubanta ga lallausan tafin hannunsa kamar me tsoron wani abu,sannan ta miqa masa hannun nata a hankali,ya miqa nasa ya riqe yatsun nata. Qaramar qara ta saki da siririyar muryarta me zaqi wadda ta ratsa dodon kunnensa da kyau,idanuwansa ya rintse sosai sannan ya budesu ya zubesu saman fuskarta wadda tuni hawaye sun fara mata zarya,ya dinke fuskarsa tsaf yana ci gaba da tsare gida "What is that?,zaki kashemin kunne ne?" Kai ta girgiza,gaba daya hawaye ya wanke mata fuska,ta wani narke cikin wani yanayi daya darsa tausayinta cikin ransa,sai ya janye idanunsa yana qoqarin kawar da wannan ya mayar kan hannun nata. Da sauri ya janye yatsunsa daga inda ya riqe din,saboda yadda wajen yayi jaa,da alama a wajen ta qone din,kafin yayi wani abu baba tabawa ta iso "Lafiya dai ko maimunatu?" Tayi tambayar tana dubanta "Subhanallahi" baba tabawan ta fada sanda taga hannun nata "Garin yaya?" Ta jefa mata tambayar,rashin sanin amsar da zata bata yasa ta maida dubanta ga ja'afar,dauke kansa yayi kamar baya wajen,kamar bashi take kallo ba,kujerarsa ya sake jawowa gaba kadan,ya zamana dab da ita sosai "Silly girl" ya fada qasa qasa,sake mele baki tayi zata sake sakin kukan,kamar yasan da haka ya kuma daga shanyayyun idanunta acikin nata,sai tayi hanzarin kulle nata idanun,ita kadai tasan me yake haifar mata idan ya mata irin wannan kallon,yana qara mata razani a kansa da kuma wani irin kwarjini da takeji kamar zai sata narkewa a wajen. Sannu baba tabawa ta matso tana mata sanda ta duqufa yana mata tofi a hannun nata,ya kwashi kusan minti talatin yana mata tofin babu tsayawa,sannan ya zare hannunsa daga cikin nata "Sannu maimunatu" baba tabawa ta fada fuskarta na nuna alhini,idanunta akan hannun nata da yayi jaa abinka da farar fata,kanta ta gyada "Ko za'a kaita asibiti?" "no need,bazai komai ba....in sha Allah,zanma hisham magana,zai prescribing mata pain killer,sai a kawo,she will be okay" "To Allah yasa"baba tabawa ta amsashi,duk da bata gane komai da komai da yake fada ba "Ki cire hijabin kisha iska" baba tabawa tace da ita,sai ta noqe taqi motsawa,ta yaya zata fidda hijabin data saka saboda yiwa jikinta shamaki,ya fuskanci sarai saboda shi din taqi motsawa,sai ya miqe kawai yana kwashe wayoyinsa ya xuba a aljihunsa "Manya....ai ba abinda kaci" kai ya gyada "Am okay,thanks" daga haka ya juya yana barin falon,yana kuma sanya hannunsa a aljihunsa yana laluben key din motarsa,don yau a masallacin wuro bokki yakeson yin ssallar juma'a,yanason kuma samun gaba gaba,ya tabbatar abbi ma yana ciki yanzu haka. 48 Sai daya jima da barin wajen sannan ta tashi ta wuce dakinta,ruwa ta hada tayi wanka,sai taji dadin jikinta,kaya ta saka marasa nauyi cotton wanda bazasu takurata ba,komai takeyi cikin kasala take jinta,sai kawai ta haye gadonta,ta lumshe idanunta. Fuskarsa da qamshinsa ne suka fara bijiro mata,the way daya dinga treating dinta,yana kuma watsa mata nauyin idanuwansa da suke da wani irin magnet a cikinsu me qarfi,wani juyi tayi,wanda cikin rashin sani ya sanyata danne hannunta dake dan zugi har yanzu,sai data ce wash Allah. "Wai meye haka?" Ta jefi kanta da kanta da wannan tambayar,sai taja qaramin tsaki,ta miqa hannunta ta dauko wayarta dake saman kanta,videos din data dauko ta shiga,ta zaba drama daya ta kunna ta fara kalla. Bata dauki dogon lokaci ba ta fahimci zaa buga soyayya sosai,abinda yasa ta tattara hankalinta akai,tana kuma biye dasu,lokaci lokaci tana sakin murmushi,a qalla tayi kusan awa uku sannan barci ya soma fusgarta,babu jimawa kuwa ya dauketa gaba daya daga duniyar nan zuwa tasa duniyar. Sau biyu baba tabawa na leqota don taga ko lafiya?,duk sanda ta leqo din sai taga wayarta tana yi,sai ta koma ga zatonta idanunta biyu,kallo kawai takeyi. Tunda ya fita yana masallacin,ya kuma samu gaba kamar yadda yakeso,a gabansa liman ya iso,ya gabatar da kuduba aka kuma tayar da sallar,sanda aka idar ya samu ganin abbi,saidai kuma yana ta fama da mutane,don haka ya masa sallama yace sa hadu a gida. A harabar masallacin ya suka gamu da jabir,abinda ya sake tsaidashi kenan,ganin maganar tasu ba zata qare ba,sai ya kira driver dinsa yace yazo ya dauki motar suka wuce a motar jabir din. Gidan mahaifin jabir qanin abbi suka fara zuwa,suka gaida uncle usman da matarshi,sun jima suna hira dashi kafin su baro gidan,suka wuce gidan abbi dr marwan. Kamar ko yushe sassan ammansa ya fara shiga suka gaisa,ya taras da amna ta tashi a bacci,tana ta taba rigimarta,ganinsa yasa ta watsar da komai ta dafeshi tana fadin xata bishi,yarinyar nason binsa,shima kuma a duniya yafi kowa son kasancewa da ita a muhalli guda,to amma kuma idan yace zai dauketa wa zai kaiwa ita?,wa zai kula masa d ita?,ya tabbatar ba zata taba samun kwatankwacin kulawar da take samu ba a wajen su amma,bai amsata ba ya sabeta ya wuce wajen ammi suka gaisa,sannan ya wuce sassan mutuniyar tasa anni yana sabe da amnan yana mata tambayoyi da suka shafi karatun makarantarta,tana ta bashi amsa dai dai,abinda yayi matuqar faranta masa. Da sallama a bakinsa ya shiga sashen,mutum uku ne zaune,anni jabir da ya riga shi yo gaba sai kuma hafsat,wadda sallamarsa ta sanyata rudewa gaba daya,ta kuma tattaro dukka nutsuwarta ta dawo da ita jikinta,gami da janye qafafunta data miqe a dazun tana kadasu,ta sanshi ta kuma san halinsa sarai,baya tolerating nonsense,har ya qaraso wajen tana satar kallonsa,tana jin kamar ta hadiyeshi,kishin unaisa da maimunatu yana saukar mata,kada ma unaisa taji labari,don ta samu labarin maimunatu ba mazauniya bace,makaranta take zuwa,bugu da qari tana ganin tayi qanqantar da zata bata wuya wajen shigowa gidan da kuma cimma muradinta. Cikin salo iyayi da kuma kwainane ta gaidashi,kansa na wani sashen ya amsa mata,abinda yayi matuqar qona ranta kenan,saidai tayi biris taci gaba da zama a wajen ba tare data motsa ba,kunnuwanta duka suna ka maganganunsu su da anni "Lallai da gaske anni tafison wadan nan guys din,kada ma wannan dan mulkin nata yaji labari" ta fadi a ranta,wanda a zahiran zaka dauka danna waya takeyi "A zuba muku abinci" gyara zama jabir yayi "Eh nikam a kawo,don nasan zaiyi wuya na samu idan na koma,don batajin dadi,banson cin kuma na yarinyar da aka kawo matan" sai da anni ta waiwaya ta dubi hafsat tace taje ta hado musu abinci a kitchen,ta kuwa miqe da hanzarinta tana aje wayarta gami da jin dadin wannan aiki da anni ta bata tayi kitchen din,sannan anni ta maido kanta ga jabir "Jikinne har yanxu?" "Wlh anni,yau da lafiya gobe babu" "To Allah ya raba lafiya" murmushi yadan saki yana shafa kansa cikin dan jin nauyin annin,baki ta tabe "Kaga dan nema,ja'iri,wai yau ni ake jin kunya" dariyar da yake riqewa ya qarasa saki,anni anni?,Allah dai yaja musu kwananta. Kamar taa bar zanca sai kuma ta dubu sashen da ja'afar ke zaune,har yanzu amna na saman cinyarsa "Allah yasa muji irin wannan labarin a gidan wancan kurman,kema yarinya kya samu kiga 'yan uwanki ko maraici da kewar da kike ciki zata ragu" yi yayi kamar ba dashi ake maganar ba,kamar kuma baiji ba,duk da maganar ta tsaya masa a rai "Ya jikin maimunatun?" Ta sake zungurarsa da magana ganin baice komai ba,dai dai sanda hafsat ke fitowa a kitchen din dauke da kwanukan abinci,gabanta yadan fadi,tana son jin qarashe zancen,kada dai ace ciki gareta "Alhmdlh" ya amsa a taqaice "Inaga kamar ya kamata tabawa ta dawo hakanan,dama tamin magana kan tanason tahowa" baiso annin ta fadi hakan ba yanzu,ko ba komai yana samun abinci kwana biyu yaci ya qoshi hankali kwance,ya rage zuwa eatery neman abinda zaici "Ba laifi" ya amsawa anni,dai dai sanda ta iso wajen,ta fara ajjiyewa jabir,sannan ta qaraso inda ja'afar din yake,cikin salo ta duqa tana ajje masa nasa abincin,wanda zubin data masa ma daban yake,in a stylish way ta shirya salad din dake saman abincin. Hannu ta miqawa amna "Taho daddy ya samu yaci abinci ko?" Kafada ts maqale tana kallonta "Ahaf.....wannan 'yar wulaqancin fa sai wanda ta zaba,wuce ciki abinki" batas anni tafada haka ba,taso zama ne a wajen taci gaba da jin hirarrakinsu,ta kuma morewa kallon ja'afar din,don yau din wani kyau yayi na musamman,kayan sunyi matuqar karbarsa. Dakin dake opposition da dakin ta shige,ta zare key din dake jikin qofar tana leqensu ta jiki,abun haushin duk yadda ta tsara masa abincin bata wani ga yaci komai ba a ciki,hasalima amna taga ta sanya cokali tana cin abinta,ruwan kawai taga ya dauka yasha,shima ba mai yawa ba. Ana sallar la'asar daga masallaci gida ya wuce bayan sunyi sallama dasu anni,already dama yayi kiran driver,don haka kafin su idar ma ya iso,ya daukeshi suka wuce,yana mota yana tunanin amnan,duk sanda yazo gidan sai yarinyar tayi attempting din binsa amma tilas take sawa yace mata a'ah,to yau ka harda kukanta,abinda yasa kenan yayi deciding next month ya dauketa su danyi yawo kadan,koda zuwa lagos ne,yasan hakan zai mata dadi,zai kuma debe mata kewa. Samansa ya wuce direct,ya bude dakin yana kallonsa,gaba daya it's not in order,komai na dakin bai masa yadda yakeso ba,sai ya koma da baya ya bude daya bedroom din nasa ya sauka a can,kayan jikinsa ya sauya kawai zuwa wata farar jallabiyya ta maza mai sulbi da kuma wide neck,ya hada dukka aikin dake kansa wanda a qa'ida yau zaiyishi a office,amma yau din juma'ar qarshen wata ne,yana basu hutu yawanci duk qarshen wata,musamman idan akwai raguwar aiki sosai a lokacin. Har zai zauna ya fasa,saboda cikinsa da yaji yana buqatar sanya masa wani abu,sannan kuma yanason jin ya hannun nata,don ya tabbatar a yadda yaji anni na masa magana a kanta yau,tabbas idan wani abu ya faru kai tsaye ma zata iya cewa shine ya qonata. A nutse yake saukowa daga stairs din,duk inda ya gifta sassanyan qamshinsa yana biye dashi,rigar ta masa kyau ta sake maidashi cikakken mutum mai cikar kamala zati da kuma haiba. Da tattausar sallama a bakinsa ya shiga falon,baba tabawan ce kadai xaune tana kallo,tana yi kuma tana duba girkinta dake kitchen,duk da abincin ma yau kusan ita daya taci na safen har na ranan,ta rasa wanne irin bacci maimunatun takeyi. Cikin fara'a ta amsa sallamar tasa ta kuma yi masa maraba,ya tambayeta hannun nata "Wallahi manya ban sani ba,tunda ta shiga ta kwanta bansan ma bacci take ba sai daga baya" baice komai ba ya miqe,hannunsa cikin aljihun rigarsa,ya nufa dakin nata. A hankali ya tura qofar ya sanya jikinsa,kamar ko yaushe dakin gauraye da madaidaiciyar iska dake cakude da qamshi iri iri wanda ya bada wani scent na musamman,kasancewar yamma tayi dakin ya rage hasken dake akwai,yaci gaba da takawa zuwa inda yake hangenta a cure waje daya,saidai hasken wayar daketa aiki ta haske fuskarta sosai. Gab da kanta amma ta bayanta,idanunsa suka sauka tun daga dogayen qafafunta dake harde waje guda,saidai kuma taba motsasu a hankali duk bayan wasu sakanni,da alama mafarki takeyi,don haka take dan motsa hannayenta ma,yawo yaci gaba dayi da idanunsa,yadda take kwancen sai yakega.kamar kwanciyar tata batai dai dai ba,sosai qugunta ya fita ta cikin rigar,sai ya dauke idanunsa da sauri ya saukesu kan screen din wayar. Minti daya kacal ya tuna film din,one of the best dramas nashi,ya akayi ta nemoshi take kuma kalla?,hannunsa ya sanya ya zare earpiece din dake kunnenta ya maida a nashi kunnen idanunsa still suna kan wayar,lallausan murmushi ya qwace masa,abinda ya qarawa fuskarsa wani mugun kyau,abinda ba kasafai yake faruwa dashi ba kenan,ya tuna scene din,ya tuna wajen,murmushin yaqi daukewa daga fuskarsa,,ya tayar masa da wani tsohon memory da kuma wani sweet moment,sai yaji yana da sha'awan sake kallon drama din,ya duqa a hankali ta saman kanta da zummar dauko wayar ya kashe mata,abinda yasa yayi mata kamad rumfa a saman kanta. Juyi tayi cikin hanzari tana sakin wata qaramar qara,abinda yasa ta bugeshi,ya kuma fada saman kanta saboda unexpected ta bugeshin,baiyi tsammanin zata motsa ha a sannan,qamqam ta riqeshi,tana tsamamnin cikin mafarkinta ne,saboda shine cikin mafarkin,ta kuma sake gasgata mafarkin takeyi jinsa a jikinta qamshinsa yana shiga qofofin hancinta. A nutse ya zube idanunsa saman sleepy face dinta,karon farko da sukayi kusanci mai zurfi a tsakaninsu irin haka,har suna musayar numfashi,wanda yake fita da tare da qamshin jikkunansu,yayi gab da ita qwarai,kamar me shirin kissing lips dinta,sosai shagwababbiyar fuskarta ke shiga idanuwansa har yana ganin qananun gashin dake qasan hancinta wadanda suka sanya wajen danyi duhu kadan,cikakkiyar girarta da ta kusa hadewa da 'yaruwarta,siraran labbanta da suke dauke da wasu irin Pink lips masu daukan hankali. Wani abu ne ya motsa zuciyarsa,har sai daya saki wasu irin tagwayen numfashi guda biyu a jejjere kamar mai sheshsheqar kuka,yanason zame kansa data zagaye hannayenta dashi saidai ya fuskanci mafarki take,kamar ma kuka kuka,saboda yadda shagwababiyar fuskartan nan ta narke gaba daya,ci gaba yayi da kallonta,a hankali murmushi ya soma maye gurbin yanayin kukanta,ya zubawa dan qaramin bakinta daya soma motsawa idanu "Kayi haquri......." "Yaa hisham" sunan ya fita can qasa,shi kansa motsi da dan qaramin fitar sautinta yabi ya fahimci me take cewa,mamaki ya cikashi,hisham?,hisham kuma take kira cikin mafarkinta?,for what reason?,fuskarta yaci gaba da kalla nasa yanayin na sauyawa ba tare daya sani ba,a hankali fuskarta ta koma normal mode na masu bacci,da alama ta gama mafarkin da takeyi kenan,sai ya zame hannunta daya nutse a qeyarsa cikin lallausar sumarsa,ya miqe tsaye yana ci gaba da kallonta bayan ya goye hannunsa a qirjinsa,kiran sunan hisham da tayi ya dawo masa,yadan rufe idanunsa sannan ya sake budewa,wani abu yaji yadan taba ransa,sai ya miqa hannu ya jawo hannunta dake boye a gefanta,zugi ya ratsa tsakiyar baccinta,abinda ya sanyata farkawa kenan. Sai data bude ta kuma rufe idanunta sau uku don son tabbatar da cewa yanzun ma mafarki ne ko ido biyu,yaji alamun ta farka amma kuma baiko daga kansa ga dubeta,yana dai nazarin hannun nata ne,sai daya tabbatar batayi ko alamin tashi ba sannan ya sake mata hannun,a hankali kuma ya aza mata idanunsa masu nauyi da suka tilastata janye nata,ya basar ya kuma motsa kaman zai fita sai kuma ya dakata "Karki qara kwanciya bakiyi addu'a ba,that's why kuke rubbing mafarkai" yana kaiwa nan ya taka sannu a hankali ya fice. Idanunta ta waro waje tana bin hanyar daya wuce da kallo bayan ta tabbatar da fitarsa,kada dai yana tsaye ta gama mafarkin da tayi yanzu,saita cusa kanta tsakiyar pillow tana son tuna me da meye ya faru cikin mafarkin,tsahon minti kusan biyar kafin ta sake daga kanta da sauri ta kalli agogo "Kai" ta fada da sauri tana wantsalowa daga gadon,ganin lokacin salla ya qwace mata sarai. 49 A kasalance yabar sashen nata zuwa nasa,gaba daya ta sakarwa jikinsa wata irin kasala,ya rasa dalilin da ya sanya duk sanda incident irin haka zai faru tsakaninsu sai haka ta kasance. Sam bai kula da wanzuwar mutum a wajen ba,har ya kama stairs zai hau yaji an kirayi sunansa a tausashe,sai ya tsaya cak,ya kuma waiwaya a hankali. Unaisa ce tsaye,sanye da wata fatar gown,kanta babu dankwali sai qaramin vail data yafa a kanta me shara shara,idanunta a kansa,tana dubansa cikin wani irin kallo wanda ya nuna yadda tayi laushi har cikin idanunta,qasan ranta tana jin wani irin qaunarsa tana fusgarta,zuwa yanzu takai maqura,hakanam tana jin haqurinta yana neman gazawa,tayi iya matuqar qoqari a irin yadda ta saba rayuwarta,sai ta sake sassauta fuskarta tana fatan ya duneta da idanun tausayi,bata taba kawowa cewa izzarsa miskilancinsa da kuma jin kansa sunkai har haka ba,tayi tunanin a kurkusa zata tagi da imaninsa kamar yadda yake tafiya da imanin duk wani da namiji,fara takowa tayi a hankali,yana biye da ita da idanu,har zuwa sanda yaga tana shirin wuce iyakar da yakega ya kamata ta tsaya "Stop there" ya fada da muryarnan tasa dake dauke d wani irin amo,ba zato babu kuma tsammani sai jinta yayi ta fada jikinsa gaba daya,ta kuma sanaya hannunta ta qanqameshi da kyau idanunta yana tara qwalla. "Meye haka?, what's this?" Ya fada yana yunqurin tureta daga jikinsa,saidai hakan bai samu ba saboda yadda ta sake cukuikuyeshi tana fadin "Na gaji.....na gaji,am going to kill my self indai ba zaka saurareni ba" furucin nata yayi masa banbarakwai sosai atsakiyan kansa,diyar musulmi ke zance aikata ta'addanci a karan kanta?,bawai don ya damu ko kima ya tsorata da furucinta ba yace "Okay,okay......sakeni tukunna" kamar ba zata sakeshin ba sai kuma ta sakeshi,ta kuma ja da baya tana dauke qananun qwallar fuskarta,hannyensa ya shiga yarfewa kamar wanda wani abun qi ya tabawa fata,fuskarsa ya sake hadewa ya tsare gida sosai yana dubanta "Am all ears" ya fada yana goye hannuwansa a qirji,idanunta tadan watsa bangaren sasan maimunatu,ta yaya zatayi irin wannan maganar dashi a waje.irin wannan,by mistake yarinyar tazo guftawa ta jisu?,ta tabbatar idan haka ta faru ajinta ya gaba zubewa a idanunta har abada "Am not comfortable here......i need privacy" kamar bazai amsata ba,sai kuma ya juya ya soma takawa zuwa saman a nutse cikin takunsan nan na daban,ta bishi da kallo tana jin wani abu yana tsarga mata,kafin daga bisani ta soma bin bayansa,tana qiyasta irin kalmomin da zatayi amfani dasu wajen ganin tasha kansa. Suna isa tsakar falon idanuwanta na sake sauka ga hotunan shaheeda,yadda ta tsani mutuwarta haka ta tsani bude idanu taga wadan nan hotunan,asalima tana kishinsu fiye da yadda take jin kishin maimunatu,tunda a yanzun maimunatu bata tsare mata komai ba,bata ma.kallonta a matsayin matsala gareta,saidai tana jin haushin amsa sunan matar mijinta da tayi,harara ta jefi hoton dashi,wanda ja'afar dake qoqarin ganin ya saurareta idanunsa suka shaida masa hakan,wani abu me kama da mamaki ya saukar masa "Harara?,for what?" Maida idanunsa yayi ga sassan da hoton shaheeda ke maqale,dai dai sanda ya dauke dubansa zuwa ga unaisa,itama dai dai sannan ya dauke idanunta zuwa kansa,sai suka hada idanu,kamar an zare wani abu daga zuciyarta taji,bataso ya ganta ba,amma ita ba wannan ne damuwarta ba,damuwarta ta fidda wadda ke cikin hoton daga zuciyarsa gaba daya,kamar yadda ta five a filin duniya,ita kuma ta maye gurbinta "Uhmm.....go on" takowa ta soma yi tana sake nufoshi,ta dora dukkan wani yanayi da zai baka tausayi a kan fuskarta,saidai tana zuwa gab dashi ya sake dakatar da ita "Don't do it" ya fada calmly gami da yi mata nuni da hannu kan yana saurarenta,bata da wani zabi illa fashewa da kuka harda sheshsheqa,abinda ya bashi mamaki ganin cewa shi din bai aikata mata komai ba,fuska ya hade sosai yana dubanta,sai kuma ya kau da kai yana jan tsaki can qasan ransa "Bansan meye laifi na,ban kuma san me na aikata maka ba,don kawai nace ina sonka ja'afar?,ta yaya da hakkina a kanka tsahon shekara kusan guda ka takemin kamar bakasan da wannan ba" "Anzo wajen" ya fada a ransa yana jin tana sake ficewa daga ransa,ta yaya yarinya mai cikakkiyar kunya da nutsuwa zata iya duban idanun da namiji.....duk da kasancewarsa mijinta,amma a matsayin budurwa ta gaya masa hakan?,well.....batayi laifi ba,tunda hakkinta ne kamar yadda ta fada din,amma bayajin koda danneshi akayi zai iya aikatawa,hes not in the mood gaba daya,bayajin wani feelings a yanzu a kanta ko dis. Kujerar dake daura dashi ya qarasa ya zauna a hannun kujerar,yaci gaba da dubanta hankali kwance sanda taketa kukanta tana sake qara ma kukan salo a fatan da take na samun nasara a kansa,can qasan zuciyarsa yake qissima ta yadda zai raba kansa da wannan matsalar.....eh.....matsala mana,zuwa yanzun yana jin unaisan ta zame masa matsala,babu abinda take haifar masa banda kwasarwa kansa zunubi,bayan yana da tabbacin abune mai wahala ya iya karbarta cikin rayuwarsa,zuciyarsa wata irin zuciya ce mai wahalar sha'ani "I already told you,zamanmu abu ne mai wahala da ban hango yiwuwarsa,ni am ready to dismissed you,the choice is yours.....karki sake tara ta da irin wannan shirmen" daga haka ya miqe ya nufi bedroom dinsa,ta yunqura zata bishi,saidai ko kafin ta isa ya maida qofansa ya rufe,ta daga hannu kamar zatayi knocking sai ta sauke,ta fahimci wasu daga cikin halaye da kuma dabi'unsa,idan ta sake tayi knocking masa qofa,batasan me zai biyo baya ba,sai ta juya da gudu gudu tana sauka daga stairs din kuka yana kufce mata,ta gaji gaskiya,ta kuma kai maqura,tana jin ta iso geji,batason kuma ta bata dukkan wani tanadi da tayi masa,zata dauki mataki na gaba itama da takeji har cikin ranta da zuciyarta shine dai dai. °°°°°°°Ta tabbatar idan har ta zauna a wajen baba tabawa babu abinda zai hanata cewa taje takai masa abincin dare,wannan shine worst abu da zata sanyata,bata jin zata iya hada idanu ko muhalli dashi,gaba daya ya ajema ranta da zuciyarta wani abu,wani irin nauyi da kwarjininsa daya qaru cikin idanunta,gefe guda wani abu me kama da haushinsa da take ji,gaba daya halayyarsa batayi mata ba,hisham ya fishi sauqin kai kirki fara'a da iya mu'amala da mutane,komai nasa cikin tsumewa da tsare gida?. Leqawa kawai tayi ta duba baba tabawan don tasan ta tashi kuma lafiya take,don ko ita tayi mamakin jimawar da tayi tana bacci "Zan koma na kwanta baba,jikins yau banajin qwarinsa" "Ashsha.....amma dai ba ciwon bane ko?,yana shirin dawowa ina shirin tattara komatsaina na koma inda nafi wayo?" Dubanta da kyau maimunatu tayi,gabanta ya fadi,sai taji an cire dukka sauran walwala daga zuciyarta,komawa tayi ta zauna a maimakon tashi da tayi dazun "Tafiya kuma baba?" Kai ta gyada "Eh,ai gwara na koma gida hakanan,tunda naga jikin naki ai yayi kyau,banda tsautsayin da ya faru yau ma ai da yau din a gida zan kwana" gaba daya jikinta ya gama mutuwa,batason tafiyar baban,saboda tasan ba komai bane zai faru sai zaman kadaici kara dadi,wanda a yanzun ta fara sabawa da rayuwa da mutane,daya daga cikin dalilan da ya sanya ko hutun makaranta bata fiya son ayi ba,banda tanason tazo taga anni wasu lokutan. "Don Allah baba ki bari sai zuwa wani lokaci,ko kuma idan zan koma hutu,saura kwana ashirin gaba daya mu koma" kai ta girgiza "Banda abinki maimunatu ta yaya zan zo cikin yara gotai gotai dani na zauna banda ma lalura ta rashin lafiyar?,ai gwara na tafi,kema kyafi sakewa kiyi bautar aurenki yadda ya kamata" daga qarshe ta shagwuba mata magana,wadda ta sanya bata sake cewa komai ba,sai tayi qas da kanta. Bata sani ba ko kewar baban ta fara, yadda ta tsara guduwa daki batayi hakan ba,sai ta zauna suna fira sama sama,yayin da baban tayi amfani da wannan damar tana sake jan hankalin maimuntu a fakaice akan rayuwar auren nata. Washegari gaba daya bata fito a daki da wuri ba,tana qiyasta lokacin da zai shigo gaida baba tabawa,ta kuwa qiyasta dai dai,don kuwa ya shigo gaida ita din,saidai a gurguje,don yana sauri zashi gida karbar kudin auren salma hafsa da kuma nadiya,harma da laila,sosai baba tabawa taji dadin labarin,bayan kuma maimunatu ta fito ta shaida mata. Tun a waya ta kira laila tayi mata murna,saboda tasan yadda take son auren,don babu wanda ya zaci ma za'a karba harda nata,ta kuma dan tsokaneta,baba tabawa na zaune tana jinsu tana dariya,ko bayan ta gama wayar ma hirar familyn dr marwan din suka shiga,wanda duka baba tabawan ce ke bata labarin yawan zuri'ar khalidu akko,da kuma karamcin mutan gidan dr marwan din,wanda ita kanta maimunatu shaida ce,bata taba zaton a duniya akwai mutane irinsu ba,sun samu dukkan wata dama ta rayuwa,amma hakan baisanya sun wulaqanta kowa ba,ko kuma sun dauki kansu a wani abu ba. ***********Washegari tun safe maimunatu tana dakin baba tabawa,gaba daya yau din ranta babu dadi,tare sukayi abincin safe,baba tabawan ta dora na dare da wuri,saboda da yamma sukayi da driver zaizo ya dauketa,ko mai maimunatun takeyi cikin kasala da rashin dadin rai takeyinsa,tana jin inama ace zata iya hana baban tafiya,inama zata yarda suyi zamansu tare,saidai tasan hakan ba mai yiwuwa bane. Suna gama girkin ta wuce dakinta,tayi wanka,sannan ta shirya cikin wata chiffon gown da aka fidda mata desin me kyau,ta bude sosai daga qasa,ta gyara kanta,ssnnan tayi rolling vail din da tazo dashi shima na plain chiffon mara ado a jiki,jikinta na fidda sassanyan qamshin turaren burberry london,bata saka komai a fuskarta banda powder da lip balm,saidai fuskar tata koda yaushe fresh take,saboda hutu data samu sosai,uwa uba fatarta me kyau ce,babu wani qurji ko pimples ko daya,yan makarantarsu da yawa suna zaton tana shafa wani.mai ne na musamman,saidai ko kadan,haka fatarta yake naturally,ta dauki wayarta,ta sake fitowa wajen baban. Zuwa la'asar din baba tabawan ta kammala komai,ta kuma dauko jakarta zuwa falon maimunatun,yayin da take biye da baban dauke da wata leda data cika mata ita da kayayyakin da tasan zataji dadinsu,fuskarta gaba daya a narke take,tana riqe da ledar har zuwa sanda suka fito babban falon gidan,sai baba tabawan taja ta tsaya "Af....niko nace bai kamata na tafi bamu gaisa da abokiyar zamanki ba,tunda nazo banga fuskarta ba" "Gaskiya kam" maiminatu ta fada tana dan kallon sassan nata,bata manta when last data shiga sassan nata ba,tun daga ranar itama bata sake sanyata a idanunta ba,sau daya tak dai ta hangota a parking lot na gidan zata fita cikin motarta,saita amsa jakar baba tabawa ta riqe mata,don batajin xata iya shiga sassan matar. Ko minti uku cikakke baba tabawa batayi ba ta fito,fuskarta babu yabo babu fallasa,bata dai ce da maimunatu komai ba suka wuce inda mota take jiranta. Maimunatu bata bar gaban motar ba sai da taga fitarsu daga gidan,ta sauke ajiyar zuciya tana jin jiki da zuciyarta babu dadi,ta juyo a hankali ta soma takawa zuwa cikin gidan,tana wassafa zaman kadaicin da zatayi na kwanaki ashirin,har zuwa sanda zata koma makaranta. Tun kafin maimunatun ta qaraso ita ta ganta,ta zuba mata idanu sosai tana kallonta, yadda ta fahimci ita bata ganta ba ya bata damar kallonta yadda taso,suna sake kusantar juna wata irin fargaba ba ratsa zuciyar unaisan,wanne irin kyau da canzawa yarinyar takeyi?,ba haka tasan fuska da jikinta ba,lokaci guda taga kamanninta na juyewa,tana tashi daga maimunatu 'yar ruga zuwa wata balarabiya daga yankin qasashen larabawa,brown mayafin data yane kanta dashi ya sake taimakawa wajen fidda haske da kuma kyanta,wani dunqulallen abu me tauri ya daki zuciyar unaisa,tayi qoqari qwarai wajen ganin ta dauke idanunta sanda suke gab da juna,ko don gudun kada maimunatun ta ganta amma kuma ta kasa,matsowar nata kusa da itanne ma ya sake haifar mata da wani ciwon a zuciya,kyanta ya sake fitowa fes ga idanunta,lallausan qamshi me aji dake fita daga jikinta,sai taja wani tsaki mai qarfi sanda taga yarinyar ta wuceta ba tare data ko nuna ta ganeta ba bare tayi yunqurin gaidata. Wani abu ne yazo ya tsaya mata a wuya,me yarinyar ke nufi?,tana nufin wuyanta yayi kauri kenan?,ko tana nufin zata goga da ita ne?,zata amsa sunan kishiyarta?,anya kuwa babu wani abu daya taba ratsa gsakaninta da ja'afar wanda ya sanya faduwar darajarta a idanun yarinyar da har zata iya gotawa bata gaidata yadda ta saba ba?,idanunta ta kulle da qarfi tana girgiza kai,bata fatan ya santa kafin yasan yarinyar,wannan shine abu mafi muni a gareta,indai hakan ta kasance ta tabbatar akwai gagarumar matsala,dole ta samawa kanta mafita da kuma 'yanci,don haka sanda ta bude lafiyayyar motar tata ta shiga,sai ta zaro wayarta tahau kira,a maimakon ta kunnata ta fice kamar yadda tayi niyya da farko. 50 Itako maimunatu ko daya ta manta da sha'anin unaisa,tunda ta wuceta ta isa sashenta,sai ta kulle falonta abinta,da farko ta rasa me zatayi,don babu wani aiki da zai debe mata kewa,daga bisani ta tashi ta debo litattafanta na makaranta ta soma dubawa,don tunda ta dawo rashin lafiyar da tayin bata barta wannan karon tayi karatun kirki ba. Bata bar kan litattafan ba sai da aka kira sallar magrib,bayan tayi sallar ta kuma ci abinci sai ta jawo wayarta tahau watsapp,shaf tama manta dashi,kasancewar bata wani saba ba,ya kuwa debe mata kewa sosai,don bata sauka ba sai da aka kira isha'i,tayi isha'in,ta kashe dukka wutar dake falo ta wuce dakinta,kayan bacci ta canza,ta haye gado,sannan ta duba last episode data tsaya a drama dinta ta kunna abarta ta dora daga inda ta tsaya. Karfe tara harda mintuna ya shigo gidan,ya jima sosai yau a office fiye da yadda ya saba,duk da cewa dama lokaci irin wannan da suke soma shirye shiryen lissafin shekara da kuma tafiya hutun qarshen shekarar yana dan samu jimawa a office din fiye da ko yaushe. Daga yanda yake takowa kadai zakasan ya gaji tubus,ya tura qofar falon ya shige kansa tsaye,don yasan babu wanda zai samu a falon,sannan ya soma haura samansa kai tsaye,yadan dubi sashen da qofar falon sassanta yake,yadan sasssuta saurinsa kadan kamar xai tsaya,sai kuma yaci gaba da tafiyarsa zuwa saman da dan sasssarfa. Fridge ya fara isa ya ciro ruwa mai madaidaicin sanyi,sannan ya dawo saman daya daga cikin qawatttun turkish chairs din da suka qawata falon ya zauna,ya bude murfin gorar ruwan ya kafa bakinsa,yanajin yadda sanyinsa da baiyi yawa ba yana ratsa hanjinsa,rabi kawai yasha ya dire robar,ya sunkuya yana sabule takalmi da socks na qafarshi hadi da janyesu gefe,sannan ya miqe yana dauke briefcase dinsa,daya hannun nasa kuma yana sassauta tie din wuyansa,don burinsa shine kawai yayi wanka a yanzun,ko qafafunsa da hannayensa da suka sage zasu samu sassuci "Oh shit" ya furta a hankali sanda wayarsa ta dauki daddadan sautin ringtone,ya murda handle na bedroom din nasa ya tura ya shiga gefe guda kuma yana qoqarin ciro wayar ya duba me kiran. "Anni kuma?" Ya fada da dan mamaki a ransa,don yasan ko dazun sai daya biya ta gida,jakar ya wulla saman gado ya soma rage suit din jikinsa,sannan ya danna alamar kore na amsa kira,ya kuma dora wayar saman qawataccen dressing dinsa ya sanyata a hands free. A kasalance yayi mata sallama,saidai yanayin yadda ta amsa sallamar yaja hankalinsa,har ya maida dubansa ga madubi yana kallon kansa da kansa,tare da jiran jin abinda zata fada "Kana jina jafaru?" Ta fadi a kausashe kuma kanta tsaye,idanunsa ya lumshe ya kuma bude duk a kusan lokaci daya sannan yace "Ummm" "Idan kaga ma ba zaka amsa ba duk bazanyi mamaki ba,tunda dai xuwa yanxu wuyanka ya isa yanka,sannan kayi sama da haka ma......inason a gobe kafin ka wuce wajen neman kudin daka maidashi ibada sama da komai,ka tattaromin kan matanka ka kawomin su dakai kanka,dukkanku inason ganinku" qit ta kashe wayarta,sai ya aza idanunsa akan wayar tasa ba tare da yace komai ba,kwanyarsa na masa bita yanayin sautin muryar anni da kuma abinda tace masa goben yayi "Matansa?, what's happening?" Ya yiwa kansa tambayar da bashi da amsarta,sai kawai ya zabi jefa damuwar samun amsar tambayar a bayan damuwoyinsa,ya dage kafafa in i don't care manner,yaci gaba da zare kayan jikinsa ya kuma wuce toilet ya hada ruwa me zafi yayi wanka,wannan kusan dabi'arsa ce,ba kowa ne zai iya wanka da ruwan da yake wanka dashi ba saboda yayi zafi da yawa. Daya fito yana sharce sassalkar sumarsa dake jiqe da ruwa,qugunsa daure da towel wanda ya bayyana dukka wata kyakkyawar qira ta jikinsa,gefe guda maganar anni na dawo masa,sai ya janyo wayarsa a hankali sanda ya tuna voice note din da amna tace tayi masa ta wayar khadim,ya lalubo number dinsa ya shiga,ya kunna na farko yana samun waje ya zauna yana ci gaba da goge jikinsa. A hankali tsadadden murmushin nan nasa ke fita a fuskarsa,abune me mugun wahala ka ganshi ga fuskarsa,duk da yadda yake qara masa mugun kyau,sai daya gama ji tsaf sannan ya jawo wayar yana kasheta,can qasan ransa yace "You deserve my time amne na,i promise you,i will make you happy ending month in sha Allah". Sai daya gama shiryawa sannan ya tuna bashi da abinda zaici,ya sani yau baba tabawa ta koma gida,it means zaici gaba da bulayin neman abinci?,anya ba cook zai dauko ba kuwa ya aje cikin gidan?,sam ba girmansa bane a dinga ganinsa a eatery da sunan siyan abinci,bayan yana da komai,Allah ya mishi komai,yana da arziqin da idan abincin wata qasar yakeso yaci kullum to fa zai sameshi,sai ya miqe yana fita zuwa ga fridge din falonsa ko zai zamu wani abu da zai iya ci,gefe daya yana tunanin yadda zai gaya musu su shirya goben zasu wajen annin. **********Karfe goma na safiyar washegari,wata safiya da aka tashi da haduwar gajimare wanda me dan duhu,cikin abubuwan dake alamta fara saukar damuna kowanne lokaci daga yanzu. Tsaye a gaban daya daga cikin motocin dake fake a harabar gidan yake,sanye da wata shadda sky blue me matuqar kyau da daukan hankali,anyi mata dinkin zamani wanda ya dace da yanayin qirar jikinsa,ya kuma tafi da structure na jikinsa a matsayin cikakken namiji da ya amsa sunansa,mai haiba cikar kamala da kuma zati. Qarasowarsa wajen kenan,cikin hanxari drivernsa ya fito yana karbar jakar hannunsa,gami da qoqarin bude masa seat din baya kamar yadda suka saba duk sanda xasu fita. Hannu ya daga masa ya qarasa cikin coolness dinsa ya sanya hannu zaya bude gidan gaba,a dai dai lokacin ta qaraso cikin shigar wata irin gown da aka mata wani dinki,kanta yane da qaramin mayafi,yayin da fuskarta ke dauke da wani makeken sun glasses da yayi shigen kala da kayan jikinta,wani babban bangul ne a hannunta ke zobe guda daya,sai hig hill shoes data sanya a qafarta,mahadin figigiyar hand bag dinta,ta fito a unaisarta sak,unaisar shekarun baya,diyar gidan minister,shigarta gaba daya batayi kama da shigar wadda zata gidan surukanta ba,ga mutumin da ya fara ganinta yanzu,zaiyi zaton wani taro daya shafi siyasa ko kuma jiga jigan 'yan boko zata je. "Good morning" ta fada cikin salo,idanuwanta na kan ja'afar,wanda tuni ya bude gaban motar yana yunqurin shigewa "Morning" ya amsa mata a taqaice,sannan ya zura jikinsa a hankali kafin ya dauke qafafunsa dake saye cikin wani lafiyayyen half cover shoe na kamfanin louise vuitton,hannunsa dake daure da wani lafiyayyen gogon kamfanin Blancpain ya zura da niyyar rufe murfin motar,unaisa tabi hannun da kallo bayan ta gama qarewa takalminsa kallo,take ta sake sallamawa,da gasken gaske dan gayu ne shi din na qarshe,wanda yasan sirrin kwalliya tare da ta'ammali da designers kayayyaki,bata sake cewa komai ba itama,saiya bude back seat amma ta saitinsa ta shige,tana dora idanuwanta kan fuskarta da take iya hange ta madubin gaba,wanda tuni ya bude news paper ta safiyar ranar da drivern sa ya miqo masa,yawanci dukka safiya yakan dudduba jaridan data fito a safiyar,musamman page din da suke wallafa al'amuran da suka shafi kasuwanci. Tana so ta tambayi wanda suke jira amma wani irin kwarjininsa daya cika motar ya hanata cewa komai,sai ta fidda wayarta ta bude watsapp dinta,ta hau turawa anty talatu saqo,abinda ya dan janye hankalinta kenan,saboda maganar da suke da anty talatun nada matuqar muhimmanci. Karo na uku kenan ya daga kansa yana duban hanya da niyyar idan bata fito ba zasu wuce kawai,ta biyosu daga baya,har yadan fafa hasala,saidai bai nuna ba kamar yadda ko sau daya baiyi qorafi ba,kasancewarsa mutum ba mai yawan magana ba,saidai a cikin sa'a ya hangeta tana tahowa. Glass din fuskarsa da yakanyi amfani dashi lokaci lokaci ya zare a hankali tare da qoqarin kau da idanunsa daga sashen da take tahowan,bawai don yana tunanin tana ganinsa ba,a'ah......daya daga cikin dressing na shaheeda tayi,dressing din da kusan zai iya cewa ita daya ce macen da yasan tana yinsa,kuma har yau shi dai bai sake ganin wata da irin shigar ba sai ita....bai sani ba,ko don idanun gaske dana zucin ma gaba daya tare da hankalinsa kacokam basa tare da kowacce mace?. Shigar lafaya tayi blue black me adon gold a jiki,ko ba'a fadi ba kalar tana daya daga cikin kalolin dake haska farar fata ainun,rashin sabo da yanayin shigar ya sanyata take jin kamar zata harde,wannan ya sabbaba mata taku cikin nutsuwa da takatsantsan,abinda ya zame mata kamar ado,kamar wadda ke yin tafiyar da gayya da kuma wata manufa ta daban. Dukka cikin sakannin da basu haura goma ba ya gama kallonta kafin ya zare idanunsa ya maida kan news paper din nasa,dai dai lokacin da ita kuma unaisa ta daga kanta da xummar gyara zamanta,idanuwanta sukayi kyakkyawan ganin da ya sanya tunaninta qwacewa na wasu daqiqu "Damn it" ta fada can qasa,tana jin wani abu me qarfi yana fusgarta,kishinta ya soma huda zuciyarta yana ratsata da gasken gaske,bata iya dauke idanuwanta ba,har zuwa sanda ta iso dab da motar. Batasan waye da waye a ciki ba,don haka tadanyi knocking kadan,drivern ya motsa da niyyar fita ya bude mata kamar yadda ya yiwa unaisa,sai ya cira kansa a hankali daga cikin news paper din "Ummm ummm", ya fadi a taqaice,sai ya waiwayo ya kalleshi,yayi masa alama da ya zauna,a ladance ya amsa masa,ya ajjiye news paper din,sannan ya kama handle na motar ya bude,ya zuro qafarsa waje guda daya. Kusan a tare suka hada idanu ita dashi,dukkansu cikin gaggawa kowa ya killace ganinsa,cikin dakakkiyar muryarsa ya magantu "Bana iya zaman jiran kowa....wannan ya zama shine lokaci na qarshe da zaki aikata hakan" ya qarashe fada da muryar warning gamida da kausasa maganar tasa. Sauka idanuwanta sukayi kan unaisa,wadda tadan rage glass din xuwa qasa kadan saboda ta samu damar jin a inda zasu fada,ita unaisar ke kallo,sai da suka hada idanu kuma sai ta tabe baki ta kuma janye idanun nata daga kansu ta mayar ga wayarta,a hankali maimunayu ta dauke idanunta daga wajen itama,tana jin yadda idanun nata suka cika da qwalla,cikin muryar nan tata dake cike da rauni....wadda ga wanda bai snata ba zai kira hakan da zallar shagwaba tace "Kayi haquri" lafazin suka fita da sanyi da kuma zaqun muryarta,bashi ba,hatta da unaisa sai da salon da tayi maganar yaja hankalinta,ta sake maida idanunta kanta ba tare data shirya ba,tana jin kamar ta samu abu ta boye maimunatun,idanu su daina kaiwa zuwa gareta. Sai daya lumshe idanunsa kana ya bude duka kusan lokaci guda,ya sake zube dubansa akan fuskarta,yana kallon yadda idaninta keta qyalli saboda ruwan hawauen da sukayi guzuri,yana mamakin saurin kukanta....me yasa ita din bata da tsayayyar zuciya,saurin bada haquri saurin kuka da kuma shagwaba kamar wata yayayya. Qaramin tsakin da ita daya ta iya jinsa yaja yana maida jikinsa cikin motar "Shiga mu tafi" ya fadi s gajarce,sai tasa hannu ta buda murfin motar ta kuma shiga bakinta dauke da sallama,driver ya amsa,yayin da da bakin J din yadan motss kadan alamun amsawa,ta fannin unaisa kowa ko uffan bata ce,can qasan ranta a mugun quntace. Kaf maganganunta na jiya bata ga inda ta sanyo maimunatun a ciki ba,don me xa'a tafi da ita,ta maslahar aurenta ita daya kawai takeyi,bata qaunar ganin kowacce mace ta giftawa wannan buri da muradin nata. Sosai qamshinta ya cika motar,har yaso yayi gogayya da nashi turaren,ya rufe news paper din a hankali ya ninketa gida biyu yana jan numfashi sosai wanda ya cika da qamshin nata,yana fesarwa kiran anni na shigowa wayarsa,ya dubi fuskan wayan bayan yayi kamar bazai dauka ba "Am on my way" ya fada a taqaice,ya zame wayar daga kunnensa ya maidata inda ya dauko ya ajjiye,gefe daya na zuciyarsa yana cike da mamakin kiran meye haka anni ke masa da har ta qagu su iso,tabe bakinsa yayi,baisan da wacce rigimar zata zo masa yau ba,don bata rabo da rikici,amma koma dai meye...... he's ready akan duk wata rigima da takeji da ita,don yayi mata iya abinda zai iya,duk da ransa da zuciyarsa basa so. 51 Shuru ne ya biyo baya cikin motar,tsakanin unaisa da maimunatu babu wanda ya cewa da dan uwansa uffan,sai ogan daketa amsa waya cikin wani yare da dukkansu basu gane wanne ba,daga bisani unaisa ta fahimci turkish language ne. Girman kai da shegen son girma yasa unaisa taji zafin yadda maimunatu ta shareta,a ganinta maimunatun bata isa tayi mata haka ba,yarinyar gaba daya nawa take?,sa'annan kuma wace da ita?,banda martabar aure da ja'afar din daya hadasu qarqashin inuwa guda,bata jin maimunatu takai koda matsayin 'yar aikinta ma bare zaman kishi,amma zata nuna mata ita din ba komai bace,sannu sannu bata hana zuwa ai,muddin ta samu ja'afar a hannunta sai ta gane shayi ruwa ne. Itakam maimunatu gaba daya hankalinta na kan wayarta,chart suke da afrah tana bata labarin ahmad dinta,a zahiri gwasale afran take,amma a badini yadda salon soyayyar tasu take shine yake burgeta,abinda ya sanya murmushi kenan saman fuskarta lokaci lokaci,har bata maida hankali ga unaisa dake gefe tana ji da girmanta ba,bare ja'afar dake amsa waya cikin yaren da batasan wanne bane,saidai lokaci bayan lokaci idan yayi wata maganar lallausar muryarsa na ratsawa cikin hankalinta da yayi nisa a wajen jin labarin da afra ke bata. Karamin tsaki unaisa taja,har cikin ruhi da zuciyarta tana sake jin zafin shariyar maimunatu,gefe guda kuma yadda yarinyar ta canza ya tsaye mata a rai,ta lura idan ta tsaya wasa sai wankin hula ya kaita dare,dole tayi amfani da dukka wayewarta da kuma iliminta da kuma gogewarta tayi abinda take ganin shi ya kamata. Qaramar ajiyar zuciya ta sauke sanda motarsu ta tsaya a babbar mashigar gidan dr marwan,drivernsu ya saki horn me gadi ya taso ya bude musu,cikin girmamawa yaja da baya kana ya rusuna musu har xuwa sanda motar ta qarasa shigewa yaja gate din ya kulle. Tun kafin motar ta tsaya suka hangi abbi shi da ammi,tana riqe da briefcase dinsa da alama rakiya tayo.masa zaya fita,wannan kusan dabi'ar dukka matan gidance,girma ko shekaru basu sanya sun canza ba,abbi din yana riqe da hannun amna,wadda tayi kyau cikin dinkin atamfa straight gown,kanta babu dankwali saidai a taje yake cikin band da aka matse mata yalwataccen gashinta dashi,ta noqe kanta a kafada,da alama rigima take tabawa. Dukka hankalinsa nakan yarinyar tasa,don haka yayi sallama da wanda suke magana a wayar ya kashe yana sanya wayar cikin aljihun rigarsa,dai dai sanda motar ta tsaya ya bude yana fitowa kamar yadda suma su maimunatu suka fito,dukka suka dunguma zuwa inda abbi da ammi suke tsaye,wanda hankulansu yayi wajen motar tun tsaiwarsu. Idanu amna ta fiddo sanda ta hangi daddynta ta kuma hangi anty maimoon,da sauri ta zame hannunta ta manta da rigimar ma da take wa abbi ta nufesu da matuqar sauri,saidai tana isa dab dasu ta yanke ta nufi maimunatu wadda ta bude mata dukkan hannayenta fuskarta fadade da wata lallausar fara'a da murnar ganin yarinyar,ta dauketa cak suna dariya su duka "To alhamdulillahi,shikenan rigima ta qare,an fansheni" abbi ya fada sanda suke sake qarasowa wajensa,ammi da maimunatu suka saki murmushi,banda ja'afar da ya dauke kansa daga kansu,karon farko da amna ta taba ganinsa ta wuceshi,koda waye ta gani kuwa shine mutum na farko da take fara zuwa wajensa kafin kowa,sai kuma unaisa da wani haushi ya saukar mata,wanda ya bayyana har saman fuskarta,ta kuma kasa danneshi. Maimunatun ce ta fara isa gabansu,ta zube tana gaidasu,cikin nuna kulawa suka amsa,tadan miqe dauke da amna a hankali sanda ja'afar ya iso shima ya sunkuya yana gaidasu,bata tsaya jiransu ba tayi gaba abinta da amnan zuwa sashen amma,amna nata zuba mata zance yadda ta saba,ita kuma tana biye mata suna dariya,har suka isa sassan amma. A falo suka gaisa da masu aikin amma cikin mutuntawa,suka shaida mata tana wanka,amma dab take da fitowa,sai ta zauna saman carfet tana dakon fitowarta. Sallamar da akayi cikin falon ta sanyata daga kanta,hisham ne ya shigo,sanye da jallabiya, da alama yau din bashi da niyyar fita kenan,duk da ranar ranar aiki ce bawai weekend ba "Matar babban yaaya" ya fada cikin dan zolaya yana wucewa gaban freezer din amma dake falon ya bude yana duba abinda ya shigo dauka din "Barka da safiya" ta gaidashi cikin mutuntawa da kuma jin nauyi "Barka kadai yayarmu.....jiki yayi sauqi kenan?" "Alhmdlh ya hisham na warware" "Allah ya qara afuwa......rigima'u,yau kuma me aka tashi dashi?,wa kike juyewa rigimar safiyar alhamis din?" Yayi maganar yana duban amna dake zaune gefan maimunatu,saidai ta kanainayeta gaba daya,duka gwiwoyinta na kan cinyarta,kamar jira take ta miqe ta isa gareshi,da niyyar fita ya shigo,amma dole amnan ta tsaidashi ya samu waje ya zauna a nan,ya ballowa kansa ruwa kenan. Maimunatu na daga gefe tana murmushin jin yadda rigima ta barke tsakanin hisham din da amna,sauqin kansa da yadda ya iya tafi da rigimammun yara yana burgeta,gaba daya ya maida kansa shima kamar amnan,dai dai lokacin da ja'afar ya sako kansa zuwa falon. Akan fuskarta idanuwansa suka fara sauka,fuskar dake cike da fara'a,jerarrun fararen haqoranta da suka bayyana,da wata lobawa ta musamman dake tsakiyar habarta,hasken fatarta ya sake fitowa sosai ta tsakiyar fuskar hijabinta,tana gab da dago idanunta don amsa sallamarsa ya kauda kansa,ya maida dubansa ga amna,wannan karon sauri tayi ta sabule daga gefan hisham da take zaune,ta nufoshi da sauri tana wara hannuwanta "Dadddyy" tana isowa ya dauketa cak a hannunsa yana kallon fuskarta dake matuqar kamanceceniya da tasa,yasa yatsuntsa guda biyu yaja kumatunta,cikin low sound wanda ita daya zata jishi yace "Naqi wayon,babu wani daddy,tun dazu ba'ayi welcoming daddy ba sai yanxu?" Wuta ta langabe masa fuskarta a narke "Sorry....sorry dad" ba tare da ya shirya ba murmushin gefan baki ya kubce masa,yadda tayin sai ya tuna masa da maimunatu dake zaune a gefe,kamar ita,koda yaushe aka kamata ko ake tuhumarta da laifi ko aka ritsata haka fuskarta yake komawa,yayi kaman zai kalleta sanda yaji hisham na magana da ita amma sai ya dauke kansa,saidai kunnensa na sauraren hirarsu,yana mamakin yadda take dan sakin jiki haka da hisham din. Yana qoqarin zama amma ta fito,maimunatu ta dubeta cikin girmamawa tana mata sannu da fitowa,fes ds ita cikin atamfa super exclusive,kai baka ce itace ta haifa kamar ja'afar ba saboda tsabar gayu da gyara. Waje ta samu ta zauna lokacin hisham ya kama hanyan ficewa "Me yasa ne baka tafi ba hisham?" Amma ta jefa masa tambayar tana zama,fuska yadan yatsina yana satar kallon ja'afar,suka hada idanu kuwa,ja'afar din ya watsa masa harara,sai yadan saki dariya hisham din,kafin ma yace komai amma tace "Kada ka daka ta tashi,dama ka sani ba zuwa yake ba,tun can baya ma sai na matsa sosai yake zuwa,yanzun ma ya daina gaba daya" gyara tsaiwarsa yayi "Taron family dinne anni..... sometimes kawai gulma ne da kuma daukan bangaranci,ga yarinyar can fawwaza.....ta cika naci wlh,idan ma naje ba barina zatayi na sake ba" ya qarasa maganar yana sanya kansa wajen,dauke dubanta amma tayi daga kansa tana cewa "Allah ya kyauta" sannan ta maida kallonta ga ja'afar "Ya kamata ku dinga daurewa kuna zuwa koda ba zama zakuyi ba,ba zai yiwu ace ko da yaushe saidai matan suje ba,nima banda yau na tashi banajin dadin jikina ai babu abinda zai hanani zuwa" "Me ya sameki amma?" Ja'afar din ya fada da sauri cikin nuna tsantsar kulawa,tafin hannunta ta murza kadan "Ba wani abu serious bane,kawai nauyi naji jikina yayimin" motsawa yayi yana miqewa "Noo,bai kamata ace kin zauna ba bakiyi checking me yake faruwa ba,dauko mayafi amma muje a dubaki" qaramin murmushi ta sauke,ta jima da sanin irin soyayya da kulawa da ja'afar ke mata ta dabance ko cikin yaranta,shi yasa komai nasa itama ya fita daban cikin zuciyarta,duk da tana qoqarin dannewa "Ba komai fa,jiki ne da jini,dama ba za'a yita zama haka ba ba'a taba lafiyarka ba,yanzu ba gani a zaune ba muna magana" duk yadda yaso suje amma tace masa aah,dole ya haqura ya zauna,saidai dukka hankalinsa yana kanta "Ina fatan kuna lafiya" amma ta fada,tambaya ce guda daya,amma tana dauke da ma'anoni,kara ya hanata buda tambayar,kai maimunatu ta gyada kanta a qasa cike da kunya da kuma surukuta,yadan saci kallonta,yadda takeyi din kamar yadda shaheeda kema amman,can qasan ransa yaja tsaki,me yasa yake yawan kwatanta da shaheeda bayan ba ita bace?,sai ya miqe yana fadin "Zan shiga wajen anni" "To ba laifi,ki shiga ku gaisa maimunatu" ta fadi don tasan yawanci direct nan suke fara yowa sai sun gaisa suke wucewa sassan annin. A hankali suke takawa zuwa sassan annin,yana gaba tana biye dashi a baya,tamkar wata maras gaskiya,jifa jifa take satar kallonshi,yadda yake takawa majestically,cikin aji da izza,ba zato taga ya ja birki ya kuma waiwayo,ta daga idanunta a hankali tana duban inda yake tsaye ba tare data iya kallon qwayar idanunsa kai tsaye ba,nuni yayi mata da hannu kan ta wuce gaba,sai ta tako a hankali tazo ta giftashi,ta wuce kamar yadda ya buqata,lumshe idanunsa yayi sanda iska ta kwaso masa qamshinta,wannan qamshin dake maqale a wani bangare na kwanyarsa tun a wancan lokacin,sai ya rufa mata baya,suna ci gaba da takawa daya bayan daya. Yaso yima idanunsa shamaki amma hakan bai samu ba,qwayar idanunsa na biye da duk wani taku nata,ance ido guba ne,kuma dafi gareshi,koda bata waiwaya ba tasan kallonta ake,cikin jikinta takejin idanuwansa bisa kanta,abinda ya sanyata daburcewa gaba daya,ta kuma ji tana hardewa a tafiyar tata,saboda laushi da qafafuwanta sukayi,wannan ya taimaka wajen yin baya zata fadi lokacin da taci karo da wani dan qaramin dutse. Baisan ya isa gareta har ya tallafota ba saida ta samu masauki a jikinsa,qamshinta ya cika masa hanci,fuskarta na kallon sama ne,yayin dashi kuma ya zame mata kamar rumfa,wannan ya sanya idanuwansu sukayi saurin haduwa wajen guda,sai ya zareta daga jikinsa da sauri yana hade ransa tsaf,kamar bai taba dariya ba,ya miqe da dukka tsahonsa ya tsaya sosai yana sake zuba mata arwa,sai ta rasa abinda zatayi,don haka ta bige da gyara zaman hijabinta tana bashi baya,kamar zaice mata wani abu kuma sai ya fasa,ya zarce da yin gyaran murya saboda yadda yaji muryarsa ta maqale,duk wani furuci da zaiyi ya kakare masa a maqoshi "Thank you" ta fada tana daga qafarta zuwa next step,saidai wannan karon ta sanya idanuwanta ne a qasa,gudun maimaituwar faruwar abinda ya farun yanzun,tana shaqar iska me tsaho zuwa hunhunta wai ko zata rage kaifin qamshinsa daya cika mata hanci,wani irin scent dake haifar da wani yanayi me dadi a zuciya da gangar jiki,koda mutum baiso ba,ya kuma canzawa zuciya tsarin tunani,sai taci gaba da zuqar iskar tana fesarwa a hankali,qamshin yana sake yi mata yawo a hanci,yana kuma haduwa da iskar safiyar dake kadawa da wani irin yanayi dake nuna da gabatowar zafi. Muryarsa cikin sautin sallama ita ta maye gurbin tata siririyar muryar,mutum biyu ne suka amsa sallamar,anni da hajiya munubiya(mahaifiyar hafsat),ta ukunsu unaisa ce,wadda a maimakon amsa sallamar tasu,sai ta bisu da idanu sanda suke shigowan. Daga annin har haj munubiyan suma sai da duka bisu da kallo,saidai kowanne da irin kallon da yake musu,ta fannin anni wani farinciki ne ya tsarga mata,zallar dacewa ta hango mai yawa tsakaninsa da maimunatu,ganinsu tare kuma ya ninka kwadayinta nason daidaituwar al'amura a tsakaninsu,ya kuma sake saka mata kwadayin son dorewar alaqarsu,sannan kuma ta hangi wani haske a tattare dasu da take fatan tabbatarsa da kuma dorewarsa. Haj munubiya kuwa wani abu ne yayi mata tsaye a rai mai kama da kishi qyashi da hassada,tun shigowar unaisan ita kadai ta fara jin hakan,a yanzun kuma ya sake qaruwa da shigowar maimunatu da ja'afar din,yadda taga ya sake fresh ya kuma qara haske ya tabbatar msta da gaskiyan labaran da suke ji a kansa na yadda yaketa samun budi,arziqinsa kuma ke dada ninkuwa,wannan shine dai dai lokacin da ya kamata ace diyarta ta kasance daya daga cikin jerin matansa,saidai sam bata mata sha'awar zama mace ta uku kwata kwata,inda da hali so takeyi ta zama mace qwalli daua tilo ga ja'afar din,to amma hausawa sukance da babu gwanda babu dadi,ya kamata tayi wani abu akai,ta kuma gwada sa'arta,koda basu zama du uku ba ya kasance su biyu ne,wannan tunanin yasa ta sake fuskarta sosai tana gyara zamanta gami da dubansu maimunatu tare da sanya baki wajen musu marhaba,tana kuma qara kaifin hankalinta da hasashenta akan fuskar unaisa,take ta fara shinshino al'amura,ta kuma fara kuma tunanin daga inda zata dasa harsashinta.a 52 Fuskar anni kadaran kadaham sanda yake gaidata,duk da ba wani kallonta yayi can can ba,amma kuma jiki da zuciyarsa sun gaya masa lallai akwai wata a qasa,maida idanunsa yayi ga haj munubiya,matar da tun da can ba wani yi masa tayi ba,dama babu wani jituwa sosai a tsakaninsu,duk da ba wani abu bane yake shiga tsakaninsu ba,amma jininsu bai hadu ba. Tata gaisuwar mai guda daya ya miqa mata,ta amshe da sauri tana cewa "Lafiya qalau manya,ya ayyuka ya iyali?" "Alhamdulillah" ya amsa mata a taqaice idanunsa akan qafafun anni dmda aka shafawa magani,ta kuma miqesu,da alama ciwonsu ya motsa "To Allah ya taimaka,ya kuma dafa mana" bai maida hankali kan amsa addu'arta ta qarshe ba,cikin muryarsa me taushi da wani lokaci kan fito da wani amo da nauyi yace "Anni,har yanzun duka tarin magungunan da kike amfani dasu basa aiki?" Dan duban qafar tayi kafin ta maida dubanta gareshi "Abunne kasan dacewa ne,anata yi dai,sai sanda Allah ya dauke" "Bare ciwo,kasan idan ya hadu da girma sai haquri" haj munubiya ta tsoma musu baki,ba tare da yabi ta maganarta ba ya zaro wayarsa,ya budeta,yayi kiran waya sannan ya sanya ta a kunne. A hankali ya fara magana cikin yaren da maimunatu taji yana magana dazun,sai kuma yadan miqe a nutse yayi gaba dasu kadan can wajen dining din annin yana ci gaba da yin wayar,dai dai lokacin da khalid yayi sallama cikin falon. Kan maimunatu idanunsa suka fara sauka,zuciyarsa tadan motsa,ya dan kafeta da idanu yana qarasowa cikin falon,sanye da qananun kaya,ya cusa hannunsa guda daya a aljihun jeans dinsa,daya hannun kuma riqe da key din motarsa yana dan kadawa "Har ka dawo?" Haj munubiya ta fada,don ba haka taso ba,bataso dawowarsa a yanxun ba,saboda tana son fara aiwatar da shirinta,maganarta tasa ya dauke dubansa ga maimunatun zuwa kanta "Eh,naji kince sauri kike ko?" "Eh.....bawai wani sosai ba,dama abinda yasa nace kayi saurin kazo mu wuce,hafsat tacemin zata shiga makaranta,to kuma yanzun naga tex dinta ta fasa fitar,kuma na dan kwana biyu ai banzo gidan ba,ya kamata nadan zauna kadan mu gaisa sosai,don ko wajen yaaya marwan din ban shiga mun gaisa ba" anni dake sauraronta baki ta tabe tana kauda kanta gefe,a dan zuwan da take jifa jifa bata taba ganinta ta shiga sashen marwanun haka siddan ba,saida dalili,saboda haka kawai ta dorawa aishatu amma tsangwamar da babu dalili,face zallar faccalanci,amma yau abun mamaki wai ita ke zancan bata shiga sun gaisa ba,kafada ya daga yana maida kallonsa kan maimunatu kamar da ita suke maganar "Well.....shikenan,zan koma ni,driver ya maidake gida kenan?" "Eh zan kirashi,ko zuwa azahar ne sai na koma". "Ina kwana" maimunatun ta fada sanda ta fahimci sun gama maganar,fadada fuskarsa yayi da fara'a yana amsa mata tare da tambayarta gida da kuma karatu,sai tayi mamakin yadda akayi yasan tana makaranta,amma tadai amsa masa da "Alhamdulillah" dai dai sanda ja'afar ke saukowa yana shigowa cikin falon,idanunsa duka akan khalid din,tunda ya shigo yana karance dashi,yana ganin kuma kome dake wakana cikin falon,wani dan zafi yake ji a qirjinsa da baisan dalili ba. Waiwayowa khalid din yayi sanda yaji muryarsa yana fadin "I will call you back later" cikin wayar,sai ya tako a hankali yana miqa masa hannu cikin sakewar fuska,ja'afar na daya daga cikin mutanen da yake burin inama ace shine su,abubuwa da dama masa suna burgeshi,saidai girman kan da yake dashi yasa yake dannewa tare da hudubar haj munubiya dake nuna masa cewa gaba yake da ja'afar din a wajenta,kada ya sake ya nuna masa shine sama dashi. A daqile ya bashi hannun sukayi musabaha,haka kawai yakejin zafin har yanzun a cikin ransa,idanuwansa kuma ya kasa kaudasu tsakanin maimunatu dake zaune properly waje guda,bata ma san meke faruwa ba,don dukka idanunta ta tattarasu kan wayarta ne "Ba zaki sake amfani da kowanne irin magani ba,nayi magana da wani qwararren asibiti a turkey,zan qoqarin nema miki visa in sha Allah" ya fada muryarsa na dauke da wani irin amo kamar wanda yake fushi. Sak hajiya munubiya tayi,cikin ranta tana debowa ja'afar tsinuwa,dan rawar ganin da yaronta yakeyi take taqama dashi,iyayensa maza ke yabonsa yana kula da mahaifiyarsu shine wannan shegen yaron me kafirin izza da jin kai zai soke? "Amma.......naga a nan akwai likitan da nake turata abuja tana gani" khalid ya fada yana jin ba dadi cikin ranshi,kai tsaye ya kalla khalid din "I know......."ya bashi amsa,gyara tsaiwa khalid din yayi,yana jin shima namiji ne kamar ja'afar din,kuma yana da say akan annin kamar yadda shima yake ganin hakan "To inaga a barta zuwa wani lokaci mana" "Ciwon yaci gaba da cin jikinta har sai ta daina tafiya?,banga wani ci gaba ba" ya fada hakan bayan yaja dan qaramin tsaki. Idanu anni ta zuba masa tana karantarsa tare da son lalubo dalilin wannan fushin da kuma inda ya deboshi bayan ba haka ya shigo ba,dole ta tsoma baki,don kada ja'afar din ya sake fadin wani abu da bazaiwa munubiya dake zaune tana kallonsu dadi ba,batason kuma wani sabani ya dinga giftawa tsakanin jikokinta,bata jina da kashe case din khalid din da hisham ba,kada kuma wata sabuwa ta danno kai "Shi ciwo fitarsa aisai a hankali,kuma shima likitan inajin dadin maganinsa sosai,kwana biyu ne da naqi komawa lokacin da yace abun ya dawomin" bai sake cewa kowannensu komai ba,sabida ya riga daya qudurce a ransa abinda yayi niyya,bazai kuma fasa ba. Sallama khalid din yayi musu,sai haj munubiya ta miqe tabi bayansa,don tana son tace wani abu dashi,tanason kuma kafin taje ta dawo su gama abinda zasuyi itama ta dora nata "Bari na shiga mu gaisa" "To" anni ta bita dashi,don dama wajen takeson ta fita ta basu. Falon ya dauki saiti shuru ba wanda yace komi,cikin zuciyar unaisa fal haushi,ita ba wannan ya fiddota gida ba,so take kawai a fara maganar da data tarasun. Duban unaisa anni tayi,tana sane tace "Shiga kitchen unaisa ki hadowa mijinku abinci" don ta sani sarai bai karya ba,don ba sanin jiya ko yau ta yiwa ja'afar din ba,kai ya girgiza "Coffee kawai is okay" ya fadi a hankali yana rage kaifin idanunsa,har yanzun yana jin ransa yana suya. Haushi ya sake qume unaisa,itakam meye hadin zuwansu nan da shiga kitchen ne?,ita tsakaninta da coffee ai saidai tasha,batasan takan yadda zata hadashi ba,to amma ba yadda zatayi,sai ta ajjiye maqallaliyar jakarta ta miqe ta nufi inda anni ke nuna mata. "Bakwa bawa mijinku abinci ne maimunatu?" Anni ta jefa mata tambayar kai tsaye,sai maimunatun tadan rude, saboda bata tsammaci zuwan tambayar a sannan ba,ta daga kai ta kalli anni,sai kuma ta mayar ta sunkuyar ba tare da tace mata komai ba,ta yaya zata amsa mata?,tace mata batasan lokacin tashinsa da fitarsa ba?,ko kuwa tace batasan dawowarsa da lokacin buqatar abincinsa ba,ajiyar zuciya annin ta sake ta share maganar itama bata sake cewa komai ba. Bata jima ba ta dawo dauke da mug a hannunta,ta ajje masa a gabansa tana sauke numfashi,sannan ta koma inda ta tashi ta zauna tana baza kunne. Kurba daya yayi masa daci ya gauraye masa baki,sai ya maida ruwan coffee din cikin cup din yana duban unaisa da batasan ma me ake ba,saidai duka anni tana ankare dashi,ransa yaji ya quntata,ya dire cup din yana cewa "Baaba tabawa fa?" "Taje a lallabe mata kanta" bai wani san lallabewa ba,sai kawai ya lumshe idanunsa ba tare da yace komai ba "Ko a canza maka wani?" Ta tambayeshi,kai kawai ya kada idanuwansa na a lumshen,tunda unaisan ta kasa hada coffee yayi dadi ina ga maimunatun haihuwar shekaran jiya?,qilan ma har gwara na unaisa akan nata. "Ku bani hankulanku nan" anni ta fada tana saka seriousness cikin muryarta,dukka suka maida hankalinsun nasu a kanta,jaafar din shima ya bude nasa idanun ya zubesu akan annin "Maimunatu" ta kirayeta kai tsaye,gaban maimunatu ya fadi,ta amsa mata cikin sanyi "Akwai cutarwa a zamanki da ja'afar?,ko akwai wani abun qi da yake miki?" Tirqashi,girman tambayar da taji a tsakiyar kanta ya wuce yadda zata misalta,wannan shi ake kira da 'yar tinqe,me anni take son tace?,me takeson ji daga gareta? "Uhmmm,ina jinki" anni ta fada tana kafeta da idanu,kamar yadda ja'afar shima ya kafeta da nasa,mamaki da kuma son gano manufa ko kuma ma'anar tambayar na masa yawo a kwanyarsa. A hankali ta girgiza kanta,don itakam bata data cewa,to me take buqata daga gareshi?,bata taba rasa ci sha suttura ko magani ba,meye ya rage mata "Kin tabbatar?,banda ci sha da suttura komai ma kina samu?" Anni tayi tambayar cikin fillanci ba tare data bayyana komai ba,sai ta sake gyada kanta tana tabbatarwa anni. Dauke idanunta anni tayi daga kanta tana sake jin girma martaba da darajar maimunatu na ninkuwa a idanu da zuciyarta,ba zata iya fitowa kai tsaye ta fadi laifi ko aibun jikanta ba gaban idanunta,kunya kara da yakana suna tattare da jininta,tasan yadda komai ke wakana tun dawowar baba tabawa data matsa sai taji,tun kafin ma unaisa ta daga waya ta kawo mata qararsa "Kefa unaisa?" "Bani da matsalan wannan duka,saidai......" Shuru tayi tana dan jin nauyi ita kanta na fadin abinda ke ranta yake kuma damunta "Uhnnnn......fadi matsalarki,ai dama dalilin zaman namu kenan" "Ban taba kwana a dakinsa ba,shima kuma bai taba kwana a nawa ba" ta qarashe maganar tana baiwa kanta qwarin gwiwa da taimakon qarfafa mata gwiwa da anty talatu tayi kan ta fadi maganarta kanta tsaue,saboda indai aka dace aka shawo kansa to wannan abun shine hanya guda daya tilo da zata mallakeshi,kuma hanya mafi sauqi da zata ja masa zarenta yadda take so. Wani abu mai nauyi ne ya sauka saman kansa,sai ya rufe idanunsa,zallar mamaki da takaici suna cin zuciyarsa,kan unaisan daya kuwa?,da zata furta wannan maganar wa anni,bayan kowanne mai hankali kai tsaye zai fahimci abinda take nufi. Waiwayawa anni tayi ga maimunatu "Karya kikamin kenan?" A rude maimunatun ke girgiza kai,don gaba daya ta rude,mamaki da al'ajabin unaisa ya cikata,kunya kamar zata kasheta "Ba gashi abinds 'yar uwarki ta fada ba?,kuma ni nasan hali,sanin hali kuma yafi sanin kama,sannan nasan abinda yaci doma bazai bar awai ba" saita maida dubanta ga ja'afar,ta kuma kira sunansa da kakkausar murya,a nutse ya bude idanunsa yana kallonta,kallon da anni ta tsani ya mata shi,saboda zaka haqiqance ne kana fada,amma sai kaga fuskarsa na nuna hankalinsa kwance yake,ya zuba maka ido yana kallonka kamar wani kurma har kayi ka gama "Kalleni da kyau,kuma kayi ta kanka wallahi kafin nayi maka mai dungurungum,su yaran da aka kawo maka ka zubesu kana dirka musu abinci ce maka akayi auren yunwa sukayi?,ko babu abinci a gidajensu?,shi kadai aka kawo maka su ka basu?" Kamar ga maimunatu tayi tambayar,sai gata ta miqe cak tsaye,annin ta saurara tana kallonta "Ina zaki?,zauna" "Toilet zani,fitsari nakeji" jin abinda ta fada sai anni ta barta ta maida dubanta ga ja'afar,kamar wadda za'a kama haka maimunatu ta nufi sassan da zai sadata da toilets na sashen. Tana shiga ta maido qofar ta rufe,ilahirin jikinta rawa yakeyi,gaba daya maganar ta birkita mata kwanya,ga wata irin kunya da taji kamar qasa ta tsage ta shige,yanzu fisabilillahi banda abin anni me ya kawo wannan zancan ana zaman lafiya?,ina zasu kai ja'afar?,wannan abun me shegen wahalarwa annin ke kira musu?,bayan a drama din da take kallo,da karance karancen da afrah ta koya mata tana ganin yadda ake jin jiki,duk da wadanda take kallo da karantawa ba kai tsaye suke nunawa ko fadi ba,amma ai alamun qarfi yana ga me qiba. Minti kusan goma harda doriya ta kwashe kafin ta dage zaninta tayi fitsarin da ya cika mata mara tun sanda anni tayi mata tambayar farko,sai data daura alwala ko zataji dai dai,ta goge fuskarta ta kuma gyara daurinta sannan ta fito. 53 A tsaye ta taddashi,da alama anni ta gama tartsatsin nata,bata iya duban fuskarsa ba kamar yadda takejin ba zata iya hada idanu da kowa cikin falon ba "A nan zaka barsu?" Annin ta jefa masa tambayar "Driver zai maidasu gida, office zan wuce,akwai wadanda na basu lokaci zamu hadu qarfe daya" "Ni gida zan wuce,ka saukeni mana" unaisa ta fada tana rangwada kai,zuciyarta fes,tana jin lokaci yayi da za'a kirata amarya da gaske,farincikin da take ciki yasa takeson komawa gida ta baje kolinta,sa'an nan ta fara shirin shiga turakarsa. Ko kallon gefan da take baiyi ba ya soma yin gaba,don bayajin zai iya daukarta cikin motarsa,dukkansu sunzo masa iya wuya,daga yadda anni ke maganar nan ya tabbatar qararsa aka kawo mata,to amma wace a cikinsu?. Maimunatu da bata son tafiya yanzu sai tabi bayansu tana son gaya masa a barta sai zuwa anjima,bata tsaya ga unaisa dake sallama da anni tana mata godiya ba tabi bayansa,saidai ta kasa bude murya ta tsaidashi. Cak ya tsaya jin ana bin bayansa "Don Allah......zan zauna zuwa anjima" ta fada da sassanyar muryarta dake cike da wani sauti na tsoro,idanunsa ya dan rufe kadan ya bude,har yanzu yana jin wannan zafin na tun dazu cikin ransa,kamar ya juyo ya rufeta da fada,sai kuma yaga fadan me zaiyi mata?,wanne laifi taqamaimai tayi?,yana da tabbacin wanda yakai qararsa ga anni cikin su biyun?,ko kuma itace ta kira khalid da har xai fusata a kanta har haka?,wannan dalilin ya sanya ya gyada mata kai kawai ya fara takawa zuwa parking lot na gidan,yana jin jiyo motsin komawarta ciki cikin murna. Ran unaisa fes take takowa zuwa wajensa,har zata wuce parking lot ta sameshi,sai kuma ta tuna dazun bata shiga ta gaida ammansa ba,don haka ta juya akalarta zuwa sassan amman. Tarba me kyau amman tasa aka mata a matsayinta na surukarta matar ja'afar dinta,wadda tayi zuwan farko cikin gidan tsahon aurensu shekara guda,saidai kuma gaisuwar ma a tsaitsaye tayi mata ita,ta gaya mata ja'afar din ke jiranta zasu wuce gida,bata wani tsawwala ba itama sukayi sallams ta fito tana duba agogonta,tasan tadsn bata masa lokaci,amma babu komai zata wanke kanta,wuyarta ta samu kansa daga yau gobe zuwa jibi. "A'ah,badai har kun fito ba?" Muryar haj munubiya ta yiwa unaisa tsinke,ta waiwaya a hankali,hajiyar na biye da ita a baya kamar ma hanzari take ta cimmata,cikin murmushin yaqe kasancewarta ba wata meson jama'a ba tace "Eh...." "Shi yasa naga kinata sauri ai" ta sake fada tana jifanta da murmushi "Eh,zai saukeni a gida ne" "Ayyah,gashi kuma naga ya fita yanzu yanzu,dab da zaki fito daga gaida surukuwarki" idanu unaisa tadan fidda tana duban inda ya faka motarsa,wayam babu ita,ta dauke dubanta daga wajen,ranta na mata wata irin suya,da gaske tafiya yayi ya barta?. "Indai ja'afar ne wannan ba komai bane a wajensa....amma kada ki damu,gidan surukan naki ai cike yake da direbobi" ta furta tana karantar fuskar unaisa. Unaisan batace komai ba,sai ta sauke jakarta ta fara qoqarin fiddo wayarta "Ba matsala,zanyi waya a kawomin motata" ta fadi cikin zallar bacin rai,tunda ya tafi ya barta ba zata shiga motar gidansu ko daya ba,don indai motace wannan tafi qarfin duk wata mota "Uhmmm,ai dama shiryawa hakan akayi,shi yasa ita dayar tace ba yanzu zata tafi ba ai,kekam Allah ya baki wuyan dauka" haj munubiya ta fada tana motsawa gaba kadan kamar zata bar wajen,duk da ba ainihin hakan bane a ranta,tayi hakanne don jan hankali,taa kuwa jaa hankalin unaisan,don daga kanta tayi ta dubeta "Kamar yaya?" Tambayar tazo ma haj munubiya a dai dai,abinda takeson ji kenan "Ba zakiji mutuwar sarki a bakina ba,kedai kije kiyita haquri" yadda tayi maganar tana niyyar wucewa sai hakan yaja hankalinta,da sauri ta dakatar da ita,ta jima tanason sanin wasu abubuwa game da gidan dama ja'afar dinta,to amma bata saki jiki ba bare ta saba da kowa ballantana ta samu wasu labaran,sai a yanzun da hajiyan ta tareta da kanta "Karki tafi,don Allah ki gayan abinda ke faruwa" jimm tayi kamar batason cewa komai kafin tace "Banyi niyyar cewa komai dake ba,to amma kuma mahaifiyarki hajiya Aayag ta tabamin wani alkhairi da bazan manta dashi ba,shi na tuna a yanzu, shine kuma kawai zai sanya na taimakeki na shiga lamarinki" "Uhmmm,ina saurarenki" ta fada cikin zaquwa da son jin abinda haj munubiyan zata fada. Dan waiwaya tayi,tana duban gefe da gefanta,sannan ta maida idanunta ga unaisa "Magana a nan ba zata yiwu ba,kizo gida ki sameni" kallon haj munubiya unaisa tayi,ta mance diyar wacece ita da zata ce taje gidanta?,lallai tayi araha da yawa,ya kamata ta dawo da girma martaba da izzarta da auren ja'afar yasa ta watsar,abinda yake ta yiwa mahaifiyarta haj Aayah ciwo kenan "Saidai kizo ki sameni,bazan iya zuwa gidanki ba" murmushi hajiya munubiya ta saki,dama hakan takeso,batason karon farko tace zata je ne,kada ta zargi wani abu a ranta,ko kuma kimarta ta zube "Karki damu,bana saka manta alkhairi ni din,zanzo in sha Allahu" "Kamar gobe?,zan aiko da mota a daukoki?" "A'ah,banason kowa ya zargi wani abu,mu barwa nan da kwanaki biyar ko zuwa rana ita yau,amma fa kafin sannan ki sanya idanu da dukka abinda zakiga ya faru,maganganuna zasu bayyana miki komai" kai kawai ta gyada,sannan ta buda jakarta ta ciro sababbin kudi masu dama ta miqa mata,da murmushi ta karba,ta lura kallon faqiriya take mata,batasan tafi qarfin dukka buqatunta ba,batajin cikin familyn khalid akko diyoyin anni akwai mabuqaci da baifinqarfi ci sha da suturarsa ba,gami da sauran buqatu na dan adam harda ra ra "Bana buqatar komai a wajenki 'yar nan,don Allah zan miki,da kuma qaunarki da Allah ya sakamin" "Na gode" ta fada tana maida kudinta jaka. Kasancewar bata samu number da take kira ba,tilas ta shiga motar gidan driver ya maidata gida,don ta qagu ta isa gidan suyi magana da anty talatu,sannan kuma ta fara tsare tsare da shirye shiryenta. *_ADAMAWA_* _RIGAR UMMARU_ A matuqar rude zaninta a hannu,tana tafe tana qoqarin maida zanin nata ta daurashi dai dai yana sake qwace mata,duk da hakan bata saurara da uban saurin da take zambadawa ba zuwa makwantar sabbin,inda take jiyo muryar laulo yana qwala mata kira babu qaqqautawa,ta kuma tabbatar ba lafiya ba,don dama duka kwanakin musiba da jarrabawa take. Daga nesa ta tsaya cak tana bin dabbobinta da kallo,wanda da kadan da kadan sun zaizaye sun rame,dukka wannan cikar tasu kyau da kuma qoshin lafiya babu ita a tare dasu,kamar wadanda ake suda,ko kuma annoba ta fadawa. Gabanta dukan uku uku yahau,ganin nagge guda hudu manya runtuma runtuma aqas babu alamun rai tattare dasu,tun kafin ta qaraso wajen ta dora hannayenta aka idanunta suka tara ruwan hawaye "Yauwa inna,gasunan,nidai bansan me ya faru ba,ba zagaya zan kama ruwa,dana dawo na tarar babu gajee a wajen,dana duba da kyau kuma sai na samu wannan naggen guda biyar a zube a bakin ruwa,to guda daya ce me sauran rai,na ruga na kira na lami ya yankata ya siya,yace zai aiko miki da kudinki" sulalewa kawai tayi a wajen,tahau taba naggen daya bayan daya,batayi aune ba qwalla ta qwace mata,ta soma sharbar hawaye "Wadan nan ne sukayi dakon jawosu,tunda kinsan anyi doka an hana yarwa,yana taba amfanin gonar manoma,saiki biyasu" daga haka laulo yayi gaba abinsa ba tare daya tsaya bi takan inna furera ba. Kamar zata fadi haka don baqinciki,haka ta nufi shiyyar dakunanta ta dauko.musu kudin,qarta qartan samarin fulani ne majiya qarfi sun zuba mata idanu,banda haka bataga abinda zai sanyata biyan wadannan kudaden ba bayan asarar data tafka goma da ashirin. Da qyar tayi sallar magariba ta hadeta da isha'i,tana zaune a wajen,ita ba addu'a ba ita bata bar wajen ba,sai qiyasta girman asarar da take tafkawa takeyi,tunda maimunatu tabar hannunta komai ya sake tabarbare mata,tun bayan tafiyarta take qunzuge kudaden da anni ke aiko mata,taqi daukan mai mata kiwon,ta tilasta gajee fita kiwo ita da laulo,da sunan gajeen takewa tanadin kudin daki dama na biki gaba daya,don tace bata ga abinda ubanta yake dashi ba da zai kai mata gidan aure. To gajen dai ba'a son ranta ya fara fita kiwon ba,don dama gaba daya bata saba ba,a sangarce ta tashi,uwa uba kuma ita aure kawai takeso da himu,wannan yasa gaba daya ita da dabbobin suka shiga wahala,babu kulawa me kyau,a hankali suka fara lalure lalure,sai kuma haka siddan suka fara mutuwa,yau wannan gobe waccan,kudaden da taketa tarun su ta dunga diba tana musu maganu tare da karbo taimako na kambun baka da maita,waiko mayu ke kadar mata da garke,ita kuwa gaje ba abinda ya shalleta,idan suka fita kiwon sai tayi batan dabo,shi dai laulo baisan ina take zuwa ba,amma dai bata dawowa yawanci sai gab da zasu koma gida,tun inna furera bata gane meke faruwa ba,har ta gane,qaura wambai ta fadi ina take zuwa amma ta qeqashe qasa taqi fada,har inna ta haqura ta zubawa sarautar Allah ido. A hankali ta bayyana wani baqon bafullatani take bi su fice daga shiyyar abinsu,haruna kyakkyawan bafulatanine wanda yake ruwa biyu,wani irin kyau ne dashi don hatta qwayar idanunsa launinta daban yake,idanun haruna a bude suke,sabida sunyi yawon kiwo gari gari qasa qasa,don haka babu wuya ya yaudari yarinya ta fada soyayya dashi,da wannan kyan nashi yake amfani,ya yaudari 'yammatan dashi kansa baisan iya yawan adadinsu ba,da haka ya yaudari gaje ta fada soyayyarshi da sunan aurenta zaiyi,tana da son abu me kyau,don soyayyar himu fiye da rabinta kyansa ne yake janta,sai gashi ta samu wanda ya fishi. Hankalin inna furera ya tashi qwarai,ta tashi haiqan don rabasu amma a banza,da sun fita kiwo suke jonewa,kuma gashi ta gaza hanata fita kiwon,saboda bata dame fidda mata dabbobin,daga qarshe ta yanke shawarar bari kawai ta samu daadar himu da maganar aurensu,gwara ayi a daura,duk tsiya idan tasan da igiyar wani a kanta kome zai yanke,shima harunan bazai bita ba. Sai data gama maganarta tsaf sannan daadar himu ta watsa mata wani kallon banza "An gaya miki shashasha nike?,ko ba'a cikin garin nan nake ba ai nasan kome ke faruwa,da farko kinso kai diyarki birni ki hana dana,saboda kina ganin acanne zata samu me arziqi,da hakan bai yiwu ba sai kika haqura,yanzun kuma diyarki ta gama lalacewa....ta gama bidar maza shine kikeso ki joganawa dana?,bazai yiwu ba,nima na fasa hadin,dana fita zaiyi duniya ya nemi arziqi kamar kowanne namiji,ko nima zan kere sa'a cikin rugar nan" sosai ran innafurera ya baci,ta dinga zage zage tana cewa daadar himu ta yiwa diyarta sharri,daga abun arziqi sai ya zama na tsiya?,idan himu bazai auri gaje ba ai basai ta hada da sharri ba. To itama daadar ba baya bace,sai ta tasowa inna furera,suka fito har tsakar gida suna yi,yuuma na jinsu bata ce musu ta tafas ku sauke ba,sosai daadar himu ta tasar mata,har ta fara bankada sirrin inna fureran,da roqarta da tayi kan ta rufa mata asiri,shine silar alqawarin da ta yiwa daadar himu na bawa himu gaje don su samu suci dukiyar a tare asiri a rufe "Barni yuuma,rabu dani na nunawa matar nan nima ba kanwar lasa bace" daada tace da yuuma sanda ta taso tana shirin kashe rigimar,saboda yadda suka fara tonawa junansu asiri,da qyar ta samu ta raba,bayan mutane 'yan gulma sun fara marmatsowa,kowa yana son jin abinda ya shiga tsakanin tsaffin aminan,tun daga sannan sukayi baram baram,aka rabu dutse a hannun riga(dama duka tarayyar da babu Allah a ciki,to tabbas qarshenta kenan koma fiye da wannan). Ajiyar zuciya inna furera ta saki,sai ta miqe tana zura takalmanta,ta kuma nufi turken dabbobin,tsaiwa tayi tana qare musu kallo,baqinciki na sake sudarta,wai me yasa komai yake shirin tabarbare mata ne?,watsewar wadan nan dabbobin dai dai yake da watsewar dukka farincikinta da kuma kima da daraja data samu a baya cikin qauyen ta dalilinsu,kuma hanya ce da zata bawa maqiyanta kamar su daadar himu damar yi mata dariya gami da zundenta,kai ta girgiza da sauri,ba zata taba barin hakan ta faru ba,ko ta yaya sai ta dawo da garkenta kamar yadda yake ada,amma kuma ta yaya?,ina taga kudin da zata sake siyan wasu dabbobin ta cakuda da nata?. "Maimunatu" shine sunan daya fado mata,tabbas!,wannan itace amsa,tun daga kan kayan lefe sadaki da irin mutanen da suka je daurin auren yarinyar ta tabbatar ta taka wani babban shinge,kuma koda bata gani ba,jikan tsohuwa anni ai ba wasa bane,tunda tasan anni,sani na daga ni sai ke ba sanin shanu ba,ko daga motocin dake shigowa da ita garin da irin rabon da take zakasan ba qananun mutane bane. Murmushin samun mafita ne ya subuce mata,ta saki ajiyar zuciya,hankalinta kuma taji ya kwanta sosai,dole ta nemo gidan maimunatu,tana da tabbacin zata samu dukkan kudaden data yanka mata,ai dai komai lalacewarta ita taci gaba da riqonta bayan bacewar ubanta da kuma gushewar uwarta daga doron duniya,idan ta kama ma sai ayi lissafin din abincin data dinga ci da ita har zuwa sanda aka aurar da ita,da wannan tunanin ta juya zuwa cikin gida,saidai abu daya da take ganin zai kawo mata tarnaqi shine,ina zata samu kwatancen gidan maimunatu,daga nan har garin gombe?. "Yuuma mana" tsukakkiyar kwanyarta ta bata amsa,take kuma ta gamsu,don haka ta dage katifar ciyawa dake dakinta tana laluben sauran kudaden data adana,ta lissafa taga nawa suka rage mata?,tunda tun bayan auren maimunatun anni tace yuuma ta shaida mata,kudin aikatau an gama biyansu,tunda a yanzu tana gidabta tana zaman aure bautar Allah bata mutum ba,a ranta take qiyasta adadin kudin zasu kaita gwambe?,don bata tunanin kudin dawowa,tasan ko a jirgi tace tanaso a dawo da ita za'a kawo ta. Barazanar daukewa numfashinta yake daga qirjinta sanda ta daga wajen ta kuma kakkabe katifar taga wayam "Hukumullahu min zalika" ta fadi kalmar da ita kanta batasan cikakkiyar ma'anarta ba,yadai fadane kurum,gumi ne ya fara tsargo mata,ina kudadenta suka shiga?,cikin lokaci qalilan tayi gumi kashirban,ta koma bakin itacen gadon ta zauna tana sauke numfashi kuka kamar zai qwace mata,ta xurfafa tunaninta kan waye yabi dare yabi rana ya dauke mata kudinta?. 54 Kudin da iya su kenan cikin abinda ta mallaka?,sai ragowar dabbobin da suketa sulalewa suna qarewa daya bayan daya,sauran kuma suna bushewa kamar ana lasarsu?. Sallamar jauro yayi dai dai da tunanin daya darsu a ranta na cewa tabbas shine ya debe mata kudin,domin kuwa taga yana ta gyaran bangare daya na cikin gidan,idan bashi ba bataga wanda zai debar mata kudi ba,tunda dai saman katifar suke kwana,kwana biyu ne ma yayi qaura yabar dakin saboda fushin da yake da ita kan abinda ke faruwa game da gajee. Zumbur tayi ta miqe ta fito,tayi tsaye a bakin qofar dakin nata,hannuwanta a qugu tana kallonsa,sai ta zare hannuwan nata ta miqa masa tana dubansa da idanuwanta dake cike taf da rashin kunya da diban albarka,bin hannuwan nata yayi da kallo cikin mamaki,don baisan me take nufi ba "Meye hakan ke kuma?" "Ai kafi kowa sani,kudi na....kudi na nake so ka tafen ka bani,kuma wallahi sisi idan yayi ciwon kai sai ka fiddoshi" kallon mara cikakken hankali yake mata,don shi gaba daya kwana biyun nan kamar a zare kuma a firgice yake ganinta "Kanki daya kuwa?" Ya soma da tambayarta,saboda yasan ta inda zai kamo maganganun dake bakinsa "Ras nake jauro,kuma babu abinda zaka layancemin,kudina kawai nake da buqata,zaa cuceni a ha'inceni,har an tada gini ban sani ba" qare mata kallo tas yayi,yadda take girgije girgije ya tabbatar masa da gaske take maganarta,shikam a yanzun bashi da magana da ita,burinsa kawai ya gama gininsa lafiya Lau a daura masa aure da bazawararsa sadiya,ya tabbatar zatayi dai dai da furera da kuma dukka iskancin dake kanta "Allah ya baki lafiya furera,na fuskanci tunda dabbobin marainiya suka fara kama gabansu aka soma taba naki tunanin,Allah ya kawo manzan sauqi,amma ki sani,koda zanyi sata bazan saci dukiyar haram dukiyar marayu irin taki ba,na dirkawa cikina wutar sa'ira,zan shiga dakina,kada kuma ki kuskura ki biyoni ballantana kice zakimin hauka,kije can ki nema inda dukiyarki ta salwanta" ya dire maganar tasa cikin tsananin kaushi da tsaurara harshe,sannan yayi gaba abinsa dauke da jakar buhun da ya dawo da ita daga cin kasuwar cikin wani qauye dake gaban nasu. Binsa tayi da kallo,tafi kowa sanin jauro,kuma yadda yayi maganar ya sagar mata da gwiwa,tare da debe tunanin shi ya dauka kudin,sai ta koma bakin karan gadon ta zauna gwiwa a sanyaye tana zurfafa tunaninta kan inda kudinta suka shiga. Zumbur ta sake miqewa tana kama sunan gaje,sai a sannan ma ta tuna yarinyar bata shigo gida ba har yanxu,mayafinta taja sannan tayo waje ba tare da neman izini ko ta tsaya gayawa jauron zata fita ba. Tana tafe a hanya tana surutai ita kadai tare da tuna cewa dazu da safe sanda take fitowa daga bandaki taga fitowarta wuff daga dakinta,saidai bata kawo komai ba,ta dauka sauri take ta dauki kununta ne zata kada dabbobin su fice. *GWAMBE* Suna idar da sallar la'asar cikin masallacin dake cikin katafariyar ma'aikatar tasa ya dawo third floor,inda anan makeken office dinsa yake,direct ya isa saman freezer ya dauki agogonsa ya daura,sannan ya dauki hularsa yana gyara karinta,a hankali yana tuna abubuwan da suka faru a yau din,dukka abubuwane masu tsayawa a rai,kai qararshi zuwa ga anni sai abunda yafi komai tsaya masa a rai ba tare da yasan dalilin hakan ba.....irin kallon da yaga khalid yana jifanta dashi,kallon titsiye kallon qurilla kuma kallon haramun,lips dinsa na qasa ya cije yana jin kamar yanzun abin yake wakana,ya daga hannunsa da niyyar sanya hularsa saman kansa Jabir ya turo qofa ya shigo office din,wanda a yau wannan shine shigowarsa karo na wajen hudu,abinda kusan ba al'adarsa bace. Duk shigowarsa ta dazun yayine don yaji wani abu daga bakinsa,saboda yana da masaniya akan kiransa da anni tace zatayi,da goyon bayansa ma ta aikata hakan,saidai ko a fuskar gogan bai nuna masa ba,duk da cewa ya karanci akwai wani abu a qasan ransa,uwa uba kuma basa boyewa junansu komai "Fita zakayi ne?" Jabir ya fada,saboda yasan lokacin tashinsa bai qarasa ba,saura kusan one hour,shanyayyun idanunsa ya daga ya kalleshi "Eh,i have to go,ina da uzuri" "Munyi maka,mu masu mace daya ma muke samun kanmu cikin irin wadan nan uzurorin balle kai me biyu?" Yayi maganar ta manufa biyu ne,da kuma salon jan zance tare da neman tsokana,ya sani sarai,amma sai ya shareshi,baiko daga kai ya kalleshi ba bare ya biye masa suyi,saima yaci gaba da gyara hularsa,sannan ya qarasa gaban dan madaidaicin madubin dake manne da bango cikin office din,zaka zaci ma wani abune a wajen idan baka sani ba saboda design din da aka masa,ya kafa hular da kyau a gaban goshi,sai gashi ya fito fes da wani irin kyau me daukar hankali tare da kwarjini "Allah ya gyaraka,yasa ka koma ja'afar dinka na asal" Jabir ya fadi a fili,a wannan karon waiwayowa ja'afar yayi ya kalleshi "Wait.....wai me yasa yau ka takura min ne?" "Saboda yau kake ango" ya furta yana danne dariyar dake cinsa,maganar tasa ja'afar qarasa waiwayo gaba dayansa,ya zuba masa shanyayyun idanun nan nasa "Daina kallona haka malam,ba maimunatu ko unaisa bane" "Duk wani zagon qasa da akemin na fuskanci dakai ake shiryashi ko?" "Dai dai kenan,munason ka zama mutum kamar kowa,ka ajjiye wannan son bayan rai din,ka fuskanci reality,ka kuma yima shaheeda soyayya ta gaskiya ta hanyar samarwa kanka farinciki ka kuma dawwama da yi mata addu'a,da kula da abinda ta bari" kashe bakinsa gaba daya jabir yayi,ba wanda yasan abinda yakeji sai Allah,yana tsintar kansa a matuqar damuwa da qunci duk sanda ya tuna yadda ya wofantar da kulawa da soyayyarta,bai tashi fargar jaji ba sai daya rasata,wannan yafi komai damunsa da hanashi dukkan wani sukuni da walwala,akwai ciwo ya zamana kayi rashin mutumin dake maka soyayyar gaskiya,baka tashi gane hakan ba sai daka rasashi,ya tafi,yayi maka nisa,nisan da babu dawowa,koda zaka salwantar da dukka abinda ka mallaka don ganin dawowar tasa. " Ga sauran agreement din nan,ka duba idan komai yayi ka sanya hannu,munata loosing opportunity dinmu,bansan a kwanakin nan me yasa ka kasa concentrating akan aiki ba,is there any problem?" "Nop" ya amsa masa a taqaice,ya ciro wayarsa yana turawa driver dinsa tex kan ya fidda mota zai sauko "Okay....i hope so" jabir din ya fada shima yana miqewa,ja'afar bai sake komai ba suka fito tare suna tattaunawa. A parking lot suka rabu,jabir din yayi motarsa,shima ja'afar ya shiga tasa,ajiyar zuciya ya sauke sanda suke fitowa a company din,idanunsa na bisa titi yana wani tunanin na daban. Maimunatu bata wani jima sosai ba a gidan su laila suka dawo,sai gidan ya rayu ya cika da hayaniya,don an jima ba'a hadu ba,rabonta da gidan tun kafin a koma makaranta,da aka dawo din nan kuma ta dawo da rashin lafiya,bata fito zuwa gidan ba sai yau. Harda anty maama suka dawo ita da yaranta,duka a falon anni suka yada zango,sai maimunatun ta dinga jinta sakayau,zaman kadaici sam baiyi ba,hirar tasu ta dinga debe mata kewa,duk da ba kasafai take sanya musu baki ba "Kiri kiri manya yaqi kawomin ke,kusan shekara daya tunda hisham ya kawoki har yau baki sake dawomin ba,shi yasa nima nayi fushi naqi zuwa gidanku" anty maama tace da maimunatu wadda ke lallabewa 'yar anty maama ta uku kanta da manyan kalba, yarinyar tana da suma,amma kuma batason kitso kwata kwata. Murmushi tayi "Makaranta yasa bai kawoni ba,amma zanzo anty in sha Allah" "Ina zuba ido" ta amsa mata tana bude wata leda me dauke da wani babban tambari da kuma suna,wasu kayayyaki ne a ciki,ya fiddosu ta ware wasu,sai ta dubi maimunatu "Allah yasa kina amfani dasu,siya nayi daga baya kuma dana duba naga sunmin yawa,kada su lalace ban shanyesu ba,kwashe wadan nan kiyi amfani dasu" kunya ce sosai ya saukarwa maimunatu sanda ta kalli kayan,ko wanda baisan na meye ba idan ya duba jiki zai gane,magunguna ne irin na ma'aurata,da bayaninsu balo balo a jiki,a kunyace ta debe tana cewa "Na gode anty" "Ba komai,amma akwai wani a ciki miqo in gani,ki shanyeshi,don idan yakai gobe tace zai lalace" ba zata iya cewa da ita komai ba,saboda kunya da kuma nauyinta da takeji,hakanan ta karba takai bakinta a hankali ta fara kurba. Sosai abun yayi mata dadi a baki,tana sha gardinsa yana ratsa harshensa,shi ba gardin madara ba bana kwakwa ba,a hankali sai gashi ta gama dashi,dai dai sanda laila ke shigowa dauke da babban plate data shiga kitchen da kanta ta zubo musu abinci "Me akasha ba'a rage mana ba,naga wani hadadden bottle haka a hannunki matar yaaya" tayi maganar tana ajjiye tray din tare da miqa wuya tana leqawa "Matsa malama,ba irin naku bane,saiki jira sai anzo kanku" "Don Allah a bani na dandana,da gani abun dadi ne wallahi anty maama kika sata a loko ita kadai kika bata" laila ta sake fada tana daga robar zata kai bakinta. Buge roban anty maama tayi tana harararta "Baki da hankali ne laila?,baki gane me nake nufi ba kenan?,to kika sake kika sha wannan yau saidai abbi ya bada sadakar aurenki ko babu sadaki" ta qarashe fada tana sake zabga mata harara idanunta kamar zai fado. Dariya laila ta saki tana qunshe bakinta,ita har ga Allah tunaninta baikai can ba sai da tayi mata dalla dalla,nadiya dake chart ta sauke wayarta tana harararta itama "Wannan inda abbi bai karba kudin aurenki ba,ina jin kanki da kanki zaki kai gidan auren,duk gidan nan banga mai jarabar son aure irinki ba" dariya sauran suka saka mata,saita bata fuska "Nifa Allah ban gane na meye ba,shi yasa nace a bani nasha,naga yamin kama da milkshake ne" "Ke kika sani dai fitsararriya" nadiya ta sake fada tana gyara zamanta "Anty.....ki mata magana don Allah" laila ta fadi tana duban anty maama "Ke nadiya.....kiyi ta kanki,banason shashancin banza,idan bataso aure ba boko zata so irin naku?,aini walle duk cikin jikokina ba wadda ta burgeni kamar laila?aure ai shine cikar mutunci da kamalar mace,ko wacece ita a duniya kuwa....ehe" Anni wadda shigowarta falon kenan ta kuma datsi maganar ba tare da tasan akan me suke tattaunawa ba tace laila,da wannan ta kashe bakin maganar,dole kowa yayi shuru,saboda sunsan halin anni,yanzu sai ta baro musu aiki. Abincinsu suka ci gaba daci,ana kuma tattauna yadda bikinsu zai kasance, kasancewar watanni shida kacal aka sanya,kafin lokacin duk sun gama exams nasu,laila ma ta gama nata,zata shiga 300ll level ne,a wannan hutun aka tsara za'ayi komai a gama. Gida yakeson komawa ya kwanta ko zai samu hutu daga gajiyar da ya rasa musabbabinta,har sun dauki titin da zai sadashi da gida ya dan yima drivern gyaran murya,a ladabce ya waiwayo "sulaiman kumo road zamu shiga" "Okay sir" ya fadi a ladabce yana sanya signal,yayi yanke ta wani titi dake gabansu kadan,wanda zai kaisu inda yace din. Baisan me yake daukan hankalinsa zuwa gidan ba,ya tabbatar dai zuwa yanzu tana gidan,da wuya ace ta koma,zuciyarsa ta kasa nutsuwa akan ya tafi ya barta a gidan,sai yakejin kamar khalid xai iya dawowa gidan,tunda yaji haj munubiya tana fadin ba yanzu zata koma gida ba. Wani sashen na zuciyarsa na tuhumarsa....shin meye damuwarsa ne a kai?,yayin da wani sashen ke fadin "Ko babu komai akwai igiyarka har guda uku a kanta,sannan sadakinka daka fidda daga aljihunka zaka barshi ya tozarta?,ko auren wasa ne a tsakaninku yafi qarfin a wulaqantashi" sai yaji zuciyarsa na aminta da hanzarin da wani sashen na zuciyar tasa ya bashi. Tuni ta gama gama cin nata abincin,amna ce kawai zaune a cinyarta tana bata nata a baki,lokaci lokaci kunnuwanta na sauraren hirarkinsu da suke sanyata dariya can qasan ranta,saidai a saman fuskarta murmushi kawai takeyi,hirarrakinsu shigen nasu afra ne,ko da yaushe idan aka zauna maganar aure ce dai,itakam bata taba tsintar kanta da jin wannan cikin zuciyarta ba,ko don bata rayu da mutane irin rayuwar da kowacce mace budurwa ke yi ba shi yasa batasan wannan ba?. A nutse yayi sallama falon anni wanda a yanzun ita da anty maama ne kawai a zaune,don sun sauya mazauni zuwa daya falon saboda sufi cin karensu babu babbaka,da mamaki anni ke amsa sallamar tashi,tasan dai daxun da safe yazo gidan,wanda zuwa daya yake ba kasafai yake zuwa biyu ba,idanma zaiyi zuwa biyun to dab da magarib yake sake zuwa,ko bayan sallar magariba da kadan. 55 Yana daga tsaye ya dauki yaron anty maama yana dan jan kumatunsa suna gaisawa da ita,tana dan dubansa yadda yake sake zama fresh cikar hankali zati da kuma kamala na sake bayyanar masa,wanda sau da yawa cewa akeyi captain J yayanta ne,itama ba musawa take ba,cewa takeyi eh,don ba kowane zai yarda kan qaninta bane "Sun wuce gida ne?" Ya aza shanyyun idanunsa dake nuna zallar gajiya kan fuskar anni yana tura mata tambayar "Maimunatu?....tana ciki" baba tabawa dake fitowa dauke da plate data yayyanka fruit ta amsa masa saboda tayi tsammanin da ita yake. "Da kin barshi ai tabawa,dan kusun uwa,mutum sai shegen izza?,sunan iyalinka ba xaka iya fada ba,so nayi naga qarshen iya shege" anni ta bishi da mita sanda yake takawa da kansa zuwa cikin gidan,baiso ma ya tsaya bata lokaci wajen,don yasan yau a ciki suke da juna shi da anni "Haba anni,kaara dai yake miki,sunan ne na zamani dai,ba'a fadi dai a gabanki ba" anty maama dake dariya a ciki ciki ta fada qasa qasa yadda bazai jiyota ba "Shidai ya sani,wallahi gwara yayi ta kansa tun wuri bai qure masa ba" annin ta fada taba miqe qafarta sosai yadda zata fi jin dadin zama sosai, anty maama dai nata tsokanarta,don batasan me ake ciki ba game da gidan ja'afar din ba,daga annin har baba tabawa sun sirranta abin,suna fatan komai zai dai daita a kurkusa. Ba zato ba tsammani sukaga an dauke labulen falon,kamar saukar ruwa da daukewarsa kowa yayi tsit,idanunsu suka sarqafe guri daya lokacij data daga kai don ganin wanda ya shigo din,da qyar ta qwaci kallonta daga kansa,ya jingina da bakin qofar hannayensa shoke a aljihunsa yana ci gaba da kallonta. Dan kwalinta ya zame ya koma rabin kanta saboda santsi,hakanan babu lafayar jikinta ta cireta ganin cewa su kadai ne,santala santalan fararen qafafunta sun fito sosai har qaurinta saboda miqe qafar datayi ta dora amna akai,sai ya lumshe idanunsa yana jin zuciyarsa nadan bugawa kamar alamu na fara jin bacin ransa, imagining yake a ransa khalid ko hisham.....wani a cikinsu ya shigo ya sameta a haka?,tunanin da yasa ya gaza bude idanunsa,yana jin sautin muryar qannensa dake wucewa ta gefansa sumi sumi daya bayan daya suna gaidashi,ba wadda ya amsawa,haka suka wuce don idan da sabo sun saba,idan ta motsa masa hakan yake musu. Sautin muryar amna data taho da sauri tana kiran "Welcome dad" ya sanyashi bude idanun nasa,kana ya bude mata hannayensa gaba daya ta taho da sauri,tashin amna daga saman qafafunta ya bata damar miqewa itama,haushi yadan kamata na yadda duka suka sulale suka barta ita kadai,sai ta gyara dankwalinta sosai,tayi masa sannu da zuwa,sannu da zuwan da yayi kaman bai jita ba,ta duqa a hankali ta dauki wayarta,sannan itama tayi hanyar fita. Yana sane da ita,amma ya basar kamar baiga tahowarta ba,sai data ratso ta shiga tsakiya,sannan ya juyo,da wani irin zafi da zafin nama yana fuskantarta,fuskokinsu suka hadu waje guda,sai ta tsorata da yanayin da taga fuskarsa,duqawa yayi a hankali ya sauke amna qasa "Jeki cema maama ta goge miki baki da tissue,am coming" "Zan bika dad?" Ba tare da ya gama tantance me ta fada ba ya daga mata kai,sai ta cilla tayi gida cikin tsananin murna. Tazarar dake tsakaninsu ya sake ragewa,abinda ya sabbaba musu fara musayar numfashi,ya kafeta da dukka idanunsa yana kallon matsoraciyar fuskarta,wadda har ta runtse idanunta,zuciyarta na wani irin bugawa fiye da kima,a hankali kuma tsigar jikinta ta fara tashi,jikinta ya fara saukar mata da wani feeling saboda dumin numfashinsa dake gauraye da lallausan qamshinsa wanda ke sauka saman fuskarta,yar yar jikinta ya fara yi tako ina,wani baqon yanayi da tunda take bata taba jinsa a tattare da ita ba. "Me yasa kika zauna haka?,kin manta ke matar aure ce?" Maganar da sam ba ita yaso yi ba ta subuce ta fita daga bakinsa da husky voice dinsa wadda ta cika kunnuwan maimunatu. Jikinta ne gaba daya ya dauki rawa,wayar hannunta ta sulale a take ta fadi a qasa,qarar faduwar tata ya sanya idanuwansu shida ita kaiwa kan wayar,suka kuma dauke a tare suna kallon juna,sai ya tsaya kawai yana kallon kyawawan idanuwanta da suka sakeyin kyau kamar kullum a lokaci irinn wannan,idanuwan da suka dan sauya launi,suka kuma cika da qwalla,ya sanya hankalinsa sosai ga qwayar idanun nata yanason karantarta A hankali ya zame idanuwansa daga cikin nata,ya maida qwayar idanun nasa ga jikinta yana kallonta har zuwa saman tafin qafarta,sai yaja baya ganin yadda jikinta ke dan rawa,mamaki na darsuwa a ransa,baiga wata magana da yayi da zata sanyata shiga wannan mood din ba,amma sai ya sassauta kafin fushinsa wanda baisan me yake sake hasalashi ba "Ki dauko mayafinki ki sakemi a mota" yayi maganar yana bata hanya,tuni ta tsallake,ko takan wayar tata bata bi ba ta wuce da sauri sauri,ya bita da kallo,sai data bace ya maido dubansa ga wayar,sai ya duqa a hankali ya daukota,ya dannan gurin power ta kawo haske. Face dinta dake cike da cuteness ce ta cuka screen na wayar,cikin uniform dinta na makaranta,lafiyayyen murmushi ne kwance akan fuskar tata daya qara mata wani kyau na musamman,duk da screen din wayar ya fashe amma hakan bai hana bayyanuwar kyan hoton ba,samun kanshi yayi da kallon hoton na wasu sakanni,sannan ya kashe hasken wayar,ya sanyata a aljihunsa yana miqewa,a kasalance yabi ta qofar baya ba tare da ya koma ta cikin gidan ba ya fice parking lot na gidan. Toilet ta fara shigewa ta maida qofan ta rufe,numfashi take ajewa gami da cure hannayenta waje daya,tanason ta gama tantance abinda ke damunta tukunna,tsahon minti biyu kafin bugun zuciyarta ya dai daita,hawayenta kuma suka tsaya,saidai abinda takeji cikin jikinta bai sauya ba,famfo ta kunna,ta tara hannayenta ta wanke fuskarta da kyau ta gyarata sannan ta fito,tana takawa a hankali cikin sake daidaita nutsuwarta don kada yanayinta ya nuna wani abu. Ranta fal haushinsa,me tayi haka da zai sanyata a kwana yana mata irin wannan tambayar?,ya kuma rutsata da idanuwansan nan data tsani ya kalleta dasu,tana cewa dukkansu a haka suke zaune kamar ita?,meye tayi wanda ba dai dai ba?,ko wani tafi a cikinsu?,don kawai tana da aurensa?. Laila fa'iza rahama da sahla 'yar anty maama ne sukayo mata rakiya,sai amna dake riqe da hannun maimunatu wadda ta kafe kai da fata yau fa a wajen anty moon zata kwana. Daga dan baya kadan dukka suka tsaya,saboda kowannensu shakkarsa yake,ta qarasa ta sanya hannu ta bude qofar,tana addu'ar Allah yasa ba'a bayan yake ba,gaba daya batason haduwar sabgarta da tashi sam,saidai yana zaune a owners corner,hannunsa dauke da ragowar ruwan daya dauko a hanyan kitchen kafin ya fito. Tana shiga amna ta shigo tana fadin "Daddy.....tare zamu tafiko?" Ta wuce kai tsaye kusa dashi,duban maimunatu yayi,bata yarda sun hada ido ba,sai kuma ya maida kallonsa ga amnan "Ban miki bayani ba?,ba yau zamu tafi ba,I have prepared something for you soon" kafada ta maqale,idanunta na hada ruwan hawaye "Nooo daddy....,nafison na bika yanzu" yadda ta narke din sai ta bashi tausayi matuqa,tana yawan son ta bishi,amma kuma sai yake ganin kamar ba zata samu kulawa irin tasu amma ba. "Let's go" "Yeeyy..... that's my dad" dolensa tasa murmushi kubce masa,sai yasa hannu ya lakaci kumatunta "That's my baby" shima ya mayar mata.murmushin da bata shirya ba mai dan sauti ya kubce mata,fitar sautin sa ya sanyashi waiwayowa ya dubeta,sai kuma ta maze,kamar ba ita ba,ta maida idanunta da hankalinta sosai ga titi. Bata sake tabbatar da surutu da kuma wayon amna ba sai da suka dauki hanya,hakanan ya daure ya dinga biye mata a wasu maganganun nata,itakam farinciki ya cikata,yau zata kwana a wajen daddynta. Shuru maimunatu tayi tana saurarensu,a hankali taji kewa sosai na cikata,kewa ta mahaifi,tana iya tuna wasu abubuwa da suka faru tsakaninta dashi,gata da soyayyar da yake gwada mata a wancan lokacin,bata manta wasu ba duk da shekaru sun fara nisa,gefe guda kuma tana bin yadda jikinta keta motsawa, mood dinta yana dan canzawa kadan kadan,wanda ita kanta batasan dalili ba,wannan yasa motsinta ya dauke kwata kwata daga cikin motar,har sai da amna tace "Anty moon,zaki dafamin pepper chicken?" Murmushi ta sauke tana duban fuskarta,har cikin ranta take jin tausayin yarinyar data rasa yar uwarta dama mahaifiyarta tun batasan rayuwa da dadinta ba "Komai ma kikeso amna....zaki samu" juyi tayi.najin dadi "Bazan sanwa khadim ba,saboda ya cinyemin wanda amma tasa raliya tayimin jiya,nayita kuka" "Zan sake miki wani" Allah ya taimaketa hirar ta sake komawa tsakaninta da daddyn nata. A hankali motarsu ta sanya kai cikin gidan,a lokacin yammaci sosai ya qara yi,qeme me amna taqi takawa da kanta,ta noqe kafada "Daddy ka daukeni" sai ya sunkuya a hankali ya azata saman kafadarsa,cikin jin dadi kuwa ta saki dariya tana kwantar da kanta saman kafadarsa tana ci gaba da dariya. Ta rigasu yin gaba,ta buda sashen nata ta shige,kafin ta maida qofar sai gashi sun iso shi da ita,ya duqa a qasa a hankali yana fadin "Get down" tsalle tayo ta sauka tana dariya ya juya yana fita gami da cewa "Am tired amnee,let me rest for a while,i will get back to you" "Okay dad,rest well,am waiting for" qaramin murmushi ya kuma saki na gefan baki,daga tahowarsu tare zuwa yanzu tana ta debe masa kewa tare da rage masa tamper dake ransa,ya yadda ya kuma sake tabbatarwa nisanta da tayi a rayuwarsa bau qareshi da komai ba sai qarin qunci da takura,sai ya samu kansa da tunanin yadda zai dawo da ita kusa dashi kamar haka,ko babu komai he will get some one who will take away his loneliness. 56 Dakinta suka wuce da amnan,ta ajjie lafayanta jaka da kuma takalminta,sannan ta sauya kayan jikinta zuwa wata doguwar riga "Me zamu dafa amnee?" Murmushi tana fidda ido "Kema irin na daddy?" Gira ta dage mata tana murmushi "Eh yafi dadi ai" sai yarinyar ta saki dariya "Nima nafi son shi" "Yeah,me zamu dafa?" Dan daga idanunta tayi kadan "Ummmm,daddy's favorite" ta fada da sauri bayan ta gama tunaninta "Me kenan?" Maimunatu ta tambyeta tana dubanta "Sinasir funkaso or masa" ido ta zaro "It's late but I'll cook it later,i promise" "Yayi anty moon,i like it nima" "Zan miki in sha Allah amnen daddy" ta fada tana jan kumatunta. Tare suka wuce kitchen din da ita,tana aikinta ita kuma tana mata labari,tana ta biye mata,sai taji aikin yayi mata sauri,hakanan ranta fes,babu tunane tunane ko kuma jin kewa. Soyayyiyar taliya tayi musu data wadata da kayan lambu,duk da haka kuma sai ta hada potato salad,sai kuma farfesun kifi ragon ruwa me kyau,wanda shima yaji kayan qamshi,kamar zata hada lemo taga aikin zai mata yawa,ga magrib an idar bata kuma samu ta sauke farali ba,don haka ta tattara komai takai saman dining,ta kuma gyare kitchen din,amna nata nacin ta bata ko mopping tayi mata amma ta hana,koda ta gama din tare suka wuce daki, maimunatu ta tube ta shiga wanka,bayan ta fito ta shirya cikin wasu white and soft fabric,skirt ne handkerchief style sai shirt off shoulder, design na rigar ya baiwa fararen kafadunta dake qyalli daman fitowa sosai,suka kuma fidda kyansu da kuma sigarsu,hakanan albarkatun qirjinta suka zauna daram daga qasan rigar,saidai ko yaya tayi sunkuyo za'a iya ganinsu saboda yanayin rigar,kayan sun mata kyau sun kuma amsheta,abinda ya bata sha'awa ta sanyasu ganin basu da nauyi ta kuma ji dadinsu a jiki. Sai data yima anan wanka itama sannan sukayi sallah,suka fito cin abinci,hannun maimunatu ta kama ta riqe sanda take shirin serving nata "Anty moon,daddy fa?" Kai ta daga a dubeta "Me ya faru dashi?" Narkewa tayi tana duban qwayar idanunta "Zaici abincin,yanason kifi" nauyi yadan kamata,to amma kuma jagwal zata ja mata,don ita bata shirya komai dashi ba,bata kuma shirya ganinsa ba bare ga tsareta da wannan kallon nata ya dagula mata lissafi ba "Kinga baya nan ai,kuma baice yana jin yunwa ba" "Please anty,zai dawo fa,he promised,kuma daddy na baya saba alqawari,Allah anty na tabbatar zaici,he like it" yadda ta riqe mata hannu ta kuma marairaice mata dole ta ajjiye serving spoo din tana sauke ajiyar zuciya,nan suka zauna jiransa,duk bayan mintuna sai amnan ta duba qofa,maimunatu ta biye mata ne kawai,amma ita ta sani ba shigowa zaiyi ba,tunda ba shigowar yakeyi ba,sai ta kunna musu mbc three daga nan saman dining din da suke ko zata ragewa yarinyar zaman jira. A tashinta na karo babu adadi sai amnan ta fice ba tare da maimunatu ta lura ba,kanta tsaye ta haye stairs na ja'afar tana sauri sauri,ta wuce balcony ta tura qofar falon da sallama abakinta tana leqe leqe. Yana tsaye gaban tv yana sauya tasha,bayan ya cika dakin da sanyin ac kaman babu gobe,hannunsa daga dauke da cup na black tea,yana sha yana tunanin abinda zaiyi order wanda zai dace da yanayinsa,yayu matuqar kewar tafiyar da baaba tabawa tayi. Da mamaki a fuskarsa ya waiwayo yana dubanta,sai yadan sakar mata murmushi,ita kuma ta tsaya daga bakin qofar tana maqale wuya "Daddy,your dinner is ready" idanu ya fitar alamun mamaki "Who prepared it for me?" "Anty moon ce,ka taho daddy please,munata jiranka tun daxun" "Amneee.....zo kiji" ya fada yana ajiye cup din gami da yafitota,kafada ta maqale "You promise fa daddy,kace zaka koma,please daddy let's go" tayi maganar tana tahowa gami da jan hannunsa,idanunsa ya lumshe kana ya bude yana murmushi,baisan inda ta samo dan banzan wayo da kuma surutu ba,iya yau kawai ta sanya murmushi sau babu adadi saman fuskarsa,bashi da sauran zabi tunda yayi alqawarin illa bin bayanta da yayi. Duka hankalinta ya dauko ga tv din,saijin muryar amna tayi tana rangada sallama,riqe da hannun mahaifinta tana gaba yana biye da ita a baya,sosai gabanta ya fadi,ya shiga tattare zamanta tare da gyara jikinta a fakaice,tuntuni idanuwansa suka sauka a kanta,idan yace ma batayi masa kyau ba lallai ya shimfidawa kansa qarya ne kawai,mutum ne shi ma'abocin son fararen kaya,don ko a yanzun moroccan abaya dake jikinsa fara ce sol da adon golden zare,sai ya maidashi tamkar wani basarake sak. Kame kame ta shiga yi sanda ya iso wajen,yana daga tsaye idanuwansa akanta ya jama amna kujera daya ta haye,saita jaa masa itama kujerar dake kusa da ita,wadda daga ita sai wata empty chair sai kujerar da maimunatu ke zaune a kai "Have a seat dad" ta fadi a shagwabe,baice komai ba ya sake janye kujerar ya zauna din,wanda a take qamshin turarensa ya mamaye wajen. Ya tabbatar da cewa kallon da yake matan ya wuce yadda ya kamata,don haka yayi qoqarin tattara hankalinsa ga amna,yana saurarenta yana kuma lumshe idanu gami da gyada kai,kusan shine amsarta,don ya tabbatar idan yace zai biye ma surutunta zata bashi ciwon kai a daren,saboda hirar amna bata qarewa. Cikin qoqari da jarunta ta tattara nutsuwarta ta soma serving dinsu,yana ankare da ita yadda take ta loda musu abinci a plate,caraf ya riqe hannunta ganin abincin yayi yawa kamar bata kula,a razane ta saki warmer din tana dubansa,wani abu tsarga mata tun daga yatsun qafarta zuwa kwanyarta,ya kumma kunno mood din da taketa qoqarin ganin ta danneshi. Hannun nata ya saki ya sulale a hankali sannan yace "Enough mana, yayi yawa" yayi maganar don baya tsammanin shi zai iya ci,baisan taste dinta ba,kuma bashi da tabbacin abincin zai dace dashi,duk kuwa da qamshin spices da ya cika wajen. Sakin spoon din tayi,ta koma da baya a hankali ta zame saman kujerar,sai yaja plate daya,ya sanya spoon ya matsar gaban amna "Uhnnn....bismillah" murmushi ta saka sanann ta dauki cokalin ta soma diban abincin tana kaiwa bakinta,wani murmushin ta kuma yi "Yummy...." Ta fadi tana duban fuskar ja'afar "Daddy,mucu, you will enjoy it over" murmushin gefan bakin dai ya kuma saki "Ki cimin amnee,tunda ya miki dadi" qememe ta tubure kan shima fa sai yaci din,ta haura saman table din ta dauko masa wani spoon din,sanan ta tsareshi da idanu,tilas ba don yaso ba ya diba abincin dan kadan ya sanya a bakinsa yana taraddadin abinda zaiji. A hankali dadin abincin ya fara zagaya harshensa ya kuma gauraye bakinsa gaba daya,sake diban second spoon yayi,sai ya kuma jin real taste din fiye dana dazu,sannu sannu sai gashi yana ta kaiwa cikinsa abincin yana kuma sauraren hirar amnan yana amsa mata da ka,kafin kace meye wannan sai ga plate din wayam babu komai. Idanu amna ta fitar tana duban ja'afar "Daddy,a qaro ne?" Kai ya girgiza yana shafa cikinsa,ta wani sashen kuma yana cika da mamakin yawan abincin da yaci,duk da dama shidin bamai wasa bane da cikinsa musamman idan ya samu abincin daya dace da taste dinsa "No.....am full amnee, thank you" "Thanks to anty moon,ga kifin dad" sai yayi kamar bazaici ba saboda qoshin da yaji yayi,amma shima yana tabin farko ya bude cikinsa yaci kifin sosai,har sai da sukaci kusan rabi,sannan ya dakata,ya yagi tissue ya goge hannunsa daya baci "Anty bakici komai ba,ba kyau fa zama da yunwa" sai a sannan hankalinsa yakai kanta,ya kalli plate din abincin nata,kusan babu abinda ta taba a ciki "Daddy kace mata taci" miqewa yayi ya zube hannayensa a aljihunsa,kana ya saukar mata da dukka nauyin idanuwansa yana kallonta "Eat it" ya fadi a gajarce "Daddy yace kici anty moon" saita jinjinawa amna kai "Zanci amna" a hankali ya janye idanuwan nasa yana mamakin kansa,baisan me yasa ya maida kallonta one of his favorite thing to do ba a duk sanda zasu hadu a muhalli guda,bayason hakan ko kadan,sai ya kama hannun amna suka fice da sassan nata. Nannauyar ajiyar zuciya ta sauke tana hade hannayenta waje daya da qarfi,abinda take ji cikin jikinta yana qara qarfi,tuni kowacce gaba ta jikinta ta fara amsawa,hakanan launin idanunta suka fara sauyawa,ko kusa ko alama babu wata yunwa da takeji,infact cikinta ma a cunkushe yake,sai ta tashi zuwa bakin fridge ta dauko sassanyan ruwa ta balle ta soma sha tana tsammanin ko zataji sauqin abinda takeji din. *_UNAISA_* Tun bayan sallar isha'i ta gama dukkan wani shiri nata na tarbar ja'afar,girke girke tasa aka masa har kala uku,ta kuma fece kwalliya bayan ta sallami dukka masu aikin nata,ta qwame tana jiran jin shigowarsa ko kuma wani motsi nasa. Lokaci lokaci tana tana duban agogonta,har awannin suka fara nisa,ta fara debe tsammani da xuwansa,wani girman ksi hadi da maganganun da suka fara da haj munubiya suka sauko mata,suka sanya mata wani bala'e'en haushi da takaici,ta kuma shiga safa da marwa amma sai ta kasa daurewa,don haka taja wayarta ta kira anty talatu "Karkiyi gaggawar zuwa wajensa,ki sake jira daga nan har xuwa sha daya ko sha biyu mu gani,duk wayon ango dai dole yazo hannu ai,yana zuwa hannu kuma ai ya gama yawo,da wannan ta koma din ta zauna tana kada qafa,idanuwanta a kan tv,duk da hankalinta ba'a kai yake ba. Da qyar ta samu ta tsakura farfesun kifin,saboda abincin bata jin zai shiga cikinta,ta kwashe komai ta maida kitchen,ta gyara ta kuma wanke kwanukan,dukka a daddafe take komai,saboda zuwa sannan gaba daya mararta ta daure tamau,sai danshi da taji tana zubarwa,wanda tayi tsammanin ko period ne yake zuwar mata. Bandaki ta shiga ta duba jikinta,saidai kuma ba period din bane,wani ruwa ne daban,tsarki tayi tana cije lebe ta fito ta baro toilet din tana takawa da qyar,kayan bacci ta canza tana duba kokaci,amna tana ranta,saidai tunda tasan tare suke da daddynta ba buqatar sai ta dami kanta,sai ta saita freshner din dakin sake fesa kansa da kansa duk bayan wasu sakanni,ta saisaita hasken wutar dakin zuwa dim light,sannan ta haye gadon a hankali taja duvet zuwa qugunta tana cije lebanta hadi da hade qafafunta waje daya. Ajiyar zuciya unaisan ta saki sanda ta kalla agogo,qarfe goma dai dai na dare agogon ya buga,awanni biyu masu zuwa da anty talatu sai takejin sun mata nisa,ba zata iya bari ba,don haka ta miqe ta nufi bedroom dinta,ta fidda kayan jikinta ta wuce toilet don ta sake shiryawa,ta gama tsara cewa fitar zatayi ta taddashi a duk inda yake. Hannunsa guda daya yana saman kan amna,yana shafa sumarta a hankali,yayin da dukka hankalinsa ke kan tv yana kallon news a tashar al_akhbaar,yaqe yaqe ne kawai ke tashi tako ina a duniya,abun akwai daukar hankali sosai. Ajiyar zuciya ya sauke sanda suka kai qarshen labaran,ya janye idanunsa ya maida kan fuskar amna,kallonta yake,sosai take tuna masa da shaheeda,ta wani sashe tana dan diban kamanninta,duk da idonta lips dinsa da skin color irin nashi ne,sai ya tofa mata addu'a sannan ya sunkuya a hankali yayi kissing din goshinta sannan ya miqe ya sabata a kafadarsa ya taka a hankali yana ficewa daga falon. 57 A hankali ta sake dawowa saman gadonta tana runtse idanu tare da sake cije lebanta ta kwanta a hankali kamar wadda ke da gyambo a jikinta,karo na uku kenan tana shiga bandaki tana canza pant dinta tare da sake tsarki,sai a sannan ta tuna da maganin dazun da tasha na wajen anty maama,ta tuna yadda ta tankwabe gorar daga hannun laila dake niyyar sha,filo taja ta dora kanta tana sake tuna abinda anty maama tace da laila "Baki da hankali ne laila?,baki gane me nake nufi ba kenan?,to kika sake kika sha wannan yau saidai abbi ya bada sadakar aurenki ko babu sadaki" tana kaiwa nan wasu hawaye masu dumi suka silmiyo mata zuwa saman filon,batasan wannan aikin zai mata ba,batasan abinda zai sanyata ji ba kenan,mugun feelings kamar zata fashe haka takeji,inda ta sani ta kuma fahimci maganar anty maama koda wasa ba zata shashi ba,sai ta sake takurewa waje daya tana cusa fuskarta cikin pillow,tana jin yadda mararta ke sake daurewa,ta dafeta sosai tana fidda hawaye,dai dai lokacin ya dora hannunsa akan handle na qofar,ya kuma turo qofar dakin sannu a hankali,cikin wasi wasi,don ko daya baiso ya samu bata falon ba bare ya bata amna ya koma ba. Tattausan qamshin dake gauraye da sanyin ac madaidaici wanda baiyi yawa ba,kana baiyi kadan ba yaa doki hancinsa,cikin qamshin ya iya tantance qamshin turarenta da take amfani dashi,take wata kasala ta saukar masa,ya soma takawa a hankali qafafunsa na nutsewa cikin tattausan carfet dinta daya dauki sanyi sanyi. Yana iya hangen direction da gadon yake,don haka bashi da buqatar haske,ya qarasa a hankali ya tsugunna a gaban gadon ya kwantar da amna,ya dora hannunsa saman kanta idanunsa suka sauka a kanta. Yana iya hangenta saboda fararen kayan bacci dake jikinta,wanda a ido kawai zakasan suna da wani sulbi,silk ne masu asalin santsi da daj taushi taushi,milk duvet dinta ya tsaya iya qugunta,sassalka baqa kuma yalwatacciyar sumarta ta baje saman filon,baka iya ganin ainihin fuskarta saboda nutsata da tayi cikin filo. Idanunsa ya kauda daga kanta ya lumshe su yana jin wani iri cikin jikinsa,gaba daya weather din dakin ya fara canza masa yanayi,ya kammala mata addu'ar ya tofeta da ita,sai ya laluba babu pillow kusa da ita. Can ya hangi filon dab da gwiwarta,yana jin cewa tayi bacci,don tunda ya shigo baiga ta motsa ba,don haka ya haura saman gadon a hankali,ya sanya hannu yadan xame filon "Wayyo Allah na" ta fada cikin wata iriyar wahalalliyar murya tana kai hannu da niyyar damqe filon,duk da batasan waye ya shigo na,saidai cikin rashin sani ta kama hannunsa gam ta riqe cikin tattausan tafin hannunta dake da wani irin dumi,motsa filon tamkar ya motsa mararta ne,don ta jingina qafarta ne dashi wai ko zata zamu relief. Hannunsa dake cikin nata ya kalla kafin ya maida dubansa gareta,sai a sannan ya lura da yanayin kwanciyarta,yakai hannunsa a hankali saman kafadarta yana yunqurin juyota,saidai sam taqi yarda da hakan ya faru,don ya zuwa yanzu lallausan night scent dinsa ya gaya mata waye cikin dakin,ba zata so kuma yaga yanayin da take ciki ba,duk kuwa da cewa ita kadai tasan meke faruwa da ita. Hankalinsa yaji yadan tashi,kada dai ace yarinyar bata da lafiya?,take zaune a daki zata kashe kanta,wannan tunanin yasa ya qara qarfinsa kadan,sai gata ya birkitota gaba daya, tashin farko kuma ta afka jikinsa gaba daya,ta samu kyakkyawan masauki a faffadan qirjinsa dake cike da lallausan gashin dake bada wani ni'imtaccen qamshi na musamman,gashin da duka gaza boyuwa ta tsajiyar maballan pyjama dinsa masu salki,gashin kanta kuma ya baje masa saman fuska,daddadan qamshin hair mist dinta ya ratsa hancinsa zuwa qwaqwalwarsa,take kuma ya aika da wani muhimmin saqo,ya sake nutsa fuskarsa zuwa tskaiyar kanta ba tare daya damu da yadda gashin ke shige masa baki da hanci ba. "What's wrong with you?" Ya mata tambayar da wata irin kwantacciyar murya,wadda shi kansa baisan yana da ita ba,maimakon ta amsa masa saita sake qanqame hannunsa dake cikin nata har yanzu,wata sabuwar qwalla na zarto mata daga idanunta,dumin qwallar da ya sanyashi jin hankalinsa ya tashi,ya hada dukka qarfinsa waje guda ya dagata da niyyar sake tambayarta,saidai a wannan karon ma sake shigewa tayi cikin jikinsa da kyau,don bata qaunar hada idanu dashi ko kadan,gani take idan ya kalleta zai iya karanto ko meye ke damunta,idan kuwa har ya fahimta batasan wanne irin abun kunya ta barwa kanta ba,samun gurbinta cikin jikinsa yasa haduwar wasu sassa na jikinsu waje daya,take kuma suka aika da saqo xuwa ga kowanne sashe na jikinsa shima,kowanne sashe kuma ya amsa "Tell me what's going on?" Ya sake qarfin halin tambaya,don so yake ya fara sanin matsalarta kafin yasan maganin da zai bata ko yasa a rubuta mata. Hannunsa kawai takai saman mararta ba tare data shirya ba,tunaninsa take ya rabu gida biyu,yanayinta yana alamta wani abu,amma kuma tunaninsa yafi karkata ga cewa ko period ne,saidai kuma yadda mood dinta ya canza fa?,period na sanyasu haka?. Da qyar ya samu ya gyara zamansa ya fidda wayarsa,ya kuma turawa hisham tex bayan ya riqeta sosai cikin jikinsa,duk da yadda yakejin wani abu na taso masa,kowacce jijiya a jikinsa na harba jini da sauri tana kuma aike masa da saqonni. Saqon na shiga ya samu reply,ya duba ya miqe zai kwantar da ita,saidai taqi sakinsa, kitchen yakeso ya shiga ya dauko abinda hisham yace dashi amma taqi sakinsa,tausayinta ya saukar masa saboda gumin da yaga tana hadawa,duk da sanyin ac mai dadi dake zarya a dakin,dole ya koma ya zauna,ta kuwa kifa fuskarta akan cinyarsa da kyau,abinda yasa numfashinsa ya kusa daukewa,sai ya sanya hannunsa ya dauketa,ya maidata saman pillow din yana gyara mata kwanciya. Ko kusa ranso baiso,amma dole bashi da wani zabi da ya wuce yayi mata uterus massage,ya matso dab da ita,ya sanya hannunsa yana dauke rigarta daga saman shaffen cikinta,wanda kwata kwata baiyi kama da cikin dake cin abinci ba. Lallausan tafin hannunsa ya dora saman marar tata,daga ita har shi sai da suka qwaci numfashinsu da qyar,ta runtse idanunta sabbin hawaye na kunya suna fita,ya motsa hannun nasa a hankali ya fara shafa marar "Hasbunallahu wa ni'imal wakil" ya furta jin yana niyyar loosing control dinsa,sai ya runtse idanunsa yana aro jarumta,tare da tunawa kansa wasu abubuwa da suka taimaka wajen riqeshi da riqe kansa. Lokaci mai tsaho suna a haka,sannu a hankali yaji jikinta ya saki gaba daya,yanayin fitar numfashinta ya canza,sai ya bude idanunsa a hankali akan fuskarta,bacci ne ya dauketa,duk da bata bar fuskarta a saitinsa ba,ta kauda fuskarta daya bangaren ne,ta yadda ba zasu iya ganin juna ba saidai idan leqawa zaiyi. Wata iriyar qatuwar ajiyar zuciya ta kubce masa,yanajin yadda ko ina a jikinsa ke motsawa yana qin yarda da ban haqurinsa,a hankali ya dauke hannunsa daga saman mararta yana dan duban wajen,red pant dinta ya fito ta qasan wandon rigar baccinta ya haska fara sol din fatarta,da baya da baya ya fara zame jikinsa yana sauka daga saman gadon,bayan ya sauka gaba daya sai yaja duvet din ya rufesu su duka,ya dauki remote na acn ya sake dai daita musu temperature din,sannan ya aje remote din yayi hanyar fita yana hada hanya. Da zafi zafi ya dinga hada steps din bibbiyu yana haurawa samansa,yana shiga dakin ya fidda dukka kayan jikinsa,ya rage daga shi sai pant na maza daya sanya kafin ya fita,gaba daya zufa ke karyo masa sosai,bugun zuciyarsa na canzawa,tun ba yau ba yasan kanshi sarai,ta wannan fannin ba kasafai yake da dauriya ba,dabi'arsa kuma ta banbanta data sauran maza,wannan ya sanya ya riga kowa aure a cikin sa'anninsa. Zama yakeson yi amma ya gaza zaman,sai ya matsa ya diba remote na dukka acn dake falo da kuma bedroom dinsa ya qure temperature dinsu,ya watsar dasu a gefe guda. Dai dai lokacin da unaisa ke takowa zuwa saman nasa,duk taku daya tana yinsa ne da manufar practical na yadda zata tunkareshi,tana ji a ranta yau komai zai qare tsakaninta dashi,itama zata kai wani bigire da tsohuwar matarsa takai,zata tsallake shingen da take da tabbacin tsallakewarta zuwa nan wajen ne kawai zai bata soyayya da martabar da takeso daga wajensa. Knocking ta fara yi,abinda yaja hankalinsa ya kuma bashi mamaki kenan,ya zubawa qofar idanu qwaqwalwarsa nason tuno masa waye yayi saura a gidan da xai doshi sashensa a wannan lokaci?,unaisa ya bawa kansa da kansa amsa,sai ya maida wandon pajama dinsa ya nufi qofar kawai kai tsaye,ya mance cewa babu riga a jikinsa. Mutuwar tsaye tayi sanda sukayi arba dashi,idanunta qur bisa fuskarsa zuwa qirjinsa,wani abu ya soma zagaya jikinta,lallai kaman dai tazo da sa'arta kenan?,batayi qasa a gwiwa ba ta sakar masa murmushi,sannan cikin dabara ta turo qirjinta zuwa gaba tana karkacewa cikin kwarkwasa. Koda bata ce komai ba shi din ba yaro bane qarami,dai dai gwargwado yasan mata ciki da bai,ya kuma karanci mabanbantan hali da dabi'a irin tasu,uw uba ma ya taba yin aure,don haka daga uya sleeping dress da ta saka a jikinta take tsaye kuma a gabansa ya isa ya gaya masa me take nufi? "Zanyi maganinki" ya ayyana hakan a ransa yana mata duban baki da wayo,yayin da ita kuma ke masa duban so da kuma sha'awa........ 58 Assalamualaikum NAFISAT K ABDULLAHI Is an actress in the kannywood industry She's a singer and can sing all types of songs You can't afford to miss her newly released song named *KADDARATA* part 1-4 on her YouTube channel *OFFICIAL FEENAT* You can only click on this link and stand a chance to listen and watch her amazing video https://youtu.be/t__84EwU7Fo Dont only enjoy the emotional video but also *SUBSCRIBE* to anable you to be notified when ever she upload another video Like and drop your comment under the video to encourage her do more of that . The only way you can support and encourage her is by *SUBSCRIBING* to her YouTube channel below https://youtu.be/t__84EwU7Fo She is used to noticing those following and commenting on her videos . *GUESS WHAT*? https://youtu.be/t__84EwU7Fo Click and see for yourself Thank you so much ________________________________ 58 Gefe ya janye mata,abinda yayi mugun yi mata dadi kenan,ta kuma bawa kanta tabbacin akwai nasara kenan,sai ta fara takowa zuwa ciki tana kuma sauya salon tafiyarta cikin kwarkwasa da taku d'ai d'ai. Dab da zata gotashi tayi rangaji ta kuma fada jikinsa,bai tarota ba bai kuma hanata ba,damar data samu kenan ta ruqunqumeshi gaba daya cikin jikinta,duk yadda taso ta daure amma ta kasa,sai ta fara masa wasanni cikin son shagaltar dashi. Tabbas tayi nasarar sake kunnashi,tunda dama a kusa yake,saidai daga lokacin da ya jata ya fara nuna mata nata salon qwarewar sai al'amarin ya sauya,tun tana iya jurewa irin salon wasanninsa har ta fara gayawa kanta akwai matsala fa,tasan kanta,duk jarabarta akwai iya limit dinta,tana da matuqar rauni ta nan bangaren wanda ba kasafai ta fiya son a dameta ko a zurfafa ba,ko saurayi ne ka fiya nacin manne mata yau gobe jibi zata qara maka wuta,takan ce ita ba riga bace da za'a yita wanketa,daga dukkan alamu yadda yake aike mata da saqo cikin wani irin zafin nama kadai ya isa gaya maka wanne irin kalar mutum ne shi. Tuni idanunta suka raina fata,ta kuma fara qoqarin guduwa,ta tabbatar ba zata iya ba,ba zata daukeshi ba,don komai zai iya faruwa,qarfinta tattara ta watsala qasan gado tana dafe da lips dinta dake mata radadi kamar zasu yanko su fado,yunquri yayi kamar xai bita abinda ya sanya babu shiri ta miqe ta lalubi hanyar fita da sauri. Saman gadon ya zube yana fidda wani irin murmushi,shi ya sani ba kowacce irin mace bace zata iya daukeshi ba,ko shaheedansa tasha fama kafin ta saba,saidai da yake mutum ce mai juriya sai ta saba din a hankali,take kuma kula da duk hanyar da zatasan zata sama masa farinciki da nutsuwa. Ko baya son mutum ba kasafai yake fidda hakan quru quru ba,amma baisan dalilin da ya sanya sam ko sau daya bai taba jin wani abu guda daya daya motsa zuciyarsa a kanta ba,a hankali ya saki tsaki yana saukowa daga saman gadon,sai yaji gaba daya yana qyamar jikinsa bawai don ya fitar da najasa ko wani abu ba,toilet ya shiga ya hada ruwan dumi sosai yayi wanka. Abu kaman wasa sai gashi gaba daya daren yazo masa a wani irin birkice,sau biyu yana sake wanka,a wannan karon dai wankan ibada ne,tsakiyan dare da kuma kafin sallar asuba,me yasa mafarkinta ya hanashi bacci?,me yasa mafarkinta ya hanashi sukuni?,yana gaban mudubi a zaune yana lissafa tsaho shekaru da watannin daya dauka baiyi rayuwa da mace ba,sai ya furzar da iska daga bakinsa,tabbas wannan abun da ya farun yana da nasaba da dadewar da yayi da nisantar rayuwa dasu,bawai wani abu bane na daban. Dab da liman zai tada sallar asuba ta buda idanunta,tana budesun abubuwan da suka faru a daren jiya suna dawo mata fes cikin kanta,sannu a hankali ta waarasu cikikin dakin,yana nan a yadda yake har hasken data kunna kafin ta kwanta,saidai sanyin dake busawa ya fara mata yawa saboda iskar asuba data gauraye duniya. Hannunta ta daga tana shafa saman mararta a hankali,sakayau take jinta,babu wannan ciwon,hakanan babu feelings din gaba daya,sai ta sauke ta juya hannun damanta,idanunta suka sauka akan amna dake baccinta cikin kwanciyar hankali,hannunta ta dora kan fuskar yarinyar da wasu lokuta take mata yanayi da fuskan mahaifinta,batasan ya akayi murmushi ya kubce mata ba,sai ta miqe ta zauna sosai tayi kissing goshinta,sannan ta sake gyara mata kwanciyar gami da ja mata bargon sosai. Bandakinta ta wuce,ita dinma sai da tayi wanka don bata yadda da kanta ba,sannan ta dawo ta saka prayer jilbab and skart da takanyi amfani dasu musamman a sallar asuba irin haka,ta tada sallarta. Ko data idar qur'aninta ta dauka,bata wasa da tilawa ko don saboda haddarta,ta buda daga inda ta tsaya jiya ta dora,cikin qaramin sauti da kuma lallausar muryarta dake koyi da qira'ar shaik khalilul khusari. A nutse ya turo qofar dakin a hankali,sautin karatunta ya baqunci kunnuwansa,sai ya maida qofar kawai ya rufe ba tare daya katse mata karatun ba,ya juya yana barin wajen,sautin karatun yana bin kunnuwansa har zuwa sand yayi nisa a wajen. "Itama matarka ce" zuciyarsa ta raya masa sanda yake shirin wucewa zuwa saman sa ba tare daya biya sassan unaisa ba,wannan tunanin ya sanyashi sauya akala,ya isa qofar falon ya murdata,sai ya jita a kulle, knocking ya soma,saidai babu alamun za'a bude masa,mutum ne da bai fiya tsawaita abubuwa ba,don haka yana qara biyu ya juya yayi gaba,taku hudu cikin na biyar yaji an bude qofar,ya waiwaya a hankali idanuwansa a kanta. Kana kallonta zakasan a birkice take,don hatta gashin kanta a hautsine yake,hakan na nufin a yadda ta shigo jiya a haka ta kwanta bugu da qari kuma har yanzun bacci take,bugunsa ya tadata "Lokacin salla zai wuce" daga haka yayi gaba,ya soma haurawa zuwa saman,unaisan kuma ta bishi da idanu,abubuwa da yawa take rayawa a ranta,indai har shirinta na jansa zuwa gareta ya tabbata,to batasan yadda sauran abubuwa kuma zasu kasance ba. Tana gama azkar dinta amna ta farka,sai ta rakata toilet tayi brush sannan tayi alwala,komai ta iya perfectly,da alama ta samu background me kyau. Sallar ma sanda tana yi tana ankare da ita,gyaran dake ciki da kusakuran basu da yawa,ta jinjinawa amma sosai,ta kuma sake ganin kimarta da martabarta,hakan kuma ya tabbatar mata da cewa ita din uwa ce ta gari. Basu koma wani baccin ba,ko surutu da hirar amna ma ba zata bari su koma ba,don haka ta jata kawai suka wuce kitchen. Break fast me kyau ta shirya,wanda ya dauketa awanni kusan uku kafin ta kammala,har masu aikin unaisa suka gama hada nasu break din suka fice suka bata wajen,sau tari dama idan girki ya hadasu lokaci daya ita ke tsaftace kitchen din,koda sun gyara baya mata dai dai,saita shiga ta sake killace komai. A dining ta shirya komai,kamar ita da wasu zasuci abincin,hakan kuma zabin amna ne,ita ta dinga dauko warmers din daga kitchen din tana ajewa saman dining din,bedroom dinta suka wuce ita da amnan don yin wanka. Tun suna wankan ta dameta da tambayar daddynta,don haka suna fitowa ta fara shirya amnan,tayi kyau sosai cikin fara shirt da gray color din skinny jeans,ta hade mata uban sumarta tsakiyar kai,tana ta qamshi yarinyar ta cilla ta fice zuwa sassan daddyn nata,sai sannan maimunatu ta samu sukuni,ta zauna gaban mirror ta buda manta ta fara shafawa,ta shirya kanta cikin favourite shigarta na chiffon fabric,sun ray pleat design da rigansa drawstring data zauna mata a jikinta ta mata kyau sosai. A jikinta dama taji sai amna ta jawoshi sassan nata,aikuwa tana tsaka da hade sumarta cikin band amna ta turo qofar da sauri "Anty moon,daddy xai fita,kizo kiy serving dinsa,yace bai yarda nima na iya girki ba,wai ba tare mukayi ba" dariya ce ta kusa qwacewa maimunatu,ta cikin madubin take kallonta tana saka band din,sannan ta janyo siririn mayafin kayan ta yafa saman kanta ba tare da taji shakkan fita dashi ba,tunda babu wani abu a jikinta daya fito,dukka yanayin dinkin me sakin jiki sosai ne "Muje in gaya masa,amna ta ta zama 'yammata,she can cook" dadi ya cika amnan,ta saqale hannun maimunatun suka rankaya zuwa falon. A tsaye suka sameshi,ya bawa qofar da zasu fito baya,hannuwansa cikin aljihun wandon suit dinsa,wata iriyan suit mai daukan ido da hankali,koda bakasan tsadan sutura ba zakasan taja kudi,komai nashi designer ne me tsada,duk da bata ga fuskarsa ba amma ta baya tana iya hangen sumarsa da tasha gyara sosai,qafafunsa dake saye cikin safa sun nutse a cikin center carpet din dake wajen "Daddy ka zauna mana" amna ta fadi tana zame hannunta daga na maimunatu ta kuma nufeshi. A hankali ya waiwayo,a kanta idanunsa suka fara sauka,haka ma ita,duk yadda taso ta zamewa kallonsa amma sai da idanuwansu suka hade waje daya,duk da haka tayi namijin qoqarin kau da nata idanun,wani irin nauyinsa yana cikata,abubuwan da suka faru a daren jiya suna dawo mata cikin kwanyarta daya bayan daya,sai taji ba zata iya ci gaba da tsaiwa ba, nauyinsa da kuma nauyin idanuwansa na sake qara mata kasala da kuma nauyi,duk da abinda takeji a jiya cikin jikinta babu shi a yanzu,amma har yanzu cikin jikinta tana jinsa a mace yayi wani irin laushi,sai ta zame saman one sitter din dake daura da ita ta zauna akai,tana kwaranyar da dubanta ga tv ba tare da tana fahimtar abinda ke gudana ba. Yadda ta rage tsahonta ta hanyar zama haka ya bita da idanuwansa,kyakkyawar zagayayyar fuskarta da tayi wani iri garai garai ta kuma yi fresh ta fito tarwai a tsakanin duhun kalar vail din dake kanta,kamar yadda jajayen siraran lips dinta ke qyallin lips balm "Ina kwana" ta gaidashi da sak irin muryar data dinga gigitar dashi cikin mafarkansa na jiya,sai daya lumshe idanunsa yana hadiye wani abu sannan ya motsa bakinsa "Lafiya Lau" tayi tsammanin zai mata magana kan abinda ya faru da ita a jiya ko wani abu makamancin haka,amma sai taji baice komai ba,hasalima ya tattara hankalinsa ga diyarsa "Fita zanyi amna,am late,ina da alqawari da mutane,banason na saba" ya fada with softness lokacin da amnan ta dage sai ya zauna yayi breakfast dasu,haka ya juya suka fice tare yana lallabata ita kuma tana tuburewa. Baki maimunatu ta tabe,bata taba ganin mutum irinsa ba,idan komai ya faru ma yana iya nuna komai din bai faru ba,shariya ginshira da kuma izza,ita dama bata wani damu yaci din ba,banda amna ta dage ma ba nemansa take ba iyakar zamanta a gidan,sai taci gaba da zamanta a nan tana jiran dawowar 'yar rigima anma suyi break din tare. Ba'a rufa minti uku ba sai ga amnan ta dawo dauke da kwalin sabuwar waya "Ga wayarki inji daddy......sannan yace na hada masa abincin a foldable basket,yau da girkina zashi office" hannu tasa ta amsa wayar ta aje gefe,tana dariyan maganan amna,tunda dai yau ta tayata yanka veggies ta damu kowa da zancan ita tayi girki,sai ta miqe ta shiga kitchen din,ta hada komai a basket din ta riqowa amnan,har zuwa dab da inda motarsa ke kunne yana jiran amnan. Tana hangoshi yadda yake duba agogon dake daure ga tsintsiyar hannunsa,sai ta gyara tsaiwarta sosai,ta kuma tsaya a wajen data tabbatar bazai ganta ba,so take ta qare masa kallo irin wanda bata taba ba tsahon saninta dashi,tanason ta gano dame yafi sauran maza da yake da kwarjini izza da kuma qasaita har haka?,saidai tun batayi nisa da bin qwaqwafin nata ba ta fara ganewa cewa tabbas da bambanci,sai ta lumshe idanunta tana sauraren sautin bugun zuciyarta,ta cikin idanuwanta kuma tana hango wancan lokacin da ya sanya yatsunsa biyar saman fuskarta,ta bude idanunta da hanzari kamar a lokacin abun ya faru,ta saukesu a kansa sanda ya saki wani qasaitaccen miskilin murmushi yana jan kumatun amna bayan ya karba kwandon hannunta. Qaramin tsaki taja tana kauda kanta daga dubansa,haushinsa yana saukar mata,sai ta juya a nutse tana barin wajen,ta tsani duk mutumin dake busa hayaqi qwarai,har batason hada muhalli dashi,batasan ya akayi take manta wannan a kansa ba. Koda ta koma sabgarta taci gaba dayi cikin gidan ita da amna,bata tashi tunawa da wayar ba sai da azahar bayan ta idar da sallah amna tayi bacci, fiddota tayi daga kwalinta ta budeta,sabuwa ce dal,sannan daga gani ba qaramar waya bace,mamaki ya kamata,me ya sami tata wayar?,bata sani ba,iya abinda zata iya tunawa kawai shine sanda wayar ta sulale ta fadi daga hannunta sanda ya tareta ya sanyata a wata iriyar koma. Baki ta tabe ta miqe ta jonata a charge,sannan ta dawo ta kwanta saman kujerar ta buda daya daga cikin novels din afra dake wajenta,wanda batasan ta hado dashi cikin kayanta na makaranta ba,sai yanzu data qarasa zazzage akwatin,don baifi kwanaki goma sha hudu suka rage musu komawa makaranta ba. Guraren qarfe uku da rabi taji ana knocking sassan unaisa,sai ta gyara kwanciyarta bayan ta duna lokaci,taci gaba da karatunta,sosai littafin yake daukar hankalinta,batasan ya akayi ta qulla alaqa me qarfi da films na soyayya da litattafansu ba,zama da madaukin kanwa,afra ta koya mata qarfi da yaji. 59 Ya tadda schedules da yawa a company,don yana shiga kamfanin tun daga first floor PA dinsa ke biye dashi yana lissafo masa,yasan cewa laifinsa ne,tun jiya ya kamata ya buda email dinsa ya duna schedules dinsa na yau amma baiyi hakan ba,hakan kuma baya rasa nasaba da abinda ya faru jiyan,ya kuma tabbata da qyar ya tsallake rijiya da baya "Finally.....you have a trip" dakatawa yayi daga zuba wayoyinsa da yakeyi a muhalli na musamman da aka tanada masa saboda ajjiyesu,ya waiwayo yana dubansa da shanyayyun idanunsan nan dake ma kowa kwarjini "To where?" "the construction work of the estate in lagos should be checked sir" juyowa yayi gaba daya yana dubansa "Did something happen?" "Kamar akwai qorafe qorafe sir....but sir Jabir will explain to you" shuru ya danyi kana ya kada kai "Okay....you can go, I need thirty minutes to get ready before entering the first meeting, tell them,and.....send me Mr. Martin" "Okay sir" ya amsa a ladabce yana juyawa dauke da project planning manual dinsa. Iska ya furzar daga bakinsa yana murza hannayensa guri guda,yana son duk yadda za'ayi ya fita da amna zuwa wani guri da zai zame mata baqo ko na kwana uku ne,He promised her,kuma duk yadda zaiyi baya yadda yayi mata alqawari ya saba mata,bama ita koma waye zaiyi mu'amala dashi,amma kuma yaga alama kamar dama ba zata bashi damar hakan ba,sabbin sabgogi sai danno kai suke,zai yi qoqari ya duba,koda a wannan karon zata kama ya tafi lagos din da ita ne zaiyi wannan qoqarin. Shigowar secretary dinsa ya katse masa tunani,dauk da basket din da shi sam yama manta dashi "Sir,It's your food,you forgot it in the car" duban basket din yayi yana shafa gaban kanshi,daya hannun nasa kuma riqe da biro,kallon saman ido yayi masa yace "Drop it here" a ladabce ya qaraso ya dora masa shi saman table din nasa saidai kuma daga gefe guda,wai ko xaiyi abinda zai dan wanke kansa a wajensa,saboda yasan me laifi ne shi a wajensa,saidai har yanzu baice masa komai ba,shurunsa kuma bashi da sauqi sam a wajensu. Dubansa ya sakeyi,kamar zai magana sai kuma ya shareshi yaci gaba da rubutu akan file din dake gabansa,ya danyi jim yaga ko zaice wani abu amma yaga baibai ta kansa ba,sai ya danyi gyaran murya "Sir,akwai baqi dakeson ganinka...." "Ka gaya musu,yau bazan samu damar ganin kowa ba,tell them in a polite way,they're our client.....don't repeat it again" J ya fada da kakkaurar muryar dake nuna gargadi da kuma jan kunne ba tare da an fito an maka filla filla da laifin da kai kanka kasan ka aikatashi ba. A ladabce ya kada kansa "I will not repeat it sir,am sorry" bai amsa masa ba yaci gaba da aikinsa,shi kuma ya juya ya fita. Files din dake gabansa ya gama dubawa,wadanda zai sakama hannu ya saka musu,ya tattare takaddun da zaiyi amfani dasu sannan ya shige toilet din dake manne cikin office din nasa. Yana fitowa jabir na shigowa office din,kai tsaye kamar kowanne lokaci da bashi da shamaki da shigowar "Good morning" ja'afar ya fada yana sauke hannun rigarsa da yayi rolling up don kada ruwa ya taba "Morning dude,mun tashi lafiya" jabir ya qarasa maganar yana zama saman kujeru guda biyu dake gaban table dinsa "Alhamdulillah....ya jikin madam?" Goshinsa ya murza "To,da sauqi,yau kam ko breakfast ban samu ba,,she can't cook" "Allah ya bada lafiya" ya fada yana dawowa mazauninsa. Hannu ya miqa zai dauka wani file,sai ya ture murfin daya daga cikin warmers din,cikin qanqanin lokaci qamshi ya cika wajen "Wow,wannan fa?,daga ina?" Jabir ya fadi yana leqa warmer din,tambayar ta dan ja hankalin ja'afar,ya daga kai yana kallon abincin shima qamshin na cika qofofin hancinsa,kafin ma yace wani abu jabir ya buda warmers din ya fara serving kansa tare da ja'afar din a different plates,ya kammala ya tura masa gabansa shima yaja nasa. Ko sau daya jabir ya kasa riqe bakinsa daga yabon abincin,da gaske kuma yake,dadin abincin yakai masa ko ina,duk yadda ja'afar yaso basarwa qamshinsa da kuma yadda jabir keta santi akai yasa ya gaza daurewa,sai ya rufe file din,yaja abincin shima ya fara ci. Loma biyu kacal ya yadda da abinda jabir din ke fada,saidai ya dake ne ba tare daya nuna ba "U have a great cooker" jabir yayi furucin yana gyada kai "what is happening with our Lagos contract?" Ja'afar ya kauda wancan maganar ya sako masa wannan,baice komai saboda yadda girkin ke dibansa,ya fiddo wayarsa yayi dan danne danne ya turawa ja'afar gabansa,sai ja'afar din ya bishi da kallo,ya fuskanci sosai yakewa abincin santi,kaman zai magana sai ya fasa,ya dauki wayar yana duba abinda yake son nuna masa. Ya jima yana nazari bayan ya tsaida nashi cin abincin,har jabir ya gama ya wanko hannunsa a toilet ya fito "Da zaka kyautamin yaa J ai da an samin kwano a gidanka kafin my fa'emm ta warware" sai sannan ya dauke idanunsa daga kan wayar,ya watsa masa harara "Lokacin aiki ne wannan,ba zancan family ake ba yallabai" "Magana anan fa ta zama dole,kana samun irin wannan kabakin ya kamata a ga canji a jikinka,kadan aje tumbi haka" "Irinka ne ni da zan kwanta?,so kake wataran ka kasa aikata komai a gad....." Shuru kuma yayi ba tare daya qarasa ba,kaman wanda wuta ta daukewa "A gado ko?,kuma hakane fa dude,ku da yake expert ne ta wannan fannin zaku fimu sanin sirrin farin shiga" jabir ya fada dariya sosai na kubuce masa. Karamin tsaki yaja yana tura masa wayarsa da qarfi gabansa,banda jabir din yayi hanzarin saka hannu ya tareta da babu abinda zai hanata faduwa qasa,har yanzu dariyarsa yake kafin yace "Na duba mana ticket na tafiya lagos jibi in sha Allah" "Hakan yayi" ja'afar ya fada yana miqewa tsaye don shima ya wanke hannun nasa,ya wuce jabir daketa qunshe dariya har yanzu. Sai gab da la'asar sannan ya samu kansa,sanda ya dawo office ya taras da miscall har uku,bai iya biba sai daya dawo daga sallah,yana zaune daman cussion yana dan sauke gajiya yabi bayan kiran. Sosai tayi zurfi cikin tunani lokacin da take kwaba qullin alkubus din data yiwa amna alqawarin yi yau,amna na gefanta tana faman zuba mata surutu kaman yadda ta saba,zaune saman sink daura da tap din dake kitchen. Tabbas fuskar hajiya munubiya ta gani tana fitowa daga sassan unaisa,unaisan na biye da ita,amma duka ba wannan bane yafi tsaya mata ba a rai,maganganun da kunnuwanta suka jiye mata "Duk sharrin ammansa ne d wannan makirar tsohuwar,na gaya miki kiyi da gaske,kiyi kamar kinayi,ki kuma zuba ido sosai,zakiga dukka abubuwan da na gaya miki" me amma ta tsare ma haj munubiyan?,me kuma anni itama ta tsare mata?,meye alaqarta da unaisa da har ta zabi ziyartarta a kebantaccen lokaci irin wannan?,bayan basu jima da haduwa a gida ba?,bama wannan ba duka,ame zata zuba ido?,kwata kwata zuciyarta bata kwanta da zuwan haj munubiya ba,duk da bata ganta ba amma ta fita daga gidan ba tare data nema kowa ba. "Anty moon ana kira,Allah yasa daddy ne" amna ta fada tana tattara hankalinta,ko daya maimunatu bata ma fuskanci wayarta bane saboda sabon ringtone dake kai. Dab da zata tsinke ta daga,saboda sai data tsaya ta dauraye hannunta ta kuma gogeshi "Assalamu alaikumm" yarrr yaji tsigar jikinsa ta tashi,sai ya zame kadan yana sake jingina sosai da kujerar,ya kuma dauke dukka qafafuwansa ya dora kan center table din yayi crossing nasu. Har zata sake maimaita sallamar tata jin shuru,sai tashi muryar ta ratso ta cikin wayar,ta kuma isar da saqo zuwa ga qwaqwalwarta cikin lokaci qarami,har cikin bargonta taji sautin nasa,tsigar jikinta ta zuba itama "Wa'alaikumus salam" ya amsa mata muryarsa can qasa kamar wanda ya tashi a barci,a hankali ta cira wayar daga kunneta ta juya ta miqawa amna,idanunsa na a lumshe muryar amna ta maye gurbin tata muryar da yake sanya ran ji "Daddy i missed you, please daddy ka dawo da wuri,anty moon tana maka favourite dinka,daddy zaka dawo?" Murmushi mara sauti ya kubce mata "In sha Allah amnee" "Thank you dad,daddy pizza please" "Amnaaaa" yadan ja sunanta,da sauri ta tareshi "Please daddy say okay" "Okay" ya amsa mata kamar yadda taso,sai ta shiga murna tana masa godiya. Duk yadda yaso ya daure amma sai ya kasa,hakanan ya samu kansa da cewa "Bata wayar" da sauri kuwa amna ta miqa mata,saita tsare amnan da ido tana son bin ba'asi,murya can qasa da sigar rada tace "Daddy" amsar wayar tayi,kamar zata sanya a kunneta sai kuma ta latse wayar ta ajeta gefe taci gaba da kwabinta,dubanta amna keyi cikin rashin jin dadi kamar zata saki kuka, murmushi maimunatu ta saki,yarinyar ba zata gane ba,matuqar zata ci gaba da jin muryarsa to akwai damuwa,har yau bata fita daga tarkon maganin data shama kanta ba,lallabawa take "Daddy yana aiki,ba'a son a dinga disturbing nasa,ko kinaso yayi ciwon kai?" Da sauri ta girgiza kanta "Okay,budemin ledar can maza a dafawa daddy abinci" sai kuwa ta hau bude mata fararen ledojin,saboda dasu xatayi amfani,cikin ranta tana mamakin tsabar wayo na yarinyar da har ta iya daukan wayarta ta zuba numbers din daddyn nata ta kira,wanda already ta dade da haddace ta. Daga wayar yayi daga kunnensa yana kallo cikin mamaki,yaji sanda yarinyar ta bata wayar,it means kashe masa waya tayi?,sai yaji wani abu ya tsaye masa a rai,karon farko kenan da wata diya mace a duniya ta taba yi masa hakan,ransa ya sosu sosai,ya furzar da iska daga bakinsa "me hakan ke nufi?,ta dauka shi sa'anta ne?,she doesn't know who I am" ya fada yana jin zafi har cikin ransa(a hayye,mai yi ne yau akayi masa,ashe dai babu dadi😝). 60 Cikin mamaki ta sauke idanunta daga fuskar laulo zuwa kan kwanon da laulon yake ajjiyewa a gabanta "Gashi inji innarmu,tana gaisheki,wai kuma tana hanya" maganar laulo ta sake jefata a wani mamakin bayan wanda take ciki,duk da haka yuuma batayi qasa a gwiwa ba ta girgiza kai da dan guntun murmushi saman fuskarta "Haii laulo,yau kuma tuwo ne a idanunka ka mance da dakin daada ka kawo aiken nan?" Kansa ya girgiza "Nan inna tace na kawo,dakinki yuuma" mamakinta sake ninkuwa yayi fiye da dazu "Ni kuma laulo?" Kai ya gyada "Eh ke", kafin ta sake samun damar cewa wani abu yaron ya juya ya five abinsa. Har sai daya baceea ganinta sannan ta dawo da dubanta ga kwanon,lafiyayyen dambu ne daya wadata da kayan zogala da gyada,maida murfin tayi ta rufe kana ta matsar da kwanon gefe cikin tantama,zuciyarta na bata za'aje a dawo. Tasan babu wani abu da ya hadata da innar da har zata nanngo abinci irin wannan ta kawo mata,tabbas laulo shirme yayi,zaya kuma dawo,da wannan tunanin ta tashi ta shiga sabgarta na kula da sanwar abincin daren data dora. Dai dai sanda ta sallame sallar la'asar inna fureran ta kwada sallama a tsakar gidan nasu,gaba gadi ta kuma tako sassan dakin yuuma,ba tar data waiwaya ta kalli sashen daada ba. Sauraren isowarta yuuma tayi,fuskar inna fureran fal fara'a tayi sallama ta danno kai "Anata sallah hajiya yuuma?" Cike da qarin wani mamakin tace "Eh la'asariya ce na idar,maraba furera" ta fada tana ware mata babbar lallausar daddumar dake gefanta,wadda duk cikin siyayyan da anni ke mata ne. Zama inna fureran tayi tana qarewa dakin kallo a fakaice,wannan shine kusan karon farko data shigo dakin a lokaci irin wannan kuma a nutse tayi zaman dirshan, komai na dakin yuuma me kyau ne,batajin kaf rugar tasu za'a samu daki ya nata,babu ko shakka maimunatu nacan a muhallin daya kere wannan din,lallai ko zata samu kudi babu ko tantama a wajenta "Barkanmu da almuru" yuuma ta fada ganin irin kallon da takema dakinta,sai tayi caraf ta amshe "Barka kade yuuma,ina wuninmu?" Gaisawa sukayi,itadai yuuman nata saurare,saboda ta tabbatar ruwa baya tsami banza. Shuru ne ya biyo bayan gaisuwar tasu,sai da yuuma tace "Saiga laulo da dambu yayo batan kai dashi ya kawo dakin nan" bakinta har qeya tace "Kai haba,ba batan kai bane wallahi,dai dai yayo,ke nace ya kawowa" cikin mamaki ta jinjina kai "Ni kuma?,harda wahala haka furera?na tsammaci na daadar himu ne" "Babu komai fa,banda abun yuuma ai mun xama daya,daada?,ai wata kusan tafi kusa,ai yanzu munfi kusanci da ita akan ke" "Gaskiya ne,gashi kuma naga ta fita" "Dama.ba wajenta nazo ba,wajenki nazo mu sada zumunta,tunda jininki ya auri jinina kuma ai yanzu dangi muke ni dake yuuma" inna furera ta fada tana ta gyara zama kamar wadda ke zaune akan qaya "Gaskiya kam" yuuma ta amsa mamaki yana kasheta,kafin ta fita a wannan mamakin kuma sai taji inna furera ta fashe da kuka,cike da wani zallar mamakin da kuma tsoron kada ta qulla mata wani sharrin take kallonta "Toooo.....subhanallahi, meye haka furera?, lafiya?" "Dole nayi kuka yuuma,dole nayi kuka,kusakuren dana tafka wa yarinyar nan maimunatu,kiga yadda ta gujeni,aka dauketa daga wajena aka aurar da ita a wani waje daban,har yanzu bata waiwayeni ba,ni kuma bansan muhallinta ba bare naje na nemi yafiyarta" sai ta kama habar zaninta tahau fece majina. Dariya hade da mamakin furera suka kama yuuma,saidai ta danne kawai taci gaba da kallonta tana cewa "Allah sarki,ai sai a godema Allah da yasa aka gane kuskuren da akayi,alhamdulillahi,Allah ya yafe mana" "Ameena....ameena" ta shiga amsawa tana sharce hawaye,wanda kusan hawayennata dukka akan naggenta da suka dinga mutuwa ne,asarar data tafka. Sai data gama dukka koke kokenta ta miqe zata tafi sannan tace "Umm....nace ba,ai sai a bani kwatancen gidan nata,can inda take a gomben ko?,sai a leqa aga dakin nata,a kuma nemi yafiya,bai kamata a matsayina na uwar riqonta ba kuma ya zamana bansan inda mazauninta yake ba" "Tooo....anzo wajen" yuuma ta fada,ta shafa addu'ar da takeyi sannan tace "Yanzu kam bana ce miki ga inda muhallin maimunatu yake ba,tunda ba zuwa nayi ba ko sanda ake bikin,ban samu na leqa ba" gaban inna furera ya fadi,har yanayin fuskarta yadan sauya "To,ikon Allah,to kuma su can gidan surukan nata fa?" Kai yuuma ta sake girgizawa "Shima bana ce ba,tunda nafi shekara rabona da garin gombe,sannan koda can ma kinsan ba ni nake kai kaina ba,yafendo ke aikomin da mota ta daukeni daga nan qofar gidan zuwan wancan" shuru furera tayi,ga qoshi ga kuma kwanan yunwa,yanzu ya kenan?. "To ai inaga ta zo da sauqi ko,me zai hana ki waya da ita ki gaya mata surukarsu nason ganin dakin diyarta,idan yaso nima basai motar tazo ta daukeni ba?". Binta da kallo yuuma tayi galala,sai kuma ta gyada kai "Haba furera,dama dai na tashi zuwa ne" "Zan iya jiran tafiyar taki indai ba zatayi tsaho ba" "Allah ya bamu aron rai" ta amsa mata a taqaice,sabida takaicinta daya fara kama yuuma,murna ta cika inna furera "To alhmdlh,don Allah a qoqarta muje anan kusa yuuma,na gode Allah ya qara zumunci" ta fita tana zabga mata addu'a tare da hango nesa a kusa,duk daba haka taso ba,so tayi gobe ko jibi ta dage. A tsakar gida sukayi kacibus da daada,sai tabi fureran da kallo cike da mamakin abinda tazoyi gidan,harara suka zabgawa juna,inna furera tayi gaba tana yada habaici "A hayye na gaba kam ai yayi gaba,na baya ko tsintar hula ba zaiyi ba,yo mu da muke jinin sa'a da nasara,haihuwa me rana,ta jefa mu gidan arziqi,ai an rabu ne kuma ba'a rabu ba,yuuma gidan karamci" sak daada tayi tana duban dakin yuuma,ta sani cewa yuuman ba munafuka bace,da sai tace wani abun suke qullawa,hakanan ta san yuuman bata daukar raini ko cin kashi bare tace zata je tayi mata tatas kan ganin furera da tayi cikin gidan,amma duk da haka sai ta kasa daurewa,ta ajjiye faifan dake hannunta ta nufi dakin yuuma. Yuuman na tsaka da nade abun sallah daadan ta shigo,ta daga kai ta dubeta "Mamaki nake yuuma da ganin fitowar furera a dakinki,me tazo yi?" Tambayar sai ta bata mamaki da haushi,salon yadda tazo mata da maganar mai kama da titsiye "Kunfi kusa ai,nima tare na ganku,sai kije ki tambayeta ai" daga haka taci gaba da aikinta,shuru daada tayi,don bata da sauran ta cewa,sai kuma ta juya ta fice daga dakin sukuku,yuuma taja qaramin tsaki,sun dauka ita din sakarai ce da zata biyewa shirmensu daga ita har fureran?,kallonsu kawai takeyi amma tasan halin kowa. A hanya fureran keta sumbatu ita kadai,Allah yasa dai kada yuuma taja mata lokaci ko kuma taqi zuwa da ita "Idanma taqi idanuna zan murje na tafi gembu,nayi musu kwance kwance har sai na samo kwatancen gidan,don ko da tsiya koda arziqi saina fanshe wahalata,ato" da wannan tunanin ta koma gida hankalinta kwance. ********Tunda hajiya munubiya ta tafi take ta juya maganganun da sukayi da ita,ranta ke mata wani irin ciwo da suya,sadakarta aka bayar shine abu mafi ciwo da qona rai a wajenta,musamman da hajiya munubiyan ta gaya mata dukka familyn dr khalid akko kallon da suke mata kenan,zuwa yanzun ta soma gasgata cewa amma da anni basa qaunarta,don ta lura da wani kulawa da soyayya ta musamman da suke nunawa maimunatun tun zuwan da sukayi a shekaran jiya,sannan abubuwan da suka afkun da yadda aka turata kitchen hado masa abinci maimunatu na zaune, bayan itace qasanta,ta fita daraja ta fita mulki da kudi,babu ko tantama akwai abinda aka kitsa a shigarta kafin ta fito "Bari na baki wani sirri guda daya,kinga wannan mijin naku,a gabanmu ya tashi,babu wani hali da dabi'arsa da bamu sani ba,bari kiji,indai kinaso ki tsira da mutunci da martabar ki,to karki ragawa kowa,ki tsaya a tsayenki sosai,ki nunawa kowa ke din daga madaukakin gida kika fito,shi kuma ja'afar,kada ki yarda ki bada kanki ta sauqi,mutum ne shi da ya tsani yaga ana nuna masa soyayya,ke ko matarsa data mutu wadda ya kusa zama mahaukaci a kanta ko nace yama zama.....don duka yake wani lokaci harda cizo idan ciwon ya motsa masa....." tsoron da unaisa bata taba jinsa ba yanzu ya darsu a ranta,zancan da aketa fada wai wai yau sai gashi daga bakin matar qanin babansa "Eh....Allah dai ya kiyayeku kawai ya tsare kada wata warana ya illataku.....ina gaya miki,ita kanta baqar wahala tasha a wajensa saboda nuna masa soyayya da tayi,to ki watsar dashi,kija girma da mutuncinki,ina gaya miki idan na rantse ko kaffara banyi,idan ya fahimci kedin babbace kuma me aji,da kansa zakiga yana shanshanarki,a nan zaki murza zarenki yadda kikeso" sanda ta yima anty talatu wannan bayanin cewa tayi "Ban yarda da maganganun matar nan ba" "Saboda me anty?,don me zata zo ta gayan qarya ko ta shiryamin zance?,bayan suna da alaqa dashi?,ita ba kishiyar babarsa ba bare nace qiyayya da kishi ya sanyata aikata haka ba,sannan ba mai jini a jiki bace bare nace sonshi take take shiryan gadar zare,hasalima 'yarta daya kuma an sanya ranar aurenta,saura watanni biyu bikinta,bamu taba gamuwa ba sai ranar dana kai qararshi gaban anni, gida zata tafi amma saboda ni ta tsaya,da qyar ma nayi convincing dinta tazo gidana mukai wadan nan maganganun" wannan hasashen na unaisa ya sanya anty talatun itama hankalinta ya karkata "Kuma gaskiya kika fadi,mu jarraba mu gani din". Ajiyar zuciya ta sauke tana komawa inda ta tashi dazun ta zauna,tana lissafa adadin kwanaki ko watanni idanma ta kama shekarar da zatayi kafin ja'afar yazo hannunta,tabbas zata tsaya akan kowa har sai sun fahimci girma da martabarta,amma batajin zata iya daukewa ja'afar qafa,babu tabbas. 61 Tunda suka gama komai ta sake wanka ta kuma gyara amna,ta shirya ta cikin wani Three quater mai kyau da shirt dinsa,itama ta shirya kanta,abinci ta zuba musu amma amna tace sam ita sai daddy ya dawo,duk yadda ta lallabata amma amnan taqici,yau kam kwanciya takeso tayi,tanason ta kalla qarasa kallon dramas dinta,idan da sauran lokaci ta duba karatuttukanta,bata son ma su hadu dashi kwata kwata,tana tunawa da abinda ya faru jiya,ji take kamar ta maido lokacin ta goge dukkan abinda ya farun. Daki suka koma duka ita da amnan,saidai lokaci bayan lokaci tana zancan rashin shogowarsa,daga qarshe dole tasa maimunatu ta bude mata qofa ta tafi dubashi. Yafi awa da shigowa cikin gidan amma ba wanda ya sani,sabida tarin ayyukan da yakeso.ya hattama,bayason barinsu su zame masa kaya,ga tafiyar dake gabansa jibi,wadda yake saka ran sai ya huta sosai kafin ya dawo din. Idanunsa ya dauke daga kan system din yana duban amanan,gaba daya yarinyar ta narke fuskarta tana dubansa,sai ya sakar mata murmushi,yana jin dadi har qasan ransa,shigar tayi mata kyau,kuma ko ba'a gaya masa ba alamu sun nuna tana samun kulawa tare da jin dadin zaman gidan,kafin tace komai ya hade hannayensa waje guda "Am sorry angel" dole ta saki dariya,ta tako da gudu ta fada jikinsa tana dariya,gefansa ta zauna tana qorafin dai "I say sorry ko?" Ya tuna mata yana dubanta,dariya tayi tana tura kai lallai sai ta karanta abinda yake rubutawa a fuskar system din "Daddy ka ajjiye don Allah muci abinci" sosai yaji dadin tayin data masa,don yunwa yakeji,ya kuma yo takeaway amma ya gaza ji,sai tattarashi yayi ya ajjiye,saboda kwata kwata taste din bai masa dadi ba,har yanzu taste din breakfast din safe yana jinsa akan harshensa,wannan yasa ya kasa jin dadin kome,amma kuma baison yarinyar ta fahimta haka,bayason raini,saidai kafin ya sake kowanne tunani amna tayi caraf da hannunsa,ta kuma riqeshi gam,babu damar ci gaba da aiki,dole yabar komai ya miqe yabi bayanta tana gaba janye da hannunsa. Yankewa tayi kawai ta fara karatun bayan shigarta daki kada bacci ya dauketa bata karanta komai ba,har ta zauna sai kuma taji sha:awan shan gwanda,don haka ta miqe tayo kitchen,ta dudduba freezern gaba daya babu ita,da alama ta qare kenan,dama kuma last hisham ne ya siya ya bayar a kawo mata,ranta babu dadi ta rufe freezer din ta dawo daki,sai ta yanke kawai ta kirashi ta roqeshi ko zata samu wata,tana matuqar sonta. A bakin qofar dakin amna ta sake masa hannu "Daddy ka kirawo anty moon,yau tayi aiki sosai,zan dauko mana spoons da plates kafin ku qaraso,na iya zaka gani,anty moon ta koyamin" sai ta juya da hanzari ta bar wajen cikin zumudi ba tare data tsaya sauraren me zaice ba. Da kallo ya bita har ta bacema ganinsa,baisan wanne irin qauna bace tsakaninta da ita ba,yana ganin zumudi sosai a fuskarta da farinciki duk sanda zasuci abinci tare,kansa ya girgiza yana sakin qaramin murmushi a fuskarsa sannan ya maida kansa ga qofar dakin. Gaba ya matsa kadan ya dora hannunsa akan handle,sai a sannan ya tuna da abinda tayi masa dazun,hakan yasa ya qara hade fuskarsa,sannan ya murza qofar a hankali ya tura qofar dakin. Tsaye take a gaban gadonta inda litattafanta suke ajjye,ta bawa qofa baya,sanye da farin high waisted skinny leggings da baqar armless robber shirt,gashinta data daure da siririn band mara fadi yana ta reto a bayanta,kanta babu dankwali,hannunta riqe a qugunta,ta kara wayar tata a kunnenta "Ya hisham don Allah,Allah yasa ban takura ka ba" ta fada cikin karyar da murya,saboda batason matsanta masa da gasken,don dai batasan wanda zata kira din bane sai shi "Kada ki damu matar yaaya,za'a kawo in sha Allah" "Na gode sosai ya hisham,you are such a kind person" fusgar wayar da akayi da wani irin zafin nama yasa bata samu daman jin me hisham ya fada ba,sosai ta tsorata ta kuma juyo a razane,don ko kusa ko alama bataji shigowar mutum ba. Dab da bayanta yake a tsaye,abinda yasanya ta kusa fadawa jikinsa kenan sanda ta juyo din,cikin sauri ta zare idanunta daga nasa,saboda wani kallo da yake mata,wani irin abu ne ke gilmawa cikin idanuwansa,yayin da qirjinsa ya cika da wani irin qunci fushi da kuma bacin rai,abinda ya sanya launin qwayar idanunsa canzawa kenan cikin qanqanin lokaci. Taku biyu ya qara ya kawar da dukka tazarar dake tsakaninsu,fuskarta ta sauka tsakiyar qirjinsa saboda yadda ya bata tazara wajen tsaho,yayin da shi kuma habarsa ta sauka a tsakiyar sassalkan gashinta,da sauri tayi taku biyu baya saboda sake bata ratar daya hade a tsakaninsu,bata sauke diddigenta a qasa ba ya maara mata baya,sake jaa tayi da baya ya sake maida qafarshi inda ta sauke,bata gushe ba tana matsawa yana binta har ta qure da bangon dakin. Idanuwanta dake cike fal da tsoro ta daga ta kalleshi,sai taji tsoronta ya ninka na baya,fushin data hanga saman fuskarsa da yadda idanuwansa suka sauya ya sake tsoratata,ci gaba yayi da aza mata kallonsa yana kuma sake hade gap din dake tsakaninsu,dab da ita ya tsaya ya daga hannunsa, abinda ya sanya maimunatu qanqamshe hannayenta tana jiran jin saukar duka ko mari,duk da batasan ainihin laifin data masa ba,amma wani sashe zuciyarta na gaya mata kashe masa wayan da kikayi daxu,ba abinda zuciyarta ke hasaso mata sai irin marin data taba karba daga wajensa shekarun baya da suka shude,da qyar idan yau ba za'a maimaita ba. A hankali ya sauke hannuwan nasa yana morewa kallon fuskarta dake cike da tsoro,duk da idanuwanta a kulle suke amma hakan bai hana kyanta fita ba, siraran jajayen lips dinta nata motsi,koda ba'a gaya maka ba kasan kuka take shirin saki,bai gama wannan tunanin ba kuwa hawaye suka ratso rufaffen idanunta,bin hawayen yayi da kallo,sai yaja baya a hankali,ta gama karya lagonsa,baisan dalili ba bai kuma san me yasa ta shiga sahun mutanen da hawayensu ke saurin karya shi ba,ba abinda wannan ya tuna masa sai shekarun baya sanda ya mari marainiyar fuskarta,abinda ya tsaye masa a rai tun a wancan lokacin fiye da komai,zuciyarsa yaji tayi laushi,amma kuma bacin ran dake can qasan ransa har yanzu yana motsawa. Daga hannunsa yayi yana kallon wayar da ya qwace din,number hisham din ce,sai ya danneta ya shiga wajen block yayi blocking nasa sannan yayi deleting number kwata kwata daga kan wayar,bai tsaya a nan ba ya sake shiga contact nata,numbers din dake kai ba masu yawa bane,duka duka na 'yan gidansu ne sai na wasu mutum hudu afrah besty teema ummu,numbers dinsa ya saka ya shiga wajen kira,number batayi appearing ba,alamu dake nuna cewa kenan bata da number dinsa?,yaja qaramin tsaki can tsakiyan ransa,sai ya samu kansa da yi mata saving number,ya kuma sanya mata full name dinsa _*ja'afar marwan akko*_,ya daga kansa a nutse ya sauke a kanta,tana tsaye manne da bango kamar zai tsage ta shige,fuskarta duk danshin hawaye,sauka idanunsa sukayi saman qirjinta wanda shape dinsa ya fita sosai saboda robbern da rigar ke dashi,komai a zaune das sun kuma cika rigar,sai sama da qasa qirjinta yake alamun tsoro da kuma bugawar zuciya. Yana son ya tsaida ganinsa a nan amma ya kasa,sai ya samu kansa da zarto da kallonsa zuwa faffadan qugunta,cinyoyinta sun fita sosai kamar babu ma wando a jikinta sai fatar jikin nata kawai kasancewar leggins din skinny ne ya zauna mata yadda ya kamata,zaka tsammaci ciko tayi musu don sun fita yadda ya kamata,kai kace zana mata qugun zuwa cinyoyinta akai "Allah...." Ya fada can qasan ransa tsigar jikinsa tana tashi,wani irin mahaukacin kishinta karo na farko ya sauko ya lullubeshi,karon farko da tunanin yaya uniform din makarantarsu yake ya taso masa?,wando ne?,ko kuwa doguwar riga ce?,wanne irin kaya take sanyawa a matsayin house wear?,hannunsa ya dunqule ya kuma yarfar,ya cije lips nasa na qasa ransa na masa suya,shi kansa ya yadda dari bisa dari yana da tsananin kishi,bashi da sassuci ta bagarori da dama,amma tasha yi masa fada ya dinga sassautawa "Open your eyes" ya fada da wata tattausar murya da maimunatu bata taba tsammani ba,cikin kokwanto ta soma bude idanun nata a hankali,tana gama budesun sabbin hawaye suna sake wanke mata fuska "Ya salam" ya fada a boye yana jin yadda zuciyarsa ta wani irin harbawa ganin yadda ta narke gaba daya tana sauke sabon kuka,rarrabuwa hankalinsa yayi,baya son kukan,amma kuma baisan ta yadda zai rarrasheta ko ya tsaidata ba "Keep quiet" yafada da kakkausar murya,tsai da kukan tayi cak tana qanqame jikinta waje guda,sosai ya hade fuskarsa "Waya baki izinin yin waya da wani?" A mamakance ta dago kai ta kalleshi,duk da taso tsirashi da ido yadda yake mata amma sai ta gaza,tadan kauda idanun nata dake cike da lema,hisham dinne wani?,ta tsammaci ya duba yaga waye tunda ya karba wayar a hannunsa ai "Don't let me repeat my question....." Ya fada yana jin siqewa a ransa,wani sashe na zuciyarsa kuma najin damuwa da zubar da hawayenta keyi amma kuna yana danne hakan,sai data kauda kanta gefe,cikin muryar kuka tace "Yaa hisham ne" "who is hisham?" Ya fada yana goye hannayensa a bayansa,har yanzu bai rabu da kallon baby face dinta ba,dan daburcewa tayi,saboda bata fahimci inda tambayar tasa ta dosa ba,duk da haka tayi dauriyar cewa "Yaa Hisham dai....." "Ba hisham qanina ba,koda ciki daya kuka fito dashi na sake ganin kuna waya sai nayi matuqar saaba miki?,kin fahimta?" Kai ta daga masa sabbin hawaye na fito mata,shuru yayi yaci gaba da kallon ta,haka kawai yaji baiso tsaiwar tasu ta yanke,kallon fuskarta kuma kamar yana qarawa lokaci gudu ne,tare da sanya wucewarsa nan da nan "Me yasa kika kashemin waya dazu?,ni sa'anki ne?" Kamar zata kalleshi sai ta fasa,saboda yadda gaba daya ya dafa mata jiki da kallonsa,takejin kamar ba zata iya ci gaba da tsaiwa ba,zuciyarta kuma tayi raunin da bazata iya ci gaba da amsa tuhume tuhumensa ba,sai kawai ta soma sulalewa a wajen tana sakar masa kuka. Baisan ya isa inda take ba sai da ya ganshi tsaye a kanta,ya duqa a hankali sai kuma amna ta turo qofan dakin da murnarta,turus tayi jin kamar sautin kuka,sauri ta qaro ta iso gaban maimunatu dake duqe a wajen ja'afar na tsaye "Daddy kuka?,kaine ka sata kuka" Amna ta fada tana durqusawa a gaban maimunatu itama kamae zata fashe masa da kukan,rasa wacce amsa zai bawa yarinyar,ta fara qoqarin son dago kan maimunatu abinda yakeson yi kenan tun dazun,tambayarta take "Anty moon,daddy ne?" Kai ta girgiza mata alamar a'ah,sai ta sake dagowa tana dubansa "Daddy ka bata haquri.....ko zatayi shuru" wannan fa shi ake kira qaqa qara qaqa,sai ya debe hannuwansa zuwa aljihun rigarsa ya boyesu a ciki kamar baison wani ya gansu,a hankali labbansa suka motsa "Am sorry" maganar ta fita da wani irin taushi da kuma qaramin sauti,sai ya juya a hankali yana barin dakin,amma kunnuwansa na ciki har sai daya fice. 62 Har suka gama cin abincin bata sake ba,tana ta juya cokali cikin abincin,har yanzu fuskarta babu cikakkiyat walwala,hakan yasa amna ta kasa sakewa. Yatsun hannayensa ya hade guri guda yana duban amnan,ya tabbatar albishir din da zaiyi mata a yanzun zai sanyata ta ware "Are you ready?" Kusan tare suka daga kai,saidai ita maimunatu ta basar kamar hankalinta bai wajen "For what daddy?" Ta tambaya with full excitement tana kallonsa kamar wata babba yadda ta tambaya din,hannunsa ya sanya a aljihun rigarsa ya fidda ticket ya nuna mata "Trip to Lagos" ihun murna ta saki harda miqewa tsaye,yadda ya zata din kuwa haka ne,nan da nan ta sake,ta fara zayyano masa ina da ina zasuje,yana zaune yana kallonta kawai,duk sai data gama murnar sannan ta zauna tana fadin "Daddy,ins ticket din anty moon" shuru yayi, yarinyar ta iya tambayar qure,baisan me zaice mata ba,a hankali ya saci kallon maimunatu wadda har yanzu bata bar jagula abincin ba,kamar ma bata wajen,don fuskanta baiyi kama da wadda taji abinda amna ta fada ba,tunda ta taya amna murna ta kame kanta. Da idanu ya yima yarinyar sign na ta tambayeta hadi da dauke kansa ya azasu bisa wayarsa,amma kunnuwansa suna saurarensu "Anty moon.....zaki bimu nida daddy ko?,zai kaimu yawo sosai,zamuje har kifs beach garden,qawata tana ban labari suna zuwa ita da dad dinta duk sanda suka je". Qaramin murmushi mara sauti tayi,tadan dafa kan amna "A'ah amna......saura kwanaki mu koma school,banason nayi missing komawata makaranta" haka kawai yaji amsar tata wani iri,bai zaci zata ce hakan ba,amma sai ya basar yana miqewa daga wajen sanda amna ta soma magiyar ta bisun,da taga kuma ya tashi sai tayo wajensa,wai wayowa yayi,ya dora hannunsa saman kanta ya tofa mata addu'a sannan yace "Ki kwanta anan amnee,ina da aiki da yawa da nakeso na gama kafin mu wuce" da yake cikin murna take sai batayi wani rigima ba ta yaddan,ya juya yana barin falon,yayi hakanne don baison ya sake shiga dakinta kada wani abun ya sake giftawa da zai hanashi cikakken bacci,don jiyan da qyar ya qwaci kansa. Yana fita ta miqe tana gyara gurin,tayi mamaki sosai da yawan abincin da taga yaci,don kusan rabinsa shi ya cinye,tana aikin amna na sake mata magiya,sai data bar komai ta kama hannunta ta sanya cikin nata "Kinaso a kori antynki daga school?" Kai ta girgiza da sauri "Good girl,to kinga indai bakison hakan,dole na koma makaranta da wuri,next time sai muje tare" "U promised?" Kai ta gyada,duk da bata da tabbaci tasan ta amsa ne kawai,amma kuma bata da mafitar data wuce ta amsa din. Washegari gaba daya bai zauna a gida ba,ita kanta amna din bata ganshi ba kwata kwata,su biyu suka wuni,wannan ya sanya koda dare bata yi wani wahalar abinci ba,sai tayi musu jallop na taliya kawai wadda aka wadata da veggies,bayan sallar isha'i kadan amnan tayi bacci saman qafafun maimunatu suna tsaka da kallon wani film,sai falon yayi shuru saura ita kadai. Shirye shiryen tafiyar shine ya tsaidashi yau a waje,bai dawo cikin gidan ba sai qarfe tara da mintina ashirin har da doriya na dare,har ya gota sassan unaisa sai ya dawo da baya,yayi knocking qofar,minti kusan daya sannan aka bude qofar. Cikin matuqar girmamawa ta xube a qas tana gaidashi,daya daga cikin masu aikinta ne,masu aikin da ba'a nema izninsa ba kafin zuwansu gidan,abinda yasa ua dauke wuta kaman baisan da xamansu ba,ita kanta unaisan ba wani tunawa yake da lamarinta sosai ba bare wadanda ta ajjiye,komawa baya tayi ta lafe sanda yake shigowa,yana gama shigowa tayi wuf ta fita a sashen. Zaune take saman three sitter dinta,tana sanye da doguwar rigar atamfa,sai dankwalin kayan dake aje a gefe,kanta dake cike da gashin doki da aka yiwa kitso tamkar nata yana a bude,ta miqe qafafuwanta tana kadasu,hannunta dafe da wayarta da alama chart takeyi,gefanta teburin glasa ne dake hargitse da ragoyin abinci gorar ruwa data lemo dukka da tasha. Sosai tayi mamakin ganinsa a sassan nata,karo na farko kenan tsahon zamanta a gidan,duk yadda taso ta danne farinciki da mamakinta amma sun gaza boyuwa,tana daga zaunen tace masa "Bismillah ga waje....." Ta datsi maganar tare da qwallawa dayan ne aikin nata dake cikin bedroom dinta tana gyaro mata shi kira,sai gata jiki na rawa,ta zube itama tana gaidashi,da hannu kawai ya amsa mata ba tare da ya dubi sashen ta ba "Ki hado masa abinci da abun sha" ta bata umarni kai tsaye,sai ta miqe da hanzari ta fice,cikin zuciyarsa yake jin qyanqyamin maganarta,yar aiki?,ta kawo masa abinci da abin sha?,definitely batasan shi ba,batasan komai a kansa ba,ta yaya zai fara tsara zama da irin wannan?. Daga kai tayi ta dubeshi still yana tsaye hannayensa saye a aljihunsa "Have a seat" ta sake maimaitawa,tana jin wani dadi da izza tana shigarta,ko har ta fara cikin nasara ne ya biyota da kansa?,indai ko hakane lallai zata nutsu ta yanka qa'idojinta da sharudda wanda zasu dace da rayuwarta ba matsi balle takura. Baice mata komai ba,yafidda hannuwansa daga aljihu tare da daurin kudi sabbi ya matsa gaba kadan ya ajjiye mata su "I don't have your account digits....zan xanyi tafi....so koda zaki buqaci wani abu" sai ya ciro dan qaramin qawataccen complimentary card dinsa milk da aka yiwa ado da zaiba ya aje mata "You can contact me" dauke idanunta tayi daga kan card din ta mayar fuskarsa,wani abu na mata yawo a zuciya,wannan tafiyar da yake fadin zaiyi a qa'ida ace da ita zai tafin,amma sai wani girman kai ya taso mata,meye nata na damuwa ko nuna zakwadin tafiya?,bayan sun zagaya duniya da kyau,kudi sosai daddynta ke fitar musu duk sanda suke son su fita wata qasar,kada ma tayi magana ya rainata yaga kamar so take yaje da ita ne, shikenan sai ta amsa tayin da haj Aaya tayi mata na zuwa inda itama kafin sun dawo,don haka ta koma ta jingina da kujerar tana cewa "Allah ya kiyaye hanya" labbansa kawai ya motsa alamun amsawa,sannan ya juya yana ficewa daga sashen hadi da bar mata qamshin turarensa. Ajiyar zuciya ta sauke sanda ya ida ficewar,ta lumshe idanu tana zuqar daddadan qamshin nasa,ashe yadda take hangensa da tsada daga nesa yafi haka wuyar samu ma daga kusa?,amma dai ko yaya ne ita ba zata sake bada kanta ba,zata ci gaba da amfani da girma da martabarta,har sai ya fahimta ya kuma kawo kanshi. *******Tun da ta farka da safen amna ta kasa komawa barci,wai batason tayi barci daddy ya tafi ya barta,tunda yace flight din safe ne zasu bi, maimunatu nata mata dariya tana kuma shirya mata kayanta,dai dai da yadda tace haka daddy yake shirya musu idan zasuyi tafiya,ba wasu kaya masu yawa ba masu.kuhimmanci kawai ake dauka,sauran abinda basu da,yafi ganewa ya siya musu a can. K'arfe tara da minti ashirin ta kammala komai harda break fast dinsu,ita dince kawai.batayi wanka ba,tun jiya bata ganshi ba,tana daki dai ya shigo sunyi magana da amna,kafin ta fito sun gama ya fita,kamar ta shareshi amma sai taga bai kamata ba,kodon diyarsa dake qaunarta,don haka ta dauki kwando ta shirya komai dai dai da yadda amnan zata iya dauka "Muje na rakaki ki kaiwa daddy" daman zaman jira take,ta kuwa sauko da saurinta,maimunatu ta dauki kwandon suka fito tana tsokanar amna,kada dai ace daddy ya tafi ya barta,ta qyalqyale da dariya "Daddy baya fadin alqawari fa ya saba anty" kai ya jinjina tana murmushin yadda yarinyar tasan halin mahaifinta,duk da shekarunta basufi hudu ba. Daga second matattakala ta biyu ta tsaya ta miqa mata kwandon,sai ta tsaya tana duban amnan tana ci gaba da haurawa har takai qarshe sannan ta sauke idanunta daga kanta tana juyowa don barin wajen taje ta qarasa abinda batayi ba. Waiwayowar da zatayi suka hada ido ta ita,sanye take cikin wanu straight leg trousers da shirt spaghetti hand,siriryar silver chain ne a wuyanta da qaramin dan kunne barima, qafarta high hill ne,fuskarta ta wadata da makeup sosai. Kallon kallo suka yiwa junansu,sa'annan unaisan ta zarce da yima maimunatu kallon qurilla daga sama har qasa. Wasu soft nigh gown ne a jikinta farare tas tas kamar ba dasu ta kwana ba, gashinta mai laushi da santsi nannade cikin wata hula me zubin shower cap,kwantacciyar qananun sumarta ta gaban goshinta zuwa qeya dukka ta fito ta sake qawata fuskarta kamar ba daga bacci ta tashi ba,jikinta na fidda qamshin turaren baccinta data jima da warewa musamman saboda bacci kamar yadda afra ta koya mata,fararen santala santala hannunta dukka a waje suke saboda yanayin hannun rigar dan qarami ne sosai, tsintsiyar hannunta cike suke da duwatsuntan nan asalin wadanda ta gada daga daadarta,ko sau daha bata taba sha'awaf ciresu daga hannunta ba,sai suka kuma sake mata kyau suka haske farar fatarta dake luwai luwai fes kuma jajir da ita,kullum duwatsun kamar sake gogesu akeyi saboda sheqin da sukeyi,qafarta wani farin slippers ne mai taushi da aka yiwa wani adon gashi gashi daga sama. Da qyar unaisa ta hadiye wani abu me tauri,haushi sosai ya cikata ganin yadda maimunatun tayi gaggawar dauke idanunta daga kanta tayi gaba kamar batasan wacece ita din ba. "Agwai" ta kirayeta da sunan da tasan zai bata ranta,sai tayi kamar bata jita ba ta sakeyin gaba "Hey dake nake magana" nan ma shuru,taci gaba da takawa zuwa sassanta,zuciya ta ingiza unaisan,sai tayi saurin takawa ta kuwa sha gabanta "Don baki da kunya kina ji ina miki magana?,wato kin samu sake saboda kina zaton kin hada miji dani ko?,mijin da kike hoto a wajensa?,ba kowan kowa bace ke illa 'yar qauye mazauniyar riga,ki kiyayeni wallah,bakisan wacece unaisa ba,diya ga ministern ilimi" wani kallo maimunatu ta watsa mata,karon farko tun zuwanta gombe da taji wani ya bata mata rai,har ran nata ya sosu har haka "Duk da nike bafulatana amma ban taba daukar tallan nono ba har kawo rana irin ta yau,kiwo kuwa wannan ado ne ga dukka cikakken bafulatani,koda ma ace nayi tallan nono ai ba aibu bane ba kuma gazawa bace,saboda dan halak baya manta tushe,tushiya kuwa masomin dukka wata daawa ce da tayi tsiro ta fito al'umma ke kallonta......" Daga wannan ta kewaye unaisa ta qarasa shigewa falonta ta kuma rufe qofar ta abinta,take unaisa ta sake hasala,sai ta juya zuwa stairs din ja:afar,sai kuma ta sake ja ta tsaya,idan ta hau tace masa me?,kada mutuncin ta ya zube a idanunsa,bari,zatayi dealing da yarinyar a cikin gidan da kanta,dole tayi.laushi,kuma dole tayi mata biyayya,badai tafiya zaya yi ya barsu ba su biyun a gidan ba?. 63 Ta ja tsaki ya kusa sau goma sanda ta koma sassan nata,batasan abunda yasa abinda unaisa tayi matan yayi mata zafi sosai a ranta ba,bedroom dinta ta fara qoqarin gyarawa,sai ga amna ta turo qofa ta shigo,ta waiwayo tana dubanta,sai taga ran yarinyar a hade tana tura baki "Lafiya amnee?" "Waccan antyn mana,wai don ta kirani banje ba shine ta harareni" sakin duvet din da take take ninkewa tayi ta kama hannunta "Manta kawai,ke da zaku tafi da daddy,kullum kuna tare?,me zai dameki" murmushi ta sauke "Yauwa yace kizo" sakin hannun amnan tayi, kamar zata ce wani abu sai kuma ta fasa,batason wasu abubuwan su dinga faruwa gaban idanun yarinyar,yarinya ce mai wayo sosai,akwai abubuwan da ba zata manta dasu ba idan suka farun. Closet dinta ta bude ta ciro madaidaicin blue black din hijab ta zira ba tare da ta fidda hular kanta ba,ta kama hannun amnan suka fito. Suna fitowa ta hangi unaisan a zaune,ta dora qafa daya kan daya tana girgiza su,da biyu tayi wannan zaman,tanason ta sanya idanu a gidan game da takun kowa,gefanta breakfast dinta ne da bayin nata suka yi suka kuma jere mata. Mummunar faduwa gabanta yayi sanda taga maimunatu ta kama stairs din tana hawa,suna hira kuma tartar da amna abinsu,miqewa tsaye tayi,tayi kamar zata bisu take wata zuciyarta ta tsawatar mata "Karkiyi,ba girmanki bane" sai ta koma da baya a hankali ta zauna, zuciyarta na mata wani irin suya,dole yarinyar ta samu zarrar tsayawa ta maida mata magana,tunda har ta samu darajar hawa sassan ja'afar din,kai tsaye har haka?,ja'afar fa?,tasan ba qaramin abu bane mai sauqi ace ka samu irin wannan damar daga gareshi,damar data dade tana nemanta,wataqil ma sunsan juna sani irin na ma'aurata "Kai qarya ne,ba zata taba iya dauke wannan qaton ba,duka duka nawa take?,yaushe qashinta yayi qwari,ni na razana na janye bare ita?" Wannan tunanin ya rage mata tashin hankalin data shiga,sai ta koma ta zauna tana jiran taga saukowarsu. A bakin dining ta sameshi a tsaye,da alama shima ya gama dukka shirinsa,shirt da trouser ne a jikinsa na kamfanin armani,sai qafarsa dake saye cikin wani rufaffen takalmi na fata slip on,me wani irin qawataccen ado,batasan yadda kayan maza suke ba,amma ita kanta takalmin ya tafi da ita,kayan sun dace dashi sosai,sun kuma fitar da qirar sa sosai wadda suit ke yawan boyewa,kana dubansa zakasan yana shiga gym sosai,short sleeve shirt din ta bayyana baiwar gargasar dake dukka hannuwansa masu tarin yawa. Da ita dashi dukka tare suka dauke kansu,dukkansu suna basarwa,saidai cikin jikinsa yaji wani abu ya tsarga masa,baisan ko baiwa bace,ko ta musamman ce a cikin mata?,duk sanda tatashi a barci sai fuskarta tayi wani fresh,idanuwanta suke garai garai su kuma fito ba. Cikin kayan abincin data kawo masa ne yake shan tea,ta tako a hankali tana basarwa,qamshin turarensa daya cika falon yana kada mata hankali "Ina kwana?" Ta fada da muryarta da ko da yaushe take tuna masa da mafarkinsa,ko a yanzun ma sai daya ji tsigar jikinsa ta tashi "Kin manta da qa'idata kenan?" Ya fada yana dire cup din hannunsa saman table din,hadi da qoqarin zaro wayarsa da tayi qara na alamun shigowar saqo,kai ta daga kadan ta dubeshi sanda yake kallon fuskar wayar,fuskar nan a dinke tsaf kamar bai taba dariya ba,abinda yasa girarsa guda biyun dake da wani irin shape dake burgeta sukayi kaman zasu hade da juna,sai ta kau da kai tsigar jikinta na zubawa,bata gane me yake nufi ba,kafin ta sake cewa wani abu kuwa yace "Minti ashirin ya rage mana mu wuce,bakiyi wanka ba?" Idanu tadan fitar tana kallonsa,ta sake gazawa jure kallon nasa kamar ko yaushe "In....." Ta bude baki da niyyar tambaya,amma sai ya katseta "Don kince baki zuwa,sai nabi umarninki,ni dake waye a sama?" Take ta fara abinda ya tsana din,wato hada ruwan hawaye akan fuskarta,ta kuma fara girgiza kanta,murya a karye kamar qaramar yarinya qasa da shekarun su amna ta fara magana "Kayi haquri,zan rasa makaranta,mun kusa komawa" idanunsa ya kafeta dasu,baisan me yasa yakejin haushi yana kamashi ba idan tayi zancan makarantar nan ba,wato makarantarta tafi komai?,zai tuna mata idan ta manta,matar aure ce ita,mijinta ya kamata ya juyata bawai tunanin komawa makaranta ba,ya kamata taji wani abu a jikinta da zai dinga tunasar da ita tana da igiyar wani,yaga kaman ta shagalta bata tuna haka. Kanta yana qasa tana qoqarin tsaida hawayenta,don haka batasan ya iso inda take ba,har sai da turarensa ya shaida mata. Kanta ta daga a hankali,sai tayi yunqurinja da baya da sauri saboda rage kusancin dake tsakaninsu,saidai kuma tuni ya kaima hannunta cafka,ya kuwa damqeta da kyau saman duwatsun hannunta. Tare suka kai dubansu shi da ita kan duwatsun,a hankali ya sakar mata hannu,sai kuma yayi mata qofar rago,taku daya idan ta qara da niyyar yin gaba ko baya to zata tsinciki kanta kane kane ne a faffadan qirjinsa "Wipe these tears.....,daga yau kika na sake magana kikamin kuka ko na sake umarni kikamin musu,Allah....Allah...biyu ko?,kalli ki gani" ya fada yana ranqwafowa dai dai fuskarta,kan yin musun yayi magana,don haka ta daga kan nata kamar yadda ya buqata,saida numfashinta ya kusa daukewa sanda taga irin kusa da kusan da sukayi,suka fara musayar numfashinsu me dumi,wani abu ya tsarga cikin jikinsa,fararen idanuwanta suka sauke masa wata irin kasala,sai ya daga hannunsa ya dora yatsuntsa guda biyu saman lips dinsa "Da nan zan goge hawayen tas,na kuma cinye bakin musun" tsareta yayi da idanun da a yau takejin saukarsu cikin kowanne sashe na jikinta sama da ko ina bayan ya ciro handkerchief dinsa ya bata ta goge fuskarta "Na baki minti goma ki shiga bedroom dina ki shirya" tana son tace wani abu amma tana tsoron rantsuwar hukuncin da yace zaiyi mata,don haka saita juya kawai zuwa bedroom din nasa gabanta na faduwa saboda rashin sabo,qafafunta basu taba taka cikin uwar dakin ba sai yau. Da kallo ya bita har ta shige,sai ya daga handkerchief din nasa yana kallon inda yayi danshin hawayenta,bakinsa ya tabe,qasa qasa ya furta "Its the consequences of marrying young girl" murmushin gefan baki ne kuma ya subuce masa daya tuna haka suka dan sha daaru da shaheeda ma,me yasa wasu abubuwan nasu ke manceceniya?,hakan na nufin itama haka zaisha fama da ita tare da koya mata yadda yakeso ta kasance? "are you ready to accept her as your wife?", Katsam tambayar tazo daga wani sashe na zuciyarsa,sai yayi shuru yana son rarrabe meye amsar data dace da tambayar?. A hankali take takawa cikin tsakiyar dakin tana nufar toilet dinsa,idanunta take wulwulgawa cikin dakin,komai na dakin taji yana burgeta,komai cikin tsafta,babu datti ko qura,saidai kuma ba'a shirye wasu abubuwan suke ba kamar yadda aka san dakin mace. Duk kyau da girman dakin da kuma tsadajjen marbles da aka saka masa an mamaye kusan fiye da rabinsa da wani tattausan carfet mai daukan sanyin acn dake kadawa cikin dakin kamar yanayin hunturu,kalolin dakin gaba daya dusty pink and beige color ne,sassanyar kalar da babu hayaniya a ciki,kama daga curtains zuwa komai ma na amfanin ciki,ta wuce toilet din tana kallon katafariyar walk in closet dinsa dake cike da himilin sutturu,kai zaka tsammaci ba'a nan qasar bane,da alama wadanda suka tsarata sun qware sosai a aikinsu. A toilet ma bata yima kanta qauron kallo ba,a nutse take bin toilet din da kallo,kamar ba muhallin wanka ba,tuna abinda ke gabanta da kuma wanda ke jiranta yasa ta qara gaba zuwa jacuzzi bathtub,ta hada ruwa dai dai da ra'ayinta sannan ta koma gaban wani oval shape glass sink dake da wata qaraman drower a qasa,gaba daya kayan amfaninsa ne a ciki kana hangosu tarwai kamar ruwa bai taba wajen,kama daga brush toothpaste sponge da tarin shower gel masu tsadan gaske,sai kayan shaving nasa,clippers da sauransu. Wadda ke a bude ta dauka tare da sponge din dake wajen data tabbatar dashi yake amfani,lumshe idanuwanta tayi sanda qamshinta da dumin ruwan ya hadu waje daya,sai taji kamar kada ta gama wankan,sosai qamshin ya burgeta ya kuma zauna mata a kwanyarta. Rarraba idanu ta shiga yi data tuna bata ko shigo da kayan da zata canza ba,hakanan bazata iya maida rigar data cire din ba,ta koyi wata irin tsafta da gayu na daban,bata da wani sauran zabi,dole ta matsa jerin fararen towels din dake maqale a wata silver hanger ta cira daya,tun kafin ta raba shi a jikinta qamshinsa yayi mata maraba,ba kasafai ta fiya son cudanya da duk abinda ke qamshinsa ba,sai ta maida ta dauko wani,saidai.shima din dai sammakal,ganin tana bata lokaci yasa dole ta daurash cike da fargaba,bata manta waccar ranar ba da towel din yaso zamewa daga jikinta,Allah ya taimaketa batayi me gaba daya a gabansa ba,sai ta sake dauko wani ta lullube kanta sannan ta fito. Da amna ta fara cin karo,zaune kan sleeper sofan dake gaban gadon da game a hannunta,bisa dukkan sabuwa ce yau din ta fara amfani da ita,sam ta mance da yarinyar,dazun tana ina sanda suke magana?,Allah yasa bata a wajen. Kai ta daga tana duban maimunatu dake riqe da towel din dake kanta wanda ke shirin zamewa "Anty moon,ga kayanki" duban inda ta nuna matan tayi,sai ta gyada kai,ta qarasa gaban mirror dinsa. Kaman madubin mace,cike da kayan shafa designers amma irin na maza,bata da sauran xabi,hakanan ta bude mayukansa ta shafa na shafawa,duk amna anyi shuru an nutsu an sami game,sannan ta dawo tana daga kayan da amnan tace nata ne. Tana duba kayan pant da breezier dinta suka fado daga tsakiya,sai ta fidda idanu cikin mamaki,ta daga kai tana duban amna "Amna....waye ya daukomin kaya?" "Daddy ne,nina rakashi" wata irin kunya ce ta kamata kamar zata nutse a wajen,musamman da taji suna fidda qamshin musk,saita qanqamesu kamar ta fasa kuka, knocking da taji anyi ya sata kwashe kayan da sauri,ta kuma koma toilet ta sakasu,tana sake jajantawa kanta,shikam baiji kunyarta ba?, dakinta ma ya shiga kenan?,bayan wannan dame dame ya gani nata?,Allah yasa baiga wani abu na kunya ba a dakin. Sanda ta tsaya a gaban madubi ita kanta tayi mamakin yadda kayan suka karbeta,suka dace da fatarta,a gurguje ta shirya,ta sanya takalmanta ta kuma yi rolling silk vail din dake mahadin kayan,take ta qara wani kwarjini sosai,saidai gaba daya ranta a jagule yake,hakanan akwai raguwar fara'a sosai daga kan fuskarta,sam sam bata shirya yin wata tafiya ba,musamman ma ace dashi,bugu da qari ma tana ji da tsoron kada tafiyar ta shiga qarewae hutunsu a koma makaranta banda ita,batason tayi missing koda kwana daya ne,amma a yadda taga ya dauki abun serious bata da wanin sauran zabi. Yana tsaka da waya suka fito ita da amna,gaba daya ilahirin jikinta qamshin turaren yake,turare ne daya ajjiyeshi ya daina amfani dashi,saboda yadda yake kashe masa jiki da zuciya,ta wani glass dake jikin space din da aka maqala babban plasma din ya hangota,duk da bai juyo ba amma yana ganinta tarwai,sai ya lumshe idanunsa sannan ya sake budesu,yana ci gaba da qare mata kallo ta glass din ba tare data sani ba,har suka iso inda yake bai juyo ba bare yayi alamun ya gansu,saidai duk wani taku nata akan idanunsa ta saukeshi,kusantowarsa wajen d qamshin turaren sai ya fara raba masa hankali,da coolness din nan nasa dake bayyana kansa wasu lokutan yace "I will call you later" ya zame wayar daga kunnensa ya jefata a aljihu,ya kuma bita da hannuwansa da yake yawan sanyasu a aljihun,sannan ya waiwayo. Yawun bakinsa ne ya kusa daukewa,gaba daya kallon daya mata ta glass din gaibu ne,yanzun yake ganin ainihin zallar reality,inda ace ita ya bawa damar dauko kayan zaice tayi da biyu ne,saidai da kansa ya dauko saboda favourite color dinsa kenan,sai gashi sun mata wani mugun kyau fiye da tsammaninsa. Idanunsa ya aza bisa fuskarta,baby face dinta a hade babu sauran fara'a,idan ma ya kula da kyau ta sake tsuke dan qaramin bakinta data zizarawa man lebe daya sanyashi yake qyalli,sai yadan rage kaifin kallon da yake mata,ya maida dubansa kan agogon hannunsa,ko bai magana ba tasan qorafi zaiyi kan ta bata musu lokaci,ta zaci zai amsa,sai taga ya kama hannun amna sunyi gaba,dole tabi bayansa. Ta zaci zai bata dama ta koma sashenta ta kintsashi ko ta dauko abunda take da buqata,amma sai taga baice komai da ita ba,hakanan ta bishi kamar zatayi hawaye,wannan mulkin kama karya ne da kuma qarfa qarfa,ai ba ita daya bace a gidan,me yasa bazai dauka unaisa su wuce ba?, Da wannan mitar da take tayi can qasan ranta ta qarasa motar,ta kama daya side din ta bude murfin ta shige. Har suka isa airport bata ce ko uffan ba,yana ankare da hakan,haka kawai ya samu kansa da monitoring mood dinta,wanda shi kansa baisan dalilin hakan ba. Sosai take kallon tsarin airport din,karon farko a rayuwarta abinda ko kusa bata taba kawowa zuciyarta zai faru a rayuwarta ba,saidai tayi qoqarin kame kanta,bata wani zarme da yawa ba,tana bin komai da lura,sai kuma abinda taga sunyi sannan,hakan ya sanya batayi wani abu daga kwafsa ba,dama kuma a idanu batayi zubin wadda zaka tsammaci ba sananniya bace a fagen,duba da jibga jibgan motocin da suka yima ja'afar din rakiya bisa jagorancin shugaban ma'aikata na kamfanin nasa. Bayan an gama checking luggage dinsu suka amsa boarding pass sannan suke wuce gates,wannan karon amna ta dawo hannunta,dukka passingers ne dake jiran tashin jirginsu daga gomben zuwa Lagos,cikin kujerun dake wajen ta hangi jabir da fa'eemansa,tana kwance sosai ajikinsa,da alama wani abu yake nuna mata cikin waya. Yaga jabir din amma baiyi ya ganshi din ba ganinsu tare da fatiman,miskilancin ya motsa,muryar amna tana kiran sunansa yasa ya ankara da shigowarsu wajen,da sauri fatiman ta gyara zamanta abinda ya bawa jabir daman tashi yana sanya wayar a aljihu,yayin da fatima ta budewa amna hannunta,akwai sabo tsakaninsu saboda tana da son yara fatiman,don haka ta nufeta, maimunatu ta bi bayanta,sai taji ta fara sakewa,don da alama da fatiman zasu wuce gaba daya. *_To masu karatu, honeymoon za'a je ne ko yawon bude ido?,meye zai faru?,😂,nidai bana ce ba,ku biyoni mu qarasa bin qwaqwafin labarin tare daku_* 64 Da murmushi suka dubi juna ita da fatiman,ta bata hannu sukayi musabaha sannan suka fara gaisawa,fatima na matsa mata gefenta ta zauna,amna na saman qafafunta. Cikin mintunan da sukayi suna jiran lokacin tashinsu ta sake sabawa sosai da fatima,kamar su dauki shekaru tare,tana da sauqin qai da kuma yawan hira,ta dauki maimunatu kamar mate dinta,duk da ta bata aqalla shekaru uku,don ita ta rufa shekara ashirin,wannan yasa maimunatu ta sake sosai,suka shiga hira da fatiman,suna baiwa juna labarin makaranta,duk da fatiman ta gama secondary school,yanzun haka tana 200level ne. Tare da fatiman suka shiga jirgin,sai itama ta duba jikin boarding pass dinta kamar yadda taga fatima tayi ta laluba seat number dinta. A hankali take dubawa har ta iso gurin,tuni daya kujerar wadda ita ke bakin window me ita yana zaune akai,saita juya tana duban inda su fatima ke zaune,ita da amna ne seat number dinsu daya, jabir kuma da ja'afar wadanda seats daya ne suka rabasu,batasan tsarin jirgi ba,tunda ba sabawa tayi da shiga ba,don haka ta zame qaraman jakar dake kafadarta ta zauna saman kujerar bakinta dauke da bismillah. A hankali ya waiwayo yana dubanta,matashin saurayine wanda duka duka bazai wuce shekara ashirin da bakwai ba,kana kallonsa zakasan wayewa da hutu sun ratsashi,unexpected ya ganta a kusa dashi,sai ya tashi ya zauna sosai idanuwansa a kanta,duk yadda yaso basarwa amma ya gaza,cikin muryarsa dake nuna zallan iyayi yace "Sannu 'yammata" a hankali ta waiwaya ta kalleshi,sai ta dauke kanta tayi gyaran murya kawai ba tare da tace komai ba, shima sai yayi shurun,amma kuma lokaci lokaci yana waiwayowa ya kalleta,saidai ta basar,ta kuma tsuke fuskarta da kyau,kamar yadda ko sau daya bata waiwaya ta dubeshi ba. Tunda ta zauna a seat dinta ya fuskanci wanda yake abokin xamanta hankalinsa ya gaza kwanciya,kunnuwansa naga jabir ne dake ta masa bayanin wasu receipt da suka biya kudin wasu clearance a wajen custom's,saidai dukka hankalinsa yana kanta. A hankali yaji kamar ana matsa zuciyarsa sanda ya fahimci saurayin yana yawan juyawa yana kallonta,ya dinga qoqarin dannewa da kuma kauda hankalinsa amma sai ya gaza,agogon hannunsa ya daga ya kalla,akwai awa kusan biyu a gaba kafin jirginsu ya sauka a lagos,sai yaja wani dogon tsaki,abinda yaja hankalin jabir kenan,sai a sannan ya fahimci bama fahimtar bayanin nasa yake ba,yakai idanuwansa inda ja'afar din ke kallo,sai a lokacin ya gane abinda ke faruwa,cikin taqaitaccen lokaci jabir ya qare masa kallo,hatta zamansa bai zauna properly ba,kamar wanda taushin kujerar bai masa ba,amma da alama duka bai fuskanci hakan ba shi. Gimtse dariyar dake son qwace masa yayi,ya buda baki zaiyi magana dai dai lokacin ja'afar din ya dunqule hannunsa ya buga a hannun kujerar da yake kai "It can't" ya fadi yana miqewa zumbur,ya taka a hankali ya fito daga inda yake ya nufi wajensu. Cikinsu ba wanda yasan da wanzuwar tasa a wajen,dai dai sanda saurayin ke qoqarin miqa mata tissue ganin ta rufe bakinta atishawa nason fita,ido hudu sukayi da ja'afar dake tsaye a kansu,ya goye hannuwansa a qirjinsa ya zuba masa wannan idanun nasa dake saurin ladabtar da kowa,wasu kibiyoyi da baisan suna fita a idanunsa ba nata spark. Sosai kallon da yake masa ya dakeshi ya kuma yi masa kwarjini,sai ya janye tissue din bakinsa na subucewa da cewa "Lafiya?" Cikin fargaba tare da tunanin qila matar aure ce kenan,tunanin da baizo ransa ba sai a lokacin,maganar da yayin tasa maimunatu daga kanta,suka hada ido,sai ya mata inkiyar ta tashi,yayi gaba,ta miqe tana sake saqala jakarta ta biyo bayansa. Kafin su iso jabir har ya miqe yabar mususeat din,dariya kaman zata kasheshi,ya koma inda ta taso din,saidai koda hakan shima ya taya J dinsa kishin da yaketa qaryata kansa bashi yakeyi ba,ya dubi matashin "Ku dinga hankali da matan mutane" ya fada yana jifansa da wani kallo me kama da harara,don shi din dama yafi ja'afar magana. Shi daya ya dinga quncin rai,yaja tsaki yafi a qirga,ita dai bata dashi komai ba,har awannin da suka rage musu ya cika jirgi yayi landing a lagos cunkus dakin tsumma. Motar kamfaninsa ta nan lagos ce tazo daukarsu wadda aka tanadar masa saboda irin haka dama sauran mamyan baqi da sukeyi daga qasashen waje abokan kasuwancinsu,already jabir ya musu booking na dakuna a daya daga cikin five star hotels,wanda kuma yafi kusa da inda sukazo duba ayyukansu,ciki da falo ya kamawa su ja'afar saboda amna,shi da fatinsa kuma single room. To tun saukarsu lagos basu samu zama sosai ba,idan motar company tazo ta saukesu tun safe sai dare,wannan ya bawa su maimunatu damar yawo sosai cikin garin lagos,jabir yasa wata motar daga company musamman take zuwa duk sanda suka gama shirinsu ta daukesu tayita zagayawa dasu guraren shaqawatawa kala daban daban,ya tura musu enough kudi ta account din fatima,ga kuma bandir da J ya ajjiye mata itama,basu da wata matsala ta komai,duk yadda maimunatun tayi tsammanin ba zataji dadin tafiyar ba sai abun yazo mata akasin hakan,taji dadin garin fiye da zatonta,sunyi yawo sosai,hakanan fatima ta musu siyayya mai yawan gaske,musamman maimunatu da batazo da wasu kayan ba,saidai kuma ita fatiman kusan duka qananun kaya ne siyayyar nata,sai sakakku da zata iya fita dasu cikin gari,don haka maimunatu ta ware kowanne jaka daban,wandancan da takejin ba zata iya fita dasu ba,da kuma wadanda zata iya sakawa. Duk yadda garin ke mata dadi amma bata mance da lissafin lokacin komawarsu makaranta ba,sunyi waya da afrah itama tana sake tuna mata "Allah ya nuna mana,amma bana gida ma,muna lagos,kuma banga alamun dawowarmu ba" dariya sosai afra ta sake "Wannan abu yayi min dadi,tsuntsun soyayyar ya fara sauka kenan,honeymoon aka tafi ne?" Kamar tana gabanta saita saki harara "A'ah milkmoon aka tafi,tare fa muka tafi da amna,harda su fatima" "To sai me?,bikin magaji zai hana na magajiya ne?,amna ina ruwanta?,zatafi kowa son a bawa daddynta kulawa,fatima kuwa na tabbatar saidai ta tayaki,kuma nasan ba daki daya kuke ba,kidai zauna garin kallon ruwa kwado yayi miki qafa" "Mtsweew,Allah ya shiryeki afrah,gwara hajja tayi miki aure ta huta" "Wallahi ko gwara a aurar dani a huta,idan ba haka ba......." "Ba'a kunne na zaki qarasa wannan zancan naki ba,ya girmi kunnuwana" saita datse wayar tana dariya. A hankali ta aje wayar a gefanta _ki tsaya dai kallon ruwa kwado yayi miki qafa_,wai me yasa kowa maganarsa kan ja'afar ne,kowa kusan abinda yake fadi mata kenan idan irin wannan zancan ya hadusu,sai ta sauke ajiyar zuciya,idanuwanta na hango mata kalar soyayyar jabir da fatima,wata irin soyayya me nuna zallar kulawa da kuma shaquwa,ita kanta abun yana burgeta,sau tari idan ya kirata bayan ya fita tunda yawancin lokutta suna tare,sai tayi kasaqe tana sauraren kalar hirarsu,ta fahimci ita kanta fatiman ta gano kalar zamansu,don wani lokaci ta taba cewa da ita "Shi namiji da kike gani,babu abu mai sauqi wajen sarrafawa irinsa,sau tari dama suke nema ko jira ka basu,mijinki ko?,hmmmmmm,astagfirullah,soyayyarsu ta dabance,duk sanda suka tashi nunawa mace soyayya za'a sha mamaki,saidai suna da wani irin aji da kamewa,wanda zaisa ki gaza fahimtar inda suka dosa" ajiyar zuciya ta sauke tana gyara kwanciyar rub da cikin da tayi saman kujerun falon,amna na daki tana bacci,dama a ciki suke kwana ita da ita,shi ya canjesu a falon. Qarar security na jikin qofar taji,kafin kuma ta ankara an murda handle din an turo qofar,sai ta daga kai da sauri don ganin wanda ya shigo din,saboda ta san wannan ba shine lokacin dawowarsu ba,zata iya cewa tun zuwansu tsahon kwanaki takwas yau,sau uku kawai suka hadu ita dashi,tana qunshe a daki sanda zai fita,kafin ya dawo ta tattare tayi kwanciyar barci abinta. Tun kafin ya saki handle din idanunsa ke manne a kanta,wata gown ce a jikinta ta wani material maras nauyi,wannan yasa kwanciyar rub da cikin da tayi ya bayyana mazaunai da qugunta sosai. A hankali idanuwansa suka kai kai,ya lumshe idanunsa tsigar jikinsa na zubawa,sai ya juya ya maida qofar ya rufeta,sannan ya soma takowa cikin dakin bakinsa dauke da sallama. Tuni ta miqe ta zauna kanta a qasa tana wasa da yatsun hannunta,itakam dawowarsa a yanzun kamar takura ce a wajenta,dole saidai ta koma daki tayita zama "Sannu da zuwa" ta fada a hankali tana miqewa tsaye duk da bataji ya amsa ba,taku biyu tayi taga ya babbake gaba daya hanyar wucewarta,idanuwansa a kanta,yau din kallonta tsakiyar idanuwanta yake kansa tsaye,ya karkatar da wuyansa gefe daya yana son hukuntata da idanun kamar yadda ya saba "Am...zan zan wuce" ta fadi muryarta nadan rawa,saboda jiki da zuciyarta da taji sun fara amsawa "Idan naqi fa?" Ya amsa mata yana hade fuskarsa,mamaki amsar da ya bata ta bata,sai ta dan tsuke bakinta kadan kafin ta sakeshi,idanuwansa suka kai kai,ya sake jin wani abu na sauka a dukka sassan jikinsa,yana kuma gauraya da gajiyar daya kwaso,idan yace pink lips dinta basa burgeshi yayi qarya,qara taku uku yayi qwarara sai gashi a gabanta jikinsu na gogayya waje daya,kafin ta qara wani tunani ya sanya hannuwansa ta baya ya dorasu saman mazaunanta,take a kuma lokaci guda kowanne numfashinsa ya fara barazanar daukewa na wucin gadi,namiji ne shi tsayayye,ita kuwa mace mai rauni,wannan yasa fa gaza tsaiwa a muhallinta ta fada jikinsa gaba daya,kafin ta samu ta fusgo numfashin nata,ta fara qoqarin raba jikinta da nashi,amma tayi latti,don ya zagaye bayanta da hannuwan nasa gaba daya. Ji yake kamar an jan jininsa da na'urar lantarki mara zafi,wani irin shock yakeji sosai,gudun zuciyarsa ya fara rawa "Hope ba da irin wannan kayan kike fita ba?" Yayi maganar yana dagata daga jikinsa,muryarsa na wani irin fusga,kamar zata narke a wajen haka takeji,kanta a qasa ta gyada masa kai,fiye da rabin hankalinta yana kan qofar daki,kada amna ta fito,ilai kuwa sai ga qaran qofan bude dakin,ba tare daya juya sashen ba yaja da baya ya sulale saman kujera "Hadamin ruwan wanka" ya bata umarni karo na farko kenan,don da kansa yake hadawar. Kamar qafafunta ba zasu iya daukanta ba haka ta jasu tayi ciki,amna kuma ta fito tana masa sannu da zuwa,a jikin bangon toilet ta jingina bayanta bayan ta kunna ruwan tana jiran na dumi ya sauko,kowanne sashe na jikinta ya zama week,wai me yasa?,me yasa irin hakan ke faruwa da ita?,tuno irin wani sassanyan qamshi gami da laushin daya ratsa fatarta tayi lokacin da ta isa ga jikinsa,kawai sai ta goye hannayenta aqirji tana matse jikinta waje guda kamar me jin sanyi. Ta gama hadawa ta juyo ta kama handle din da nufin bude qofar sai aka rigata shigowa,ja'afar dinne,sanye da trouser dinsa da fara qal din singlet dinsa kamar ba'a sanyawa jiki ita,ya cika qofar ya kuma taho gaba daya,so babu wani space da zata rabeshi ta fice,dole ta janye da baya har ya shigo,idanuwanta na kallon qasa,don ba zata iya kallonshi a haka ba,tsoro yake bata,gaba daya dantsensa wasu irin muscles ne dake nuna yadda ya qware wajen motsa jiki da kuma daga qarfe,daga hannuwansa zuwa qirjinsa duka sun bayyana albarkatun gargasar dake tattare da wajen. Ta dauka zai janye mata ne,sai taji ya maida qofar ya rufe,ya kuma fara zare singlet din da tayi saura a jikinsa,da saurinta ta qara gaba tana yunqurin bude bandakin,saidai ya saka lock a jiki,ta saka hannunta zata murza ta bude,ta tsinci husky voice dinsa na mata gargadi "Karki sake ki budeni,am taking bath" tashin hankali,sai taja da baya ta sake jingina da bangon zuciyarta na wani irin bugawa cike da tsoro,to wanka zaiyi itama wankan akace masa zatayi?,tsoro ya sake kamata ganin yana zare trouser din jikinsa,ta rasa a wanne side zata tsaya ba tare da taga kominsa ba?, kowanne sashe na bandakin glass ne da zai baka damar ganin abinda ke faruwa a kowanne bangare da bandakin,kota juya ma gabanta glass ne,idan kuma tace shi zata fuskanta ba?,inaa,ba zata iya tsaiwa gabansa bama,sai ta runtse idanuwanta gaba daya hawaye na taruwa cikin idanun nata. Rufe idanuwan nata ya bashi damar kallonta son ransa,ba abinda yake fuskarsa irin qirjinta dake cike sosai,ya kuma zauna ta cikin rigar saboda wata tattarar roba da aka yi mata daga sama, qaramin murmushi na gefan baki ya sake sanda ya fidda trouser din saboda yadda yaga ta cuno baki gaba,komai nata akwai childishness a ciki,some times ba abinda take tuna masa illa lokacin amarcinsu irin wannan shida shaheeda,tana tuna masa abubuwa masu yawa tattare da ita,ko a yanzun sai yake gani kaman ita dince. Rataye trouser din yayi,pants na maza ne kawai ya rage a jikinsa "Miqomin sponge" kamar ya mata tsawa a tsakiyar kanta haka taji,ta yaya zata iya bude idanuwanta ta kalleshi a haka?,sake maimaita mata yayi,sai ta fara tattakawa a hankali tana lalube ba tare data bude idanunta ba,qaramin murmushi ya qwace masa ganin ta saba hanya,tana ta lalube har arean da yake tsaye,sai ya zuba mata ido ya rabu da ita,baice mata komai ba har zuwa sanda ta damqi hannunsa. Saki taso yi da sauri amma cikin zafin nama ya riqeta,ya kuma janyota cikin jikinsa gaba daya,yayi mata rumfa da yalwataccen qirjinsa,ya kuma lullubeta da tattausar fatarsa,matseta yayi sosai cikin jikinsa wani numfashi mai nauyi yana qwace masa ba tare da ya shirya ba,wani irin body contact ya samu da ita irin wanda bai taba ba,tudun mazaunanta ya taba sashe mafi kima a jikinsa. Rasa abinda zatayi yasa gaba daya ta qanqameshi ta cusa kanta cikin qirjinsa bayan ya juyo da ita suna facing juna,hawayen da take boyewa suka sauka suka fara ratsa gargasarsa suka tadda fatarsa,dagata yayi kadan daga jikinsa yana duban fuskarta daya danyi jaa,ya lumshe idanuwansa da suka fara sauya kala saboda wani abu data harbawa kowanne sashe na jikinsa,siraran lips dinta na motsawa a hankali,sai ya sanya fuskarta a tsakiyar tafin hannunsa yana ci gaba da kallon labbanta,baya jin yau zai iya skipping komai da komai,for now yana jin komai nasa yana developing,kamar ana dawo da old version ne na ja'afar daya dade da bacewa wasu shekarun baya da suka shude. Shi kansa baisan yadda akayi ba ya tsinciki labbansa saban nata,yadda ya zacesu haka ya samesu,da wani irin dumi da kuma sulbi don bazaice taushi ba,abinda ya sake tabashi kenan sosai,ya kuma haukatashi sai yayi amfani da harshensa ya buda bakinta sannan ya zura harshen a ciki. Wasu irin hot kisses daya jima da kashesu a duniyarsa ya dinga bata,ciki da wajen bakinta ba inda bai tsotse ba,da zafi zafinsa yake aiwatar da komai,zafin da ya bayyana har cikin fitar numfashinsa dake sauka saman hancinta,take kuma shaqarsa zuwa huhunta,tana fiddo masa da nata numfashin shima yana aikawa nasa huhun,abinda ya sake haifar musu da wanu irin dimuwa gaba dayansu,gaba daya ta gama rudewa,jikinta duka ya dauki rawa kamar wadda zazzabi ya kama,wani irin baqon yanayi ne da batasan dashi ba,bata kuma taba kawowa zai risketa ba,ta sanya hannunta itama gaba daya ta kama kansa ta riqe tana son janyeshi daga fuskarta,saidai bata da wannan qarfin,ta rasa yadda zata rabashi da kanta kamar ma sake shige mata yake,kawai saita saki hawayenta suka soma zuba sosai. Danshinsu ya taba fuskarsa,ya kuma sanya a hankali komai ya fara sakinsa,ya zare bakinsa a hankali,yana kuma dawowa cikin hayyacinsa,a nan ya tuna me ya aikata?,tsananin qarfin hali irin na namiji sai ya hade fuskarsa bayan ya janyeta still yana dubanta 65 "I hate it,i already told you,duk sanda kika sakemin kuka irin hukuncin da zan miki kenan" sai ya matsa a hankali ya bude mata qofan yana dubanta "Open your eyes" kasa budewar tayi,shi wai bazai fuskanci halin da take ciki ba "I said open your eyes ko na sake punishing dinki" jin haka yasa ta bude idanuwan nata a hankali,tana ganin qofar a bude ta taka da hanzarinta kamar zai sake kamata ta fice. Gaba sink ya tsaya ya dafe hannayensa yana jin yadda mararsa ta riqe sosai,wani abu da yayi fama dashi shekarun baya kafin aurensa da shaheeda,wanda kusan shine silar aurensa na farko,sai yayi qas da kansa yana tattare hankalinsa waje daya,yana jiran komai nasa ya dai daita,wanda a qalla ya kusa kashe minti goma sha biyar a haka kafin ya sakarwa kansa ruwa mai bala'in dumi sosai,yana jin yadda mararsa keta murdawa tana saki. Sanda ya fito bata dakin,koda duba falo bata nan,sai ya sanyama qofar key ya shirya a hankali,sallah yaso fita yayi cikin jam'i amma sai ya kasa,cikin daki yayita,yana idarwa amna na shigowa nan ta zauna tana masa zubar tata. Bayanan duka duba aikin yakeso ya shigar su tattara za'a miqawa gwamnatin lagos tare da wasu muhimman takardu da kuma roqan a qara musu wasu gurare dake daura da wajen,ya debo duka kayan aikin ya jona system a charge amma sai ya kasa komai,jikinsa ya mutu murus,mararsa kuma ciwo take da gaske,bai dauki ciwon a bakin komai ba,ya zaci surutun amna ne zai hanashi aikin,don haka ya zaunar da ita,ya jawo mata suratul mulk yace tayita biyawa,cikin qarfin hali ya jawo system din ya kunnata. Tun aikin baiyi nisa ba yaji ciwon ya matsa masa,sai ya dauka wayarsa ya turawa jabir tex don ba kasafai ja'afar din ya fiya son kiran waya ba,yace ya fiddo key din mota zai rakashi wani waje,ya maida wayar ya ajjiye yana jingina jikinsa da bayan kujera,dai dai lokacin da maimunatu ta shigo dauke da coffee. Duk lokacin daya dawo takan dafa masa,saidai amna take bawa ta kai masa,yau din da bata ga amnan ba batason sake shigowa su hada idanu,amma dole ta dauko ta shigo dashi. Idanuwansa a kanta,har ta qaraso ta ajjiye masa,sannan ta danja baya tana fita a dakin ya bita da kallo,kunnuwansa nakan karatun amna da yake saurare yana mata gyara inda ta kuskure kadan kadan kuma marar tasa naci gaba da murda masa. Maimunatun ce ta sake turo qofar "Yaa jabir yana magana" ta fada masa idanunta a qasa,baice komai ba sai ya miqe kawai ya dauki wayoyinsa yana duban amna "Ina zuwa,yanzu zamu dawo" ya fada yana fita daga dakin,ya wuce ta falo ya fice. Cikin mota ya sameshi zaune yana jiransa "Ina zamu?,na gama tsara bazan fita ba sai gobe,gaba daya hutun da naso samu aikin nan bai barni na sake ba" ya fahimta sarai me yake nufi,baice masa komai ba sai ya karba key din motar,sukayi exchanging seat ya tada motar suka fice bayan ya saita map ta wayarsa,ya dinga directing nasa zuwa nearest private hospital. Da mamaki jabir ya kalleshi bayan ya sanya hancin motar cikin asibitin "Waye ba lafiya?" "Nine" ya amsa masa kai tsaye, cikin damuwa jabir din yace "Subhanallah,me ya sameka?,daga dawowarmu?" "I don't know" ya amsa masa a taqaice,sai ya qyaleshi kawai,da alama 'yan miskilancin ne suka motsa. Sanda suka shiga akwai likita,amma kuma da layi,saidai akwai special service,amma kudinsa ya ninka normal consultancy fee din da ake biya. Jabir ne ya biya komai kamar yadda suka saba,duk sanda wani zaiyi wani lalurar rayuwa indai daya yana wajen shike biyan komai,kai tsaye suka isa qofan consultancy room "Ka shiga kawai,zan jiraka a nan" jabir ya fada,bai matsanta masa ba ya shiga ya barshin. Musabaha ya bawa inyamurin likitan hannu sukayi,ya tarbeshi da fara'a da girmamawa da alama yasan aikinsa,duk wani bayani daya kamata yayi masa yayi masan,ya kuma dubashi harda scanning,ya daga takardar yana kalla,sannan ya dawo da dubansa kansa cikin harshen turanci "Yallabai,ka taba samun matsala irin haka?" Idaonsa ya lumshe yana gyada masa kai "Amma ba'a taba gaya maka kayi aure ba?" "An taba" ya amsa masa kai tsaye "Seriously dole kayi aure,kana buqatar hakan,binciken da nayi ya nuna ba zaka iya zama a haka ba,kayi qoqari kayi,zan rubuta maka magungunan da xaka samu relief,pain din ya ragu" shuru yayi kawai yana saurarensa,kamar yanzunne ake gaya masa wannan maganar a shekarun baya,akwai case kenan ya fada a ransa. Har suka fito jabir baice masa komai ba,shi dinne ya cewa jabir zasu tsaya a pharmacy zai karba magani ya ajjiye takardar a tsakiyarsu,kallon takardar jabir yayi,har zai tada motar yace "Am sorry,ina zuwa" ya bude murfin motar ya koma ciki,bai wuce mintuna goma ba ya dawo,still bai sake ce masa komai ba ya tashi motar suka wuce. Jin shurun yayi yawa sai ja'afar din yayi gyaran murya "Jibi ne zamu koma....ka siya mana ticket?" "Zan siya" ya amsa shi a taqaice. Kusan zaman kurame sukayi har suka siya maganin suka koma masauki,fuskar jabir din kamar akwai abinda yake nazari. °°°°°°°°A nutse ja'afar ya daga kai ya kalli jabir bayan ya miqa masa ticket din guda biyu ya kuma gama karanta abinda ke jiki,hankalinsa kwance yake cin abincinsa "Ticket din lagos to gombe ya kamata ka siya mana,amma ina ganin na lagos to johannesburg" "Eh,daga nan can zamu wuce,ya kamata mu dinga samun lokaci muna dan hutawa koda ba yawa,just one week kawai zamu dawo" shuru yayi na dan sakanni yana duban jabir din,jabir din wani mutum ne na musamman cikin rayuwarsa,yana da matuqar muhimmanci a rayuwarsa,hakanan ya isa ya yanke hukunci cikin rayuwarsa kamar yadda yasan shima hakan take a wajen jabir,bayason ya maida niyyar alkhairin da yayi masa,uwa uba kuma shi kansa yasan yana buqatar wani hutun, tunda ko da sukazo nan din wani irin ayyuka ne suka hadar musu,ba wani hutu ko qanqani,amma kuma bai shiryama wannan tafiyar ba kwata kwata "But.....kasan amma tayi maganan amna,akwai biki a dangin mommynta,jibi kuma zasu wuce har da ita" "Nayi waya da hisham,yacemin ya shigo lagos jiya,yaje wani aiki a teaching hospital,gobe zai koma,so na yankan musu ticket shi da amnan zasu wuce gombe gobe da yamma,mu kuma zamu bi south african airways flight sha biyu na rana" boyayyar ajiyar zuciya ya sauke yana ajiiye ticket din a gefansa,duk wani hanzari nasa jabir ya kasheshi,bashi da wani sauran uzuri kuma da zai bayar. Shuru kawai maimunatu tayi tana binsa da kallo sand ayake ficewa daga dakin,bayan ya gama gaya mata inda zasun,idanuwanta suka tara ruwan hawaye sosai,saura kwanaki hudu kacal a koma makaranta,tana murna gobe zasu koma sai kuma wata tafiyar bagatatan ta taso?,hakanan ta shiryama amna kayanta da sauran tsarabarta ta nan,ta hade jakankunan dana qananun kayan da fatima ta lodo mata,don babu inda zata je dasu. Tun tara na safe hisham yazo ya dauki amna,bata damu sosai ba don ta saba da uncle hisham din,ta kuma san cewa gwani ne wajen iya kula da yara da biyewa shirmensu,haka kawai ja'afar ya hanata fita su ko gaisa da hisham din bare suyi sallama da amna,ya rufe qofan dakin ya fita da card key din suna sallama dasu a farfajiyar hotel din,sai ta window ta leqasu,tana nan a tsaye har suka fice,shi kuma yana tsaye suna magana da jabir din. Maimakon ta saki labulen ta koma kamar yadda take so saita kasa,ta aza idanuwanta akansa tana kallonsa,sanye yake da long sleeve zip up hoodie wine color da wandonta,gashinsa a kwance kamar ko da yaushe baqi sidik,kana kallonsa kaga baqin bafullatani,qafafunsa slipper ne,ya dan kere jabir tsaho da kadan,amma kana duban fuskarsa zakasan ba ma'abocin fara'a bane,saboda yanayinsa ya nuna,sabanin jabir da ko yaushe fuskarsa ke a sake,kadaran kadaham. Kamar wanda aka yiwa cunenta ya daga kansa zuwa saman yana saukesu a bakin window din,cikin jikinsa yaji kamar ana kallonsa,cikin hanzari ta saki labulen taja da baya ta fada saman gadon gabanta yana faduwa,idanu ta fitar "Allah yasa bai ganni ba" ta fadi tana dafe goshinta,idan ya ganta aita tafka abun kunya. Sauke idanunsa yayi daga kallon wajen,yaga labule ya motsa alamun an koma da baya,gaba daya lissafin tafiyar ne cikin ransa,baisan me jabir ya qulla ba,amma yafi kowa sanin halinsa,bai taba wata magana data dangancin iyalinsa dashi ba,amma ya tabbatar da biyu ya shirya wannan tafiyar,koma meye zaiyi qoqarin kame kansa da mutuncinsa,ba zaiyi abinda mutuncinsa zai zuba a idanun qaramar yarinya ba(niko nace sannu gembo sarkin son girma,muje dai zuwa 😒). Tun kafin sukai ga shiga jirgi ta fahimci tafiyar gaba daya kamar ta musamman ce,kamar kusan koma fiye da rabin matafiyan couples ne(wato miji da mata),kowa ka ganshi tallafe da matarsa,harda jabir wannan karon murje idanunsa ya ja fatimansa jikinsa sunata hirarrakinsu qasa qasa. Karon farko da taji abun ya burgeta,sai ta dauke idanunta zuwa sashen da ja'afar din ke tsaye tun dazu yana amsa waya,cikin sa'a ta samu ita yake kallo,kallo kuma na kai tsaye,abinda bata sani ba ya dan jima a tsaye yana karantar expression nata directly,ya karanci akwai wani abu da ya motsa zuciyarta. Cikin kunya ta kauda idanunta daga kansa,sai ta zaro wayarta daga qaramar jakar da tayi amfani da ita ta kunna data ta shiga watsapp dinta,rasa me zatayi tayi,bata da interest nayin chart yanzu da kowa,sai ta koma viewing status na mutane,kafin ta gaji da wannan,ta shirin sauka notification na wani app ya shigo mata,sai ta danna ta shiga,tana duba sabbin pictures da quotes na soyayya da suka dora,wannan yadan dauke mata hankali. Sanda suke wucewa zuwa jirgi fatima da jabir suna bayansu su kuma suna gaba,ya daidata kafadarsa da tata,abinda yasa ta sake gane tazarar tsahon dake tsakaninsu,batasan me ya faru ba,a hankali ta tsinci tattausan hannunsa cikin nata,ya hada dukka tafukan hannayensu ya matse guri daya,daga ido tayi ta kalleshi jikinta yana amsawa sai taga idanuwansa na kallon wani waje,a hankali ta maida dubanta wajen,sai a sannan ta fuskanci me yakewa,daya daga cikin ma'aikatan airport din ne,sanye da kayan aiki,ya zuba dukka idanuwansa a kansu,kafin daga bisani ya janye ganin ja'afar din ya kama hannunta,qaramin tsaki yaja bayan sun giftashi da kadan,ta zaci zaici zai sakar mata hannun amma sai taga yaci gaba da riqeta,har suka isa cikin jirgin. Batasan seat number dinsu daya bane sai da tazo zama,kallonta yayi sanda yake sanya luggage dinsa daga saman kansu,hannunsa daya dauke da da wata sweater mara nauyi me kyau "Anzo wajen,Allah yasa ba sanyi garesu ba" ta fada cikin ranta,don babu abinda yake takura ta a rayuwarta irin sanyi,batason zafi,amma kuma idan sanyi yayi yawa yana damunta. 66    A tausashe ya zame duka hannuwan rigar daga jikinta,yakai bakinsa a hankali saman wuyanta yana sauke mata hucin numfashinsa da kuma dumin dake kan soft lips din nasa,take tsigar jikinta ya zuba da wani irin yanayi daya tsarga har cikin jininta,ta runtse idanunta da kyau,tana jin saukar wani abu a jikinta,kamar a yanzun ne tasha maganin wajen anty maama,cikin kunnensa yakai bakin nasa,cikin laushi kamar mai jin bacci da wata irin murya me zurfi "Uhmmm,tell me.....me kike tsoron?" Yadda yayi maganar tsakiyar kunnenta sai ya rikitata gaba daya,taji kamar zata fadi duk da a zaune take,bata gama dawowa hayyacinta ba ta sake jin dumin hannunsa saman wuyanta,kamar mai tafiyar tsutsa ya shafi wuyanta zuwa saman qirjinta,wani shock ya sake sakar ma jikinta duka,hannunsa ya sanya ya kama habarta ya juyo da fuskarta,karon farko da idanunsu ya sarqafe cikin na juna a yanayi irin wannan,wani irin kallo yake mata kamar zai narke a cikin idanun nata,duk da idanun suna cikin nata amma sun gaza tsaiwa saboda abinda yake ji cikin jiki da zuciyarsa,duk bayan sakanni sai ya lumshesu ya kuma budesu a kan fuskarta,yana jin kamar lokaci yayita tsaiwa a haka ya daina motsawa.        Ta qasan rigar ya zura hannunsa ya shafi mararta,mutuwar zaune ta sakeyi,wannan karon tayi yinqurin riqe hannunsa,fuskarta a narke tana girgiza kai tana kuma kallonsa da idanuwanta da suka yara qwallar kunya da tsoro,abinda ya sake qara masa shauqi kenan a kanta,sai ya sakar mata wani galabaitaccen tattausan murmushi,sannan shima ya girgiza mata kai alamun a'a,ya zame hannunsa daga cikin nata,ya sanya duka tafukan hannuwansa a gefe da gefan qugunta,ya fara murza rigar zuwa sama(scrolling up),a hankali tattausan fari sol din jikinta ya fara bayyana,idanunsa cikin nata yana dasa mata wasu irin kibiyoyi da suke isa direct daga ruhi zuwa gangar jiki su kuma sauka a azuciya.      Ci gaba yayi da nade rigar tas a haka,har hannuwansa suka isa ga qirjinta,sai yasa hannu ya zare rigar gaba daya kamar nannadaddiyar takarda ya jefar da ita gefe guda tabi bayan fasashen kofin tea dinsa na dazu.      Zaucewa ya kusa yi sanda ya yiwa hannuwansa masauki a samansu,maimunatu kuwaqi wani irin numfashi mai sauti ta zuqa ta kuma sauke,sannan ta aza nata hannuwan saman nashi da zummar turesa tana kuma yunqurin miqewa daga saman cinyarsa "Noo,please... don't...... do....." Ya fara fada a tsintsinke,bai kuma iya qarasa fadar ba,saboda kasa jurewar da yayi,ya janyota cikin jikinsa da dukka qarfinsa,ya tura kansa tsakiyar qirjin nata ya zagaye hannuwansa a bayanta ya matseta gam har taji kamar zata balle balle biyu,wani irin salo ya fara mata tsakanin dukiyar fulaninta,sai taji gaba daya wuta ta dauke mata,ta shiga wani irin shauqi da yanayin da tunda tazo duniya bata taba jin irinsa ba,tana jinsa yana bidirinsa yadda yaga dama,ba inda bai yamutsa a jikinta ba yadda yaso,ba inda harshe da hannuwansa basu kai ba,wani irin galabaitaccen numfashi dukkaninsu suke saukewa,bugun zuciyarsu na wani irin sauri,kada ma ja'afar yaji labari,wanda yakejin zuciyar tasa kamar zata faso qirjinsa ta fito,yana jin heart beat din nasa har cikin kunnuwansa,wanda banda shi da qarar fitar numfashin maimunatun babu wani abu da kunnuwansa ke iya ji,ciki harda knocking din da jabir keta musu don su karba dinne dinsu,da ya gaji sai ya koma daki ya dauki wayarsa ya kira number ja'afar din,saidai ko kadan ko kusa ko alama ma cikinsu ba wanda yaji ringing na wayar.      Cak ya dauketa kamar wata baby,bai sauketa ko ina ba sai saman gadon,sai daya tabbatar ya fida duk wani abu da zai kawo masa delay daga jikinsa sannan ya sanyata tsakiyar qirjinsa yana boyeta,haduwar fatar jikkunansu a waje daya ya haifar musu da wani irin gigitaccen yanayi mr tafiya da qwaqwalwa dama dukka tunanin dake cikinta.      Cikin zafin nama yaci gaba da aike mata da saqonni masu nauyi,cikin salo na qwarewa tausasawa da kuma sanin hanyar zautar da mace,abinda ya sake gigitar da maimunatu kenan,shi kuma ya sake ficewa daga hayyacinsa,gaba daya jikinsa rawa yake,zaka dauka matsanancin sanyi yakeji,irin sanyin dake tafe da zazzabi mai zafi,sai daya tabbatar bazai iya qwacetar kansa ba,yakai matakin da babu abinda yake buqata illa maimunatu,illa kuma kasancewa da ita,ya sanya fuskarta a tsakiyar tafukan hannayensa yana dubanta da jajayen idanuwansa,fuskarta ta kada tayi jazir saboda yamutsa da tasha da kuma nauyin saqonninsa zuwa gareta,hade fuskarsu yayi waje daya suna musayar numfashi,yana fusgar kalaman bakinsa da qyar labbansa suna rawa "Kiyimin alfarmar......do me this favor" ya matseta sosai a jikinsa  "bana bir iyilik yap" ya sake fada cikin turkish language yana mannewa a jikinta yanajin kamar ya narke su xama abu daya tsabar yadda yakeji.      Sai da hankalinta ya fara dawowa gangar jikinta sanda yake neman hanyar da zata maidasu xuwa abu guda ita dashi,sai a sannan ta fahimci bata da wayo,ta kuma gane zallar wauta da rashin hankalin data tafka,cikin tsananin azaba ta riqeshi gam tana roqorsa gami da bashi haquri,kalma daya da take fada bai fahimta ba,illa dai ruwan hawayen daya fahimci suna fita daga idanunta sakamakon shafar fuskarsa da sukayi,harshensa ya maye gurbin handkerchief a ranar,ya dinga lashe duk wani hawaye daya silalo zuwa kuncinta "Am sorry,am so sorry angel" sunan ya kufce daga bakinsa ba tare da yasan hakan ya faru ba,wasu irin kalamai ne suka dinga kwance kansu da kansu daga can qasan zuciyarsa zuwa harshensa,wanda tabbas inda cikin hayyacinsa yake tabbas ba zasu fita din ba,idanunsa cikin nata yake kallonta,yaci gaba da kuma da maidata zuwa cikakkiyar mace.       Bai fahimci komai ba,yaga dai hawayen ya tsaya,sannan kuma idannta suka dinga lumshewa a hankali,kalaman bakinta suka tsaya cak,sai motsa bakin nata data dinga yi a hankali a hankali,har idanuwanta suka kammala rufewa,bakinta ya tsaya da motsi.      Wasu qididdgaggun mintuna suka biyo baya kafin ya kira sunanta da wani irin amo mai qarfi,sautin kiran da ya dawo da ita hayyacinta,ya matseta kamar xai rabata biyu gumin dake jikinsa yana sauka a fatarta.       Kuka take son saki amma kuma ta kasa,gaba daya wani irin wahalallen numfashi take saki,numfashin da baya ko sauka cikin hunhunta,sannu a hankali ta saki wani marayan kuka mara sauti sai zallar hawaye masu zafi,tana jin azaba kota ina, cinyoyinta sun mata nauyi kamar idan akace ta motsa ba zata iya ba.      Kansa na kife akan qirjinta yana sauke numfashin dake tattare da samun cikakkiyar nutsuwa,idan yace xai tuna duniyar daya tafi yasan yayi tabbas yayi babbar qarya,wani nisan kiwo yayi da tafiyar da bai taba tsintar kansa a cikinta ba,wasu abubuwa suka dinga dawo masa a kansa "Wannan itace maimunatu?,maimunatun da anni ta zaba min?"idanunsa ya runtse yana tuna me da me ya yiwa anni sanda ta shaida masa zabinta "Maimunatu...maimoon" ya sake nanata sunanta cikin zuciyarsa yana zube idanuwansa da suka koma kamar na wanda yasha abun maye ya bugu a kanta,duk da baya iya ganin fuskarta "Mallakinsa ce ita a yanzu?" Ya yiwa kansa da kansa tambayar da a yanzun yafi kowa sanin amsarta,sai ya lumshe ido yanajin wani abu mai taushi sanyi da tsafta yana gangarawa cikin tsakiyar zuciyarsa dangane da ita,ya sake janta cikin jikinsa sosai kamar zai maidata cikinsa,kamar kuwa wani ne zai qwace masa ita,bai damu da yadda jikinsa ya dauki zafi rauuuu ba,zazzabin da yakeji a danzun ya fara ninkuwa,saidai mararsa tayi masa sakayau kamar wanda ya fidda wani mulmulallen dutse daga cikinta,duvet yaja ya lullubesu da kyau bayan ya mata kyakkyawar runguma cikin jikinsa,yana wani mugun jinta cikin zuciyarsa,yana kuma jin ta riga data zama wani sashe na rayuwarsa.       Yadda yaji zuciyarta na bugawa yasa yaji bai gamsu ba,don haka yadan yaye duvet din,yana laluben fuskarta da sassalkar sumarta data cakude waje guda,saboda yamutsar da ita kanta tasha ta rufe fuskar,ta hanashi bude fuskar don haka ya cusa fuskar cikin tata ya hadesu waje guda,take suka fara musayar numfashi "My moon" ya furta a hankali,cikin wani irin salo da ya qawata sunan a bakinsa,sunan da ya canza masa ma'ana da kuma asalin yadda yake,shuru tayi masa,bata iya amsashi ba, saboda tana jin kamar bakinta ma kansa ciwo yake,idan ma tace ciwon yake batayi qarya ba,saboda shi kansa kisses din daya karba masu zafi ne,komai yayishi ne cikin gushewar hankali,tamkar kuma mayunwacin zakin daya jima bai samu abinci ba "My moon" ya sake fada muryarsa tayi wani mugun laushi,kamar yadda jikinsa da xuciyarsa sukayi tubus,jin bata amsa masa ba sai yayi qoqarin birkitota jikinsa,wani marayan ihu ta saki,wanda ya sanyashi ankara da irin barnar da yayi,cikin hanzari ya qarasa yaye ragowar duvet din dake jikinsu,sai ta qanqame jikinta guri daya saboda babu komai a jikin nata.       Da hazari ya sauya mata guri,bayan ya dorata saman pillow yana duban yadda gurin yayi staining sosai da jini "Subhanallah,ya salam" ya fada yana dafe kansa,ya akayi ya manta da qananun shekarunta yayi mata irin wannan shigar,sai ya maida dubansa gareta,yanajin tausayinta da tare da wara mahaukaciyar soyayyarta na ratsashi,idanunta na kulle amma kuma ruwan hawaye har yanzu suke zubarwa,fuskarta tadan tasa,idanunta sun kumbura,hakanan tayi jazur da ita abinka da farar fata.        Zamowa yayi ta sauka qasan gadon,ya kewayo inda take facing,a nutse ya duqa gabanta ya lalubo hannunsa ya sanya cikin nasa,yatsunsu ya sarqafe waje guda ya kuma hade tafukan hannayensu waje daya,yasan koda ya buqaci ta kalleshi ba zata yi ba "Am sorry,am really sorry angel,i don't mean to hurt you,am out of my sense..ki yafemin" saukar kalamansa ga zuciyarta tamkar wani yayyafin ruwa yayi mata,kunya da nauyinsa da kuma ciwon da takeji ya hanata bude idanuwanta ko ta nuna masa tana jinsa,wani sashe na zuciyarta nason angizo mata tausayinsa,haquri yake bata don ya karbi haqqinsa?,ba fyade yayi mata ba,matarsa ce halak malak da musulunci ya mallaka masa,ya kuma bashi damar zuwa mata duk sanda yaso a kowanne irin yanayi,is he real ja'afar data sani?,gaba daya ya wani karaya yayi laushi?,ja'afar stubborn person sannan kuma Arrogant wasu lokutan,bashi da sauqi ko kadan ita shaida ce koda daga kan qannensa kuwa.     Kwata kwata bashi da control a lokacin,tun daga bakinsa har zuwa zuciyarsa,kalaman neman afuwa ne ke fitowa a bakinsa,yana jin wami guiltiness a jikinsa,yana jin kamar yayi forcing dinta ne ko kuma ya aikata mata ba dai dai ba.     Ja'afar din nada wata irin baiwa ta iya magana da kalamai,shi yasa sau tari anni kan ce "Ubangiji shi yasan nufinsa da ya samyashi mara yawan magana,wala'alla hakan nada nasaba da baiwar iya magana da yake da ita".     Shanyayyun idanuwansa ya daga ya kalli agogon dake bedside bayan wani lokaci,dare ya fara nisa sosai,sai ya janyesu a hankali ya maida kanta,sannan ya miqa mata tafin hannunsa ya miqa mata "Kiyimin wata alfarmar,ki taso na rakaki ki gyaran jikinki,nan din ya baci da yawa" ta jishi sarai,amma batasan ta inda zata fara tashi ba,na farko kunyarsa da takeji ta ninka ta baya sau dubu,na biyu kuma ciwon da takeji a qasanta da wanda dukka jikinta ke mata ta tabbatar bazai barta ta tashi din ba,sai tasa hannu a hankali tadan ture fuskarsa daya matso da ita dab da tata,sai a sannan taji zafin dake jikinsa har ya kusa fin nata,bai bata damar sakeyin tunani na biyu ba ya shammaceta ya dauketa cak,runtse idanunta tayi gam gam saboda motsatan da yayi ya fama mata mikin dake jikinta,duk da batace komai ba amma ta saki wani wahalallen numfashi "Am sorry" ya fada a hankali sannan ya mannata da qirjinsa ya wuce toilet din da ita cikin riritawa da kuma kulawa,tamkar yana dauke da qwai. GURBIN IDO.... Chapter 67 Shafi na sittin da shida    A tausashe ya zame duka hannuwan rigar daga jikinta,yakai bakinsa a hankali saman wuyanta yana sauke mata hucin numfashinsa da kuma dumin dake kan soft lips din nasa,take tsigar jikinta ya zuba da wani irin yanayi daya tsarga har cikin jininta,ta runtse idanunta da kyau,tana jin saukar wani abu a jikinta,kamar a yanzun ne tasha maganin wajen anty maama,cikin kunnensa yakai bakin nasa,cikin laushi kamar mai jin bacci da wata irin murya me zurfi "Uhmmm,tell me.....me kike tsoron?" Yadda yayi maganar tsakiyar kunnenta sai ya rikitata gaba daya,taji kamar zata fadi duk da a zaune take,bata gama dawowa hayyacinta ba ta sake jin dumin hannunsa saman wuyanta,kamar mai tafiyar tsutsa ya shafi wuyanta zuwa saman qirjinta,wani shock ya sake sakar ma jikinta duka,hannunsa ya sanya ya kama habarta ya juyo da fuskarta,karon farko da idanunsu ya sarqafe cikin na juna a yanayi irin wannan,wani irin kallo yake mata kamar zai narke a cikin idanun nata,duk da idanun suna cikin nata amma sun gaza tsaiwa saboda abinda yake ji cikin jiki da zuciyarsa,duk bayan sakanni sai ya lumshesu ya kuma budesu a kan fuskarta,yana jin kamar lokaci yayita tsaiwa a haka ya daina motsawa.        Ta qasan rigar ya zura hannunsa ya shafi mararta,mutuwar zaune ta sakeyi,wannan karon tayi yinqurin riqe hannunsa,fuskarta a narke tana girgiza kai tana kuma kallonsa da idanuwanta da suka yara qwallar kunya da tsoro,abinda ya sake qara masa shauqi kenan a kanta,sai ya sakar mata wani galabaitaccen tattausan murmushi,sannan shima ya girgiza mata kai alamun a'a,ya zame hannunsa daga cikin nata,ya sanya duka tafukan hannuwansa a gefe da gefan qugunta,ya fara murza rigar zuwa sama(scrolling up),a hankali tattausan fari sol din jikinta ya fara bayyana,idanunsa cikin nata yana dasa mata wasu irin kibiyoyi da suke isa direct daga ruhi zuwa gangar jiki su kuma sauka a azuciya.      Ci gaba yayi da nade rigar tas a haka,har hannuwansa suka isa ga qirjinta,sai yasa hannu ya zare rigar gaba daya kamar nannadaddiyar takarda ya jefar da ita gefe guda tabi bayan fasashen kofin tea dinsa na dazu.      Zaucewa ya kusa yi sanda ya yiwa hannuwansa masauki a samansu,maimunatu kuwaqi wani irin numfashi mai sauti ta zuqa ta kuma sauke,sannan ta aza nata hannuwan saman nashi da zummar turesa tana kuma yunqurin miqewa daga saman cinyarsa "Noo,please... don't...... do....." Ya fara fada a tsintsinke,bai kuma iya qarasa fadar ba,saboda kasa jurewar da yayi,ya janyota cikin jikinsa da dukka qarfinsa,ya tura kansa tsakiyar qirjin nata ya zagaye hannuwansa a bayanta ya matseta gam har taji kamar zata balle balle biyu,wani irin salo ya fara mata tsakanin dukiyar fulaninta,sai taji gaba daya wuta ta dauke mata,ta shiga wani irin shauqi da yanayin da tunda tazo duniya bata taba jin irinsa ba,tana jinsa yana bidirinsa yadda yaga dama,ba inda bai yamutsa a jikinta ba yadda yaso,ba inda harshe da hannuwansa basu kai ba,wani irin galabaitaccen numfashi dukkaninsu suke saukewa,bugun zuciyarsu na wani irin sauri,kada ma ja'afar yaji labari,wanda yakejin zuciyar tasa kamar zata faso qirjinsa ta fito,yana jin heart beat din nasa har cikin kunnuwansa,wanda banda shi da qarar fitar numfashin maimunatun babu wani abu da kunnuwansa ke iya ji,ciki harda knocking din da jabir keta musu don su karba dinne dinsu,da ya gaji sai ya koma daki ya dauki wayarsa ya kira number ja'afar din,saidai ko kadan ko kusa ko alama ma cikinsu ba wanda yaji ringing na wayar.      Cak ya dauketa kamar wata baby,bai sauketa ko ina ba sai saman gadon,sai daya tabbatar ya fida duk wani abu da zai kawo masa delay daga jikinsa sannan ya sanyata tsakiyar qirjinsa yana boyeta,haduwar fatar jikkunansu a waje daya ya haifar musu da wani irin gigitaccen yanayi mr tafiya da qwaqwalwa dama dukka tunanin dake cikinta.      Cikin zafin nama yaci gaba da aike mata da saqonni masu nauyi,cikin salo na qwarewa tausasawa da kuma sanin hanyar zautar da mace,abinda ya sake gigitar da maimunatu kenan,shi kuma ya sake ficewa daga hayyacinsa,gaba daya jikinsa rawa yake,zaka dauka matsanancin sanyi yakeji,irin sanyin dake tafe da zazzabi mai zafi,sai daya tabbatar bazai iya qwacetar kansa ba,yakai matakin da babu abinda yake buqata illa maimunatu,illa kuma kasancewa da ita,ya sanya fuskarta a tsakiyar tafukan hannayensa yana dubanta da jajayen idanuwansa,fuskarta ta kada tayi jazir saboda yamutsa da tasha da kuma nauyin saqonninsa zuwa gareta,hade fuskarsu yayi waje daya suna musayar numfashi,yana fusgar kalaman bakinsa da qyar labbansa suna rawa "Kiyimin alfarmar......do me this favor" ya matseta sosai a jikinsa  "bana bir iyilik yap" ya sake fada cikin turkish language yana mannewa a jikinta yanajin kamar ya narke su xama abu daya tsabar yadda yakeji.      Sai da hankalinta ya fara dawowa gangar jikinta sanda yake neman hanyar da zata maidasu xuwa abu guda ita dashi,sai a sannan ta fahimci bata da wayo,ta kuma gane zallar wauta da rashin hankalin data tafka,cikin tsananin azaba ta riqeshi gam tana roqorsa gami da bashi haquri,kalma daya da take fada bai fahimta ba,illa dai ruwan hawayen daya fahimci suna fita daga idanunta sakamakon shafar fuskarsa da sukayi,harshensa ya maye gurbin handkerchief a ranar,ya dinga lashe duk wani hawaye daya silalo zuwa kuncinta "Am sorry,am so sorry angel" sunan ya kufce daga bakinsa ba tare da yasan hakan ya faru ba,wasu irin kalamai ne suka dinga kwance kansu da kansu daga can qasan zuciyarsa zuwa harshensa,wanda tabbas inda cikin hayyacinsa yake tabbas ba zasu fita din ba,idanunsa cikin nata yake kallonta,yaci gaba da kuma da maidata zuwa cikakkiyar mace.       Bai fahimci komai ba,yaga dai hawayen ya tsaya,sannan kuma idannta suka dinga lumshewa a hankali,kalaman bakinta suka tsaya cak,sai motsa bakin nata data dinga yi a hankali a hankali,har idanuwanta suka kammala rufewa,bakinta ya tsaya da motsi.      Wasu qididdgaggun mintuna suka biyo baya kafin ya kira sunanta da wani irin amo mai qarfi,sautin kiran da ya dawo da ita hayyacinta,ya matseta kamar xai rabata biyu gumin dake jikinsa yana sauka a fatarta.       Kuka take son saki amma kuma ta kasa,gaba daya wani irin wahalallen numfashi take saki,numfashin da baya ko sauka cikin hunhunta,sannu a hankali ta saki wani marayan kuka mara sauti sai zallar hawaye masu zafi,tana jin azaba kota ina, cinyoyinta sun mata nauyi kamar idan akace ta motsa ba zata iya ba.      Kansa na kife akan qirjinta yana sauke numfashin dake tattare da samun cikakkiyar nutsuwa,idan yace xai tuna duniyar daya tafi yasan yayi tabbas yayi babbar qarya,wani nisan kiwo yayi da tafiyar da bai taba tsintar kansa a cikinta ba,wasu abubuwa suka dinga dawo masa a kansa "Wannan itace maimunatu?,maimunatun da anni ta zaba min?"idanunsa ya runtse yana tuna me da me ya yiwa anni sanda ta shaida masa zabinta "Maimunatu...maimoon" ya sake nanata sunanta cikin zuciyarsa yana zube idanuwansa da suka koma kamar na wanda yasha abun maye ya bugu a kanta,duk da baya iya ganin fuskarta "Mallakinsa ce ita a yanzu?" Ya yiwa kansa da kansa tambayar da a yanzun yafi kowa sanin amsarta,sai ya lumshe ido yanajin wani abu mai taushi sanyi da tsafta yana gangarawa cikin tsakiyar zuciyarsa dangane da ita,ya sake janta cikin jikinsa sosai kamar zai maidata cikinsa,kamar kuwa wani ne zai qwace masa ita,bai damu da yadda jikinsa ya dauki zafi rauuuu ba,zazzabin da yakeji a danzun ya fara ninkuwa,saidai mararsa tayi masa sakayau kamar wanda ya fidda wani mulmulallen dutse daga cikinta,duvet yaja ya lullubesu da kyau bayan ya mata kyakkyawar runguma cikin jikinsa,yana wani mugun jinta cikin zuciyarsa,yana kuma jin ta riga data zama wani sashe na rayuwarsa.       Yadda yaji zuciyarta na bugawa yasa yaji bai gamsu ba,don haka yadan yaye duvet din,yana laluben fuskarta da sassalkar sumarta data cakude waje guda,saboda yamutsar da ita kanta tasha ta rufe fuskar,ta hanashi bude fuskar don haka ya cusa fuskar cikin tata ya hadesu waje guda,take suka fara musayar numfashi "My moon" ya furta a hankali,cikin wani irin salo da ya qawata sunan a bakinsa,sunan da ya canza masa ma'ana da kuma asalin yadda yake,shuru tayi masa,bata iya amsashi ba, saboda tana jin kamar bakinta ma kansa ciwo yake,idan ma tace ciwon yake batayi qarya ba,saboda shi kansa kisses din daya karba masu zafi ne,komai yayishi ne cikin gushewar hankali,tamkar kuma mayunwacin zakin daya jima bai samu abinci ba "My moon" ya sake fada muryarsa tayi wani mugun laushi,kamar yadda jikinsa da xuciyarsa sukayi tubus,jin bata amsa masa ba sai yayi qoqarin birkitota jikinsa,wani marayan ihu ta saki,wanda ya sanyashi ankara da irin barnar da yayi,cikin hanzari ya qarasa yaye ragowar duvet din dake jikinsu,sai ta qanqame jikinta guri daya saboda babu komai a jikin nata.       Da hazari ya sauya mata guri,bayan ya dorata saman pillow yana duban yadda gurin yayi staining sosai da jini "Subhanallah,ya salam" ya fada yana dafe kansa,ya akayi ya manta da qananun shekarunta yayi mata irin wannan shigar,sai ya maida dubansa gareta,yanajin tausayinta da tare da wara mahaukaciyar soyayyarta na ratsashi,idanunta na kulle amma kuma ruwan hawaye har yanzu suke zubarwa,fuskarta tadan tasa,idanunta sun kumbura,hakanan tayi jazur da ita abinka da farar fata.        Zamowa yayi ta sauka qasan gadon,ya kewayo inda take facing,a nutse ya duqa gabanta ya lalubo hannunsa ya sanya cikin nasa,yatsunsu ya sarqafe waje guda ya kuma hade tafukan hannayensu waje daya,yasan koda ya buqaci ta kalleshi ba zata yi ba "Am sorry,am really sorry angel,i don't mean to hurt you,am out of my sense..ki yafemin" saukar kalamansa ga zuciyarta tamkar wani yayyafin ruwa yayi mata,kunya da nauyinsa da kuma ciwon da takeji ya hanata bude idanuwanta ko ta nuna masa tana jinsa,wani sashe na zuciyarta nason angizo mata tausayinsa,haquri yake bata don ya karbi haqqinsa?,ba fyade yayi mata ba,matarsa ce halak malak da musulunci ya mallaka masa,ya kuma bashi damar zuwa mata duk sanda yaso a kowanne irin yanayi,is he real ja'afar data sani?,gaba daya ya wani karaya yayi laushi?,ja'afar stubborn person sannan kuma Arrogant wasu lokutan,bashi da sauqi ko kadan ita shaida ce koda daga kan qannensa kuwa.     Kwata kwata bashi da control a lokacin,tun daga bakinsa har zuwa zuciyarsa,kalaman neman afuwa ne ke fitowa a bakinsa,yana jin wami guiltiness a jikinsa,yana jin kamar yayi forcing dinta ne ko kuma ya aikata mata ba dai dai ba.     Ja'afar din nada wata irin baiwa ta iya magana da kalamai,shi yasa sau tari anni kan ce "Ubangiji shi yasan nufinsa da ya samyashi mara yawan magana,wala'alla hakan nada nasaba da baiwar iya magana da yake da ita".     Shanyayyun idanuwansa ya daga ya kalli agogon dake bedside bayan wani lokaci,dare ya fara nisa sosai,sai ya janyesu a hankali ya maida kanta,sannan ya miqa mata tafin hannunsa ya miqa mata "Kiyimin wata alfarmar,ki taso na rakaki ki gyaran jikinki,nan din ya baci da yawa" ta jishi sarai,amma batasan ta inda zata fara tashi ba,na farko kunyarsa da takeji ta ninka ta baya sau dubu,na biyu kuma ciwon da takeji a qasanta da wanda dukka jikinta ke mata ta tabbatar bazai barta ta tashi din ba,sai tasa hannu a hankali tadan ture fuskarsa daya matso da ita dab da tata,sai a sannan taji zafin dake jikinsa har ya kusa fin nata,bai bata damar sakeyin tunani na biyu ba ya shammaceta ya dauketa cak,runtse idanunta tayi gam gam saboda motsatan da yayi ya fama mata mikin dake jikinta,duk da batace komai ba amma ta saki wani wahalallen numfashi "Am sorry" ya fada a hankali sannan ya mannata da qirjinsa ya wuce toilet din da ita cikin riritawa da kuma kulawa,tamkar yana dauke da qwai. GURBIN IDO.... Chapter 68 Shafi na sittin da bakwai Ruwan mai dumi ya hada mata cikin bathtub,bata da wani qarfin hanasa gasata don haka ba wani gardama ko yunqurin hanawar da tayi,saidai yadda yaga tana kuka gaba daya ya sake sanya masa tausayinta sosai,kukan da take ya tuna masa da shaheeda,sai ya sanyata a jikinsa sosai yana jin kamar itace,duk da cewa maimunatu ta fita jigata nesa ba kusa ba,son shaheeda a sannan daga shi har ita farin shiga ne,wasu abubuwan sai a hankali,amma maimunatu fa?,a matsayin qwararre yaje mata,baisan cewa cuta ya tarama gangar jikinsa ba sai yanzu,ya kuma juye mata dukka a jikinta,ashe duk tsahon shekarun yana da buqatuwa,amma damuwar da ya sanya cikin ranshi ya hana hakan tasiri,ya san cewa bai mata ta sauqi ba ko kadan,don haka bai hanata kuka ba,saidai kalmar "Sannu,am sorry" har da ta kusa gajiya da jinta daga bakinsa. Sai da ya gama gasata sosai sannan ya bude wancan ruwan ya tsiyaye tas,ya hada musu wa na wankan tsarki,ta dan samu qwarin jiki kadan tayi da kanta,bayan sun gama ya sake hada wani dai still da zasuyi wankan sabulu,sai kawai ya shige bathtub din ya jata cikin jikinsa,dumin ruwan yana ratsasu shida ita,lafewa tayi sosai cikin qirjinsa,lallausan gashinsa ya zame mata kamar matashi,sosai bugun zuciyarsa ke mata tasiri a jikinta,tana jin yadda yaketa sauke qananun ajiyar zuciya kamar yaron da yaci kuka ya qoshi,sai ta lumshe ido kawai tana jin wani sauyi da yake samun duniyarta. Yaye bedsheet din yayi sanda suka fito,sai ya maida abun rufar a madadinsa,wata lallausar mini gown ya sanya mata,ya fidda sock's doguwar socks cikin kayansa ya zura mata,sannan ya sake saka mata wata zip up hoodie jacket mai dogon hannu,don ya fuskanci itadinma zazzabi ne sosai a jikinta,shikam Three quater kawai ya zurawa jikinsa,ya sake rufesu da duvet ya sanyata cikin jikinsa sosai yayi mata rumfa, numfashinsu da dumin zazzabin dake jikkunansu suka fara gauraya da juna. Dukkaninsu haka suka kwana da zazzabi me zafi,har gwara ja'afar gab da asuba nashi ya sauka sosai,nata dinne dai babu sauqi,don rawar sanyi takeyi sosai,ya sake kunne room heater ya kuma lullubeta da kyau amma a banza,dole ya dagata,ya zare mata dukka kayan dake jikinta,ya mannata da fatarshi suka samu good skin contact,nannauyar ajiyar zuciya ya sauke,don sake haduwar jikkunansu sake kunnashi ya soma yi,musamman tudun qirjinta da ya tokareshi da kyau,kai kace da gayya tayi hakan,numfashinsa ya fara canzawa tare da bugun zuciyarsa,ya lumshe idanunsa yana jin yadda take sauke numfashi a hankali cikin galabaita da gajiya,yana tausayinta,bazai iya sake tabata,taci wahalar daya kamata ace ya barta ta sake hutawa da kyau,da yaji abun yana neman fin qarfinsa,sai ya zare jikinsa daga nata bayan yaji zazzabin yadan sauka,ya sanya mata pillow,cikin bacci ta kama pillow din da hannunta da kyau,qaramin murmushi ya subuce masa,yadda tayin fuskarta a hade kamar idanuwanta biyu ya bashi dariya,ya gama saara mata wajen shagwaba da raaki,auta ce ko 'yar fari?,baisan a good awanne ajin zai ajjiyeta ba,yadda ta qanqame pillow din ya tabbatar da idanuwanta biyu ba zata yarda tayi hakan ba. Alwala ya shiga ya daura da ruwa me dumi,abun sallah ya shinfida,ya tsaya sosai akai yana fuskantar ubangijinsa,ya masa baiwa a rayuwa har karo biyu,a cikin wannan rintsin rayuwar da mata na gari ke tsada da wahala,duk kuwa da cewa duniya cike take da tarin mata birjik,amma ta aure wahala take,saidia shi din ya kebanceshi da baiwa ta musamman. °°°°°°°°°sai data yi kusan minti biyar da farkawa amma bata motsa ba,a hankali take shaqar tattausan qamshin dake fita daga jikinta jacket din nashi da har yanzu itace a jikinta,qamshin da babu abinda yake tuna mata sai daren jiya,abubuwan da suka faru suka runga dawo mata,sai ta dinga jin komai kamar a mafarki,kwanyarta ta dinga tuno kalaman da bakinsa suka dinga furta mata,sai ta sauke ajiyar zuciya me nauyi,ta kasa kunnenta taji ko zataji motsinsa ta koma ta sake lafewa?,jin shuru ya tabbatar mata da baya dakin kwata kwata,don haka ta miqe ta zauna sosai tana kallon lokaci,qarfe kusan sha daya da rabi na rana,tun asuba data yi wuf a daddafe tayi sallarta ta koma bata sake farkawa ba sai yanzu. Zaune tayi tana qiyasta da yadda zata miqe,ko ina ciwo yake mata a jikinta,cinyoyinta kamar anyi ajiyar dutse,duk da ya ragu ba kamar daren jiya ba,sai ta yanke shawarar ta sake shiga bandakin ta hada ruwan zafi ta yiwa kanta yadda yayi mata jiya,tana zuro qafarta qafa taqi bata hadin kai,sai ta narke gaba daya zuciyarta ta karye,kada dai ace ya illatata gaba daya ba zata sake moruwa ba?,idan haka ya tabbata da wanne ido zata yima mutane bayani?,take qwalla ta cika mata idanuwa,ba dadewa kuma suka fara bin kuncinta,dai dai lokacin da ya turo qofar ya shigo. Fes fararen idanuwansa da suka sake wani haske suka sauka a kanta,yana sanye da wata hoodie jacket wine color da baqin wando,ya sauke hular a bayansa,sai tattausan baqin gashinsa sake sheqi cike a kansa,ya sake wani fresh dashi,jikinsa na fidda rikitaccen qamshin nan nasa. K'as tayi da kanta tana jin inama bata farka ba,yayin da murmushi ya subucewa fuskarsa,cikin zuciyarsa ya furta "Yanzun ne ya kamata kiyi tsoro me dalili yarinya ba tsoron baya ba na sakalci da shagwaba" takowa yaci gaba dayi zuwa gabanta,yana ayyana yadda zai dasa zazzafar soyayyarsa a ranta,tunda ya fahimci ya ribatu da samun empty heart da bata taba daukan soyayya me zafi irin wadda yake buri ba,so yake tayi masa soyayyar da ba'a taba masa kwatankwacinta ba,yana buqatar ya samu qauna data ninka wadda shaheeda tayi masa,soyayyar da zata zama abar kwatance,ya riga da ya gama sallama mata rayuwarsa,saboda haka bayajin akwai wani abu da zai musu shamaki a tsakaninsu shi da ita. "Gudmorning moon" ya fada da wata murya dake cike da shauqi,shauqin da tunda ya tashi har ya fita ya dawo shine taf a zuciyarsa,wani irin memorable night da bazai taba shafewa a rayuwarsa ba muddin yana da rai "Ina kwana?" Ta fada cikin girmamawa,bai amsa mata ba,sai ya duqa a gabanta,wata kima da daraja ta samu farat daya a wajensa,ba ita kadai ba,hatta anni a yanzun yana jinta fiye da yadda take a wajensa a baya,bare kuma ita maimunatun,hannayensa ya zura ta qasan fuskarta,sannan a hankali in a low sound yace "Kwana na yana gurinki.....get up dear" fuskarta a narke ta tabe baki irin na mutumin dake shirin sakin kuka,sannan ta langabar da kanta gefe guda,ha fahimci tana son ce masa ba zata iya ba,amma baki ya gaza fada,sai kawai ya miqe a hankali,yasa hannu kamar daren jiyan dai a tausashe ya dauketa ya nufi toilet din da ita,yana tafe yana kallonta duk da ta cusa fuskarta a qirjinsa,da zata iya da tace masa ya sauketa,yanzun ma da ranar Allah sake kalleta zaiyi haihuwar daadarta?. Bai sanyata dole kan cire kayanta ba,amma ya tsaya ya gasata kamar daxun,mai ciwo yaji dadin jikinta,sai ta fara son qwacewa,sai ya kamata suka antaya ciki gaba daya shi da ita,dole tayi luf,tun tana jin zafi har ruwan ya fara mata dadi,ya sake tara mata wani sannan ya fito ya barta don ta qarasa. Manyan towel guda biyu tayi amfani dasu,daya tayi daurin qirji dashi,dayan ta lullube kanta ruf,baka ganin komai sai kwantacciyar sumar gaban kanta mai salki,yana tsaye gaba mirror yana kurbar coffee din da ya hado a hankali,ya bude idanuwansa a kan fuskarta. Sosai yaga fuskartan itama tayi fresh,farinta kamar ya qaru ya kuma sirkuwa da jaja jaja,tsigar jikinsa ta zuba gaba daya,ya hadiye sauran ruwan coffee din daya kurba,sai ya dora cup din saman morrow din,ya nufota a inda take tsaye daga gefan qofar toilet din,tana ta karatun ta yadda zata shirya yana cikin dakin,da kuma kayan da zata saka wadanda ba zasu fidda tsiraicinta ba sosai. Idanuwanta a kansa kamar yadda nashi yake a kanta,wani abu mai qarfi yaji yana fusgarsa zuwa gareta,wani abu mai nauyi da tasiri da bai taba jinsa a ransa ba. Tsoro ya hanata motsawa daga inda take,gani take kamar wani abun zai sakeyi mata,ya karanci tsoronta tsaf,sai ya saki murmushin gefen baki har ya isa dab da ita,a hankali ya sauke zip din jacket din nasa qasa,ya kuma balle botiran gaban shirt dinsa me kauri,sai ya qara matsawa taqi gaba kadan ya manneta zuwa cikin qirjinsa,a tare suka sako ajiyar zuciya,yayin da yaci gaba da sauraren bugun zuciyarta yadda yake gudu fat fat,da alama akwai tsoro tattare da ita. A hankali ya zura hannayenta ya zagaya dasu zuwa bayansa ta yadda zata rungumeshi sosai,shima haka din yayi ,ya zagaye hannuwansa ta bayanta abinda ya qara musu kusanci sosai,ta shige sosai cikin rigarsa,wani irin dumi da unique qamshin nan nasa ya sauka a hancinta,sanyin data soma ji bayan fitowarta yayi qaura,sai ya dora kansa saman kafadarsa,bakinsa saitin kunnenta cikin fusgar kalaman bakinsa sakamakon yadda tudun qirjinta ya fara rikita masa lissafi "Relax, don't scare,am not going to do anything angel" wata ajiyar zuciyar ta kuma saki,a hankali yaci gaba da shafan bayanta kamar yadda akema qaramin yaro duk sanda yake rigima,tsahon wasu mintuna sannan ya jata a hankali,suka dinga takawa kamar me koyon tafiya,saboda yasan akwai mikin ciwo a jikinta. Gaban mudubi ya tsaidata,sannan yaja mata kujera ya kuma zareta daga jikinsa yace "Seat here" a hankali ta zauna tana rintse idanunta saboda yadda wajen har yanzu yake mata ciwo,ya lura da hakan,sai ya saki boyayyen murmushi,wani sashe na zuciyarsa kuma na jin tausayinsa kan barnar da yayi mata. Man shafawarsa ya dauko,ya bude ya dora saman mirror din,ya lakato ya daga tattausan tafukan hannunta da kallo da suke jazur, saboda tsaban fari har wani kwanciyar jini sukayi,ya lakata mata man sannan yace "Lemme help you" sai ya koma daga bayanta ya fara shafa mata a baya. Idanunta ta lumshe kawai,zallan mamakinsa suna sake shigarta,kamar ba ja'afar ba,ja'afar din anni da amma,gaba daya kamar wani ja'afar na daban aka sauya mata,dukka ya kwance gaba daya. Wasu abubuwa taji suna mata yawo dukka jikinta,in a romantic way yake mata shafan man,tana iya kallonsa ta cikin madubin yadda gaba daya yanayinsa ya canza, tsoro ya sake cikata,ta riqe kukanta da kyau wanda ke shirin qwace mata,idan yace zai sake wani abu da ita ta tabbatar mutuwa zatayi,ba zata iya sake dauka ba. Sosai ya dinga qoqarin controlling kansa,bayan ya gama shafa mata zuwa inda yasan ba zata iya ba sai ya dauko hand drayer, already ya iya wannan,shike gyara ma su amna da amra kai sanda suna raye,harma shaheeda,tunda dukansu suna da yawan suma,mamarsu ce kawai bata kaisu ba,don su shi sukayo wajen yawan sumar,don baya sati baiyi gyaran fuska ba,tunda ba kasafai yake rage sumar kansa ba. Tsaiwa yayi shi da kansa yana kallon innocent face nata ta madubi bayan ya gama gyara mata gashin ya kuma kame mata shi da band,fuskarta ta fito fayau kuma tayi wani irin fes,idanunta sun sake girma da haske,hakanan siraren labbanta kamar an sake qawatasu,sai ya sunkuya yayi kissing tsakiyar kanta yana lumshe idanunsa. Dukka kayanta noqewa tayi taqi sakawa,daya fita ya bata option na ta saka kayan da taga sun mata a dakin,har nashi luggage din ya bude mata yace ta zaba. Wata farar turtle neck shirt nashi ta dauko,tana da dan kauri,sannan itama dogon hannu ne da ita,a sake take,don ba size dinta bane,ita ta saka,ta tsaya tana duban kanta a madubi,rigar tayi mata kuma tayi mata kyau sosai,saidai kuma tana kunyar ya ganta da kayanshi a jikinta,ta lumshe idanu tana shaqar daddan qamshin dake fita daga jikin tattausar rigar,batasan me yasa qamshinsa yake kashe mata jiki ba,bata gama wannan tunanin ba ya buda qofa ya sake shigowa dauke data leda mai kauri,sai ta bude fararen idanuwanta da sauri. Kamar wani sakarai ko kuma yau ya fara ganinta haka ya saki baki yana kallonta,bai taba ganin kyan rigar ba sai yau data sanyata a jikinta,kallon kallo sukaima juna kafin ta janye kallonta daga kansa,ya tako a hankali zuwa ciki yana ajjiye ledar,zuciyarsa nason ya qarasa gareta amma kuma wani sashen yana masa burki,yana kuma gaya masa "Dole ka bita a hankali,sai ka rage tsoronka daka dasa mata tukunna, ayanzun a tsorace take dakai,dole kadan nisanceta kadan" da wannan shawarar ya samu waje ya zauna,ya fidda komai dake cikin ledar,breakfast ne da qamshinsa ya cika dakin,da alama wadanda suka tsarashi sun san sirrin girki "Oya,come and take your breakfast" yayi maganar da mayen kallon nan nasa,qas tayi da kanta,sannan ta fara takowa a hankali,yabi qafafunta da kallo,yadda take tafiyar kawai ya isa ya shaida maka lallai wani abu me girma ya faru da ita. Suna cikin yin break din wayarsa tayi qara,sai ya duba me kiran,jabir ne kamar yadda ya zata,daga wayar yayi,amma sai ya sanyata a hands free ya dorata saman cinyarsa,idanuwansa akan fuskarta yayi masa sallama "Yallabai,wai anya kuwa lafiya?" "Me ka gani?" Ya tambayeshi kai tsaye "Jiya nayita bugu na baku dinner dinku,yauma da safe haka zamu wuce strolling da fa'eema zata dan ga gari shima shuru" sai da yayi sipping coffee dinsa sannan yace "To sai akayi yaaya?" Dariyar da yaketa riqewa ce taso fitowa,ya sake danneta "A'ah wai kada ka mace ma mutane a daki ne,shi yasa nake cigiyarka,kuma jiya da dare naji dakin kamar ba lafiya ba,har zan kawo dauki fa'eema ta hanani" tsaki yaja yana saurin kashe wayar daga hands free din da ya sakata ya karata a kunnensa "Amma qur'ani cewa yayi idan baku samu kowa cikin gida ba kada ku shigesu har sai an muku izini,idan ma akace ku koma to ku koma,na meye wannan bin qwaqwafin?,ni bazan huta ba?,ko kai kadai ne me iyali?" "Allah ya baka haquri,daga abun arziqi?" Yayi maganar yana tuntsirewa da dariya,fatima nata mintsininsa da yi masa sign na ya daina don Allah,don shike maganar amma ita kejin kunyar, batasan yadda zasu hada ido da ja'afar ba,tana matuqar girmamashi "Inda kazo min daki a jiyan ma saina farfashe maka kai,banyi laifi ba" "Sai ogaaaaa,tuba nake" ya fada dariyarsa na fita gaba daya "Da anni fa zan kira.....wallahi nace mata ba lafiya ba" ya sake fada cikin wani karsashi tare da son sake tunzuro ja'afar din "Sai ka bada himma" daga haka ya yanke wayar kit,wani murmushi da baisan daga inda yake ba na fita a fuskarsa, jabir jabir?,dan uwan da babu kamarsa,yasan ya fahimci komai,don yaga gilmawarsa a fitar da yayi,ya kirashi ne kawai ya zolayeshi,kuma sai yayi din sannan hankalinsa zai kwanta,jabir ya masa haka ina ga anni,gardin case kenan,ya fada a ransa. 69 Ya tabbatar anni ba zata qyaleshi ba ba zata daga masa qafa ba,ko a yanzun ma baisan wanne kalar tijara zata masa ba idan ta fahimci abinda yake faruwa. "Gaskiya kana sakani jin kunya wallahi" fatima ta fada tana jifan jabir da harara,ga mamakinta murmushi ne kwance saman fuskarsa,amma kuma hawaye ne ke shirin sauko masa,sosai hankalinta ya tashi "Sweetheart.....menene?" Hannunta ya kama ya riqe gam yana duban fuskarta "Real version na ja'afar dina ne ya dawo, alhamdulillah.......bansan wanne kalar godiya zan wa Allah ba,bansan wanne kalar godiya zan yima maimoon ba......jikina ya bani,sannan yanayinsa ya nuna tun daga yadda yake amsa wayata,my ja'afar has back" Sai siraran hawaye suka biyo gefan hancinsa,ajiyar Zuciya ta sauke,ta kuma riqe tafukan hannuwan nasa da kyau "Alhamdulillah,ita zaka yita maimaitawa,sai kuma ka yawaita yima annabi salati saboda nuna zallar godiyarka ga ubangiji" kai ya jinjina yana sake qaunar matarsa,ko yaushe kalamanta akwai Allah a ciki "In sha Allah,bansan da waa zan raba wannan farincikin ba bayan ke.....kinsan inda daa ne,ko uffan bazaice min ba,har nayi na gaji na gama,abinda bamu saba dashi ba kenan,duk miskilancin sa babu ni a cikinsa" kai ta jinjina,ita kanta taji dadin hakan sosai. Wuni sur a dakin sukayishi shi da ita,shima kuma jabir bai sake namansa ba,sosai ta dinga dari dari dashi da kuma jin kunyarsa,don da daddare bayan ya sake sanyata ta gasa kanta,tana tsaye bayan ta fito amma taqi kallonsa,sai ya qaraso gabanta,ya dora hannunsa saman nata sannan ya dagasu ya dora kan kumatunsa na hagu da dama "Me yasa bakison kallo na?,har yanzu tsoro na kike?,irin tsoron da nake gani a idanunki yanzu,irinsa na gani sanda hannuwana sukayi kuskuren marinki......na baki dama,ki rama marinki adadin yadda kikeso" zame hannunta tayi da sauri tana girgiza kai,ta kuma kasa ce masa komai "Just do it....kar kiji komai" sake girgiza kanta tayi,bakinta yana rawa "N......na yafe" shuru yayi yana sake zuba mata idanu,hannayensa zube a aljihun wandonsa yana kallonta,baya gajiya da kallonta kwata kwata,sai ya taka a hankali ya rungumeta ta baya,cikin wani sauti da yafi kama da rada ya soma magana "Tun randa hannuwana suka kai kan fuskarki na gaza mantawa da abinda nayi mikin,nakeji ban kyauta ba,ban sani ba.....ko tun a sannan ubangiji ya zuba dukkan abinda zai zuba a tsakaninmu?,a lokacin da nake jin duk duniya ba wanda ya kaini rashi,na mareki ne a lokacin da nake cikin tsananin damuwa na rasa shaheeda da amra ta,bisa dukkan alamu Allah ya bani wata shaheedan......zaki samar min new amra?" Karon farko da murmushi mai cike da kunya ya qwace mata,sai ta juyo ta cusa kanta a qirjinsa tana murmushi,kafin kuma ta zare jikinsa a nata,binta yayi da kallo,baiso hakan ba,yaso ne su dan jima a tsaye ko hakan zai rage masa zafi. °°°°°°°°°dukka kwanakin ukun da suka biyo bayansu kusan biqinta ya dinga yi,bai sake neman komai daga gareta ba,saboda ya tabbatar ta jigata a hannunsa,duk kuwa da cewa kawaici kawai yakeyi da kuma qoqarin kame kansa,amma yana ji a jikinsa,har yanzu bata sake masa jiki yadda yakeso ba,yanata qoqarin ganin yabi kowacce hanya data kamata da zai dasa mata soyayyarsa a ranta mai zafi,amma baiga alamun komai ba daga gareta,saidai shi din ya yadda da kansa,ya kuma tabbatar babu.macen da zata iya tsallake tarkonsa. Shirinsa bai kammala ba,don haka sanya jabir ya gabatar masa da batun komawa sai ya dubeshi "Wai nikam duka kwana nawa mukayi?" Cikin mamaki da dariyar yadda lissafi ya bacewa ja'afar din nasa yace "Iya kwanakin da na gaya maka mana,har ka manta?" "Gani nayi kamar bamu qarasa ba ko?" Yayi tambayar kamar yana kokwanto,dariya dai sai data zowa jabir "Akramakallah mr ja'afar,kace kawai honeymoon yayi dadi" cikin basarwa ya dauke kai ya kuma sake hade fuska ganin jabir din yanason ramfoshi "Mtsweew,matsalata dakai kenan,kawai akwai wasu ayyuka ne da ban kammalasu ba,banason kuma su zame min kwantai" "Gaskiya ne yallabai.....saika bada himma,zaka iya kammalasu nan da yammacin gobe kafin tashin jirginmu ai,musamman idan ka samu network me kyau" kai tsaye ya fahimci inda jabir yasa gaba,sai ya shareshi kawai bai tanka masa ba. Gyaran murya jabir din yayi "Munata waya da anni ne,tana complain na an koma makaranta bamu dawo ba,maimoon din anata kira daga makarantarsu,har sunci satin farko". A sukwane ya waiwayo yana duban jabir din,sai da yaji zuciyarsa ta tsinke,tabdijan,ai shi gaba daya ma ya ma manta da wani batun makarantarta,ci gaba yayi da duban jabir din kamar wanda ke neman mafita daga garesa "Yaya dai?" Ya tambayeshi yana dubansa,kansa ya dauke "Nothing,kawai babu yiwuwar ta koma din" "Banjin anni zata bari gaskiya,don tanata maganar kada a katseta" "Eh,tunda ita ke aurenmu ba ni da ita?" Baki jabir ya bude dariya na matuqar cinsa "Annin?" "Eh maryam farouq kumo ba" idanu jabir ya fidda gaba daya sannan ya miqe shima kamar yadda ja'afar ya miqe "Ah wallahi ka sha kaina,kafi qarfina,an tashi a wasan,zaka maimaita kuma a gaban wadda ka kama sunanta" "And so what?" Ya fada cikin rashin damuwa,tunaninsa a yanzu shine kawai yadda zai fuskanci anni da maganar qin maidata makaranta,musamman idan ya tuna yadda kwashe dashi sanda take shirin hanashi kaita,hannunsa ya sanya ya shafi sumar kansa tare da furzar da iska daga bakinsa. °°°°°°°°°°°tun saura awa guda jirginsu ya tashi zuwa nigeria suka isa OR tambo international airport din,don haka dole suka zauna a gates zaman jiran cikar lokaci. Jabir da ja'afar gaba daya suna waje basu shigo ba,sai ita da fatima,jifa jifa suna taba hira da ita,saidai hankalinta gaba daya ya kasu kashi biyu. Kashin farko yana ga qofa,tana duban ta inda ja'afar din xai bullo,yau kawai da suka dauki mintuna ba kusa da juna ba sai takejin kamar tayi missing wani muhimmin abu,daya kuma gefen hankalinta yana ya daukuwa ne ga wasu matasan yara su biyu,dayar a qalla zatayi shekara goma,yayin da dayar kuma takai kusan shekara sha biyar,tunda suka zauna a wajen take kallonsu,fuskarsu taketa kalla,sai take ji cikin jikinta da ruhinta kamar ta sansu,kamar ta taba rayuwa da ita,abu na biyu kuma mamarsu da tunda suka shigo wajen fuskarta na kallon babban glass dake wajen,wanda ta nan kana iya hango farfajiyar airport din da jiragen dake girke a wajen,shuru ita daya,bata magana da kowa,saidai lokaci bayan lokaci takan waiwayo tayi ma yaran dake amfani sa wata tab da alama game suke,ta musu magana ta sake maida kanta ga wajen,kamar wadda ke cikin wani zuzzurfan tunani. A duk sanda tayi magana sai maimunatun taji gabanta yayi mummunar faduwa,saboda sautin muryar irin tata sak,kuma irin ta daadarta,saidai sautin yafi nata nuna shekaru,batasan mene yaketa fusgar hankalinta akanta ba,ta kuma gaza ganin fuskarta,sannan kuma ta gaza dauke idanuwanta daga kan 'yanmatan. Sau biyu babbar ciki na kallonta,itama sai ta maida kanta ga tab dinta,bata kuma sake dagowa ba,taso sosai ta daina kallon nasu don kada su tsargu,amma kuma ta gaza hakan,tana jin kamar ana fusgar idanuwanta ne. Cikin haka taji maqogaronta ya dan bushe kadan,sai ta dubi fatima "Bari na samo ruwa" "Ehenn,ki tahomin dashi" a nutse ta miqe,ta fara takawa zuwa wajen dispenser dake girke a gefe guda,wadda daura take da matar da hankalinta keta daukuwa a kanta,dab da zata qarasa ja'afar din ya shigo wajen,da fari bata ganshi ba amma shi ya ganta,daga bisani ne taji kamar qamshinsa ya cika wajen,sai ta waiwaya,yana tsaye yana kallonta kansa tsaye,baya ko jin nauyin mutanen dake zazzaune a wajen. Ta soma karantar da yawa daga cikin dabi'u da halayensa,murmushi yake mata,amma idan normal mutum ne ya kalleshi ba lallai kai tsaye ya fahimci murmushin ne,wani irin sirritaccen murmushi,sai ta dakata daga takun da take har ya cimmata,kansa tsaye ya saqalo hannunta cikin nasa,yadan ranqwafa kadan ya rage tsahonsa yakai.bakinsa ga kunnenta "Banason ki dinga yawan zirga zirga,akwai idanuwa da yawa a nan,ina zaki?" Kaf yawun bakinta ya dauke,saboda yadda ya saukar mata da kasala,ya kuma aike mata da wani abu da ya sanya tsigar jikinta zubawa,musamman yadda yake murza tafin hannunsa cikin nata "Ruwa zan sha" ta motsa labbanta ta fadi murya can qasa,bata ma zaci zaiji ba,sai taji yace "Okay,muje na rakaki" tare suka jera suna takawa zuwa wajen,idanuwan mutane da yawa yayi kansu,musamman jajayen fatar dake wajen wadanda suka.kasa boye zalamarsu "Nice couple,perfect match.....wow" sune irin sautukan da suka dinga fadi qasa qasa,duk wanann abun hankalinta nakan matar,har suka isa gaban dispenser din,ya dauki disposable cup din ya fara taara mata ruwan. A hankali matar ta waiwayo tana duban yaran nata da idanuwanta dake nuna zallar jigata da damuwa irin wadda ke sanya idanu su xuge kamar ka shekara kana kuka "Idan daddynku ya kira fa ku sanar mini" ta qarasa maganar idanuwanta na sauka kan fuskar maimunatu da ta waiwayo gaba daya zuwa gareta. Cak tunaninta da kwanyarta suka daskare suka daina aiki na wucin gadi,kafin kuma su dawo dai dai,ta miqe tsaye zumbur tana duban maimunatu wadda ta zame hannunta daga na ja'afar,tanason qafafuwanta su dauketa su kaita inda matar ke tsaye amma sunqi mata wannan aikin "Maim.... maimunatu ce?" Ta tambaya bakinta yana rawa don kawar da shakku "Umma sa'adeee" ta fadi sunan da wani irin qarfi sannan ta kwasa da mugun gudu tayi wajenta,tana isa umma sa'aden ta bude hannuwanta ta kuma rungumeta da kyau,sannan dukkaninsu suka saki kuka a tare kamar ransu zai fice. Kiran sunan juna sukeyi,kowa yana jin kamar a duniyar mafarki yake,yayin da yaran matar suka zubar da duk abinda sukeyi suka qaraso wajen,cikin tashin hankalin kukan da mamansu takeyi suka tsaya carko carko suna kallonta gami da kiran sunanta. Tuni ja'afar ya riga jabir isowa wajen,shi da fatima na tsaye a bayansa shima cikin rashin fahimtar meke faruwa?,zaya matsa gaba kadan ganin yadda maimunatun sa ke kuka jabir ya riqeshi,saboda ambaton sunanta da maimunatu tayi ya tuna masa da ko wacece ita a rayuwar maimunatu. Taga tagar da sa'ade zata fadi yasa maimunatu da yaranta tarota,ta samu ta tsaya sosai tana sake kiran sunan maimunatu,gami da dagowa tana riqe da fuskarta,wasu irin hawaye masu zafi suna mata zirya a kuncinta,tana kallon fuska mafi soyuwa a fuskar maimunatun,fuskar 'yar uwarta qwaya daya tal data mallaka wato shatu "Umma ki zauna,kinga shirin faduwa kike" diyarta ta fada cikin damuwa,sai maimunatu ta kamata da kyau suka koma saman abun zama suka zauna,tana riqe gam da hannun maimunatun kamar zata sake bace mata. Sai a sannan idanuwanta ya hangi su ja'afar dake tsaye,suma sai lokacin suka ga fuskarta da kyau "Momma?" Jabir ya fada yana dubanta "Jabir?" Itama sa'ade ta fada tana kallonsa,sai ya matsa daga inda fatima take ya tako gabanta "Barka da rana momma" "Jabir barka kadai,kai da waye?,daga ina haka kake?" Ta tambayeshi fuskarta jiqe da hawayen da taketa qoqarin tsaidasu,waiwayawa yayi ya kallo ja'afar da dukka hankalinsa yake kan maimunatu,kukan da take yana ta tabashi,banda jabir ya hanashi da tuni ya isa gareta ya janyeta "Dude" yayi kiran ja'afar a tausashe,sai a sannan yakai fuskarsa kansu,ya gane fuskar matar,matar baaba ambassador ce,kuma tamkar uwa take a wajensa,sign jabir yayi masa na ya matso,don yana tsammanin ja'afar din bai ganeta ba,saboda yasan ba shiga sha'anin mutane yakeyi ba,sai ya waiwaya ga fatima itama ya kirayeta. "Ja'afar?" Ta kira sunansa shima sand ya iso din "Nigeria zamu wuce,munzo hutu ne na sati daya,ga mijin maimunatu" wata ajiyar zuciya me hade da qwalla sa'ade ta sauke "Allah kai ne Allah,Allah mai yadda yaso da bayinsa,Allah mai qaddara dukkan abinda zai afku,ubangiji kai kasan kalar abinda ka shirya har ka qaddaro min matsalar da bazan iya fita daga qasar daka ajiyeni ba tsahon shekaru,sannan kuma ka qaddaramin fitowa daga wannan qasar a yau,Allah na gode maka" sai ta rungume maimunatun sosai suna sakin sabon kuka. Idanu ja'afar ya runtse kana ya budesu,bayason kukan da maimunatu take ko kadan,yana jinsa yana sauka can tsakiyar zuciyarsa,kiran da akema wadanda zasu tashi a jirginsu ya katse komai,saidai kuma sa'ade taqi rabuwa da maimunatu,tana riqe gam a hannunta,har zuwa sanda aka kammala komai suka shige jirgi. 70 Seat din kusa da ita fareeda diyar sa'ade ta barwa maimunatu,dukkansu suna ta kallon maimunatu cike da zumudi a zukatansu,saboda suna da.labarinta sarai,sannan ita fareeda tana dan tuna wasu abubuwa da suka faru,tunda da dan wayonta suka bar gembu. Cikin tafiyar awannin da suka cur hannun sa'ade yana cikin na maimunatu,kaf maimunatu ta labarta mata dukkan abinda take da buqatar sani,saade ta lumshe idanu hawaye masu dumi suna fita akan fuskarta "Wata shari'ar sai a lahira,inno taci amanata taci amanar shatu,Allah ya jiqanki 'yar uwata,matsala na samu akan dukka abinda ya shafi bayanaina,aka samu wasu suka dauka sukayi amfani dasu suka aikata laifi,ya zamana ni ake zargi aketa nema,wannan dalili yasa abbansu yayimin kyakkyawan boyo,sannan akaci gaba da bincike,don yasan muddin ya fiddani aka kamani babu mai fitar dani sai Allah,wannan dalilin ya hanani dawowa gareku,saidai duk da haka nayi amfani da abbansu nayi aike gembu,waya kudi da kaya,ina amfani da wani boyayyen layi ina yawaita kiran inno akan yaya kuke ya lafiyarku?,koda yaushe nunamin take kuna nan lafiya,bana jimawa akan waya shi yasa bana samun damar cewa a bani ku,aike nake akai akai na kudi da kaya ashe baya samunku,ashe sun gama shirya abinda suka shirya,ashe sun cutar min da shatu na,sun kuma cutatar dake kema" sai suka sanya kuka gaba dayansu hannuwansu cikin na juna. Dogon numfashi ja'afar dake daga can bayansu ya saki,tunda suka zauna hankalinsa da nutsuwarsa tana kansu,duk da baijin abinda suke fada amma yana iya fahimtar kuka suke,yana kuma ji a zuciyarsa maimunatun kuka take da gasken gaske,yana ta son ya daure amma ya gaza,yana jin kukan nata yana tabashi sosai "Please,ka gaya mata ta daina sakata kuka haka" ja'afar ya fada idanuwansa a kansu,kallonsa jabir yayi baki galala "Kai,surukarka ce fa,sannan kuma mamanka ta wani fannin,ita za'a cewa ta daina saka matarka kuka?,bazan iya ba" shuru ya ratsa tsakani,kawai sai ganin ja'afar jabir yayi yana miqewa tsaye,da alama zuwa zaiyi kenan ya shaidar mata da kansa. Saurin damqoshi jabir yayi,don yasan tsaf xai aika "Haba mana,kayi haquri mana romeo,dole fa suyi kuka,don bakasan komai bane" da mamaki ya juyo ya dubeshi,duba na son sanin abinda bai sani din ba,ba tare da yace komai ba jabir ya karanceshi,sai yace dashi "Zauna na fada maka" ba musu ya koma ya zauna din,ya kuma tattara dukka hankalinsa ga jabir,yayin da jabir ya soma magana a nutse,dama.ya jima yana fatan zuwan wannan lokacin da ja'afar din zai san labarin maimunatu,yasan halinsa sarai,yana da wani irin tausayi na daban q zuciyarsa,sanin labarin nata zai sake haifar da wata alaqa mai girma a tsakaninsu,inda a baya ne,yasan halinsa......bazai taba tsaya ya saurareshi ba,coz bashi da interest,idan kuma yayi loosing interest akan abu babu mai sanyashi dole face mutum biyu zuwa uku a duniya,anni abbi da amma. "Ashe nesa a kusa take?,ke din matar ja'afar ce,ja'afar kamar d'a yake a wajena,saboda dan qanwar abbansu fareeda ne" "Amma?" Maimunatu ta fada tana dan fidda idanu cikin mamaki,a karon farko sa'ade ta gyada kai "Qwarai,wala'alla banda matsalar dana samu.....wadda sai yanzu ta warware,dani za'ayi bikinku,nasan anyi bikin,amma ban san amaryar ba,don a sannan ba cikin hayyacina nake ba,yau sati daya kwata kwata da bayyanar gaskiya,aka kuma damqe wadanda suka aikata laifin,wanna shine ya bani 'yancina" kai maimunatu take jinjinawa,lallai soyayya ta gaskiya abace mai kima daraja da kuma wahala,ta jinjinawa abbansu fareeda da yadda ya bata dukkan kariya,duk da cewa basa a qasarsu,amma ya tsaya mata kai da fata don ganin ya kula da amanar da aka bashi "Yaranki nawa diyam dita?,duk da nasan ba zai wuce guda daya ba tunda baku fi shekara da auren ba,saidai idan kinyo gadon dangin tamu daadar masu haifar twins" kunya ta kama maimunatu,saita kifa fuskarta a kafadar sa'ade,tana jin kamar ita da daadarta suke magana "Babu ko daya" murmushi tayi tana gyada kai "To Allah ya kawo masu amfani da albarka,yasa kiyita haifa mana bibbiyu,zuri'ar shatu na tayi dogon baya" tayi maganar cikin rauni dajin zafin mutuwar 'yar uwarta,wanda bata sani ba gaba daya sai kwanan nan. Hawayen fuskarta ta dauke,ta waiwaya kadan baya inda su ja'afar suke "Amma naji dadi da naga yadda ja'afar yake miki,da alama akwai tsaftatacciyar soyayya a tsakaninku" a kunyace ta saki murmushi tana yin qas da kanta,sai takejin kamar umma sa'aden tana iya karanto abinda ya faru tsakaninta da ja'afar din kwanaki biyar din da suka shude,don har yau bataji tafiyarta ta koma dai dai ba yadda take ada,sannan kuma ta fahimci akwai sauran dan ciwo ciwo a jikinta. Jin bata amsa ba sai ta dora "Haka nake fata,ki samu mijin marainiya,kuma ina da cikakken fatan cewa zaki samu haka daga ja'afar,indai yaro yana gadon dabi'u daga mahaifiyarsa,aishatu mutum ce nagartacciya,kawai qauna mai tsafta tsakanina da ita,bansan yaya zataji ba sanda labarin KE JININA CE ya risketa" sa'ade ta qarashe maganar tana gyada kai murmushi na kubce mata. Duk yadda umma sa'ade taso ja'afar yabar mata maimunatu su wuce gidanta ko kwana daya suyi amma ya murje idanunsa,bai ma yarda ta ganshi ba,don tuni ya isa motarsa yayi zamansa a owners corner yana jiran isowarta,awannin data dauka ba tare dashi ba sai yake jinsa kamar wanda ya rasa wani sashe na jikinsa,ya sauke hannunsa da yake duban lokaci dai dai sanda take takowa zuwa gaban motar,fareeda da umma sa'aden suna biye da ita. Sosai ya zuba mata idanu ransa yana motsuwa,yana kuma tuna labarinta da jabir ya bashi,wani irin nau'in tausayi na musamman na ratsa zuciyarsa kamar zai narkar da ita,how she survive?,rayuwa ba uwa ba uba?,babu yaya babu qani?,ba soyayya ba kulawa?.......tabbas ta cancanci samun komai,ta cancanci ta samu duk wani abu data rasa a baya,sai ya lumshe idanunsa sanda suke gab da motar,yana daukarma kansa wani alqawari,wanda ba wanda ya gayawa,tsakaninsa ne da ubangijinsa kawai. "Ina fatan za'a kawomin ita ko ni ayimin alfarma nazo na ganta ko yallabai?" Sa'ade ta fada tana murmushi,kai ya jinjina mata da nashi miskilallen murmushin ya amsata a taqaice "In sha Allah" tasan halinsa ba tun yau ba,don haka itama bata wani damu sosai ba,ta maida qofar ta rufe musu tana musu fatan sauka lafiya,kafin itama ta juya zuwa motocin da suka zo daukarta,zuciyarta cike fal da kewar maimunatu,wanda inda so samu ne su kasance tare,su kwana gado daya tana sake jin labarin rayuwarta. Bata gama dai daita zamanta a cikin motar ba ta tsinci hannunta cikin nasa,ya daga hannun nata a hankali ya cusa cikin qirjinsa yana lumshe idanuwansa. Shuru tayi kamar yadda shima yayi shurun,tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa fat fat da qarfi bisa qaramar tazara sosai a tsakani,mintuna kusan uku suka kwashe a haka sannan ya bude idanuwansa ya azasu a kanta "Awa shida kawai?,ta yaya zan jurema wasu awannin da suka fi haka tsaho da yawa?" Ya fada da mugun taushin,salon maganar daya haifar mata da wata kasala da kuma wani yanayi na daban a zuciyarta,saidai ta share ta kuma danne,taso ta zame hannunta amma ya hana hakan faruwa,yaci gaba da riqon hannun nata cikin nasa. ^^^^^^^^^^Ajiyar zuciya mai nauyi ta sauke sanda ta fito daga wanka,gajiyar da bata jita ba a daxun yanzu tana sauko mata,ta bata kusan awa uku,tunda ta shigo dakin take waya da 'yan sannu da zuwa gami da zolaya a fakaice,su laila harma da afra,wanda wayar tasu ta sake qara mata kwadayin komawa makaranta,saboda ta bata labarin yadda aketa zuba karatu,don ba zasu jima ba zasu zana jarabawar qualifying su wuce zuwa ss three kai tsaye. Tsaye tayi gaba mudubi sanye da towel hoodie robe fara tas,idanuwanta nakan kayanta data gama shiryawa tsaf na komawa makaranta tun kafin suyi wannan tafiyar,tafiyar data zame mata mabudi kuma mafari na kalolin rayuwa iri daban daban. A hankali yake saukowa daga samansa hannunsa riqe da wayarsa yana dannawa,shima yayi wanka ya canza kayansa zuwa wata lallausar over size shirt da three quater wanda ya tsaya masa iya qaurinsa. Karo na uku idanuwansa suka sauka a sashenta,ya sake canza akalar tafiyarsa zuwa qofar sassan,yayi knocking na wani lokaci,sannan yasa hannu ya murda handle din amma sai ya jishi a riqe gam,hannunsa ya daga yana kallon tafin hannunsa da ya danyi qura,mamaki ya kamashi,jikinsa kuma ya bashi lallai wajen ba kullewar dazu ko jiya bane,amma ina ta fita ba tare da izninsa ba?,ina taje?,bayan ya bar mata digits din da zata nemeshi?,bashi da wannan amsar,don haka ya juya yana barin wajen zuciyarsa na sosuwa,ransa kuma fal da bacin rai. Samun kansa yayi da nufar sashenta,ya buda qofar ya tura,wannan sassanyan qamshin nata da ya kama sashen har yanzu yana nan daram,sai ya lumshe idanu yana nufar qofar dakin da yake jin tana ciki,tunda dashi tafi amfani. Har ta gama igiyar robe din ta soma kwancewa taji an turo qofar dakin,sai ta tsaya cak cike da mamaki tana dubansa,don batayi tsammanin ganinsa a dai dai lokacin ba,tana ganin lokacine da zata sake tunda zaya zauna a sassansa. Yana kuma kallonta yana sake takowa zuwa ciki,wani abu kuma yana narkar masa da zuciyarsa,wankan da tayi ya sake sawa fuskarta tayi fresh sosai,akwai sauran lema a gashin girarta da kuma gaban kanta,zuciyarta ta shiga bugawa sanda taga yana nufota direct,amma kuma sai ta gaza daga qafafuwanta har ya cimmata. Dab da ita ya tsaya wanda taku daya zaiyi ya hade duk wata tazara dake tsakaninsu,a nutse ya daga hannunsa ya dora saman igiyar rigar,jaa daya yayi mata ta ware,rigar wankan ta fara ware kanta da kanta, tunda dama igiyar ke riqe da ita. Cikin gigita ta sanya hannunta ta damqe gaban rigar,qaramin murmushi ne ya subuce masa yana duban idanuwanta da suka hautsine da tsoro,har yanzun da sauran aiki kenan ya raya a ransa,yana ci gaba da kallon nata ya zura hannunsa ta tsagar gaban rigar,bata ankara ba ta tsinci sassanyan tafin hannunsa saman cikinta saitin cibiyarta. Cak numfashinta ya dauke na wucin gadi, kafin ta samu nasarar fusgoshi kuma hannunsa ya fara yin sama,har ya samu nasarar isa muhallin da taketa bawa kariyar,sai ji tayi ta ratsa hannuwan nasa a tsakaninsu da wani salo da ya sanyata dauke wuta. Qugunta ya riqo da kyau sanda qafafunta suka soma rawa,ya matso da ita jikinsa sosai yana sanya hannunsa ya zare hannuwanta dake riqe da gaban rigar,sannan a hankali ya hada tafin hannunsa da ainihin fatarta mai santsi da laushi ya fara zame rigar gaba daya daga jikinta. Qanqameshi tayi da kyau don hana faruwar hakan,ta tabbatar idan ya samu nasarar rabata da rigar komai zai iya faruwa,don babu wani abu daya rage a jikinta sai ita,cikin rarrabewar numfashi da yadda laushin fatarta ke shirin zautar dashi ya dora bakinsa saman kunnenta "Don't scare,baccin gajiya kawai nazo muyi" sake qanqameshi tayi tsigar jikinta na tashi,bakinta na rawa tace "Ammm.....bar.....bari na saka riga" dago fuskarta yayi da kyau yana duban tsakiyar idanuwanta da idanunsa da suka soma kaduwa,kamar bazaiyi magana ba sai kuma yace "Waye ya gaya miki saka riga ya halatta a irin wannan lokacin?,this is unfair....kamar ha'inci ne fa?,ya zaki lullubemin abun rufar da babu kamarsa a duniya da wata suturar da bata kama qafarsa daraja ba?" Ya fada cikin wani irin shauqi da baisan gana bayyana ba,ya kuma juye mata dukka nauyin maganganun hade da nauyin qwayar idanuwansa,gaba daya jikinta sai ya saki,ta runtse idanuwanta,tana sauraren yadda yake rabata da rigar gaba daya,sannan ya dauketa kai tsaye zuwa kan gadon bayan ya sauke dukka labulen dakin ya kuma rage hasken qwayayen dake ciki,sai dakin ya bada wani ni'imtaccen yanayi. Sosai ya manne fatar jikinsu waje daya,ya boyeta cikin faffadan qirjinsa,kusan tare suka saki ajiyar zuciya,ya sanya hannunsa saman kanta a hankali yana shafar sumarta,idanunsa a rufe yana jin bugun zuciyarta,kana daga bisani kuma yaji ya sauya,alamun dake nuna bacci ya dauketa,hannunsa ya dauke daga saman kan nata,ya jata jikinsa sosai yana jin kamar ya bude qirjinsa ya sakata a ciki,babu jimawa shima wani daddadan bacci yayi awon gaba dashi. *Arewabooks:Huguma* #gurbin ido ❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥❤‍🔥 *_ZAFAFA BIYAR din samari ne a rayuwar INAYAH,kowanne a cikinsu akwai wani murdadden Al'amari da ya shata layi tsakaninsa da ita,wawakeken sirri wanda a koda yaushe take kiransa da SANADIN LABARINA_* *_Amma babban abun mamakin a koda yaushe shine,ita dai tasan cewa BABU SO tsakaninsu MEYA KAWO SHI?_* *_Duk da haka tana tunanin yun qundun bala ta fitar da FARHATUL K'ALB a cikin ZAFAFA BIYAR din samarinta,duk da batason su zame mata GURBIN IDO wanda har kullum ba ido bane_* 😄😄😄😄😄😄😄 *YA KUKAJI SALON MASU KARATU?* *YADDA SALON YA BAMBANTA DAKO YAUSHE HAKA LABARAN SUKA BAMBANTA DA DUKKA LABARANMU NA BAYA* INAYA(riba biyu)___mamughee SANADIN LABARINA___Rano BABU SO___Billynabdul FARHATUL K'ALB___Miss xoxo GURBIN IDO____Huguma *ZAKI YARDA AYI TAFIYAR NAN BABU KE MADAM?* *_GARZAYA KI BIYA NAKI KUDIN KAN FARASHI KAMAR HAKA_* Biyar:::1k Hudu:::700 Uku::::500 Biyu::::400 Daya:::300 *_zaki saka kudin ta wannan account number din_* HAFSAT UMAR KABIR 2270637070 Zenith bank *Saiku tura shaidar biya zuwa ga* 07040727902 *IDAN KUMA KATIN WAYA NE ZAKU TURA TA NAN TARE DA SHAIDAR BIYAR* 09134848107 *_THANKS FOR CONTINUES PATRONAGE_*🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰🥰 71 Duk yadda ta zata zai barta ne ta huta ita daya hakan bai samu ba,don hatta da girki a ranar data musu na a abincin dare yana tare da ita a kitchen,waya ce a hannunsa yana duba saqonni,amma kuma ya kasa ya tsare da idanuwansa,gaba daya ya azata mata wani nauyi,baya minti uku cikakke bai dago ya ritsata da idanuwansa ba,duk sai tabi ta rude ta kuma gaza sakewa,dalilin hakan har ta yanke hannunta. A razane ya aje wayar,ya kuma sauko daga saman cabinet din kitchen din da yake zaune a kai,ya riqe hannun da kyau yana kalla a nutse "Hold on,ina zuwa" ya fada yana fita a kitchen din da dan sassarfarsa,babu jimawa ya dawo da first aid box "Zauna anan" ya fada yana nuna mata inda ya tashi dazun,ba musu ta zauna,saidai yana bude akwatin hankalinta ya tashi,ta fidda idanu tana zaton ya iya allura,har ta kasa boyewa "Don Allah......don Allah kada kiyimin allura" cak ya tsaya da neman cotton wool din da yake,ya daga shanyayyun idanuwansa ya zube a fuskarta,karon farko tunda suke dashi taga murmushi na zahiri saman fuskarsa wanda har yaso ya hadu da qaramar dariya,fararen jerarrun haqoransa suka bayyana,sai taji kamar jinin jikinta ya daskare a wajen "Haka murmushi ke masa kyau?" Ta tambayi kanta da kanta "Matsoraciya......kin taba ganin captain yayi allura?" Tambayar tadan sanya mata nutsuwa data tuna shi din ba likita bane,sai kunya ta kamata tayi qas da kanta,shi kuma ya janye idanuwansa yana ci gaba da neman audugar "Ban san me yasa.....fillon da tayi kiwo da dabbobi masu yawan gaske cikin daji.....babu qawa babu aminiya amma take tsoron allura ba,kin bada fulani fa(niko nace yo dama ai sun jima da baduwa,muggan ragwage ne😏🤨🤨)" cike da mamakin maganarsa take kallon fuskarsa,saidai ko sake daga kai baiyi ba bare ya nuna yasan shi take kallo,maganganunsa sunyi kama da maganganun mutumin da yasan wani abu game da rayuwarta,bai sake tankawa ba haka itama,sai ya kama hannun nata a tausashe ya fara goge mata wajen yankan,ta runtse idanunta saboda zafin da ta danji,sai ya dakata yana duban fuskarta da rufaffun idanuwanta,yaga yadda ta kebe baki ta kuma bata rai sosai "Na dade ina tunanin auta na aura ko diyar fari......shagwabarki tayi yawa,ashe dukka kika hada.....ga wautar dan fari,ga sakalcin auta" ya qarashe maganar miskilin murmushinsa na subucewa a labbansa. Wannan karon dole ta bude idanuwanta tana sake kallonsa da kyau,yanata kasheta da mamaki,a ina ya santa haka,sai yayi kamar bashi yayi maganar ba,yaci gaba da wanke mata wajen,har ya gama tas ya bata pain killer. "Abar girkin nan haka,nidai na yafe" ya fada yana rufe akwatin,sannan ya miqe tsaye,ya qarasa gaban gas din ya kasheshi,ta bishi da kallo,tana son gaya masa ya barta zata iya ta qarasa,amma sai ya tsaya gabanta yana bata hannunsa,dole ta miqa masa nata,ya jata jikinsa suka fice a kitchen din. Duk yadda yaso dauriya daren ranar ya kasa,dole ya sake kai kansa gareta,saidai yadda ta dinga masa kuka cike da tsoro yasa ya haqura,ya sanyata a qirjinsa yana sauke ajiyar zuciya kamar zai shide,shi da ita dukka sun dauki dogon lokaci kowannensu baiyi bacci ba,saidai duk da haka ta rigashi yin baccin. ^^^^^^^^^Washegari kasa hada idanu tayi dashi,ko sau daya bata yarsa qwayar idonta ta shiga tasa ba,daren jiyan ba qaramin murzuwa tayi a hannunsa ba,duk da baikai ga gaci ba amma jikinta ko ina ciwo yake mata,har cinyoyinta ma basu tsira ba. A haka ta dinga zuba idanu taji yayi mata zancan ta shirya komawa makaranta amma shuru,ko kadan shima bai sake tunawa da wata maganar makaranta ba,yana shiryawa zai fita gaida su amman wayar anni ta riskeshi,tace yazo shi da maimunatun takeson gani,amsa mata yayi da to,don bai kawo komai cikin ransa ba,gefe daya tun jiya zuciyarsa ke cike da mamakin unaisa?,ina taje?,ita dai ba qaramar yarinya ba bare ace bata tayi ko kuma an saceta,hakanan baiyi da ita zata fita zuwa ko ina ba,saidai duk da haka zaisa a bincika masa ko gida ta tafi. Sanda yace ma maimunatu ta shirya zasu gidan muraran farincikinta ya gaza boyuwa,nan da nan ta buda kayanta na lefe,ta hada kaya sosai da zata kaima su annin da sunan tsaraba,ana zaune a mota yaga fitowarta,idanunsa suka dinga yawo a kanta saboda mugun kyan da tayi masa,yana zaune harta qaraso,sai ya bude murfin motar,ya zuro qafafunsa waje,ya kama hannunta ya jata zuwa ciki,bata musa ba tabi bayansa cikin fargabar kada dai yace an fasa zuwan,tuni ta narke fuska idanuwanta suka fara tara ruwan hawaye. Closet dinta ya bude,ya fidda wasu kayan daban,sannan ya fara ware na jikin ta,hannunsa ta riqe gam tana dubansa,sai ya girgiza mata kai sannan ya zare hannunta. Shi ya sake shiryata tsaf,ya isa da ita gaban mudubin yana tsaye a bayanta,dukkansu shi da ita suke kallon mudubin,ya sakar mata tattausan murmushi yana duban qwayar idanuwanta,yaso ya rage kyau da kaifin kwalliyar data yine,shi yasa ya shiryata da kansa,amma kuma ya gaza yin hakan,wani kyau na daban ta sakeyi. Da wani irin zafin nama ya juyo da ita suna fuskantar juna,don har ta tsorata tana dubansa,hannunta saman kafadarsa, idanuwansa ya sauke kan jajayen lips dinta,wanda koda bata saka mishi jambaki ba iya man lebe ya wadatar ya fidda kyansa,miyansa ya tsinke,ya hadiye wani abu ta maqoshinsa,sannan yakai bakinsa saman nata a hankali yana lashe lips din nata hade da wani zafafan kisses. Sai da ya gama kashe mata jiki gaba daya sannan ya dauke bakinsa yana sauke numfashi a hankali,sakinta yayi sai tayi taga taga kamar zata fadi saboda rashin qwarin jikinta,da sauri ya tallafe ta yana kallonta,a karon farko yaga yadda tayi laushi,don har ta cikin idanuwanta hakan sun nuna,sai ya ajjiyeta gefan gado sannan ya wuce toilet dinta a hankali. Minti.biyu kawai ya fito yana goge fuskarsa,ya miqa mata hannunsa ta dora nata a kai sannan suka fice zuwa motar,cikinsu ba wanda ya sake cewa komai. Yau kai tsaye sassan abbi suka fara dira,saboda khadim da suka hadu dashi yace amma da ammi duka suna can,tamkar ta nutse haka maimunatu ta dinga ji,sai take ganin kamar kowa yana karanto komai daga jikinta. A matuqar kunyace ta gaida abbi sannan ammi,amma tana bedroom din abbin tana gyara masa gami da hada masa ruwan wanka,sai data fito ta gansu,sai ta shaidaws abbin ta gama tana qarasowa cikin falon. Yau fuskarta dauke da wani irin murmushi da farinciki,ta qaraso tana amsa gaisuwar maimunatu gami da sanya hannunta dukka ta dagota,sai kawai ta rungumeta "Ashe ke din jinin sa'adatu ce maimunatu?,na jima jikina yana bani kamar na sanki,kamar nasan wani da yake da.nasaba dake,ashe diyar matar dan uwana ce ke, alhamdulillah" ta qarashe maganar tana maimaita hamdalarta,yayin da kunya suka yiwa maimunatu qawanya. Shiko jabir yana zaune qafafunsa harde da juna yana kallonsu,wani farinciki yana ratsashi,shaheeda ta tafi ga wata shaheedan,komai da yake qiyastawa na shaheeda wanda yayi missing nasa ya sameshi a wajen maimunatu,harma abinda ita din bata dashi. Su laila nata kai kawo suna son samu space suyi hirar yaushe gamo da maimunatun amma kowacce idan ta shigo sai ta wayance da wani abun ta fice ganin ja'afar na wajen,sai da amma ta cikata da kayan ciye ciye a sassanta,amma ta kasa cin komai saboda kunyar amman da takeji "Maimunatu,diyata ce ke yanzu ba surukata ba, maimakon ki sake sakin jikinki sai kuma ki sake dararewa?" Matsowa gaba kadan ja'afar din yayi,ya buda dukkan abinda amman ta ajjiye ya zuba mata,kafin ma ya gama amma ta miqe ta matsa a wajen. Shanyayyun idanuwansa ya sauke mata "Ko sau daya ban taba ganin kinci abincin kirki ba.....oya matso muci" ya fada murya can qasa,narkewa tayi kaman zata saki kuka,a shagwabe tace "Nafa qoshi" idonsa ya lumshe yana cije labbansa,tana kasheshi.....har baisan iyakar illar da take masa ba idan tayi wannan shagwabar tata,tana jefashi a wani yanayi,har yana jin kamar bazai iya jurewa ba. Kaman baiji me tace ba ya matso ya dauki spoon ya saka musu a ciki,ya tsareta kuma da idanunsa,dole ta dauka ta fara motsa abincin kafin takai bakinta,a spoon na biyu kuwa hannunta ya kama yakai bakinsa,idanu a waje tayi galala tana kallonsa,bayajin kunya ko tsoron kada wani ya shigo?,saidai shi ko a jikinsa,ci gaba yayi da tauna abincin,yana jin yana masa dadi a baki fiye da kullum,ko don da hannunta ta ciyar dashi?. Wasa wasa sai gashi sunci abincin shi da ita ba laifi,shigowar anty maama yasa suka fara wucewa sassan anni ita da ita,kafin ya bisu a baya. A nutse anni tayi mata kyakkyawan kallo guda daya,a take kuma ta fahimci komai ya kankama "Anzo wajen,haka dama nakeso,zakaci qaniyanka" ta fada a ranta,tana amsa gaisuwa maimunatu,wadda ta duqa gabanta tana duban qafan annin data sake motsawa da ciwo,sannu take mata,tana jin ciwon annin yana taba ranta, tsohuwar nada kima da martaba a wajenta,sai ta karba man da take shafawar taci gaba da shafa mata,annin na tayata murnar na haduwarsu da sa'ade,da kuma maida zancan yadda abun ya kasance,anty maama na saka musu baki,itama har cikin ranta tana jin dadin kasancewar hakan "Ni kaina na jima ina ganin yanayinta da anty sa'adah da fareeda,musamman fareeda,muryoyinsu kusan daya ne,duk sanda naji muryarta sai na tuna dasu,ashe jini daya ne" "Ikon Allah kenan,ga abinda kaketa nema ashe yana kusa da kai baka sani ba" anni ta fada rana jin zuciyarta na mata dadi,abu daya ya ragewa maimunatu a yanzun shine bayyanar mahaifinta,wanda shima ta fara shirya yadda zata tunkari ja'afar da maganar,don ya kamata ayi wani abu a kai, lokaci yana dada ja. Dai dai lokacin da yayi sallama ya shigo,kamar kowanne lokacin idanuwansa suna kan maimunatu,duk inda zaya shiga ita yake fara gani,muddin tana waje. Qasan carfet yau din ya zauna,dab da anni da kuma maimunatu da jikinta yayi week tun shigowarsa,batason yayi wani abu da zai bata kunya a gaban anni,don haka tana gama shafawan ta ajjiye man ta matsa daga wajen. Gaida annin ya fara yi yana mata sannu da jiki,ta amsa tana dubansa,kafin ta dauke kai tace "Sannunku da hanya matafiya,ya gajiyar tafiya" "Alhamdulillah" ya amsa mata hankalinshi kwance,kamar bai fahimci da gatse tayi maganar ba "To ma sha Allah,ba wata doguwar magana bace,dama so nake na gaya maka,da Allah kayi da jiki ka maida yarinyar mutane makaranta,tunda dai amana na dauko,kai kuma alqawari ka dauka,to ya kamata ka sauke" ya manta rabon da yaji gabansa ya fadi sai yau,yadan lumshe idanuwansa sannan ya budesu yana duban anni "Wacce makaranta?" Dubansa take saboda yadda taga zai raina mata hankali "Makarantar da ubanka marwanu ya bude" dauke kansa yayi daga inda take,yasan anni,zata fadi fiye da haka ma,don haka ya fito mata shima a ja'afar dinsa sak "Na cireta anni,wata zan canza mata" "Dalili?" Ta tambayeshi harda riqe qugu tana qare masa kallo "Kawai" ya amsata yana sassauta daurin agogon dake hannunsa,don a take yaji kamar ya matseshi ma. "To uban maryamu,to billhuwallazi la'ilaha illa anta baka isa ba,uban kuturu ma yayi kadan ballantana na makaho,kaiiii ja'afaru,kayi ta kanka wallahi,bakasan wace maryamu ba hala,mu zaka mayar qananun mutane?,wanne irin zabine baa baka ba amma ka kafe can zaka kaita?,shine zaka tsire cireta a makaranta kanason yi mata walagigi da karatu?,to kayi qarya ka kwana da yunwa" boyayyar ajiyar zuciya ya saki,yana jin cewa ya shiga uku yau,tijarar anni ta dira a kansa "Lemme explain you mana anni....." "Lamma ma taci qaniyarta,kayi ta kanka fa,idan hausa hausa idan fillanci fillanci" hannunsa yasa ya dafe goshinsa da kyau,anni bata da kyau idan ta tubure,gashi jabir baya kusa ballantana ya tayashi,shi kuma bai iya daukan hayaniya da yawa ba har haka "Relax.....relax,ba daina karatu zatayi ba,inaso ta koma day ne,i mean jeka ka dawo" "Baka isa bafa,ita ka fara zaba mata ita zata ci gaba da zuwa,idan kaga ta daina saidai idan itace tace bata so....." Maida dubanta tayi ga maimunatu dake zaune,tayi shuru yana sauraren dambarwar tasu "Ke maimunatu.....kinason komawa makarantarki......ko kin zabi dadi miji ya sauya miki wadda yaga dama?".... 72 Tambayar da annin tayi mata gaba daya sai taji ta daburce,daga ita har ja'afar din sun zuba mata idanu,kowa yanason ta dauki zabinsa,bai taba tsintar kansa cikin fargabar jiran fitar amsa daga wani waje ba irin yau,koda aiki da kasuwancinsa da yake daukansa da muhimmanci bai fiya damuwa da rashin samuwar wani abu ba,idan yayi duk abinda ya dace yana ci gaba da harkokinsa ne ya barwa Allah zabinsa. Ita kuwa anni fatanta daya maimunatun kar ta amince da tsarinsa,wannan din wata hanya ce da zata sake samar mata da kima da daraja a idanunsa,ya dandana yaji idan tana da muhimmanci cikin rayuwarsa,musamman yanzun da ya fara sanin ainihin ita din wacece. Maimunatu kuwa zahirin gaskiya tana son makarantarta,saboda ta saba da ita,gasu afra da takejin kamar ba zata rabuwa dasu ba,kada ma afra taji labari,ko don ita kadai batajin zataso canjin makaranta "Nafison wadda nakeyin yanzu" kamar an sauke masa guduma a kansa haka yaji "Subhanallah" ya fada can qasan ransa,yana dauke idanuwansa daga kanta "To kaji,saboda haka kada ka wuce gobe baka maidata ba,tun gabanin na hadaka da marwanu ya cimin qaniyarka,don ni din yanzu na fuskanci wani sabon raini kayimin" cak ya miqe daga zaman yana cusa hannunsa a aljihun wandonsa,wani bacin rai yaji yana ratsashi,bai taba tunanin zata iya zabar maganar anni akan tasa ba,baice komai ba ya fara takawa zai fice a falon "Yauwa dakata.....iyayen marigayiya sunyi magana jiya akan debe kayan yarinyarsu za'ayi sadakarsu,na riga nace musu su sauraremu zuwa yau......ya kamata a fiddasu haka ayi mata sadaka Allah yakai mata ladan k...." Tun bata qarasa ba ya tari numfashinta "Nan da one hour su sameni cikin gidan su dauki dukka abinda zasu dauka" ya taka yana barin falon,umma tabawa da anty maama suna binsa da kallon tausayi,sunsan anni,da biyu tayi hakan. Umma tabawa ce ta sauke ajiyar zuciya "Banda abin maimunatu,ke da zaki goyawa mijinki baya,saiki biyewa anni ku kware masa baya?" "Har yaban tausayi,don Allah a sassautawa dan qanina" anty maama ta fada tana murmushi,su duka suna kallon maimunatu,kunya da nauyinsu ya sake cikata,maganar anni ta tsaida su "Kunga,ke maryamu bakisan dawar garin ba,keko tabawa da kika sani bai kamata kice komai ba,ku bamu guri ni da ita" ta buqata daga garesu,sai suka miqe anty maama tana cewa suje kitchen baaba tabawan ta sake nuna mata kwabin alkubus irin na rannan,duk sadda tayi nata da qyar takesha,sai ya kusa cabe mata yayi nauyi. "Maimunatu"anni ta kira sunanta a tausashe "Na'am" ta amsa mata kanta har yanzu a qasa "Allah yayi miki albarka,ya jiqan mahaifiyarki,ya bayyana mahaifinki,babu abinda zamu ce dake sai Allah ya kyauta qarshenki,bamu zaci dawowar ja'afar da sauri haka ba,sai gashi cikin tafiyar nan taku jabiru yana shaidan canjin da ya gani na tunkarar rayuwar ja'afar din ta sanadinki,ni kaina shaida ce,yana shigowa naga haka akan fuskarsa,banda wannan maganar dana masa wadda baiso nasan a yau din zamu jima dashi,xan kuma ga ainihin ja'afarunmu,amma babu komai,mun saba irin haka dashi,kema kada ki damu don ki goyi bayan hukuncina,dama haka naso,saboda ta hakane zaki gane girma da martabarki a ransa,karki damu da dukka fushinsa,ki bishi a hankali,zai sauko da kansa,bashi da riqo sosai musamman akan abinda yake so" kalmar abinda yake so din ta sanya maimunatu daga kai tana kallon anni,sai ta sake mata murmushin su na manya "Eh,a yadda naga yanayin ja'afar,na tabbatar indai ba mutuwa ba babu abinda ya isa a yanzu ya rabashi dake,naji dadi hakan da ya zaman kece kika samu wannan gurbin,dama abinda naketa taraddadi,kada waccan ta qwace matsayin da naketa miki fatan samunsa,abu daya kawai nake gudu, wahalar da abokiyar zamanki zataci,ja'afaru ba irin mazan dake iya zama da mace biyu bane,saboda idan suka fara son abu suna fara sonshi da gaske ne,suna kuma miqa masa dukkan yarda soyayyarsu da kuma amannarsu,shi yasa tun farko naso marwanu ya qyale batunta,amma bazaiyiwu na tursasashi ba,dukkansu suna min biyayya akan dukka maganata,to ya kamata a qalla suma na dinga basu dama cikin rayuwarsa,ba fata nake ba,ba kuma baki nake ba,amma tabbas dole akwai abinda zai biyo baya,kedai kawai abinda zance dake,ki koma makaranta abinki,karki waiwayeshi ko sau daya" kai ta gyada tana jin gamsuwa da maganar anni,hawayen farinciki yana sauko mata,ta rasa da wanne irin harshe zata yiwa anni godiya,batasan girman soyayyarta gareta ba. Ko awa daya cikakkiya ba'a rufa ba ya aiko khadim ta fito zasu tafi,sai ta narke fuska,bata zaci zaice yanzu yanzu ba daga zuwansu,wuni ta dauka zatayi a nan din,gashi ta fara jin dadin hira dasu laila. Murmushi anni tayi,a qufule yake kenan da alama,abun yana mata dadi ita kuma sosai cikin ranta,hakan na sake nuna darajar maimunatu a wajensa,sai ta dubi maimunatu "Tashi ki bishi ku tafi,zaki zo wataran ki wuni,karki damu" haka ta tashi jiki a sabule tana goge qananun qwalla,su fa'iza zasuyi mata rakiya anni ta hana kowa zuwa wajen,tace su barta ta fita ita daya. Tunda ta shiga motar baice komai da ita ba,saidai tana jin yadda yake sauke numfashi da kuma ajiyar zuciya lokaci bayan lokaci hadi da fidda wata iska daga bakinsa,da alama ransa a bacen yake,duk sai taji babu dadi cikin ranta,amma kuma sai ta kama kanta,tunda dai me zata ce masa?,tun farko shi ya zaba matan kamar yadda anni tace,yanzun kuma ita kanta bataga kamatar biye ma tsarinsa haka kai tsaye ba ba tare da an dan latsashi ba,amma can qasan ranta sai takeji babu dadi sam,abinda ya dauke walwalarta itama gaba daya,amma sai ta maida dubanta ga titi tana kallon yadda suke wuce hanya. Duk da ba sanin garin tayi sosai ba,amma ta fahimci kamar ba hanyar gida suka nufa ba,saidai bata tanka ba,tana dai kallon hanyar ne kawai. Sau kusan uku yana satar kallonta,ya zaci zata nuna damuwa ko wani abu da yayi kama da haka,amma sai yaga kamar ma batasan me ya faru ba,abinda ya sake qular dashi,ya dinga hadiyar zuciya shi daya yana lumshe idanunsa hadi da budesu,matsa mai kyau yakeson mata amma kuma driver ke jan motar ba shi ba,wannan yasa ya qagu su isa gidan. Da yake ba wata tazara tsakanin gidan nasu da government house road,nan da nan suka isa ainihin gidan nasa dake can,wanda a nan ya fara rayuwarsa da shaheeda. Tun daga tsarin ginin katangar zaka san cewa ba qaramin gida bane,ba kuma ginin wasa aka yi masa ba,shi kansa yana kimanta gidan saboda ya qunshi abubuwan tarihi masu yawan gaske da suka shafi rayuwarsa a ciki,uwa uba da kudin aikin da yake mutuwar so a rayuwarsa ya ginashi,wato sanda yake a matsayin cikakken captain ja'afar marwan akko dinsa. Tun a gate security suka fara miqa gaisuwa,yana amsa musu da hannu,saboda ba'a cikin yanayinsa yake ba,motar tasu ta sulala zuwa cikin katafariyar harabar gidan,sannan suka tsaya a parking lot. Yana gaba tana biye dashi,idanuwanta suna kallon tsarin gidan,ginin turai zam,komai kuma yana nan a tsaftace a muhallinsa tamkar dan adam yana rayuwa a ciki. Bata fahimci inda sukazo ba har sai da suka qaraso ainihin falon gidan,idanuwanta suka ci karo da hotunan shaheeda dana amna da amra,tamkar tana raye,sai taji zuciyarta na karyewa a hankali,tausayin amna yana tsirga mata,jikinta yayi sanyi sosai,dan adam ba'a bakin komai yake ba,kamar zaka kirata ta amsa,kamar zata tashi taci gaba da rayuwa a gidanta. Wani sashe na daban suka bulla,kallo daya tayi ma sashen tasan bangaren mai gida ne,falo biyu suka ratsa sannan suka isa ga makeken bedroom dinsa. Aljannar duniya shi yafi dacewa a kirasa,komai yana nan a muhallinsa fes dashi,hatta da ac din dakin a kunne take tana aikinta,ana kula da gidan sosai,don akwai amintattunsa da yake sanyawa duk bayan kwana biyu su shiga su gyara har bedroom din "Ki zauna ina zuwa" ya fada yana wani shan qamshi,sannan ya fice yana jan qofar dakin. Sai data gama qarewa dakin kallo tsaf sannan ta taka zuwa saman sofa bed din ta zauna,idanuwanta suna qarewa dakin kallo,very neat and clean,idanunta suka sauka kan tarin takardun sake saman gadon gefe guda,tayi mamaki don dakin fes yake,su kadai ne a wajen,batasan ya akayi ba ta miqa hannu ta debosu ta fara dubawa. Hotunan shaheeda 'yan biyunta da kuma ja'afar dinne,sunyi masifar kyau,ahali me kyau da daukan hankali,tana kalla tana sake jin wani abu yana tabata a zuciyarta game dashi,yadda ta ganshi cikin hoton ya gaya mata he's nice and friendly to his family,daga hoto na qarshe sai wani dan littafi dake dauke da sunan my dairy. A hankali ta soma buda shafin farko,a nan ta gane na shaheeda ne,sai taci gaba da budewa tana karantawa,tun batayi nisa ba ta fuskanci duka akan ja'afar tayi littafin sanda tana raye,da farko ya zame mata kamar novel,ta dinga karantawa yana debe mata kewa da kuma sakata murmushi,halayensa abinda yafiso da wanda bayaso,yadda fushinsa da walwalarsa take "He's arrogant and very annoyed person sometimes,but hes the best husband i know in the planet" murmushi ya kubcewa maimunatu,sai taji kamar gata ga shaheeda take gaya mata hakan,girarta ta dage "Na shaida hakan" ta fada a fili,sannan taci gaba da bin rubutun tana fahimtar kowanne zance da yake ciki,daga bisani kuma labarin ya fara tabata,har zuwa sanda tayi rubutun ta na qarshe,wanda akan amna da amra tayi. Kasa riqe kanta tayi,kuka ya subuce mata sosai,ba abinda take tunawa sai daadarta da kuma abbanta,tausayin amna kuma na sake sarqafar zuciyarta,qaunar yarinyar na sake shiga zuciyarta. Sai da kukan ya lafa mata,duk da hawayen baibar sauka ba sannan ta daga kanta tana maido da littafin shafin da shaheedan ke bayyana halaye da dabi'un ja'afar din,ta dora hannunta a kai tana sake maimaita wajen. Ko kusa bataji motsi ko alamun shigowar sa ba,har sai da taji ya sauke wata ajiyar zuciya mai qarfi,ta daga kanta da sauri tana dubansa,shima ita yake kalla,idanuwansa sun kada sun canza kala,da alama wani abu ya taba zuciyarsa sosai. A hankali tayi yinqurin hade littafin ta rufe,bakinta yana fadin "Am sorry,kayi haquri" tausasan hannayensa yasa ya riqe hannunta ya dakatar dasu daga qoqarin rufewar da takeyi,sannan ya zare littafin yana duba saqonni wajen da yaga tana karantawa,sake daga kansa yayi ya kalleta,sai ya zame shima ya zauna kusa da ita sosai har jikkunansu na gogar na juna,ya kuma sanya littafin atsakiyan su,kamar masu bitar karatun jarabawa,yatsansa tabi da kallo zuwa wajen da ya dorasu _bana jin a duniya za'a sake samun wata macen da zata soshi ta kula dashi kamar yadda nake sonshi_ abinda paragraph din ta qunsa kenan,tana kaiwa nan ta tada kanta tana kallonsa,shima sai ya sanya qwayar idanunsa a tata,suka shiga kallon kallo,a hankali ya maida littafin ya rufe,ya aje a gefansa,sannan ya kama fuskarta ya saka a tafin hannunsa,ya hade fuskokinsu waje daya,suka fara musayar numfashi. Shuru ya ratsa a tsakaninsu,ba komai dakin sai qarar ac dake kadawa da kuma qananun motsi daga harabar gidan "Wataqila an gama samun macen da zata soni ko?" Ya yiwa maimunatu tambayar da batasan amsarta ba,sai tayi shuru tana saurarensa,sai kuma ya zame fuskarsa a hankali,ya kama hannunta ya dora saman qirjinsa,ya danne hannun nata da tafin hannunsa. Wasu abubuwa ne suka bi ta jininta zuwa gangar jiki da qwaqwalwarta,jikinta ya saki tsigar jikinta ta zuba,duk sanda jikinsu zai hadu sai taji zubawae tsigar jikinta "Bansan yadda zan canza kaina ba wajen daukan duk abinda zuciyata ta gamsu da ta soshi da mugun muhimmanci ba,na rasa shaheeda,amma bansani ba ko zan samu maimoon?" Ya qare tanbayar yana ritsata da kallonsa. Gaba daya taji wani rauni ya cikata,karon farko da tausayinsa ya mamayeta,ko bai gaya mata ba tasan zuciyarsa na cikin wani yanayi na kwashe kayan da yau akayi bayan wasu shekaru,tasha jin labarin yadda ya hana a taba komai din,amma yau karon farko babu shiri ya yarda,sai ta buda bakinta a hankali zatayi magana. Tsoron jin negative answer daga bakinta ya sanyashi hanata cewa komai,sai kawai ya riqe fuskarta gam,ya kuma kai bakinsa ya hade da nata. Da dukka zafin da yakeji a zuciya da gangar jikinsa yayi amfani ya soma sauke mata hot kisses,kafin daga bisani yanayinsa ya sauya,tsiminsa da yaketa qoqarin dannewa ya motsa masa,sai kawai labari ya canza,wasan ya sauya salo,kwanyarsa ta fara barin wancan tunanin izuwa wata kyakkyawa kuma ni'imtacciyar duniya. Kamar wancan lokacin ta karba saqon yadda ya kamata,har ta kasa aiwatar da komai,saidai kuma sanda yayi yunqurin isa waccar duniyar da yake muradi da kuma marari sai ta shiga tsoro razani da fargaba,amma yayi nisan da baisan me take fada ba,fatansa kawai ya dangane da inda ya hara din. 73 Kamar wancan karon,wannan karon ma ta dandana kudarta,duk da bai qarasa gamuwarsu ta farko ba amma taji a jikinta,harshi kansa yayi tunanin anya ya gama bude hanyar wancan karon kuwa?,rashin ganin jini yasa ya fahimci wancan karon ya kammala aikin nasa,wataqila ita din irin matan da sai a hankali suke gama samuwa ne. Wannan lokacinma shi yayi barnarsa ya kuma shiga gyara,hawaye kawai takeyi tana jin yadda yaketa bata haquri gami da jero mata sannu,can qasan ranta tana mamakin yadda duk sanda hakan ta faru yake zama wani iri,kamar wanda ya aikata mummunan laifi,saida data tuna dabi'ar tausayi da shaheeda ta zayyanar akansa,sai mamakin nata ya ragu. Yadda ya dinga kula da ita yasa ta sassauta qananun kukan da take masa,zazzabi yaso rufeta yau din ma,amma kuma ya hana afkuwan hakan ta hanyar bata paracetamol,ya kuma lullubeta a qirjinsa kamar first night dinsu,suka sha baccinsu sosai bayan sun hada azahar da la'asar data riskesu a farkon lokacin shigar mukhatarin la'asar din. Basu tashi ba sai bayan magrib,ya sake wanka sannan ya hada mata itama,yace zaije yayi sallah ya dawo,haka ya fita yana waigenta kamar zata bace masa. A inda ya barta a nan ya dawo ya taddata zaune,qarasowa yayi "Lokacin sallah fa" idanunta fal da qwalla tace "Bazan iya tashi ba....waj....wajen akwai zafi" sumar kansa ya shafa da kyau yana fadin "oh sorry" ya tako a hankali zuwa inda take din,tsugunnawa yayi a gabanta kamar me shirin yin kneel down,ya kuma kama kunnuwansa da hannayensa guda biyun "Laifin abban amna ne,a yafe masa" nauyi sosai ya aza mata ganin yadda ya zube a gabanta,sai ta boye kanta a kafadarta,tana jin ba zata iya hada ido dashi ba "Yes,na gaji da ganin amna a haka,she needs a sister...." "Na yafe" ta furta da sauri don kada yaci gaba da fadin maganar da fadin maganar da bazata iya dauka ba,murmushinsa dake bata mamaki da kuma jan hankalinta ya qwace masa,sai ya faki idanuwanta yayi wuf da ita sai bandaki. Yanzun ma shi ke tayata,duk da yadda take noqewa,kusan dai shima sabon wanka ya sake sannan suka dawo dakin,ya saka kayansa da sauri saboda jun bell tana kadawa ya fita ya barta a wajen bayan ya nuna mata inda zata samu kayan sawa. Dukka side din sabbabin suturu ne na mata,ta fidda guda ta saka,tana jin jikinta ya mata dama dama,sannan ta janyo wayarta data hanga qasan gado ta kunna,low battery ta nuna mata ta sake mutuwa da kanta,saita matsa gefan gadon ta sanya mata charge ta koma ta tada sallah. Har ta idar bai shigo ba,wannan ya bata damar kunna wayarta,umna sa'adatu ce a ranta,so take taji muryarta,tana gama kunnawa kuwa kiranta ya shigo,ta saki murmushi tana dagawa "Diyam dita.....ina kika shiga yau duka wayarki a kashe?,na kira ammanku tacemin dazu kuka bar gidan,yanzu nake shirin insa driver ya kawoni gidan naki naga ko lafiya,hankalina naji ya tashi" murmushin jin nauyinta ta saki,ta rasa me zata ce mata,wacce amsa zata bata,Allah ya taimaketa dabara ta fado mata "Wayar ne charge dinta ya qare,ban kuma kula ba sai yanzu" "To alhmdlh" hira suka dan taba kadan,kasancewar ba wani sabo bane mai yawa tsakaninsu ba abun tattaunawa sosai,ta tambayi su fareeda,sai ta miqawa su faridan waya,suka gaisa,umma sa'aden ta karba wayar tace zatayi sallah zata sake kiranta. Tana sauke wayar yana shigowa,bakinsa dauke da daddadar sallama,sai ya tuna mata zamansu na johannesburg,yadda ya iya rera karatun qur'ani kamar wani baqin balarabe,muryarsa nada dadin ainun,sau tari da sautin karatun qur'aninsa bacci yake sake saceta,tana son muryarsa a guraren guda biyu,yayin karatun qur'ani da kuma sanda yake sallama. Samun zuciyarta tayi da wani irin bugawa,ta lumshe idanunta tana amsa masa sallamar,qarasowa yayi ya zauna daga bakin gadon yana fuskantarta sosai,sai ya miqa mata hannunsa ya mata alama kan ta taso,murya can qasa kamar yadda ya saba yi mata magana yace "Zo muji jikin naki"a nutse ta miqe tana isa gabansa,shirin zamewa ta zauna tayi sai ya janyota ta fada jikinsa,yayi mata masauki akan cinyarsa. Hannunsa ya sanya ya shafi wuyanta,saita karyar da kai gefe tana jin tsigar jikinta na zubawa "Thank God,babu zazzabin,ki qarasa shiryawa mu fita ki tattaka ko zaki sake warwarewa,amma inajin yau saidai mu kwana a nan ko?" Ido a narke ta dubeshi,sai yaji kamar ta watsa masa qanqara,yana masifar son shagwabar nan tata "Uhmmm,kamar akwai magana a bakinki,say it.... Don't be shy" da gaske kunyar tashi takeji,sai ta boye kanta a kafadarsa sannan tace "Bazan iya tafiya ba" har cikin b'argonsa yaji maganar,don sai da yaja numfashi sosai,maganar ta shiga kunnensa da yawa,kamar tana sane tayi hakan "Zaki iya.....am by your side,i will support you" ya qarashe maganar yana dagata sosai. Laffaya ya fidda mata a side din kayan dai data dauko,ta riqe masa ya daura mata,data kalli kanta sai taga kamar ba ita ba tsaye gaban mudubi "Me yasa kika goyi bayan maganar anni akan tawa uhunnn?" Shuru tayi masa ba tare data iya amsashi ba "Well,bakya tausayina....kuma bakya sona ko?" Salon da yayi maganar a narke yasa dole ta daga kanta tana duban fuskarsa ta cikin mudubin,gaba daya ya koma kalar tausayi,tana mamakin yadda yake komawa haka a gabanta,why?....me yasa ne?. Jin shurun ya sake biyo baya sai ya zagayo da kansa ta kafadarta,a hankali ya sakar mata kiss a kuncinta,sannan ya dawo da baya cikin kunnenta ya rada mata wata magana data sanyata sandarewa,sai ta rufe idanunta,matsananciyar kunya tana yawo da ita,maganar kuma naci gaba da amsa kuwa a kunnen nata "U are very sweet fiye da duk wani abu me zaqi a duniya" anya kuwa ba matsala ja'afar din ya samu ba?,ita maimunatu yake gayawa wadan nan kalaman?. Zaune kawai sukayi cikin mota ya dinga wani slow driving da ita manyan tituna tana more kallonta,kusan awa daya sukayi a haka,sannan ya zarce da ita wani babban wajen cin abinci me shegen tsada,babu mamaki tunda dama waje ne na wane da wane,ya bata menu ta zaba duk abinda takeso,sai ta rasa me zata zaba din,tunda dai ita ba saba fita tayi gurare irin wannan ba,uwa uba ma kuma bata iya cin abinci cikin jama'a ba tunda ta taso "Duk abinda aka kawo maka" haka tace masa,to ko da aka kawo dinma juya abincin kawai take,yana ankare da ita,ya fuskanci kunya ne da ita sosai da sosai,yana shirin mata magana wayarsa ta dauki tsuwwa,sai ya aje spoon din hannunsa ya daga wayar. Sallama kawai yayi ya tsaya yana sauraren bayanan da ake masa "How comes?" Ya fada fuskarsa na bayyanar da bacin rai,ya sakeyin shuru kafin ya sake cewa "Okay,thanks". Unaisa dubai taje?,an tabbatar kuma 'yan gidansu da suka tafi tare dukka sun dawo?,a ina ita din ta tsaya?,wannan itace tambayar da ya jefa ma kansa,ta yaya ma zata dauki qafa zuwa wata qasa bada izininsa ba? "Have you finished?" Ya tambaya maimunatu,sai ta gyada masa kai,ya kira waiter din ya aje musu kudinsu kan plate din ya qara gaba kafin ya qaraso ma,yana riqe da hannunta. Shuru suke cikin motar yana tuqi,hankalinsa yayi wani waje na daban,itama hanya take duba ganin still yanzun ma ba gida suka nufa ba,ba wata tafiya sukayi.mai tsaho ba suka shiga wata unguwa,basuyi nisa ba ya tsaya qofar wani gida ya danna hon mai gadin ya bude masa. Parking lot na gidan ya tsaida motar,ya waiwayo yana dubanta da idanunsa dake cike fal da bacin rai "Ki shiga ciki,only one hour" kai ta gyada,duk da bata gane ina bane,bata kuma fahimta ba sai data kutsa kai falon gidan sukayi ido hudu da fareeda. Karadinsu ya sanya umma sa'ade fitowa,murmushin fuskarta yaqi boyuwa,ta rasa inda zata tsoma maimunatu "Amma kun shammaceni,ke dawa?" "Shine ya kawoni" ta fada bayan ta rasa sunan da zata kirashi dashi,sai ta aike fareeda tace tace masa ya shigo,duk da ko a baya bai tana shigowa gidan ba,iyakarsa daga waje ne idan ya gama abinda zaiyi ya koma. Ta samu bayanan,mai gadi ya shaida mata yana sauke baquwar yaja motar ya fita "Ko kwana zakiyi?" Murmushi ta saki,itama zataso hakan inda zai barta,don ita yanzun tsoron kadaicewarsu ita dashi takeyi "Baice hakan ba,inajin akwai inda zaije ya dawo" ta fada tana tuna mood din fuskarsa data gani tun a wajen cin abinci. Dukansu suka hadu sai hirar tafi armashi,ta samu sunyi irin abincinsu nacan gida,don haka ta saki jiki sosai taci,sai data qoshi fareeda tana gyaran wajen umma sa'adah tace da ita "Har yanzu babu labarin abbanki?" Cikin matuqar alhini da kuma kewarsa maimunatu tace "Babu umma,Allah ma yasa yana raye" kai ta girgiza,cikin bata qwarin gwiwa tace "In sha Allah yana raye,a yanzun ne zamuci gaba da addu'a da kuma nema,sannan shi kansa a yadda nasan shi a matsayin mutumin kirki,nasan duk inda yake hankalinsa yana kanku" "Allah ameen" maimunatu tace tana sadda kanta,tana kuma tuna fuskar.mahaifin nata da har ta soma neman dusashe mata a ido. Mintuna kadan ya qara a awa dayan ya dawo,ya aika ta fito,sai umma sa'ade tace ya shigo su gaisa mana,kememe ya qiya,don shi baya shiga gidan mutane haka kai tsaye,musamman idan mai gidan baya nan "Ja'afar?,har yanzu haka yake kenan,banda abinsa nan din ai ba baqonsa bane,gidan babansa da mamarsa ce,muje na gaisa" umma sa'adah ta fada bayan ta hada ma maimunatu uban kaya,wai duka tsaraba ce aka ware mata nata,haka suka rakata mota niqi niqi. Ko a hanya hannunsa na cikin tafin hannunta yana driving,yanata kuma amsa waya,batasan akan me yaketa wayar ba,amma kuma taji ya ambaci sunan unaisa kusan sau biyu,a haka suka isa gida yanata wayar. A falo ta barshi ta shige daki,har ta gama shirin kwanciya ta kwanta bai shigo ba,bawai don tana saka ran zai shigo dakin ya kwana ba,sai tayi lamo tana jin gadon wayam,a sannan ne taji motsinsa,ya shigo riqe da wasu kaya,ya bude closet dinta ya zubasu,sannan ya shige toilet dinta. Ya kusa minti talatin sannan ya bude ya fito,daure da bathrobe dinta,wanda ta tsaya masa iya qaurinsa saboda ya fita tsaho sosai,qamshinta dake manne jikin robe din yana ta shigar masa hanci. Sassan da take kwance ya maida dubansa,sai suka hada ido tana satar kallonsa ta qasan duvet,da sauri ta runtse idanunta tayi kamar bashi take kalla ba,sai ya saki miskilin murmushin gefen bakin nan nasa,ya qarasa gaban mirror ya dauki lotion dinta,yana kallota ta cikin madubin "Satar kallon nawa na meye kuma hajjaju?, just get up and look at your husband directly" kunya iya kunya ta kamata,saita shagwabe fuska ta kuma turo baki,ya hangota ta madubi,tsaiwa yayi cak da shafa man yana kallonta,yasan yanzu zata kasheshi da shagwabar tata "Ni bakai nake kallo ba fa?" Sauke dukka hannuwansa yayi murmushi na subuce masa "To wa kike kallo?" Sake tura baki tayi tana bata fuska,sai ya waiwayo ya nufota gaba daya,idanunta na rufe sai ji tayi an dagata,abinda ya sanyata ware manyan idanuwanta a kansa wadanda suka qara haske "Ni ke nake kallo,kuma nakeso nayita kallo,jeki hadomin coffee" ya fada yans kallon light blue silk sleeping dress din jikinta,sai ya duqa a hankali yayi kissing qirjinta yana yaye mata duvet din,kana ya kama.hannuwanta ya taimaka mata ta sauko ta zura soft slipper dinta dake gaban gadon,yana tsaye yana kallonta har ta fice. Numfashi ya zuqa ya fesar,wai dama haka kakejin wanda kakeso a zuciyarka?,yadda yakeji yanzun a kanta,bai taba din abu cikin zuciyarsa kwatankwacin hakan ba,qarasawa yayi ya gama shiryawa,sanann ya zura silk pyjamas dinsa navy blue,qirar kamfanin laurent. Saman bed sofa ya koma ya zauna yana duba wayarsa, zuciyarsa cike fal da mamakin unaisa,baya son zarginta kan bin mazan banza,saboda yana tausayin mahaifinta,to amma kuma jikinsa yana yin sanyi idan ya tuna a inda ya fara ganinta,sannan kuma binciken da yasa aka masa ya nuna ita da wani ne suka koma,ya sake samun tabbacin hakan ta go and come ticket data siya,dama can ta shirya komawar kenan ba da sanin kowa ba?,zai zuba idanu yaga lokacin dawowarta. Bayan ta kawo masa coffee din sai ya tsirar mata qananun aikin da dole tayita kai kawo,yayi relaxing jikin sofa yana qare mata kallo ta cikin sleeping dress din nata,har sai daya gamsu don kansa,sannan a zuwanta na qarshe lokacin ya kammala abinda yakeyi ta kawo masa turare,sai ya hade turaren da hannunta ya dorata saman cinyarsa. Hannu yasa a tausashe ya fara zame mata rigar,wanda santsinta yasa ta fara fita ba wani wahala,sai tayi rau rau da idanu tana dubansa "Sanyi nakeji" "Kina da bargon da yafi wannan dumi.... you know what?, sleeping dress amfaninsu a wajen kadai kafin lokacin kwanciya barci ne,bana buqatarsu daga sanda zaki kwanta,i only need your skin,i really enjoy body contact" ya qarasa maganar cikin tsakiyar kunnuwanta,har sai data damqe hannuwanta waje guda tana rintse idanunta. °°°°°°°°°Karfe uku da mintuna na yammacin washegari cikin makarantar tayi musu,bayan ya gama nuqu nuqunsa fes,kamar ma bazata koma din ba sannan ya baro office da kansa ya karba key ya daukota,bayan anni ta kirashi ta gaya masa,zata turo hisham ya dauketa ya kaita. Fuska ya bata sosai,yana jin wani mugun kishi yana maqare masa wuya,yama rasa amsar da zai bawa annin "Saiki shirya kayan tafiya asibiti jiyyarsa indai ya sake yazomin gida da sunan daukarta" haba ta kama,dariya nason qwace mata amma ta maze "Iyyeee,dan nan?,dan daba ka zama,to wallahi ahir dinka da furta ta'addanci" "Me kikeso ne nayi anni?,dole saikin qure haqurina......is okay,i love maimunatu......inason maimunatu,ina sonta......ina sonta,banason kowa ya rabeta please,karki qara wannan maganar anni, maimunatu tawa ce....." Girma maganganuna nasa suka yiwa anni,taji tsoron kada ya baro babbar magana,tasan halinsa duk randa ya cika ya fara fidda abinda ke cikinsa baya ji baya gani,don haka ta dakatar dashi da sauri "Kai arcannn,yi ta kanka yaro,bani zaka gayawa wannan zancan banzan ba,nidai a maidamin yarinya makaranta ehe" da sauri ta datse kiran,sai ya sauke wayar daga kunnensa cikin wata kasala kamar wanda aka yiwa dukan tsiya,yabi wayar da kallo yana murmushi kawai,yasan maganin annin,daga yau shima zai nuna mata dan zamani ne shi,tunda so take ta qure haqurinsa. Gashi dai ya kashe motar,amma kuma bai bude motar ba,saima kwantar da seat din motar da yayi ya kashingida bayansa yana qare mata kallo,idanunsa a lullumshe kamar zai cinyeta,yana jin yadda zuciyarsa ke harbawa. Jira taketa yi taji yace ta fita din amma shuru,daga inda take zaune ta hangi su afra sunyo arean riqe da qur'ani,da alama islamiyya zasu wuce,sai taji kewar karatun ta sake kamata,tana so ko iya yau a fara karatun da ita ta rage wasu kwanakin da tayi missing. Har sukazo suka gifta su basu ankara da ita ba,suna ta hirarsu su ukun,saita dauke kanta zuwa gareshi,cikin sa'a suka hada ido "Zan iya tafiya?" Kai ya girgiza mata alamun a'ah,sai ta shagwabe fuskarta as usual,wannan karon harda tabe siraran labbanta,ji yayi kamar ta saukar masa dafi a jikinsa "My moon" ya kirata da wani.lallausan sauti,kamar wanda ya tashi a barci,daga kai tayi ta dubeshi,saiya miqa mata hannunsa ya mata sihn din tazo,ido ta fidda tana kallon gaban motar dake da farin glass,kowa zai iya hangosu,bata dauke idanunta ba taga coloured glass ya maye gurbin farin,kafin ta maida dubanta kansa ya fincikota ta fado kansa gaba daya. Riqon tsauri yayi mata sosai,ya dinga aike mata da kisses kota ina,cikin wani irin zazzafan shauqi,ba inda bai kai harshensa a fuskarta zuwa wuyanta ba,cikin qanqanin lokaci dukka suka fita hayyacinsu,tuni ya zare hijab din jikinta yayi nasa waje "I love you angel......i love you my moon.....i love you diyammm" shine abinda yake iya fada kawai cikin rarrabewar sauti,jikinsa na rawa. Dan bugun motar da akayi yasa shi tsayawa cak,wasu dalibai ne da sukazo wucewa suna hira daya ta daki motar suka wuce abinsu,sakinta yayi a hankali ta sulale daga jikinsa ta koma seat dinta tana dunqulewa waje daya,yayin da shi kuma ya dora hannunsa cikin sumarsa yana yamutsata sosai idanuwansa a rufe bugun zuciyarsa nata tsere da sauri da sauri. 74 Sun jima a hakan kafin ya bude idanunsa a hankali,sannan ya miqe ya zauna yana kallon cotton din yadinsa fari qal daya ya mutse,ya fara maida button na rigarsa,sannan ya duqa qasan motar a hankali ya lalubo hijabinta ya matsa a tausashe ya miqa mata,bata iya hada ido dashi ba,ta miqa hannu ta amsa ta zura,sai daya tabbatar ta saka sannan ya dage coloured glass din da ya sauke din,ya sanya hannu ba tare da yace komai ba ya buda murfin motar,ya zagaya ya bude mata,ta zura qafafunta a hankali ta fito. A gaba ya sanyata yana biye da ita kamar wani bodyguard dinta har zuwa office din da ake shigar da dawowar dalibi a register,ya cike komai ya kuma ce kada a sake barin kowa yazo daukanta,sai yazo da kansa ko kuma ya bada umarnin a dauketan,cikin ma'aikatan su suka daukar mata jakankunanta,cike taf da kaya fiye da yadda ta saba zuwa dasu,kamar zata bude qaramin provision. Tana takawa a hankali zuwa dakunan kwanansu amma tana jin idanunsa cikin jikinta,ta tabbatar yana tsaye yana kallonta,saidai bata waiwaya ba har ta qule. Nannuyar ajiyar zuciya ya sauke,yana jin kamar an cire zuciyarsa an wurgata can nesa dashi,sai ya waiwaya jiki a mace ya buda motar tasa ya tadata yabar cikin makarantar yana jin duk wani farinciki da yayi saura a zuciyarsa yana raguwa. Numfashi ta sauke tana duban dakin nasu,tayi missing nasa,saidai yadda ta dauka zatayi farinciki da da dawowa cikinsa sai ta lalubi hakan cikin zuciyarta ta rasa,hasalima wani mutuwar jiki takeji da kasala,sai ta zauna bakin gadon ayman,ta zare socks din qafarta da takalminta ta wuce toilet ta daura alwala. Sallar la'asar tayi,tana son binsu masallaci amma kuma batason garin murnar nan tasu suyi mata tarere,don haka sai ta bude jakankunanta,ta fara fidda kayanta tana shiryawa. Kafin wani lokaci ta gama shirya komai yadda ya dace,ta sake kintsa musu dakin,wanka take som yi amma ta kasa,sai ta koma ta kwanta gadon afrah tana jin wata lafiyayyar gajiya tana bin jiki da gabobinta,haka kawai takejin zuciyarta duka babu dadi,walwala da dokin dawowa makarantar duka sun kau,ta lumshe idanuwanta,abun mamaki sai tunaninsa ya soma mamayarta,ta fara hangen fuskarsa a mabanbantan lokutan da suka kasance tare dashi. Ganin lokaci na tafiya kuma ta gaza hasala komai sai ta yunqura ta miqe tana duban dan qaramin agogonsu dake jikin bango,wanda afra ce ta maqala musu,tace hajjanta wato kakarta ce ta bata shi,yau kamar sun dan gota lokacin dawowarsu,ta miqe ta shiga dube duben dakin babu abinci,kuma yunwa take dan ji,duk da taci abinci kafin su fito,don takeaway ya mata na musamman da abinda taji ranta yana so. Babu sauran abinci a cikin dakin,da alama ma basu dafa komai ba,a kitchen suka karba abinci,sai ta zari hijabinta har qas ta zura ta sanya slippers ta fito,tana tuna maganar da ja'afar ya gaya mata sanda suna kan hanya,hannunsa na cikin nata "Please ki kularmin da kanki,ki adanamin kanki da kyau,don babu yadda zanyi ne da anni,kamar uwa take a wajena,banda ita abbi da amma babu wanda ya isa yayimin wannan hukuncin na yarda dashi,zan iya mutuwa wallahi angel......ina da kishi sosai.... please take care of yourself". Ajiyar zuciya ta saki ta qarasa shiga kitchen din,mama's dinsu dake musu girki dukka ta samesu suna nan,kowacce cikin fara'a ta soma mata maraba,ita kuma tana gaidasu cikin matuqar girmamawa,suna son maimunatun sosai saboda yadda take martabasu,ba kamar wasu daliban da suke ganin sun fito daga gidan gata ba,ana.biya musu school fees almost one million naira so babu me takurasu "Munata jajjabin rashin dawowarki,sai afra tace ai kunyi tafiya ne keda 'yan gidanku" "Eh wallahi mama" "To madalla,an dawo lpy ko?" "Lafiya lau mama,zan samu abinci kuwa?" "Eh akwai na rana da akayi,bari na duba miki" ta fada tana buda babbar tukunyar,ta deba mata cikin plate maimunatun ta karba tayi mata godiya kamar yadda ta saba tana cewa "Idan kun tashi aiki mama kiyimin magana,sai ku karbi tsarabarku" kusan hada baki sukayi wajen mata godiya,indai kyauta ne maimunatun ba daga nan ba,ta juya ta fice da abincin a hannunta. Sam bata kula da tahowarsu ba,gab da zata isa dakinsu taji an saki ihu,kafin ta waiwayo taji an rungumeta tsam ta bata,ayman da fatima kuma suka zagayo ta gabanta suna riqe da hannunta gam,wanda saura kadan abincin hannunta ya kife a qasa "Daga ina?,saukar yaushe?,wai mu zakiwa suprise moon?,kin barmu gaba daya makarantar babu dadi?" Murmushi ta sake musu,ita jikinta gaba daya babu wani cikakken qwari "To sakeni afreen,afwa,wacce tambaya zan amsa miki a ciki?" "Duka" ta fada tana sakinta gami da zagayowa gabanta tana murmushi,sai kuma ta fidda idanunta waje gaba daya,ayman tayi caraf tace "Kinga abinda na gani sis afreen?" "Ko makaho ai dole ya gani....moon?,me captain yake baki?" "Banason iskanci afreen,zaki fara ko?" Cikin qyalqyala dariyar farinciki tace "Wallahi Allah am serious,kinga yadda kika qara fresh?,jikinki kamar jini zai diga?,don Allah bai saka miki dokar sanya niqaf ba?" "Saidai ki bashi shawara 'yan wulaqanci.....mu qarasa daki don Allah" ta fadi saboda yunwa da gajiya da tsaiwar da tayi. Cikin dakin suka bude sabuwar hira,gaba daya sun sakata gaba kan irin yadda ta qara kyau da kuma yi fresh da ita "Wallahi honeymoon tayi kyau,Allah yasa an samo mana dan lagos to johannesburg" afra ta fada tana kwanciya saman gadonta tana dariya,har qasan ranta tana jin dadin canzawar aminiyar tata. Duka maimunatu ta d'ana mata a bayanta tana cewa "Mara kunya kawai,ni ba abinda ya shiga tsakanina dashi,ni da sauran kunyata" "An fada a radio" ta amsa mata tana sake sheqewa sa dariya,dariyar ta baiwa maimunatu,sai kawai ta murmusa itama. "Allah ko,inda nice ke banga abinda zaisa na dawo makaranta ba,kuma wai boarding tabdi" ayman ta fada tana duban maimunatu,idanu ta fidda "Yaushe afreen ta bata ku da son aure?" "Dan sunna yaqi sunna" ayman ta amsa mata tana dariya. Anan sukayi sallar magariba da isha'i tare,don ko fita cin abinci basuyi ba tsabar hira,fatima ce taje kitchen ta karbo musu, maimunatu ta hada da tsarabar su mama fatiman ta kai musu. Sai wajen goma na dare kowa yayi shirin kwanciya,saboda gobe suna da shiga lab qarfe takwas,malamin kuma yace duk wadda ya rigata shiga ba zata shiga ba,tasu tsarabar ta ware,dogayen riguna ne masu kyau irin daya,sosai sukayi murna kamar basu taba sawa ba,duk da kowacce a cikinsu tafi qarfin abin,amma hausawa sukace alkhairi dadi gareshi,koda kafi qarfin abun. Ba'a rufa awa daya ba dakin ya dauki shuru,da alama bacci ya daukesu,sama ko qasa maimunatu ta nemi bacci a idanunta ta rasa,ta dinga juyi tana canza position da wajen kwanciya,saidai still dai kwanciyar babu dadi,ta dinga jan qananun tsaki,gadon ne babu dadi ko kuma katifar?,ko sauyin wajen kwana?,sai ta rasa amsar tambayar,can wani sashe na zuciyarta kuma yanata qoqarin danne abinda ke taso mata,tana ta qoqarin karyata zuciyar tata,yaushe ta sanshi?,yaushe sukayi sabon da zata ji babu dadi don babu shi a kusa?,kwata kwata sai kwanciyar taqi mata dadi,ta runtse idanunta da kyau tana qanqame filo a qirjinta,tana son tilastawa kanta yin baccin ala dole. Maimakon baccin sai memories dinsu dashi ya dinga dawo mata,haka tayita ganin komai cikin idanunta,ta jima kafin ta samu idanuwanta suyi nauyi,a hankali bacci ya fara sauko mata. Hannu ya miqa a hankali,ya rage hasken reading lamp din dake saman kyakkyawan zagayayyen table din da ya cikasu da takardu,sai ya koma da baya yayi relaxing yana shafa sumarsa gami da furzar da iska daga bakinsa,ya janyo a gogon dake gefansa a matuqar gajiye yana duba lokaci. K'arfe biyu harda minto goma na dare,qaramin tsaki yaja ya maida agogon muhallinsa,bai taba ganin dare mai tsahon wannan ba tunda yake a rayuwarsa,ya tsammaci zaman da yayi a nan zai tsinciki kiran sallar asuba ne,saidai gaba daya lokacin ma kamar baya tafiya,kamar a tsaye yake cak. Maida kansa yayi ya jinginar,ya rufe fuskarsa da tafin hannunsa yana dan lilo kan kujerar da yake zaune,gaba daya ita ke masa yawo tsakanin idanuwa zuciya zuwa qirjinsa,sau biyu yana attempting kwanciya,amma idan yaje sai yaji ya gaza zaman bedroom din,memory din data bashi yammacin jiya zuwa dare ke dawo masa,sai ya miqe tsaye yana kwasar wayoyinsa gami da kashe fitilar gaba daya ya sake nufar bedroom din. Sai daya shiga toilet ya daura alwala yayi bursh sannan ya dawo ya kashe qwayayen dakin ya nufa gadon,addu'ar bacci yayi yaja duvet yana rintse idanunsa gami da addu'ar Allah ya kawo masa bacci da wurwuri,saidai inaa,addu'arsa bata ciba,don gaba daya qamshin ta daya maqalewa pillow din data kwanta jiya akai shi kuma yau ya daukeshi yayi amfani dashi shi ya maqale masa a hanci,ya shiga tuna masa da ita gamida tada masa hankali. Dogon tsaki yaja kamar zai cire harshensa,dukka anni ce taja masa,ta yaya za'ayi mutum da matarsa amaisheshi gauro?,don ya kaita boarding school a baya....ai ya aikata hakanne a sanda baisan daraja da kimarta ba,a yanzun kuwa duk duniya yafi kowa sanin martabarta,da wannan tunanin da kuma kewar ya dinga fama har ya samu baccin ya daukeshi. °°°°°°°°sati guda kacal amma gaba dayansu kowa ya jikkata a jiki da zuciyarsa,tuni ya sallama cewa soyayyarta ce tayi masa mummunan kamu,irin kamun da yakejin labarinsa a labarai yake kuma qaryatawa,ashe da gaske haka ne?,komai yakeyi tana cikin tunani da zuciyarsa,sai ya fara samun cikas a ayyukansa na office,wasu abubuwan sai yayita mistake,sai jabir ya ankarar dashi,mamaki yanata shigan jabir,lallai gigitaccciyar soyayya ce ta kama ja'afar din "Kaga masu abu da abunsu,malaman soyayya" ya fada a ransa yana sakin qaramin murmushi. Yayin da bangaren maimunatu kuma taketa dojewa kan gajiyar tafiya ce ke luguiguitata sanda afra suke mata tsiyan ta faye zama cikin tunani,sannan bata baccin kirki cikin dare,ko tana kewan captain ne?. Tun tana qaryatasu tare da basu uzurorinta har ta soma sallamawa itama,a hankali ta sake zama so silent,duk da bata yiwa su afrah miskilanci amma a yanzu kamar ta sauya musu su dinma,tafi kebewa ita kadai ta zauna shuru,wanda ba komai take ba illa tunani. °°°°°°°°°Karfe tara na safiya ne,yana kwance bayan motarsa qiran ferrari,daga gidansa na government house road zuwa gidansa dake zuwa gidansa dake daya baro tun randa ya dauko maimunatun,bai sake komawa ba,koda ta koma makaranta ma a nan gidan yaci gaba da zama,a yanzun ya samu qwarin gwiwar zama a ciki tunda aka kwashe kayan shaheeda daga ciki,akwai takardun da yakeson debowa daga can gidan kafin ya wuce office. Gaisawa sukayi da masu gadin gidan nasa,sannan ya wuce ciki da dan gaggawarsa yana gayawa driver din nasa kada ya kashe motar yana fitowa. Bai jima ba ya dauko abinda zai dauko din ya fito,yana saukowa daga stairs din yana sake duba file din don tabbatar da cewa ya dauko komai a ciki da yake buqata. "Ka kulamin da jaka karka karcemin ita fa" muryar da yaji kenan data samyashi dago kansa,ido hudu sukayi da unaisa,wadda ke takowa cikin gidan,sanye da wata irin mini gown da straight leg trouser,kusan rabin fuskarta mamaye da sun glasses,tana tauna chewing gum. Cikin tsawa ya bawa mai gadin umarni "Ina zaka da wannan jakar?" "Ah....hajiya ce tace a kawo mata ciki" "Kana qara taku daya da ita a bakin aikinka,koma da ita inda ka daukota" cikin rawar jiki da kuma matuqar tsoron rasa aikinsa ya janye akwatin zuwa baya,bai kuma sake bi takan maganar unaisa dake cewa karya fitar mata da kaya ya qaraso mata da ita ciki. Wani kallo me cike da qasqanci da kuma qyama ya jefeta dashi,zallar kwarjinin da yake dashi ya daketa,gaba daya sai tayi collapse,har ya qaraso bakin sassan nata da ta zura key da nufin budewa,ya sanya hannunsa ya zare key din ya jefa a aljihunsa ya kewayeta ya fice abinsa ba tare daya ce mata uffan ba. Sai daya kira dukka ma'aikatan gidan yaja kunnen kowannensu kan kada wani a cikinsu ya kuskura ta sashi abu yayi mata,koda ja mata luggage dinta ne,yaja musu kunne da kakkausar murya kam duk wanda yayi hakan a bakin aikinsa,cikin bin umarni kowa ya amsa mishi,tare da tabbatarwa kansu ba zasuyi wannan gangancin ba,a yanzun samun gidan aiki me cike da kyautatawa da bayan salary dinsu harda allowance ake basu abu ne mai matuqar wahala,bai tsaya sauraren rantse rantse da ban haqurinsu ba ya shige mota ya bawa drivern umarni su fice a gidan. Ranshi ya baci sosai,amma tun kafin yakai office ya tattara damuwarta ya watsar,abu daya ne ya sani cewa ko sama da qasa zata hadu bazai taba iya zama da ita ba,bazai furta mata komai ba,amma dole takai kanta gida ta kuma gaya musu daga inda take,ta bakinta komai zai fita yana nan yana zuba idanu. A bakin office dinsa ya tarar da jabir yana jiransa,gaba yayi yana qoqarin shiga tare da fadin "I come late,am sorry" ya dauki uzuri,sabida ba dabi'arsa bace saba alqawari da lokacin zuwa aiki,binsa da kallo jabir yayi yana qoqarin karantar yanayinsa,gaba daya ja'afar din ya wani sukurkuce a 'yan kwanakin,duk da yadda yake nuna qarfin hali,anya zai jure?,bazai tayashi baiwa anni haquri ba ta sauka daga kujerar naqin data hau ba?. Koda ya sameshi a office din bashi lokaci yayi,sai da yaga ya dan nutsu sannan suka gaisa,ya miqa masa takardun ya koma ya jingina da makarin kujerar da yake kai yana kallon ja'afar din duba na kai tsaye. 75 Jan files din da jabir din ya tura masa gabansa yayi ya fara budesu yana dubawa,tun baiyi nisa ba ya rufesu yana duban jabir din "Wannan ya akayi haka?" Gyara zamansa yayi "Kai za'a tambaya malam ja'afar,tunda dai duka sanya hannunka ne a ciki,Allah yasa banyi gaggawar yin nawa sign din ba,da asara zamu tafka ba 'yar kadan ba" shuru yayi ya sake budawa yana kuma dubawa "Duka cikin satin nan nutsuwarka ba'a jikinka take ba why?" Rufewar ya sakeyi yana sauke ajiyar zuciya,ya hade yatsuntsa waje daya,sai kuma ya sake warasu yana shafa sumarsa "I'm not in a good mood jabir,anni tanason tayimin abinda zai sa na sake ajiye aikina gaba daya,very soon kuwa,idan ba haka ba zanyi ta shirme ne kawai" danne dariyarsa jabir yayi ya gyara zamansa "Tun farko laifinka ne J,ba yadda ba'ayi dakai ba kada ka kaita boarding amma kaqi,duk abinda babba ya hango yaro bazai taba hangoshi ba" "I made a mistake,what is the solution?" Shuru kadan jabir yayi sannan yace "Yanzun dai kome zakayi anni zata gane setup ne kawai,so ka qara haquri ina ganin,zuwa sanda zasu gama exams su dawo gida hutu,daga nan sai kasan me zaka.shirya da zai hanata komawar" kai ja'afar ya fara girgizawa "No... gaskiya,I can't wait until they finish the exam,lokacin yayi tsaho" "Okay,shikenan,do your worst......amma kasan anni dai" "Wait.....wai ita kemin zaman auren?" "A'ah,amma ita tayi maka auren" ya fada yana dariyar tsokana,sai akwai ja'afar din ya saki murmushi ba tare daya shirya ba yaja gajeran tsaki sannan a fili yace "Rabbish rahli sadry,wa yassir ly amry" sai ya dauka correction fluid ya bude ya soma gyara inda yake da kuskure yana gyarawa,jabir na zaune suna tattaunawa akan kasuwancinsu. Haka kawai ya samu kansa da yawo saman titi bayan an tashi daga office,jabir da ya dauko ya rakashi aka masa gyaran fuska ya dubeshi "Ka yiwa Allah ka kaini gida,na gaji da wannan ragaitar,kada fa'eema ta dauka wani gun na wuce tayi fushi dani" harara ya waigo ya watsa masa,sai ya qarawa motar wuta "Ni da kuka hada baki da anni kuka maida tawa makarantar kwana wato na mutu kenan?" Dariya sosai ya sake "Wa ya isa ya daukar maka mata ya kaita can?,kai kakai kanka" shuru ya kasa na wasu mintuna sannan ya sauke ajiyar zuciya "Abu daya zai hanani daukota yanzun,wannan aikin da nakeyi a kanta,amma da zarar ya kammala na daukota daga makarantar to ta fito kenan,ba ruwana da wata anni" dariya ya kuma yi,sai kuma ya katse yana cewa "Niko kamar naji kace unaisa bata nan?,ina ta tafi?" Ajiyar zuciya ya sauke hade da wata zazzafar iska daga bakinsa,ba boye boye tsakaninsu da jabir,a nutse ya gaya masa komai. Shuru jabir din yayi abun yana kadashi,magana ta Allah bazaiso ja'afar dinsa ya hada jini da unaisa ko ya riqeta amatsayin matar aure ba,shi kansa tun randa ya fara ganinta ya gane fuskarta,yayi shuru ne baice komai ba saboda baisan me Allah ya shirya ba,sannan kuma ma babu kyau mutumin da yayi tuba na gaskiya ka tona asirinsa,ashe da sauran rina a kaba. Shawara ya bashi ta hankali,wadda ta kusan zuwa daya da abinda ja'afar din ya yanke,saidai shi yace ya sanar da abbi abinda ake ciki "Ka qyaleta,idan baka iya kama barawo ba sai barawo ya kamaka,da kanta zata fadi me tayi da inda taje,idan tana taqamar gata sai gatan ya qwaceta" har suka isa gidan jabir din suna tattauna batun. Babu yadda baiyi dashi ya shigo ciki suci abinci ba amma yace aah,ya kunna motarsa ya qara gaba,dama yasan mawuyacine ya shigo din. Samun kansa yayi da kasa komawa gidan,saboda yasan idan ya koma din ma bawai zama zai iyayi ba,gaba daya both gidajen guda biyu babu wanda yake masa dadi,yaja tsaki yafi a qirga a saman titi,kafin ya yanke ya tafi gidansu kawai ko zai rage tsahon dare a can. Ganin lokacin sallar magrib ya kusa sai ya sanyashi zama saman motar abinsa ba tare daga shiga cikin gidan ba bayan ya faka motar a parking lot na gidan,ya fidda wayarsa ya soma dannawa,kusan babu wanda yasan ya shigo idan banda ma'aikatan gidan. Bai rufa minti ashirin ba aka sake hon,mai gadin ya tashi ya sake budewa,sau daya ya daga kai ya kalli motar,sai ya maida kansa yaci gaba da danna wayarsa,motar hisham ce,ta gangaro gefansa tayi parking. Sosai abbi dake zaune gefan hisham din yadan kafe ja'afar da ido wanda.baima san waye da waye a cikin motar ba "Miskili kafi mahaukaci ban haushi" abbaya fada yana murmushi yana duban fuskar ja'afar din,kallonsa hisham yayi shima yana taya abbi murmushin,ya karanci kamar akwai damuwa akan fuskarsa,amma ba wanda zai iya buda baki ya gayawa,yasan bazai wuce case dinsa da anni ba,ko kuma unaisa da yau minister ya kirashi ya gaya masa cewa ya turo ta gida ba tare da sunsan meye ya faru ba,bude murfin motar abbi yayi yana cewa hisham ya biyo shi da jakarsa. Yana ganin abbi din ya ajjiye wayarsa ya duro daga bayan motar ya tako inda yake cikin girmamawa yana masa sannu da zuwa "Yauwa ja'afar,ya gida ya iyali?" "Alhmdlh abbi" ya fada yana shafa kansa "To masha Allah,bari na shiga ciki na fito sai mu wuce masallaci tare ko?" "Okay abbi" ya amsa masa,zuwa sannan hisham ya qaraso,ya miqa masa hannu sukayi musabaha yana gaida yayan nashi,sannan suka rankaya ciki suka barshi a wajen. Babu jimawa abbi ya fito da alwalarsa,tuni shima yayi tasa a bayan gidan suka wuce masallacin. Bayan an idar a hanyar dawowarsu abbin yake tambayarsa "Me yarinyar nan unaisa tayi maka manya?,abun kuma har yayi girman da zaka turata gida?" Abbin ya fada a tausashe,duk da tsauri da zafinsa amma yana sauqin kai da kuma saurin fahimtar al'amura "Abbi,tafi kowa sanin abinda tayi,ita ya kamata ta gaya musu da bakinta" kai ya girgixa "Yanzun ai ni nake tanbayarka bawai su ba,me tayi maka,ka gayamin ko mene ne,sai asan yadda zq'a gyara abun" kai ya girgiza "Abbi.....banajin zai gyaru" "Meye wanda bazai gyaru ba?" A nutse ya gaya masa dukka wani abu daya taba sani a baya akan unaisan,da kuma abinda ya farun yanzu da binciken da yayi da hujjojin da ya samu. Sosai abbin ya kadu,don bai taba kawowa yarinyar haka ba,duk yadda suke takatsantsan wajen samawa 'ya'yansu maza da mata abokan rayuwa na gari,amma duk da hakan bai nunawa ja'afar din ba sai yace "Ka barni da kaina zan sake bincike" "To abbi" ya fada hankalinsa a kwance,tunda dai ya sani,koda abbin din zaiyi binciken zai binciko kwatankwacin abinda shi ya samu ne koma wanda ya fishi. Zuciyarsa ce ta dinga raya masa ya yiwa abbi zancan maimunatu,sai kuma yaga bazai iya ba,don haka ya share batun,yasan dai akwai lokacin daya dibama koma meye anni ta shirya. Sassan amma suka wuce shida abbin din gaba daya,saboda yace yunwa yakeji,yau da wuri zaici abincin darensa,baya wasa da girkin amman,saboda yadda ta qware sosai wajen sarrafa abinci,tarin masu aiki ko sarauta ko arziqin da take dashi baisa ta sako abincin mijinta ba hannun yara ko masu aiki,har yau har kwanan gobe ita keyi,saidai a tayata. Amma na shirya musu abinci suna fira sama sama,bayan ta gama itama sai ta samu kanta da zama a cikinsu,abinda ba kasafai takeyinsa ba,duk da ita bacin abincin take ba,tana ta dai serving dinsu ne,daga baya saiga hisham ya shigo shima yayi joining dinsu, khadim ma sai gashi,da yake sau tari sai ya baro abincin ammi ya taho wajen amma ci,duk da itama ammin gwana ce,amma shi dan dakin amma ne. Bai waiwayi sassan anni ba sai da ya dawo daga sallar isha'i ya kusa wucewa gida,tasan ya shigo gidan sarai,kuma batayi mamakin rashin shigowarsa ba,sanda ya shiga tana zaune a falo tana shan damammiyar fura data sha sugar,don annin ba daga nan ba wajen shan zaqi,kanta ta daga ta dubeshi sannan ta tabe baki ta maida kanta ga abinda takeyi,ya samu hannun kujera ya zauna yana gaidata,a yatsine ta amsa masa,yadan zubawa tv ido sannan ya miqe "Wannan sugar din da kike yawan sha fa yana yawa,shekarunki sun ja" dama jiransa take,saboda haushin qin shigo matan da baiyi ba,saboda ta saba anan yake sauka ko yaushe bayan ya gama gaisawa da kowa "Kai arcannnn.......kayi ta kanka malami,mu jikinmu ba irin naku bane, sugar abin banza ba abinda zaiyi mana,haka zamu mutu ras da lafiyarmu in sha Allah,damu da mazanmu ba irinku bane,wanda sai mace ta shekare a gidansu su kasa yi mata ciki sabodq tsabar raggwanta" dole ya dora idanunsa akan fuskar anni,tirqashi😂, abun yazo harda gori?,ya tabbatar dashi take,shi takema gorin baima maimunatu ciki ba,don yasan itace tata,da ita ta damu. Murmushin gefan baki ya saki yana cusa hannuwansa a aljihun wandonsa,shima bari yayi mata ta 'yan zamani "Me kike ci na baka na zuba anni?,ba tsallaken shekara daya bane?,to itama za'a ciketa,ki rubuta ki ajjiye biyu xa'a baki ko uku,nex year mu sake maimaitawa" daga haka ya juya yana ficewa daga falon,sai ta bishi da kallo,tana jin sanyi qasan ranta tare da cewa "Ameen ya hayyu ya qayyumu,'yan ameen su amsa ya rahman" can qasan ranta,amma a fili sai tace "Ahhh waima,zamu gani". Yana mota yana tuna matter dinsu da anni,sai kawai ya samu kansa da sakin murmushi,tare da imagining diyoyi daga wajen maimunatu,wanne irin kyau zasuyi?. Duk guje gujensa yau dinma sai da yasha baqar wahala kafin ya samu bacci ya daukeshi 76 A hankali ta rufe bangon littafin dake gabanta gami da sauke ajiyar zuciya,zuciyarta na wani irin karyewa da kuma samun rauni,a hankali ta zubawa wajen da afra suke zaune suna hira kallo,tun dazun suka ce mata ta bar karatun tazo tayi joining dinsu amma taqi,saboda bata da wani karsashi ko farincikin hirar,tunda ta dawo sati biyu cikin na uku zuciyarta a quntace take,ba wani walwala ko farinciki. Wayarta ta zaro ta sake kallon fuskar wayar,cikin sarewa da gajiyawa ta dora wayar saman table din data aje littafin nata sannan ta zame ta kwantar da fuskarta saman table din,daga dawowarta zuwa yau batasan sau nawa ta duba fuskar wayarta ba,haka kawai taji tana tsimayin kira daga gareshi,saidai ko sau daya bai kirata din ba,tana ta sanya rai taji ance tazo gashi,duk da tasan ba bari ake azo ganin naka ba idan bada wani babban uzuri ko dalili ba,amma tata zuciyar nata shauqin jin hakan,saidai shuru,lumshe idanunta tayi tana jin yadda zuciyarta ke tabuwa,ba zata taba kiransa ko sau daya ba,sabida tayi alqawarin jan ajinta da mutuncinta,zata kuma cika burin anni in sha Allah "Maimoon,lafiya?,me ya sameki?" Taji muryar afra saman kanta,sai ta bude idanunta da kyau a kan fuskar afran "Me kike gani?" "Kuka.....hawaye fa kike?" Bata yarda da zancan afra ba sai data sanya hannu ta shafi fuskar tata sannan taji danshinsu,abinda ya sake sanya zuciyarta karyewa,kawai sai ta saki kukanta sosai tana kifa kanta a table din. Da sauri afrah taja kujera dab da ita ta zauna tana fadin "Innalillahi,wai menene yake damunki maimoon?,meye matsalar?" Bata bata amsa ba,sai kawai tasa hannu ta zare wayarta dake gefe,tasan me zatayi mata. Contact ta shiga ta fara laluben sunayen soyayya data sama wata contact,saidai babu ko daya a ciki data gani,haka ta haqura,ta sanya ainihin sunansa saiga number din ta fito,kallon maimunatu da batasan ma tanayi ba tayi taja qaramin tsaki,wai itakam yaushe zata bude zuciyarta ta yarda soyayya takeyi?,ta kuma gane ita ke wahalar da ita?,kawai saita canza sunan dake kan number zuwa honey bee,sannan kanta tsaye ta danna masa kira. Dai dai lokacin yana kwance a wajen hutawa daya ware cikin office dinsa,tunda yazo yake zaune a wajen,ya gaza hassala komai,baisan me yake damunsa ba,gaba daya tunda ta tafi ta tafi da walwalarsa,hannunsa daya bisa fuskarsa,sai yaji shigowar kira wayarsa. Har tayi ringing dinta ta katse bai dauka ba,ta sake shigowa ta kuma katsewa,ya shareta yana ci gaba da kwanciyarsa,har sai da yaji qishirwa,sannan ya miqe zaune ya jawo wayar yana son duba lokaci,don da wuri zai fita daga company din yau,saboda ya lura bazai iya aikata wani abun kirki ba. Ganin miscall da number ta yasa ya tashi ya zauna sosai,bai zaci wayarsu na amfani ba a school,daga sama kuna tex ne _ka kira pls yaa ja'afar,qawar maimoon ce_ Bai gama karantawa ba ya fita a saqon ya kira number din,yana jin yadda zuciyarsa ta tafi gaba daya ta kuma afu gason jin muryarta. Da sauri afra ta duba kiran sannan ta dan matsa gefe kadan daga inda maimunatu ke zaune ta daga "What's happening?" Ya tambaya kai tsaye,jin ba muryar maimunatun bace "Kuka dai takeyi,na tambayeta taqi magana" "Bata wayar" ya fada cikin jin wani tashin hankali yana shigarsa,meye ya sameta?,itace tambayar daya fara yiwa kansa. "Yaa ja'afar ne" ta rada mata a hankali,kafin ta gama fuskantarta har ta nana mata wayar a kunne "Angel" ya furta cikin wani irin taushi,da zuzzurfar muryarsa data aike mata da wasu saqonni lungu da saqo na jikinta karo daya,wani nauyi taji zuciyarta tayi,hawayenta kuma ya dauke cak,ta zuqi numfashi sosai tanason fesarwa amma kamar ya riqe "Hello.....angel,my moon" ya sake fada very softly,wannan karon fidda numfashin tayi gaba daya,wanda ya zame mata kamar ajiyar zuciya mai sauti,batasan sanda tasa hannu ta dafe wayar sosai a kunnenta ba,har yanzu idanuwanta suna rufe tana sauraren saukar numfashin sa daga cikin wayar,da alama shima ta taba zuciyarsa sosai "Say something mana angel,bazan iya jurewa ba,meye ya faru?" "Zazzabi" ta fada muryarta a mugun narke,kuka mara sauti me dauke da hawaye yana kubce mata "Ya salam......jirani gani nan zuwa" ya fada yana katse wayar gaba daya. A gaggauce ya maida takalminsa ya kira PA yayi cigiyar key din motarsa,ya karba ya fice ba tare daya tsaya sauraren kowa ko kuma meeting dake gabansa awa daya mai zuwa ba. Kasa motsawa tayi daga wajen,sai kunnuwanta suka shiga maimaito mata abinda yace "Ta jirashi gashinan?,da gaske zuwan zaiyi??" Zuciyarta dai ta cika da wasi wasi,amma duk da haka sai tayi likimo taci gaba da kwanciya a wajen,har zuwa sanda ta tsinci muryar afra na kiranta irin kiran gaggawa,idanuwa kawai ta bude tana jiran isowarta "Ana kiranki office din principal,yaa ja'afar ne yazo" batasan ta miqe da hanzari ba sai data ji kanta ya saara,ta dafe kanta da hannunta sannan ta dubi afra "Muje ki rakani please" hannunta ta riqe tana murmushi,tanason tsokanarta amma kuma yanayinta yana nuna seriousness dinta kan condition din duk da take ciki,don haka shuru tayi tana taka mata zuwa office din. A nutse tayi sallama a office din,idanuwanta na kallon qasa,don ta tabbatar indai idanunta a dage suke kuma yana cikin office din,tofa lallai idanunsa suna kanta ne,ita kuma a yanzun batajin zata iya dauke idanunsa akanta,bata jin zata iya jurema wannan kallon nasa,qamshinsa kawai ya isa ya bata tabbacin yana cikin office din,taci gaba da takawa a hankali,sai zuciyarta ta gaza jurema rashin kallon fuskarsa,ta yanke shawarar ko satar kallonsa ne tayi. Ta kuwa aikata hakan,saidai kuma ya kamata,don caraf idanuwansu suka hadu waje daya,yana binta da wani irin mayen kallon da shi kadai yasan fassararsa,gaba daya yaga kamar an sake canza masa ita,ta sake kyau ta sake fresh,saidai tadan faada kadan "Zaki bishi zakuje ku dawo" principal din ya fada kansa tsaye,tunda yasan waye ja'afar din a wajenta "Okay sir" ta fada kanta a qasa,sannan ta miqe ta soma takawa a hankali tana ficewa a office din da zummar zuwa dakinsu ta gani idan akwai abinda zata dauko. A hankali taji an riqo hannunta ta baya a tausashe tana hanyar komawa hostel,da sauri ta waiwayo,tadan razana saboda hanyace da babu masu wucewa sosai a kanta,sannan kuma batasan ana biye da ita ba. Idanuwansu suka sarqe waje guda,kowanne ya jefi dan uwansa da wani abu mai matuqar tasiri a ruhi da gangar jiki,suka shiga jin kamar zasu narke a wajen saboda abinda ke zagaya zugata da gangar jikinsu,sukaci gaba kuma da kallon junansu kamar an manne idanuwan nasu cikin na juna ne,bata ankara ba ba zato taji ya fusgeta zuwa cikin jikinsa da wani irin zafi,har takalmin qafarta yana zamewa daga qafartata. Sosai ya riqeta a jikinsa saidai kuma cikin taushi,baiyi wata wata ba ya kama fuskarta da kyau ya riqe gam,ya fara sauke mata kisses,tare da lashe labbanta da yayi matuqar missing dinsu kamar hauka. Gaba daya ya kunce mata noti,jikinta ya dauki rawa,tanata qoqarin tureshi amma yafi qarfinta nesa ba kusa ba,sai da dabara tazo mata,ta kama labbansa ta ciza da dan qarfi,sannan ya saketa ya d'an ja da baya yana fadin "Wash Allah na amma na" a wahalce kamar wanda aka yiwa duka aka galabaitar dashi. Da rinannu idanuwansa yake kallonta,yayi da ita kuma dariya taso kubce mata jin kiran sunan amma da yayi kamar wani qaramin yaro,amma saita danne,ya rigata magantuwa "Wannan fa mugunta ce,so kike ki.kasheni ko?,tunda kika shigo kinqi kallona,sannan kuma kin fito kin barni ni daya irin baki damu dani ba ko?,kuma yanzun ina welcoming naki saiki cijemin labba?" Ya fada yana taba leban nasa da zara zaran yatsunsa guda biyu. Bakinta tadan rufe tana fidda fararen idanuwanta waje,wanda hakan ya qara fidda girmansu "Bafa haka bane,ban wani cijeka sosai ba,nan din hanya ce,wani yana iya zuwa wucewa" sauke yatsun nasa yayi yana ci gaba da jifanta da mayataccen kallonsa,sai ya fara takowa yana fadi a hankali "I don't care ni ko waye zai ganmu,ni ke kadai nake gani idanuwana da zuciyata gaba daya,kuma zakisan kin cijeni,you will pay" ya qarasa maganar yana riskarta gami da surarta gaba daya cikin hannuwansa. Bugun zuciyarta ya qaru,tsoro ya cikata,kada a ganta fa mutuncinta ya zube,tunda ba kowa bane yasan alaqarsu ba,shi bayajin kunya ne "Don Allah......don Allah,ja saukeni,akwai abinda zan dauko a daki" "Bana buqatar komai,ke kadai nake buqata" "To zan iya qarasa mota da kaina" "Banaso shima,jikinki akwai dan dumi amma ba mai yawa ba" runtse idanunta kawai tayi sosai,ta buda suit dinsa ta saman ta cusa kanta a ciki tana jin tsoro da fargabar wanda zai iya ganinsu a haka,cikin taimakon Allah har suka kai bakin motar basu gamu da kowa ba,dama yammace,kuma hanyar bata jama'a bace. "Sauka to madam karki hadiyeni,irin wannan riqon haka?" Ya fada yana duban fuskarta murmushi na qwacewa miskilar fuskarsa,wani zillo.tayi ta sauka jin fassarar da yayi mata,gefe guda kuma zuciyarta ta cika da mamakin dama.yana raha da tsokana irin haka?. Da kansa ya bude mata motar ta shiga,ya tattara mata hijab dinta daya fito zuwa ciki ya rufe mata,sannan ya zagaya seat dinsa yana jin zuciyarsa wasai,duk wani nauyi da tayi ya nemeshi ya rasa cikin qanqanin lokaci,yayin da itama ta langabar da kanta a kafada tana kallonsa sanda yake zagayowa ta gaban motar zuwa seat dinsa "Ya Allah,yashe ta fara sonsa har haka ne?" Saita lumshe idanunta itama sirritaccen murmushi yana kubce mata. 77 Tunda suka shiga motar ko sau daya bai sani hannunsa daga cikin nata ba,yana riqe dashi gam yana murzawa a hankali,ya dameta kan ta fada masa me yasa tadan rame ba kamar yadda ya dawo da ita ba?,ko akwai mai matsa mata?,ko makarantar babu dadi?" Tsaf ta boye idanunta cikin hijab,taqi kuma cewa komai dashi,sai ya sakar mata lallausan murmushi "Ni bari na gaya miki....tunda ke kina boyemin,kada nace kina sona ko?" Curewa ta sakeyi waje daya dariya mai dan siririn sauti tana qwace mata,abinda ya sake jan hankalinsa a kanta kenan,ya saki murmushi shima me sautin "Bana iya baccin,bana iya cin abinci,Allah kinji nace miki Allah,tunda kika tafi kika tafi da dukka farinciki da walwalata,har na dinga jina kamar marayan da babu uwa babu uba" kanta ta daga a hankali,bakinta ya subuce tace "Kamar ni kenan?" Idamunta na nuna alamun rauninta,tausayinta ya tsarga masa sosai, cikin ransa yace "Kin kusa yin dariya in sha Allah" amma a fili saiya riqe hannunta dakyau,ya jashi zuwa qirjinsa saitin zuciyarsa "Ki daukeni kamar uwa da uba a wajenki,nayi alqawari zan cike miki dukka wani gurbi da gibi da kike dashi a rayuwarki" idanunta ta maida ta lumshe,tana jin kewarsu,maganarsa ta ta katse mata tunani "Wannan zafin jikin tun yaushe kika fara shi?" "Last week ne" "Ya kamata kiga likita kenan,don kada yaci gaba" ya fada tana sanya signal a motarsa,kanta ta girgiza tana bin titin da zai kaisu gidana abbi da kallo "Yana sauka.....amna nakeson ka daukomin,tunda na dawo ban ganta ba" fuska yadan kwabe kamar yaro qarami "Noooo......so nake mu shiga duniyar da zata bamu nutsuwa,wadda babu kowa a cikinta daga ni sai ke" yadda yayi maganar yana rage gudun motar ya kuma sanya idanunsa cikin nata sai wani nauyin ya kamata,ta maida kanta baya ta jinginar tana rufe idanuwanta. A parking lot na gidansa dake government road ya tsaya,sannan ya kirayi me gadin,ya gaya masa ya rufe masa gidan,idan anzo nemansa yace he's not available😂,kasaqe mai gadin yayi yana maimaita kalmar "Yallabai kamar wani layin waya?" Ya fada a ransa "Jeka" ja'afar din ya fada yana sallamarsa,sai ya amsa da to yana komawa bakin aikinsa. Yanxun ma daukar abarsa cak yayi har zuwa sassansa,tare sukayi alwala sukayi sallar la'asar data kubce musu su duka,ya waiwayo yana dubanta a hankali bayan sun isar,sai ya zame ya kashingida yana tokare jikinsa da jikinta,idanunsa a qasa "Me zakaci?" Ta tambayeshi saboda tunawan da tayi yace bai iyacin abinci "Anything angel,indai daga gareki ne zanci,amma for now dai barci nakeji" ya fada yana zamewa a hankali,ya aza kansa saman cinyarta kwanciyar rigingine yadda yake ganin fuskarta fes,yana kafeta da wani irin kallo,idanuwansa suna lullumshewa. Hannunsa ya sanya ya zare tafin hannunta data rufe fuskarta dasu,muryarsa da matuqar rauni yace "Noooo.....don Allah please ki barni na more,don Allah,badon ni ba" sai ya maida hannuwansa ya harde a qijinsa yana ci gaba da kallonta,idanuwansa na masa nauyi,wani irin barci na rinjayar idanuwan nasa,a hankali yana kallonta suna rufewa,har suka rufe gaba daya,wani daddadan baccin da ya manta rabonsa dashi yayi awon gaba dashi. Saukar numfashin sa cikin nutsuwa ya tabbatar mata baccin yakeyi da gaske,a hankali ta sauke idanuwanta kan fuskarsa "Ma sha Allah,fatabarakallahu ahsanul khaliqin" ya fita a bakinta,asalin kyau ta gani dab da ita cakude cikin fata chocolate color. A hankali take qare masa kallo,kwantacciyar sumar fuskarsa mai santsi baqa sidik data sake qwawata fuskarsa,wani irin gyaran fuska yakeyi,kamar na jaruman fina finan qasar hindu,koma waye yake masa aski tabbas expert ne,ya kuma san aikinsa,bata taba damuwa da aski ko sanin me askin maza ke ciki ba,amma a yanzun askin ya burgeta sosai. Yatsanta guda daya ta sanya tsakanin gashin girarsa masu laushi tana zagaya girar,caraf taji ya kama hannunta,ya riqe da kyau cikin tattausan tafin hannunsa,cikin murya dake cike da mayen bacci yace "Am sorry angel,hannunkin nan mai laushi da yawa zaya hanani yin bacci,har gwara kici gaba da kallona,na baki dama,ina jinsa kamar garkuwa ne a tattare dani" yana gama fadin hakan ya sanya hannuwan nasa qasan kuncinsa yayi filo da tafin hannun nata,yana kuma sake gyara kwanciyarsa sosai cikin jikinta,kamar qaramin yaron dake jin rigima ya samu mamarsa ta dorashi kan cinyarta. Kunya da mamakin yadda baccinsa ya katse,ya kuma fahimci kallonsa takeyi ya kamata,sai tayi shuru kawai tana murmusawa kadan kadan,har zuwa sanda itama nata baccin ya iso,ya rinjayeta,sai gashi a hankali ta kifa fuskarta a tasa,sannu a hankali suka fara musayar numfashin juna. Shi ya fara farkawa,amma sai ya gaza motsawa saboda yadda tayi masa rumfa,cikin jikinsa ya dinga jin wani abu yana shigarsa yana ratsashi,ya dinga sauke murmushi shi kadai,zaiso su tabbata a haka,saidai kuma yana dan motsawa kadan itama ta farka,ta kuma tashi da sauri cikin kunya da mamakin yadda gaba daya tayi male male a jikinsa,daga kanta zuwa qirjinta. Juyowa yayi sosai yana fuskantarta kamar dazun da idanuwansa da suka dan kada kadan sabida baccin daya tashi a shi "Yunwa nakeji,please ayimin taimakon gaggawa" kai ta gyada masa tana murmushi dake nuna zallar kunya "Uhmm madam,a taimakeni,tsohuwar yunwa ta tashi" da ido tayi masa nuni kan ya dagata,bai dagata ba ya tsareta da ido amma girki yakeso,mirginawa gefe yayi da sauri yana cewa "Ya salam.....afwan" abinda ya bata damar tashi kenan,ta dauki ribbon dinta daya zame yayi nasa waje ta tattare sumarta mau santsi waje daya sannan ta tashi,yana kwancen har yanzu cikin mutuwar jiki yana qare mata kallo,idanuwansa suna lullumshewa,shi daya yana sake tsumuwa da ganin surarta,kasancewar yanzu babu hijabi a jikinta. Har takai qofa taji yace cikin wata irin murya daya cika taushi da yawa "Angel moon" sai ta tsaya cak ta waiwayo,murmushinsa shine abu na farko data fara gani sannan ya motsa bakinsa,cikin wani slow ya furta "I love you"....." Wani kunya ya bata yadda ya furta mata maganar,da kuma yadda ya kafeta da idanu,sai ta juya da dan sassarfa ta fita a dakin,bata tsaya ba sai datakai kitchen,sai ra jingina da freezer din cikin kitchen din tana sauke wata nannauyar ajiyar zuciya gami da murmushi mai taushi,ko wanne second da zaizo ya wuce mamaki J yake bata,completely ya canza,wai dama haka yake?,sai ta tuna wani hira da suka taba yi da afra,a sannan ta dauka sharrinta ne,bata gasgatata ba sai yanzu "Hmmm,rabu da miskilallun na masu jin izza da isa,da yawansu idan kikaga yadda suku sukurkucewa akan soyayya sai sun baki tausayi,Allah saiki rainasu inda xaki gansu gaban macen da suka matowa,amma suna fitowa waje sai suyita wani izza suna muzurai" saita sauke wani sabon murmushin,ta taka zuwa tsakiyar kitchen din,kwanyarta na mata searching,cikin abubuwan data karanta a dairy din shaheeda a favourite food nashi,wanne ne mai sauqi da zata dafa masa. Rub da ciki yayi bayan ta fita,ya jima a haka yana hasashen yadda yakeji a jikinsa akan maimunatu,da yadda soyayyarta tayi masa wani irin kamu,yana jin buqatuwa sosai zuwa gareta,saidai yanason ya bata space,kada ta dauka jikinta kawai.shine abinda yake buqata. Toilet ya shiga yayi aswaki da miswak na Aarak,wanda indai yayi bacci irin hakan yakeyinsa,ya fesa mouth fresh a bakin nasa bayan ya daura alwala sannan ya fito,yanason ya qarar da dukka lokacinsa tare da ita. Sam sam bataji shigowarsa ba,sai tsintar kanta tayi jingine a qirjinsa,ya zagaye ta ta qugunta,ya sanya hannuwansa saman plate tummy dinta,ya kuma dora kansa saman kafadarta yana leqen abinda take dafawa,da muryar dake wanzar da soyayya a zukata ya fara magana "Shine kika gudu?,bayan ko kwatar abinda yake raina ban gaya miki ba?,lemme tell you one to two reasons that make me love you" sai ya sake mannata cikin jikinsa sosai kamar xai maidasu abu daya,ya sake qas da muryarsa "I love you because you make me feel again that am worth something.....i love you because you make me smile when I almost forgotten how to.....i love you angel for so many reasons" gaba daya kalamansa sun kashe mata jiki,kawai saita kasa ci gaba da yanka dankalin da takeyi akan chopping board,tana riqe dai da wuqar kawai a hannunta. Sakinta yayi daya lura da haka,sai ya zame ya dawo gabanta,ya karba wuqar ya fara yayyanka mata da sauri da sauri,har yadda ya iya ya bata mamaki,yana yankan yana daga kai yana kallonta kamar zata bace masa,hakan ya sanya saura kadan ya datse hannunsa,don haka ta karba aikinta tace ta gode "Ko kin koreni ba inda zani" narai narai tayi da fuska,zuciyarta cike fal da saqonni amma kuma nauyi da kunya hadi da rashin sabon da har yanzu basuyi ba ya hanata furtawa,ya gama karantar qwayar idanunta da kyau,don haka murmushi kawai ya saki "A juri zuwa rafi da tulu diban ruwa" ya fada a ransa. Kusan shi ya tayata dukka aikin sukayi suka gama tare,tun cikin kitchen din ya zuba ya fara kaiwa cikinsa,itace mutum ta uku a duniya da yakejin dadin abincinsu fiye ma da yadda ransa yakeso,da qyar ya iya kaiwa falo ya zauna tayi serving nashi. Dadin sai ya masa yawa,ya dinga jinsa yana yawo a wani gajimaren farinciki,yana ci yana kallon fuskarta har ya kammala. Daure da babban towel ta fito a wanka bayan ta baroshi a falo yana waya,awa kusan daya kenan,a nutse ta qarasa walking closet dinsa tana dudduba kayan da zata saka,saidai babu wanda zai mata,hasalima gaba daya an kwashe sauran kayan da sukayi ragowa na mata,taja tsaki yafi a qirga,dole daga baya ta fara lalube cikin trouser dinsa ta samo daya ta saka,ya mata mugun yawa,saita tsugunna ta lanqwashe qasansa,sannan ta shiga dubawa cikin rigunansa ko zata samu wanda zata saka a jikinta. 78 Wata shirt ta zaqulo,tana da dan fadi daban,dama irinta take nema,sai ta zura,tayi amfani da turarensa ta feshi jikinta,sannan ta dauki hair drayer dinsa ta fara busar da gashinta da ya dan jiqe,ta gama fa shafeshi da mansa mai qamshi,sannan ta dauki band ya fara kiciniyar daurawa. Duk tsaiwarsa a dakin sai lokacin ya qaraso,sai daya iso dab da bayanta sannan yayi sallama,ta fito da idanunta tana kallon fuskarsa data sauya,daga fuskar da babu rahamar fa'a zuwa fuskar data saba da murmushi ciki yan mintuna qalilan,ya soma takowa zuwa inda take tsayen. "wa yace ki sakamin riga?" Ya fada cikin sigar tsokana,amma kuma yana dan bata rai,narai narai tayi da idanu tana langabe kai "Banga kayan da zan saka ba" kai ya jinjina yana isowa dab da ita,ya sanya hannuwansa duka biyu ya nade rigar sama ya riqe qugunta yana kallon fuskarta,tafin hannuwansa saman lallausar fatar jikinta yana kallon tsakiyar idanuwanta "Gaskiya bazan iya baki aro ba,nima ita zan saka" yayi maganar yana tafiya da hannayensa zuwa sama,inda yake ta tsole masa ido tare da jan hankalinsa,narai narai ta sakeyi da ido,a narke tace "Please mana,aro kawai?" Kai ya girgiza "Bazan iya ba" "Don Allah" "Ok,but let me feel your....." Sai maganar bakinsa ta.katse, numfashin sa ya fusga kadan,saboda tuni yakai.hannuwansa inda ya nufa,kafin tace komai ya tsugunna ta qasan rigar ya cusa kansa. Fara qoqarin zamewa tayi amma inaa,ya saka dukka hannuwansa biyu ya riqeta sosai ta bayanta,cikin qanqanin lokaci ya fara birkita mata kwanya,saqonnin da yake aikema qwaqwalwartata sun girmama,ta fara tangal tangal zata fadi,sai ya zare kansa daga ciki yana dubanta da idanuwansa da suka sauya launi "Please nima,ki sanmin dan kadan,i promise you wannan karon no more any pain.....i promise.....i promise angel" ya fada a dan rude saboda yadda hankalinsa yayi gaba. Bata jin dadi idan taganshi a gabanta cikin kwantar da kai yana roqarta akan hakkinsa,a hankali ta gyada masa kai tana lumshe idanu,caraf taji ya sureta yana cewa "Thank you angel moon, thank you" ya azata a tausashe saman gadon ya maye gurbin duvet yana sanyata tsakiyar qirjinsa gami da sake lullubeta da wata tattausar soyayya mai dimautarwa da kuma gigita hankali. Kaman yadda yayi mata alqawarin kuwa babu wani sauran radadi data fuskanta,saima tarin kunya da ya barta da ita, saboda yayi ta koya mata abubuwa yana sanyata tana responding masa saqonninsa,abinda ya basu wani irin dare mai matuqar qayatarwa,daren daya sake.narkar da kowannensu,ya kuma sukurkutar masa da tunani,ya sake dasa musu so da qaunar juna mai tsanani. Ko bayan komai ya kammala cikin jikinsa ya matseta tsam,idanunsa a rufe yake cewa "Let's make this lovely journey last for a lifetime,do not ever let me go,am yours as long as you want me to" wani irin abu taji yana sulalewa yana kwaranya a kwanyarta,ta gyada masa kai a hankali ta lumshe idanu tana jinta a wata duniya ta daban,dama haka soyayya take?,sai ta tuna da wani korean drama data gani,kamar haka a lokacin ta dinga imagining kanta,amma sai zuciyarta ke gaya mata it can't,ashe zai yiwu,harma fiye da yadda take hasashe. °°°°°°°°°°shi da ita dukkaninsu a shirye suke tsaf,ita cikin shirin komawa makaranta,shi kuma cikin shirin office,tsaye take shima haka,tana rungume tsakiyar qirjinsa suna musayar numfashin juna da kuma scents na turarukansu,kowannensu ji yake kamar bazai iya tafiya yabar dayan ba,cikin wata karyayyiyar murya yace "Can we go?" Ta gyada masa kanta a hankali zuciyarta na karyewa kamar kuka zai subuce mata "Okay angel.....but,inason naji kalma daya a bakinki,me yasa kikemin rowarta,baki taba gayamin ba" sai data daga kai ta kalleshi sannan ta tambayeshi "I want you to say i love you ja'afar" murmushi tayi tana cusa kanta sosai cikin qirjinsa,kunya....kunya takeji wallahi,tun jiya ya gama sakwarkwatar da ita gaba daya "Uhnnnn.... please,say it" ajiyar zuciya ta sauke,tana jin yadda zuciyarta keta azalzalarta kan ta fada din,cikin wata irin murya dake dauke da amo na daban ta fadi "Ina sonka,ina qaunarka.....i love you" "Da gaske daga zuciyarki ne?" Saita jinjina masa kai cike da qwarin gwiwa "Ina nufin dukka abinda na fadi din,da gaske nake,daga zuciyata ne" zallar farinciki ya kamashi,sai kawai ya hadeta cikin jikinsa,ta sauke ajiyar zuciya tana jin dadin kasancewarta a qirjinsa,akwai wata nutsuwa mai tarin yawa tattare da gurin,har batasan tayi subutar bakin furtawa ba "Hugging someone taller than you is the best feeling ever,bcoz you fell protected" wani murmushi mai dadi ne ya subuce masa,ya dagota yana duban fuskarta dake a kulle "Really?" Kai tsaye ta gyada masa kai "Zanci gaba da rungumarki har gaban abada,kuma.koda baki a jikina cikin qirjina kina zuciyata,and i will give you protection everywhere you go bakin rai bakin fama". Da qyar suka yakice juna ya dauketa sai makaranta. Ko cikin mota sai data kusa missing first period sannan ya barta,ta wuce dakunansu ta saka uniform ta koma aji,shi kuma yaje yayi confirming maidota da yayi yayi singing. Tun a aji suka dameta da iskanci su afra,saita sharesu saidai tana ta smiling,saboda ita kanta tasan jiyan tabar mata abubuwa masu yawa da bazata.mance dasu ba,su afra kuwa haka ta haqura da tsiyar da suketa mata har sukayi haquri sukayi shuru. Tofa captain ja'afar da maimunatu sun fasa dadin abun,kwana daya rak yaji ya kasa sukuni,da qyar ya raka zuwa qarshen sati ran Friday ya sake zuwa ya nema alfarma ya daukota,tazo tayi masa weekend,idan yaso Sunday da yamma ko Monday da sassafe ya maidota. Wani irin weekend mai bada kala sukayi, weekend din da tunda yazo duniya baijin akwai wanda ya fishi dadi a wajensa,ran litinin kuwa basu samu fita daga gidan ba sai azahar,da qyar ya taushi kansa,yana da tabbacin ya kusa gazawa,haqurinsa ya kusa qarewa,don haka ya sama kansa more effort ya gama aikin da xai sanya ya fake dashi ya raba maimunatu da makarantar gaba daya ta silarsa. K'arfe shida da mintuna ya shiga gidansu kamar yadda yawancin lokuta yake zuwa a yanzun,amma sai ya wuce sassan ammansa,ya sameta a falonta a zaune,ita daya saboda yaran basu dawo a islamiyya ba,duk girmanki a gidan dr marwan baki wuce zuwa islamiyya ba,har su salma 'yan university da ake shirin aurarwa,kasancewarsa sanannen mai ilimin addini,yakance neman ilimi baya qarewa dan adam sai idan mutuwa yayi,akwai makaranta nan saman unguwarsu me special classes irin nasu. Duqawa yayi nan gabanta ya gaidata,sannan ya zame ya zauna sosai yana jan fruit din dake gabanta hade da qaramar wuqa tana gyarawa,da alama zatayi fruit salad ne, murmushi ta bishi dashi,har yau baya ganin ya girma ko ya taka wani matsayin da zai hanashi kama mata aiki idan yazo ya taras tana yi. "Manya,me yake faruwa tsakaninka da unaisa ne?" Ajiyar zuciya mai nauyi ya sauke,duk duniya baya iya boyema mahaifiyarsa komai,don haka ya labarta mata komai a nutse. Sosai hankalinta ya tashi,amma kuma bata nuna masa ba "Haquri ake da sha'aninmu,tunda ai bata taba aikata hakan ba,sai ka bata uzuri" kai kawai ya gyadawa ammansa,amma bayajin zai taba iya riqe unaisa,bayason suci gaba da zama yana zaluntarta Allah ya kamashi kan hakan. Bai tashi a kai ba sai da suka gama aikin duka tare sannan ya daura alwala ya fice sallar magariba. Daya dawo wajen anni ya wuce,itama tana falo baba tabawa na gefanta suna kallon musabaqar duniya da ake haskowa a wata channel,wata 'yar nigeria ce ke karatun a yanzun,suna ta tattaunawa akai,saidai kowanne hannunsa riqe da carbi da alama basu jima da gama sallah ba. Baba tabawa ce ta miqe tana marabtarsa "Barka da zuwa" ya amsa mata cikin girmamawa yana zama,sannan suka gaisa "Ina uwar dakina?,tayi mana nisa" "Suna makaranta" "Uhmmm.... makaranta ko gantali daga wannan kwararo zuwa wancan?" Anni ta fada tana tabe baki,daga kai yayi ya kalleta,sai kawai murmushi ya subuce masa,shi qarfin halin anni dariya yake basa,batasan a yau idan yaso.maimunatu ta gama zuwa makaranta ba?,ya fita iya kwaso rigima sosai,amma tana da wani babban matsayi a rayuwarsa,sannan she deserved respect daga wajen kowannensu,don ta taka rawar gani a rayuwar duk wani ahali nata "A daiyi haquri a sassauta" "Yoni ai bazan dauki wannan iskantun ba,kowa ta kansa zaiyi ya shiga hankalinsa,bazan bari a haifamin jika tsakanin qarya da gaskiya ba" "Kin samawa kanki sauqi" ya fada hankalinsa kwance yana relaxing cikin kujerun hadi da lumshe idanu,dariya taso qwacewa baba tabawa saita fice,yayin da annin ta watsa masa daquwa "Kayi ta kanka ja'afaru ka kiyayeni fa?" "Na kiyeyeki" ya fada ba tare daya bude idanunsa ba,don shi yanzunma weekend dinsu na baya yake tunowa yana sa masa nishadi,tare da shirya musu next weekend yadda zai wakana. Kafin wani a cikinsu ya sake cewa komai abbi ya shigo,cikin girmamawa ya miqe yana masa sannu da zuwa,bai zauna ba sai da abbin ya samu waje ya zauna nan kusa da tsohuwarshi "Dama ina nemanka,naji dadi dana ganka" sai yayi bismillah yana zama "Zauna" ya bashi umarni,ya aikata hakan yana tattara hankalinsa akan abbi din. Maganganu ne duka kan unaisa,da yadda tace batasan wani abu daya faru ba,qarshe ma dai saita buge da fadin irin zaman da sukayi,shuru ne ya biyo baya,anni tana ta jeranta abubuwan cikin ranta,ita gaba daya yarinyar bata yi mata ba,sannan data sake kawo mata qara ta kuma kalli tsantsar idanunta tace mata ayi masa fada bata taba kwanan turaka ba saita qarasa sare mata a rai,babu kunya ko qanqani cikin lamarinta,sannan ita kanta ta sanya cikin jikokinta sun mata bincike,sakamakon ba mai dadi bane, saidai dan yau baka bashi qofa haka kai tsaye. Shima abbi din kusan hakan take,amma bayaso lokaci guda ya bashi go ahead na aikata wani abu,saboda gudun halin dan yau,don haka yace dashi "Ka samu lokaci kaje ku fahimci juna ka dawo da ita dakinta" "Zan samu lokaci" yace da abbin kawai,yanayin fuskarsu kawai ya nuna suma akwai abinda suke dannewa. 79 Weekend na musamman suka sakeyi kamar yadda ya shirya musu,don wannan karon daga makaranta kai tsaye airport suka zarce,already ya siya musu ticket zuwa kano,akwai aikin duba ginin company dinsa da yakeyi,cikin 'yan awanni ya gama dubawar suka sauka a Bristol palace,a nan suka more amarcinsu sosai,kwanaki biyun da sukayi ta sakar masa zuciyarta harma da gangar jikinta,wani sabo da shaquwa ne sosai suka shiga tsakaninsu. Ta dauka Sunday ko Monday da sassafe zasu wuce,amma sai taji baice komai ba,itama kunya da nauyinsu take ji shi yasa bata tanka masa ba,ta fuskanci makarantar takai masa ko ina,kawai lallabawa yake yana ma anni kawaici. Da wani yammaci tana zaune a balcony din dake gaban dakinsu,saman wani table dan qarami mai kujeru guda biyu,gabanta littatafanta data taho dasu saboda assignment da aka basu wanda yake a mazaunin test. Sosai hankalinta yayi gaba tanata rubutu,yana tsaye a bayanta bata sani ba,hannuwansa cikin aljihun trouser dinsa,yana sanye da slim fit shirt mai gajeran hannu,wadda ta zaune ta lafe a jikinsa,ta kuma fidda qirarsa na cikakken namiji. Murmushi yadan saka sanda ta daga hannunta tadan yarfeshi kadan,alamun ta gaji da rubutun,ji yake kamar ya dauketa.ya hadiyeta,wani irin zazzafan so ne nata yake shigarsa zuwa kowanne sashe na jikinsa,sai ya fara takawa sannu sannu har zuwa bayanta,ya tsaya sannan ya miqa hannunsa ta gefan kafadarta ya ranqwafa faffadan qirjinsa yana gogar bayanta,ya sanya tafin hannunsa ya rufe rabin littafin. Duk sanda ya kalleta ya tuna alkhairin dake shirin fuskantar rayuwarta sai yaji wani madaukakin farinciki yana ratsashi,yaya zata dauki lamarin?,zuciyarya zata samu wannan juriyar kuwa?,wannan shine tambayar da yakema kansa. Cak ta tsaya da rubutun,murmushi na tashi akan fuskarta,sai ga cira kai a hankali ta waiwaya tana dubansa,take idanuwansu suka sarqe waje daya, fuskokinsu gab da juna,numfashinsu ya fara gauraya waje guda,kusan lokaci daya kuma a tare kowannensu yadan lumshe idanunsa kana ya bude, ja'afar din baice komai ba,sai ya sanya daya hannun nasa ya zare biron dake tsakanin yatsunta ya aje,sannan ya saka hannuwansa biyu ya dagata cak ya ture kujerar ya kuma dorata saman table din,sannan ya sake jawo kujerar gabanta,ya zauna a kai,ya kuma matso da ita dab da ita kamar zai shige cikinta,ya kwashi qafafunta ya dorasu saman qafarta. Da kallo yabi qafafun nata,farare sol babu digon komai a kai,sai na baqin lalle sidik sake saman faratan yatsun nata,wanda hakan ya zama musu wani ado na musamman. Hannu yasa ya fara mata tafiyar tsutsa a qafar tata,sai ta qyalqyala dariya tare da qoqarin janye qafartata tana jin wani iri "Ka bari......don Allah" "Don Allah wa?" Ya tambayeta yana kallon fuskarta,wani irin murmushi mai cike da shauqi kwance saman fuskarsa "Nidai don Allah" "Nace don Allah wa ?,yau sai kin fada,idan ba haka ba?,....... tom" sai yaci gaba dayi,wannan karon har saman qafarta zuwa qaurinta "Don Allah my baby,my hot baby........my life line.....my hubby.....my other half.....my moonlight" dukka ta hada ta fada tana dariya tare da son ya cikata,cak ya tsaya yana lumshe idanu "Wow......wow..... great!" Ya fada yana sakin murmushi sannan ya dubi idanunta da wani irin taushi "Fantastic I really enjoy these names moon angel.......,you have the best gift ever let me give it to you" bata qara wani tunani ba ya miqe tsaye ya sunkuceta,ta cikin balcony din ya buda qofar Glass din suka zarce bedroom dinsu. Wani irin hot romance ya dinga aje mata da wasu kisses masu zafi,wani saqo me nauyi da tsayawa a rai ya dinge ajema kowacce gaba ta jikinta,sun jima a haka kafin su nutsa duniyar ma'aurata,wadda suka jima da tsarata hadi da killaceta da wasu irin abubuwa masu sanya abokin rayuwarka ya tsaye maka a rai. Tana saman mirror yana busar mata da kai da band drayer,daure take da towel wanda ya dan zame kadan yana nuna fararen qirjinta da kuma tudunsu ta sama,abinda yake yawan tafi da hankalinsa kenan,shima din towel din ne daure a qugunsa,yana busar mata da kan idanuwanta na saman gargasar qirjinsa da ko yaushe taje burgeta,tana daya daga cikin abubuwan dake sanya mata nishadi,tana da laushi sosai,hakanan wani qamshi take bayarwa na musamman "Yaushe zamu koma,akwai assignment da yawa a hannuna a satin nan" ta fada a hankali da muryarta mai taushi,duk da can qasan ranta tana jinne kamar zai maidata kurkuku. Ajiyar zuciya ya sauke,sai ya juyar da ita tana fuskantar madubi sosai,idanunsu cikin na juna,ya motsa labbansa a hankali "Angel.....na tsani makarantar nan totally yanzu...... you are my perfect place to go when my mind searches for peace,ta yaya zanso rabuwarmu kota second daya?,.....you are my world angel,if i could have one wish.....i would wish to wakeup every day to the thousand of your breath on my neck,the warmth of your lips on my cheek,the touch of your fingers on my skin and the feel of your heart beating with mine,ba abinda yafi min wannan dadi a rayuwata" ya qarashe fada yana nutsa yatsunsa cikin gashinta don ya tabbatar ko.ina ya bushe, idanuwansa kuma cikin nata,sai taja numfashi sosai,ta kuma lumshe idanunta,hannayenta ta bude gaba daya,ya saki tattausan murmushi shima ya bata dama tayi huggin dinsa sosai,a hankali tace "Ka sakani jin cewa ni wata mutum ce ta daban,ka saka duniyata cikin nutsuwa ka sani inajin cewa am protected tako ina kuma am loved,i don't ever want to live my life without you by my side" "Don't kill me please babe" ya fada yana dariya "Abun zaimin yawa,ga huggin da wadan nan kalaman masu zaqi?" Sai ya bata kunya ta cukuikuyeshi da kyau, shi kuma yana dariya abinsa,kafin a hankali ya rage sautin murmushin da yake yi din "Oya,sauko ki shirya,don idan naci gaba da ganinki a haka komai yana iya faruwa,ni kuma so nake kiyi alwala.kiyi salla raka'a biyu,ki godema Allah,akwai muhimmin al'amarin da yake shirin tunkaroki" daga kanta tayi a hankali gabanta yana faduwa tana dubansa "Menene?" Murmushi ya sakar mata saboda ya hangi tsoro da karaya a tattare da ita,sai yasa yatsansa ya lakace mata hanci "Matsoraciya,khairan in sha Allah" shuru ta sakeyi,sai ya riqeta sosai "Baki yarda dani ba?" "I trust you" "Oya.....do what I said to you" saita jinjina kanta,ya riqe mata hannu ta zamo a hankali qasan mudubin. Duk yadda taso ta manta da abinda yace matan ta kasa,tayi sallar harma sun wuce raka'o'in da yace mata,haka kawai takejin kasala da mutuwar jiki,gefe guda kuma kamar zazzabi zai kamata. Wayarta dake gefanta ce ta fara haske ba tare da fitar sauti ba,duk sanda suke a tare ita dashi irin hakan wayoyinsu dukka a silent yake sanya musu idanma anci sa'a bai karba ya kashe ba,yakance basa buqatar kowa basa kuma buqatar komai,daga shi sai ita,duniyarsu ce wannan so basason kutsen kowanne abu. Dubawa tayi sai taga afra,ta shafa addu'ar da takeyi ta janyo wayar tana amsawa,bayan sun gaisa tace mata "Kin ganni a hanyar gida daga makaranta,zanje na duba jikin daddy,jiya muslim (qaninta) yacemin basuyi barci ba,jikinsa ya motsa,wai amma hajja ke boyemin don kada nazo,ta yaya zan iya zama maimoon?,ko tsanani jikin yayi basu gayan ba oho" cikin sigar lallashi da kwantar da murya tace "Kai haba,bana jin haka,ki kwantar da hankalinki ba komai.in sha Allah" ta bata qwarin gwiwa sosai kuma afran ta samu qwarin gwiwar,sannan sukayi sallama tana cewa "Ki gaida hajjan da daddyn duka,Allah ya qara afuwa" jikinta a sanyaye ta ajjiye wayar bayan sunyi sallamar,aai tadan fada tunani kadan,kafin J ya shigo ya kore kowanne tunani da fargabar da taketa tsintar kanta a ciki. Bayan sunyi sallar isha'i motar hotel din ta daukesu zuwa shoprite,yace tayi siya duk abinda take so,kusan su amna amma dasu anni da kuma su laila ta yiwa tsaraba,sai ya tsaya yana kallonta kafin yadan ranqwasheta a tausashe "Kin manta dani?,su anni kawai kika sani?" Ya fada yana narke fuska kamar qaramin yaro,sai abun ya bata dariya har haqoranta suna bayyana "Ta yaya zan manta dakai?" Ta fada tana janyo daya cart din dake gefanta. Luxuries undies ne masu kyau da tsada na maza a ciki,handkerchief perfumes da pyjamas masu shegen kyau,sosai yaji ta burgeshi qwarai, sai ya danyi hugging dinta ta kafadarsa "Thank you,thank you my angel moon"sai kuma yace "Amma banga taki siyayyar ba da kuma ta baby na" "Ka wadatani da komai,bana buqatar komai.....baby kuma wanne bayan amneee na?" Fuskarta ya daga da yatsunsa yana kallonta,kamar mai rada ya rage murya can qasa "Baby unborn" ya fadi yana shafar cikinta da hannunsa,turesa tayi tana turo baki hadi da sakin murmushin jin kunya,dariya ya saki yana sake jawota jikinsa "Am serious,bana aikin banza,jikina yana bani very soon amneee zata samu brothers and sisters" ido ta fiddo "Bama brother ko sister ba?,harda qari?" Kai ya jinjina "Yeah,i trust my self cikin ikon Allah bana bada iri guda daya,ga example akan amna.....niba rago bane,sannan Allah na na sona,yasan inason yara da yawa" dukansa ta soma yi cikin wasa tana sake tureshi "Nidai ka daina fada please" "Zaki sani ne,na riga na bada ajiya kuma an karba,so sai randa zan karba kayata in sha Allah kawai nake jira" ta fuskanci yau din yan tsokanar suna kusa,dibanta kawai zaiyita yi,dole ya haqura ta barshi kawai,saidai kuma maganarsa tayi ta sakata murmushi ita kadai "Ni ba rago bane.....yes,ta shaida haka" ta fadi a ranta,sai kuma taji kunyar kanta da kanta,ta saki murmushi kawai. 80 Tun cikin airport din malam aminu kano dake kano tana maqale dashi kamar yadda ya saba,ba ruwansa da idanuwan kowa,ta fuskanci shi din kaifi daya ne,bashi da kwane kwane ko nuqu nuqu,baya kuma iya boye abinda yake cikin zuciyarsa. Duk yadda yayi qoqarin janta da wasa da hira don ta sake sosai amma kuma ta kasa,batasan me yasa ba gaba daya jikinta a matuqar sanyaye yake,sai faduwar gaba da takeji lokaci lokaci,a haka har jirginsu ya daga zuwa gombe. Mota daya rak ce tazo daukansu,sanda suna cikin motar ma hannunsa na cikin nata,kanta na saman kafadarsa,idanunta na biye da titi,bata ankara cewa ba hanyar gida sukayi ba sai daga bisani,batace komai ba,duk da cikin zuciyarta zata so ace gida suka nufa ta kwanta ta huta,don wata irin gajiya takeji,kamar wadda sukayi tafiyar mota. Tafiyar minti kusan arba'in sukayi,lokaci lokaci tana jinsa yana amsa waya,saidai batasan me yake fada ba,har suka isa wata unguwa,motar tasu ta gangara jikin wani dan symbol dake dauke da sunan street din. Kofar wani gida suka tsaya,ta daga kanta a hankali tana duban gidan,babban gida ne da ya amsa sunansa,yana dauke da katafaren gini manyan katangu da kuma tsayayyen bene na alfarma,sauke idanunta tayi dai dai sanda security ya leqo,ba tare da yace musu komai ba kaman yasan da zuwansu ya dage musu gate suka wuce zuwa ciki kai tsaye,ya qarasa parking lot dake gefe daya na gidan can nesa kadan da gate,ya tsaida motar. Dagata kadan ja'afar yayi yana kallonta,ya sakar mata murmushi, muryarsa a hankali yace "What's happening, ?" Ya tambayeta a tausashe,kawai sai ta fara tara hawaye amma kuma sai ta girgiza masa kai "Nothing,ba komai"hannuwansa ya sanya ya kama fuskarta,ya sanya idanuwansu sosai cikin nata yana bata wani qwarin gwiwa wansa ta jishi cikin jikinta sosai,hawayen data tara suka fara shanyewa suna komawa ciki,sai da yaga ta nutsu sannan ya bita da wani murmushi mau narkar mata da zuciya "good, everything will be fine" ya furta yana manna mata wanu kiss mai taushi a goshinta,sannan ya buda motar ya fita,ya zagaya ya bude mata,a hankali ta sauko,sai sannan ta sake kallan gidan da kyau,lallai babban gida ne "Ki shiga ciki,yanzu zan shigo sai mu wuce gida,zaku gaisa dasu ne" kai ta gyada masa a sanyaye,tana mamakin wanne irin muhimmanci ne da mutanen har haka, wanda kai tsaye daga airport sai wajensu?,bazai bari suje gida su huta ba?. Binta yayi da kallo sanda take takawa,cikin tafiyar nan tata kamar tana rangaji,qafafunta akan tsari,cat walking din nata tana burgeshi sosai,idanunsa basu taba ganin tafiya irin tata ba,a hankali har zuwa sanda yaga ta isa babbar qofar falon,ta bude ta shige,sai ya sauke ajiyar zuciya me nauyi yana furta "Alhamdulillah" cikin sanyi yana kuma lumshe idanunsa,tare da jiran abinda zai biyo baya. Cikin muryarta dake cike da sanyi tayi sallama a babban katafaren falon,dukkan mutanen dake falon suka daga kansu,banda wani babban mutum ma'abocin furfura tsalli tsalli a saman kansa dake zaune saman kujera hannunsa riqe da waya,da alama akwai wani abu me muhimmanci da yake kallo. Da idanu ta bisu da kallo kamar wadda aka kafe daga bakin qofa,umma sa'ada ce sai anni da baaba tabawa,gefe daya dr marwan ne wato abbi a zaune,sai kuma wata dattijuwa dake zaune itama dab da babban mutumin. A hankali ta maida dubanta ga mutum na qarshe wanda idanuwanta suka sauka a kansa,wata mummunar faduwar gaba ce ta ziyarceta,lokaci daya taju gaba daya kwanyarta da tunaninta sun birkice,ta fidda idanunta da kyau taba qare masa kallo kamar idanuwanta zasu fado,bakinta da jikinta dukka suka fara rawa,komai dadewar zamani,komai shudewar lokaci idanuwanta da zuciyarta ba zasu taba mantawa dashi ba "Abbuuu" ta kirayeshi da sunan da duk duniya ita daya ke kiransa dashi. Tamkar wanda aka fusgeshi ya daga kansa da sauri,take kowanne sashe na kwanyarsa ya fara motsawa yana qoqarin dawowa saiti tare da son komawa bakin aikinta bisa tsari da doka. Miqewa tsaye yayi bakinsa yanata motsawa,da alama akwai abinda yakeson furtawa amma kuma ya kasa cewa komai din "Diyammm" cikin wata irin fusga ya fadi sunan,abinda ya sanya maimunatu rushewa da kuka tana sake kiran sunansa,sannan ta diba da mugun gudu tayi inda yake tsayen,saidai kafin ta qarasa ya dafe kansa da yaji kamar an balla masa qashin kansa,ya tafi luuu zai fadi,abbi da yafi kusa dashi yayi hanzarin tarbarsa,saidai tuni ya sume "Abbuuuuu" ta sake fada da qarfi ganin ya fadi,wani irin tsoro da fargabar suna shigarta,kawai sai taji itama jiri ya kwasheta,kunnuwanta kuma suka toshe idanunta suka fara ganin gilmawar duhu,take qafafunta suka gaza daukarta,ta tafi luuu zata fadi,umma sa'ada data fisu quruciya ita ta cimmata ta tareta tana kiran sunanta da qarfin gaske,kiran da yaja hankalin ja'afar dake tsaye,ya bude idanunsa a hankali,kunnuwansa na sake isar masa da saqon kiran kunan maimunatu da akeyi,bai jira komai ba cikin wani irin hanzari da zafin nama ya nufi cikin gidan kai tsaye. A hannun umma sa'ade ya sameta tana jijjigata gami da kiran sunanta,yana zuwa ya karbeta idanuwansa akan fuskarta da jikinta daya saki gaba daya,da alama ma batasan me ake ba "Angel!" Shima.ya fada hankalinsa na neman gushewa daga jikinsa,ba abinda zuciyarsa ke hasaso masa sai rasata zaiyi,abbi ya kula yana neman ficewa a hayyacinsa ne,don ba abinda yake sai girgizata da kiran sunanta,da alama komai ya kwance masa "Ja'afar!" Abbi ya kira shi da qarfi sosai,kiran daya dawo dashi hayyacinsa "Ka dauketa ka sakata a mota,idan ka fita kace auwalu yazo yanzu yanzu mu miqasu asibiti gaba daya" cak ya dauketa kamar 'yar tsana,yana tafiya yana kallon fuskarta,kamar idan ya daina kallonta da second daya zata mutu ne. Cikin qasa da minti ashirin suka isa asibiti guda daya gaba dayansu,suna isa din aka karbesu aka shiga basu taimakon gaggawa gaba dayansu,abbu dai sai da aka kira likitansa da yake dubashi tsahon shekarun ya shiga dakin da aka bashi,yana da kyakkyawan hope din lafiyarsa ta dawo,tsahon shekarun dama abinda suketa lalube kenan,abinda zai tuna masa da wani.lamari daya shude a baya. *_BAYAN AWA DAYA_* Shuru dakin yake,babu motsin kowa duk kuwa da cewa kusan su biyar ne cikin dakin,daga saman gadon maimunatu ce kwance a miqe saman gadon,hannunta maqale da qarin ruwa,ja'afar na tsaye gaban gadon ya sanya tafin hannun da ake qara mata ruwan cikin nashi,kamar zaya koma cikinta ko kuma ya maido ciwon jikinsa,sam.ya kasa zama,baya jin nauyin kowa a lokacin,burinsa kawai shine maimunatunsa ta farka da cikakkiyar lafiya a jikinta. Anni ammi(shiyar maman ja'afar din)baba tabawa da umma sa'ade duka suna tsaye,kowanne zuciyarsa cike da tunani iri daban daban. Dai dai lokacin da liktar data gama dubata dazun ta turo qofar ta shigo. Dr noor,family friend din ja'afar ce,hakanan tare sukayi primary to secondary school,yanzun haka tana da aure harda yara uku,a nutse suka gaisa dasu anni a yanzun,ba kamar dazun dako damar gaisuwar ba'a samu ba,sannan kuma kai tsaye ta wuce kan maimunatu ta dudduba file da drip din dake sauka a jikinta,tayi dan rubuce rubuce sannan ta dubi ja'afar "Ba wani damuwa captain,komai ya dai daita,ta koma normal,tana tashi a barcin nan zakuga kamar bata yi ba,saidai idan kunga da wani matsala sai a sakemin magana,ina office dina daga nan har zuwa 10pm" "Okay,thank you" murmushi tayi "Babu komai captain,ba wucewa zatayi ta barka bafa" kadan ya motsa bakinsa alamun murmushi,sai ta juya wajensu anni,kafin ta sake magana hajja ta shigo,jajirtacciyar tsohuwa mai yawan tawakkali da daukan qaddara da jarrabawar rayuwa,dukka al'amuran nan sun bugeta sosai,to amma tayi qoqarin jurewa,duk da fuskarta ta nuna zallar tashin hankali,tun dazun ita da abbi da alhaj bello qani ga abbu suna can bakin qofar dakin da likitoci ke kansa,duk suka maida hankalinsu a kanta sanda tayi sallama tana nufar gadon da maimunatu ke kwance,idanuwanta a kanta,tana jin wata qaunar jikartata da ta kwashe tsahon shekaru tana addu'a a kanta,tana fatan Allah ya bayyanata,ubangiji ya zama gantanta,jikanyar tata data jima dauke da qauna da soyayyarta a cikin ruhinta,saidai batasan a inda zata cimmata ba,bare ta nuna mata gata soyayyar da kuma kulawa,har sai yau da buwayin sarki ya yanke komai. "Hajiya,ya jikin alhajin" "Alhamdulillahi anni,sun gama iyakacin qoqarinsu,sun kuma bada tabbacin da yardar Allah komai nasa ya koma saiti yadda yake,da zarar ya farfado zai iya tuna komai da komai" "To alhamdulillah, Alhamdulillah" suka kusa hada bakin wajen furtawa dukka su ukun. Dr noor ta jinjina kai itama "Irin hakan dama yana faruwa,amma idan taimakon Allah yazo,da zarar kaga wani abu daga cikin abubuwan da suka faru a rayuwarka ta baya komai yana dawo maka,musamman wani abu da kake matuqar so ko ka damu dashi,ko kuma yake da muhimmanci" "Haka yake,haka kam suka ce" hajja ta fada tana dora hannunta saman kan maimunatu tana shafa sumarta,fatanta itama ta tashi cikin qoshin lafiya su gana da mahaifinta. Ja'afar bai iya matsawa a wajen ba sai data farfado,kuka ta saki sosai,duk sai suka fita suka barshi shi da ita a dakin,abinda ya bata damar kwantar da kanta a qirjinsa tana sakin kuka da gasken gaske,ganinsa ba wanda ya tuna mata dashi sai daadarta,yau ga abbun da daadarta har ta mutu tana kewarsa,yau ga abbu amma babu daada a raye a duniya "Dama abbuu na yana nan?,dama yana raye?" Ta fada cikin sautin kuka "Ya akayi kasan inda abbu na yake?,dama ka sanshi?" Murmushi kawai ya saki hannunsa bisa kanta yana shafawa ta sigar lallashi,bazai hanata kuka ba,saboda wani lokaci kukan rahama ne,sannan yana tuna sanda shaheeda ta rasu,daya kasa kuka qarshe shi ya zame masa ciwon damuwa,wanda da qyar da taimakon Allah da kuma shigowarta rayuwarsa al'amuransa suka dai daita "Banason kukan nan Angel,badon kiyi kuka ba na tsaya na nemo abbunki,don kiyi farinciki ne,ki kuma rayu cikin farinciki,kukanki ko......bakisan yadda yakemin ciwo a zuciyata ba" sassauta sautin kukan tayi,duk da bata bar zubar hawayen ba. Shi ya da kansa ya kuskure mata baki yayi mata alwala,sannan ya hada mata tea tasha sannan ya zauna gefanta yana kallonta "Zanje gida yanzu na dawo,but da sauri sauri,me dame zan dauko miki?,baxan bari su sallameki ba saikin warke sosai" kai ta langabe a shagwabe tana jin tea din daya bata yana damunta a qirji "Abbu na" "Don't worry,barci yake,ance kuma kada a tasheshi,yana farkawa zan kaiki wajensa in sha Allah" kai ta gyada masa, sukayi sallama yana kissing goshinta,sannan ya fita. 81 Tare da anni da baba tabawa suka tafi,akabar ammi a nan,saboda baba tabawan zataje tayo girki sai ta dawo sannan ammi ta tafi,shima abbi acan suka barshi. Suna hanya suna tattauna yadda abubuwan suka kasance,anni ta saki ajiyar zuciya "Kaidai manya Allah ubangiji yayi maka albarka,ka gama min komai,abinda yake kullum cikin nuri da mafarkina yau gashi ga cikamin shi,na sake tabbatarwa na kuma samu nutsuwa kan zamantakewarka da maimunatu,Allah yayi maka albarka" murmushi kawai ya saki baice komai ba,yau anni ke magana dashi a haka,tabbas ba qaramin dadi abubuwan sukayi mata ba. A reception ammi ta zauna ta bawa hajja da maimunatu waje,hajjan na zaune gaban maimunatu,hannunta cikin na maimunatun tana kallonta,tana jin kamar ta maidata cikinta,kota ina ka kalleta zaka san jininta ce ita,ta dauko wasu abubuwa nasu sosai,duk da kamanninta sunfi.rinjaye dana mahaifiyarta,wadda hajja bata taba gani ba sai a hoto. Itama maimunatun kallon fuskar dattijuwar take,tana jin wani farinciki mara misaltuwa yana saukar mata,wai yau itace take da kaaka?,yau itace zaune gata ga mahaifiyar mahaifinta?,abun sai take jinsa kamar a mafarki,amma kuma tana mata yanayi da wata fuska data sani "Sannu diyam,sannunki,ina mahaifiyarki?,ina fata batayi fushi da abubakar ba?,bata masa kuma mummunan fahimta ba?, jarrabawa ce ta samu abubukar,qaddarar rayuwa da kowanne bawa baya iya tsallake mata" hajjan ta fada tana share qwalla "Daadata ta rasu" maimunatu ta fada muryarta a karye tana rawa,cikin kaduwa hajja ta kalleta "Aishatu ta rasu?,wayyo abubukar,bansan yadda zaka dauki wannan qaddarar ba,ina dan uwa ko 'yar uwarki da mahaifinku ya tafi ya bari da cikinsa?" "Ta rasu wajen haihuwarsa" ta fada tana rushewa da kuka,sai hajja ta jata zuwa cikin jikinta tana tayata kukan,sosai maimunatu ta dinga jin wata nutsuwa da sukuni sanda take jikin hajjan,sai taji kamar wani sashe na mahaifiyarta ne ya dawo. Sautin kuka suka fara ji daga bakin qofar dakin sannan kuma aka turo qofar,afra ce sanye da hijab har qasa,amma idanuwanta shabe shabe da hawaye. Tashi maimunatu tayi daga jikin hajjan tana duban afra cikin mamakin yadda akayi tasan bata da lafiya tazo gurinta,yayin da afrah ke kallon hajja da maimunatun gaba daya,tana shiga zurfin tunani,sai hajja ta sauqaqe mata ta hanyar daga mata hannu "Zo nan,qaraso ciki fannah(asalin sunan afrah,sunan mahaifiyar hajja), shigo kiga 'yaruwarki da mahaifinku ya baro a gembu" idanu afrah ta waro gaba daya tana duban hajjan ta gani wai ko tsakanarta take?,waiko tasan maimunatu ido da ido,ta kuma san irin aminci da shaquwar dake tsakaninsu shine takeson tsokanarta?,to amma kuma ko daya bata ga alamun wasa a tattare da ita ba,take zuciyarta ta gaya mata babu ko shakka dai daine abinda hajja ta gaya mata,yayin da maimunatu ita kuma ta zubawa hajja ido cike da mamaki da son fahimtar zancanta,afreen dinta 'yar uwarta ce ta jini?,kafin ta lalubo amsa afran ta sheqo a guje,tana isowa kuma ta rungume maimunatu a jikinta "Da gaske kike hajja don Allah, maimoon dita ashe 'yar uwata ce?" Kacamewa sukayi da kuka gaba dayansu,har sautin kukan nasu yaja hankalin alhaji mansur qani ga abubakar din. Shi ya tsaya kansu yana musu fadan kukan kafin kowacce ta sassauta kukan,ya fice yana gaya musu kada ya sakeji. "Nifa ji nake kamar mafarki,dama abbana abbanki ne?" Murmushi maimunatu tayi,ita daya daga ita sai ubangijinta ne kadai a yau suka san irin farincikin da take ciki,ta qagu abbanta ya farka akwai.maganganu masu yawa tasan da zasuyi "Abbanki shine abbuu na da ya bata tun ina qarama,saidai bazan taba iya manta fuskarsa ba" hajja ce ta bata labarin yadda komai ya wakana,anan maimunatu taji cewar ja'afar ne yabi diddigi tsahon wata kusan biyu yana neman dangin mahaifin nata,ya baza cigiya daga gembu ya dinga bibiya har ya fahimci yana da nasaba da gombe,don haka binciken yazo masa da sauqi,har Allah yasa ya gano sunansa da komai nasa harda address,sanda yazo ma hajja da zancan batayi musu ba,don dama sunata neman suma su samu wanda yasan wani abu da zai zame musu haske zuwa ga gembu don binciko shatu da diyoyinta,da ja'afar ya samu goyon baya,don su tabbatar da zarginsu sai ya kawo maimunatu gidan wajen abbun,cikin hikimar Allah kuma hasashensa ya zama gaskiya,tunda gashi har abbun ya kirayi sunanta,sunan da hajja ke jinsa a bakin abbun kafin ya gamu da hatsarin motar da yasa yayi loosing memory dinsa,ya manta dukka wani abu daya faru a baya cikin rayuwarsa "Afra ita kadai ce diyar abubukar har kwanan gobe,sai kuma dan uwanta musaddiq,kece cikon ta ukun" hajjan ta fada farinciki na sake kamata na bayyanar jikarta. Su biyu suka zauna cikin dakin sunata hirarraki da suka shafi rayuwar,hajja na gaya mata tarin dangin da take dasu cikin gombe da maiduguri asalin mahaifar hajjan,da kuma 'ya'yan qanne na mahaifin nata da rayuwarsa ta baya,abu guda ta gaza tambayar ta,yadda akayi abbun nata ya auri daadarta ba tare da kowa yasan garin ba har ya samu wannan matsalar data zama silar rabuwarsu dashi tsahon shekaru. "alhamdulillah" abbu alhaji ateeq abubakar ya fada yana shafa addu'a,bayan ya idar da sallolin da suka kubce masa,jin kansa yake a yau sakayau,kamar yayi dogon bacci ya farka ne,kamar dukka abinda ya faru a sanda bai cikin hayyacinsa sun faru ne cikin mafarki "Kaini wajen diyam"ya fadawa musaddiq dake zaune daura da mahaifin nasa,sai musaddiq din ya miqe "Zauna abinka bari muje" alhj mansur ya fada yana miqewa tsaye "Abba nima inason zuwa na ganta don Allah" musaddiq ya fada cikin kalar tausayi "Bismillah muje" ya fada kana ya waiwaya ga abbuu "Zan iya takawa da kaina,bana jin komai a jikina" alhj ateeq ya fada yana miqewa da karsashinsa. Da sallama ya shigo dakin,hajja ta miqe cikin farinciki "Ma sha Allah,Allah mun gode maka,Allah mun gode maka" ta fada tana qwallar farinciki,gaban gadon maimunatu ya nufa kai tsaye ya zauna yana dubanta,cikin qauna kunya da jin nauyi ta gaidashi bayan ta gaida yan uwansa da suke a matsayin kawunanta a yanxu "Diyam ina shatu?" Itace tambayar farko daya fara mata,kamar ba zatace komai ba,saidai cikin raunin murya tace "Allah yayi mata rasuwa ita da abinda yake cikinta" "Innalillahi wa inna ilaihi raji'un" ya fada sannan yayi qas da kansa,hajja da alhj mansur ke bashi baki,har zuwa sanda ya dago kansa "Ina fata bata mutu tana fushi dani ba tare da tunanin guduwa nayi?" Kai ta girgiza tana hawaye "Ko kadan abbuu,har ta mutu tana gayamin kai din mutumin kirki ne,ko guda bata taba ji a jikinta guduwa kayi ba,akwai gagrumin abinda ya faru dakai,ya kuma haneka dawowa zuwa garemu, kullum abinda take fada kenan" saita rushe da kuka,hakanan abbun shima ya kasa tsaida hawayensa "Allahu akhbar,qaddara ta riga fata" alhj mansur ya fada,afra ma kukan take,yayin da musaddiq yaketa kallon yar uwar tasa,tausayinta yana kamashi,hajja ta jima tana gaya musu suna da 'yar uwa,amma ba'asan inda take ba,yau gasu gata. Wani zama akayi na gayawa juna abubuwan da suka shude,har zuwa sanda akayi kiran sallar magariba su abbu suka fita sallah,ita kuma ta yunqura zata bandaki saboda yadda cikinta keta juya mata,batakai ga toilet din ba wani irin amai mai zafi ya yanke mata ta dinga sharara shi hajja na mata sannu,afra kuwa gaba daya ta rude,sai data gama suka kira cleaners suka gyara wajen ita kuma suka maidata gado tana maida numfashi,dr noor suka kira,sai data idar da sallah sannna tazo ta sake dubata,tace babu komai,idan ta sake zuwa anjima su gaya mata "Karki gayama j don Allah" maimunatu ta fadawa afra qasa qasa,saboda tasan idan ta gaya masan hankalinsa zai tasa. Kwana biyu rak sukayi a asibitin aka sallamesu gaba daya,duka suka dunguma suka wuce gidan alhaj abubukar,duk yadda ja'afar yaso ya dauke matarsa saboda yadda yayi kewarta amma anni tace dole yayi dagin qafa,dole dangi suna buqatar ganin diyar tasu,haka tana buqatar lokaci ita da mahaifin nata suga juna sosai,hakanan ba don yana so ba ya barta,amma kwana uku rak yace ya bata. To ita dinma kewarsa sosai ta dinga yi,batasan cewa soyayyarsa tayi mata mummunar illa ba sai a sannan,komai takeyi yana maqale a cikin ranta,duk da tarin dandaxon 'yan uwa da kuma dangi daketa cika gidan kulli yaumin wajen ganinta,kuka ta dinga yi sosai,inama ace daadarta tana raye taga wannan ranar,kullum burinta shine ta sada maimunatu da mahaifinta,yau gata ga danginta tako ina,harda wadanda suke diban kamanni duka ta gani. Kwananta biyu rak hajja ta hada gagarumar walima,dangi na kusa dana nesa kowa yazo,tace mata "Naso ace ba'ayi taron bikinki ba diyam,taron aure nakeson muku na gani na fada,ku biyu kacal Allah ya bani mata a cikin jikokina,dukka maza ne,bugu da qari abubukar na musamman ne,yasha wuya ya gamu da jarrabawa,gashi a yau Allah ya yanke masa komai,aurensa da mahaifiyarki qaddara ce mai qarfi,ya boyemin batun auren saboda yana ganin kamar bazan amince ba,don a sannan matarsa nada tsohon cikin afra,bayan kuma an haife cikin sai ya kasa gayamin din,saboda ni da matarsa baisan wai yadda zamu dauki batun ba,a haka shekaru suka fara turawa har zuwa sanda Allah yayi nufinsa ya gayan,nayi masa fada sosai naji kuma.babu dadi,sannan na gaya masa a sannan ne matarsa zatafi ji ciwon abun,za kuma tace ya munafunceta,har gwara farko farkon abun,na masa umarni da yaje yazomin da ku,ya tafi zai taho daku sai kuma aka kirashi hauwa'u matarsa mahaifiyar afra ba lafiya,sai ya yanke ya taho shi kadai idan ta samu sauqi ya dawo ya daukeku ayi mai gaba daya,ashe ba rabon abun zai ritsa daku,ya samu mummunan hadarin daya kawo masa wannan matsalar,yana cikin jinyar kuma itama hauwa'u ta rasu,duk da na shaida mata komai,tace kuma ta yafe masa,ta shaidi halinsa,ba haka yake ba,ta tabbata qaddararsu ce tazo a haka,sannan idan ta dawo Allah yayi zamanmu tare ta riqe mata afrah da musaddiq,to ashe itama Allah bai nufi ganawarmu ba" shuru maimunatu tayi tana share qwalla,tun faruwar abun kawo yau ba ranar da bazataji wani abu daya motsa ranta ba. A daren abbuu ma ya kirata,sun jima suna hira,bayan sun gama ne ya dauko wasu files da takardu a ciki ya miqa mata "Akwai haqqoqinki a wuyana masu tarin yawa da ban samu damar sauke miki su ba,hakanan akwai alqawura da na yiwa mahaifiyarki saboda kyautatawarta gareni da haqurin zama dani da tayi,wannan takardun wani estate dina ne dake new GRA road,na mallaka miki su halak malak,sauran 'yan uwanki dukkansu suna da kadara kwantankwacin taki" kamar a mafarki takejin abun,estate guda.abbun nata ya bata?,koda ta duqa zata masa godiya dagata yayi "Ban biya shatu da komai ba akan soyayyar data nuna min,fatana kawai Allah ya hadamu a aljanna,ya sake tabbatar dani da ita a matsayin miji da mata" Cikon kwana na uku ja'afar yazo da niyyar daukarta,amma saita mararaice masa,tana son binsa amma kuma tana buqatar lokaci sosai ita da abbunta,ga umma sa'adah ma tanata qorafin har yau basu zauna ba. Da farko yaqi,amma da hajja ta saka bakin kan ya qara mata ko kwana uku ne sai ya tafi ba tare da yace komai ba,saidai ita maimunatun ta cikin idanunsa ta karanci bawai ya haqura din bane. Cikin dare ta dinga jin zazzabi ta cikin qashinta,ta dinga juyi saman gadon,tana jin wata azababbiyar kewarsa,ta saba duk sanda take zazzabi irin haka cikin jikinsa yake boyeta,ba zata dauki dogon lokaci ba zazzabin yake rabuwa da ita,to amma yau din saboda babu shi a kusa da ita,sai takejinta kamar tsirara babu tufafi a jikinta. Tun goma na dare da suka gama hira da abbu da hajja harda afra da musaddiq take kwance amma sha biyu saura idanunta a soye suke,hakan ce ta faru ga ja'afar,ya shiga ya fita tsakanin bedroom dinsa zuwa parlor ya kusa sau uku,ana hudun sai yayi zaune saman kujerar falon nasa,ya miqe qafarsa saman glass center table dinsa,ya dauki wayarsa ya fara laluben number dinta. Cikin jikinsa yakejin idanuwanta biyu itama batayi barci ba,hasahensa ya tabbata kuwa,don ringing biyu tayi ta daga,nannauyar ajiyar zuciya ya sauke wadda ta ratsa har cikin kunnuwanta,saita damqe filon da take kwance akai da kyau saboda yadda tsigar jikinta ta zuba,shuru ya ratsa tsakani,dukkaninsu aka rasa wanda zai fara yin magana "Lafiyar ki qalau kuwa?" Narke fuska tayi kamar yana gabanta sai tace "Ummmmm" cikin shakku ya sake magana da wata murya mai taushi da dadin sauraro "Me kikeyi har yanzu bakiyi bacci ba?" Kamar jira take ya tambaya kawai sai taji kuka ya tsinke mata da 'yar sheshsheqa har ta cikin wayar "Ya salam" ya fada yana sauke qafafuwansa qasa gami zama sosai "Please my angel,please" ya furta a hankali yana rufe idanunsan "Zuciyata na qara yawan gudunta,stop it please,ki gayamin menene?" Maimakon tayi magana sai wani kukan ya kuma qaruwa,haka kawai batajin dadin dukka jikinta,kuma ranta tana jinsa aquntace. Shuru yayi tsahon minti guda yana sauraron kukanta,sai kuma a hankali yace "Ok,am on my way" ya kashe wayar,yana miqewa cikin kuzari yayi bedroom dinsa. Wayar ta zare daga kunnenta tana son tuna abinda yace "Am on my way fa?,yana nufin gidan zai taho a wannan tsohon daren?,ta sani indai ja'afar ne zai aikata,don haka saita shiga kiransa da sauri don ta dakatar dashi kada ya biyo hanya a wannan tsohon daren. 82 Yana gaban closet dinsa yana sauya kaya yaga shigowar kiran nata a jejjere,da kamar bazai dauka ba saboda saurin da yakeyi,amma sai ya daga ya sanyata a hands free yana saurarenta,da narkakkiyar muryarta cike da sautin kuka tace "Don Allah kada ka biyo hanya yanzu" "Why?"ya tambayeta kai tsaye yana fesa turare a jikinsa "Dare" "Bana tsoronsa,nafi tsoron nisantarki akan dukkan wani abun tsoro,so get ready,i will call you idan na iso,ki zauna kusa da wayarki" daga haka ya katse kiran,ya dauki key din qaramar motarsa cikin motocinsa ya sanyama kansa wata hula ya fito. Samun kanta tayi da zama daram tsakiyar gadon, idanunta nakan afrah dake bacci can nesa kadan da ita,da yake gadon yana da girma sosai,kamar wata me dakon jiran nasa haka ta dinga duba agogo,wasa.....gaske saiga kiransa bayan minti talatin,ta tsorata sosai da taji wai har ya iso,wanne irin gudu ya sharara haka?,saita miqe a hankali tana yaye window din dakin nata "Ki fito ko na shigo" taji ya fada a tausashe,tadan tsorata kadan amma sai ya zura hannu ta window din ya riqe mata hannu yana kallon qwayar idanunta ta cikin hasken daya gauraye harabar gidan gami da zare hular kansa,mamaki ya kusa kasheta,duk security din gidan amma ta ina ya iya shigowa da daren nan?,kallon da yayi mata kadai yasa taji duk duniya bata buqatar kowa sai shi,sai ta zame hannunta sannan ta juya a hankali ta bude dakin ta fice,bata ko sauya kayan baccin jikinta ba,duk da akwai baby hijab a jikinta. Tana riqe a hannunsa kamar zata bace har suka isa qofar gidan,sai a sannan ta lura da guard daya ne ya taso ya bude masa gidan,to ya akayi yasan da zuwansa?,wannan kuma bata sani ba,har ya bude mata motar ta shige ya shigo ya tayar suka bar layin tana kallonsa cikin mamaki "Yanzu inda wani abu ya cutarmin da kai fa?" Ta fada da wata irin murya data sanyashi waiwayo wa ya kalleta,wani irin kallo take jifarsa dashi mai tsuma zuciya data sanyashi dan dukan sitiyarin motar softly "Ba abinda zai cutar dani in sha Allah,bana jin komai inda zan kasance dake,ko meye zai biyo baya mai sauqi ne" sai ya miqa mata hannunsa ta sanya nata a ciki,ya hada ya matse gam "Don Allah karki sake yarda kije ko ina ki barni....kiyimin alqawari" a tausashe ta gyada masa kai "Nayi maka" cikin jikinsa ya dauketa tun daga harabar gidan zuwa cikin gidan,yana kallon fuskarta kamar ya riqo jaririya "Jikinki babu qwari moon,banjin kina da cikakkiyar lafiya" ta bude bakinta zata amsa mishi wani amai me zafi ya taso mata,saita zille daga jikinsa da sauri ta dire ta sheqa zuwa toilet dinsa,baiyi qasa a gwiwa ba yabi bayanta,saidai garin rufewa ta kulle bandakin gaba daya,haka yayi tsaye gaban toilet din yana kiran sunanta. Dukka abincin da taci sai daya dawo mata,sai data gama ta kuskure bakinta sannan ta fito tana takawa da qyar,riqeta yayi sosai ya samu waje nan qasan carfet ya zaunar da ita "Na fada baki da lafiya daman,me yake damunki angel,menene?" Kamar tambayarsa na zuwa da amai,sake yunqurin tashi tayi don kada ta bata kyakkyawar farar jallabiyyar jikinsa amma sai ya riqeta gam,bata sa sauran zabi illa kwararar dashi a nan,ta dinga sheqashi kuwa,sai data wankesu tas ita dashi. Sosai hankalinsa ya tashi,don a daren tayi amai ya kusa sau hudu,kafin gari ya qara haske ta galabaita sosai,qarfe shida na safiya ba tare daya damu da lokaci ba ya dannawa dr noor kira. A sannan tanata shiri da sauri sauri akwai emergency C.S da zatayi,already tasan waye ke kiran,don haka ta daga kiran,yayi mata bayani gami da neman tazo ta dubata "Karka damu,zan iso yanzu in sha Allah". Cikin mamakin yadda captain ja'afar ya koma gaba daya kalan tausayi take duba maimunatu,PT test tayi mata,saita daga kai da murmushi tana kallonsa,tunda ta shigo yake tsaye ya kasa zama,ya kafe maimunatu da ido kawai kamar zata bace,J mai tsauri da kaushi marason wasa amma gaba daya yayi laushi saboda ciwon matarsa,wacce irin soyayya ce wannan mai ban mamaki?,wadda sun fidda rai zai sake ma wata mace irinta "Congratulations captain,zaka sake zama uba again in sha Allah" idanu ya zubewa dr noor,gani yake kaman tana masa wasa ne ko kunnuwansa basuji da kyau ba "Really?" Kai ta jinjina masa tana tattare jakarta "Da gaske nake,abu daya ya rage ka kawota nayi mata scanning don na tabbatar da lafiyar komai,watanninsa da kuma expected date of delivery dinta" "Allahumma salli ala sayyadina muhammadin wasallim" ya fada da wani irin amo mai qarfi yana rufe idanunsan,sannan ya dora "Alhamdulillah alhamdulillah" har kamar bazai daina fada ba sannan ya dubi dr noor "Ki duba parking lot na gidan nan,duk motar data yi miki ki turo gobe a daukar miki ita,wannan shine tukuicinki". Sosai farinciki ya kama dr noor,dama qarshen satin nan take sanya ran sauya mota,sai kuma ga dama ta samu,godiya tayi masa sosai sannan ta juya ta fita. Zamewa yayi a hankali zuwa qasa yayi sujudush shukur,sannan ya rarrafa zuwa gaban gadon maimunatu dake kwance,wadda tuni bacci yayi awon gaba da ita,hannu yasa yana shafar gefan fuskarta a hankali,wasu qwalla suna tarar masa a ido,ashe ita din ba gurbin ido bace,ashe ido ce guda,sai yanzu idanun suka samu gareshi,ita alkhairi ne masu tarin yawa tattare da ita,rasa me zaiyi mata yayi,kawai sai ya fara kissing duk inda bakinsa yakai very softly yadda bazai tasheta ba yana fadin alhmdlh. Abinda bai sani ba tuni hawayen ya diga saman fuskartata,yana shirin miqewa ta bude idanuwan nata wadanda suka qara kyau da kuma haske,ta dubeshi cikin yanayi na masu barci,bakinta ya motsa kadan alamun magana zatayi,sai ta dawo gefanta ya zauna fuskarsa na fidda murmushi,ya taimaka mata ta zauna sosai ya jingina mata bayanta da filo "Congratulations angel moon" binsa tayi da kallo kawai ba tare dafa fuskanci komai ba,a tausashe ya rungumeta cikin jikinsa yana jin yadda take sake mamaye rayuwarsa da duniyarsa gaba daya,hannunsa ya dora a hankali yana shafar cikinta "Kina dauke da juna biyun ja'afar marwan khalid akko,zaki haifawa anni d'a,zaki haifawa amma jika,zaki kuma kuma haifawa amneee 'yan uwa" mamamki ya kamata ta kasa cewa komai,jin shuru saiya daga kansa yana duban qwayoyin idanunta dake nuna tsoro,tsoron nan dake burgeshi "Are you happy?" Qwalla ce ta subuce mata hade da murmushi,saita kifa kanta a kafadarsa tana jin kunyarsa,wai ciki?,ciki ita din?,yanzu kowa zai san abinda suke aikatawa ita dashi a boye kenan?,tunda ga ciki ya fito?. Sosai ya dinga tsokanarta,tare da.lasafta mata burikansa akan cikin,burikan nasa masu yawa ne,har ta gaji da tayashi lissafawa,sun jima a jikin juna suna wata irin hira dake haifar da sabuwar soyayya da kuma shaquwa ta musamman,idan tayi magana sai yace dumin babynsa yakeji,babyn da ko gama sanin lokacin shigarsa da kuma adadin zamansa ba'ayi ba. Sanda ya dauki waya yana niyyar kiran anni cewa tayi "Don Allah hubby......kada ka gaya musu" dubanta yayi yana murmushi "Why?" "Kunya nakeji Allah" "Kunyar me?" Cikin sakalcin dan fari da da wautar auta ta daga kai "Kowa sai yasan me mukayi na samu ciki kenan fa?,Allah bazan iya sake kallon kowa ba" dariya irin wadda takan jima bataga yayi irinta ba ya saki,ya zame wayar gefe ya riqeta da kyau,ita kuma ta tura baki gaba kamar zata saki kuka,don kukan kamar baya mata wuya "Ni baba tabawa zan kira a aiko,saboda banason ki sake komai,amma kuma kinsan halin anni,indai ta tsokaneni saina rama" kamar wasa sai ta sake masa kuka,yana tsokanarta ya dauka wasa ne sai yaga kukan take da gaske,sanyata yayi cikin jikinsa sosai,ya fara gaya mata wasu sanyayan kalamai,a hankali tayi shuru tana sauke ajiyar zuciya,zuciyarta tana yin sanyi,shima ajiyar zuciyar ya sauke, yaushe ta koyi rigima irin haka?. Bugu biyu anni ta dauki wayar,abu na farko data fara fada shine "Kai nake shirin kira yanzu,kai kaje ka sace musu yarinya cikin dare?" Sam sam ya mance daukota yayi ma daga gidan,ba wanda ya sani sai guard guda daya "Sata ce wannan anni?,matata na dauko na gaji da kawaici,ko tausayina na lura anni bakiyi gaba daya" "Kai ja'afaru ka fita idanuna......kayi ta kanka wallahi" "Zanyi ta kaina......amma kafin sannan,ki turo baaba tabawa please ta kula da ita,bata da lafiya" wani farinciki ya kama zuciyar anni, ja'afar dinsu daya daina amsa kowa ya daina hurda da maida amsar magana yau shine ake kai ruwa rana dashi akan matarsa,tun baice komai ba jikinta ya bata mawuyacine a wannan karon idan ba abinda taketa addu'a bane ya samu "Ahaf,wato daga daukota harka hadata da jinya ko?" "Ba jinyar kikeso tayi ba?,ko bansha jinki kina roqa mata ita ba?" Idanu ta fiddo "Kai ja'afaru,ni zaka yiwa sharri?....." Sai kuma tayi shuru data tuna randa tayi addu'ar,a take farincikinta ya ninka,ta kashe wayar da kanta tun bai kashe ba,ta kuma tashi da kanta ta shiga kitchen kiran baba tabawa,wadda tana ganin annin tasan kiran mai muhimmanci ne,don ba shiga kitchen din take ba. "Matar manya ce babu lafiya,zaki je ki zauna da ita......don Allah tabawa kiwa Allah kiwa ma'aiki ki kula da yarinyar nan da kyau,kada kice zaki yiwa manya kaara,basu da kunya ko kadan yaran wannan qarnin,ki kula da ita da kyau,kada wata matsalar ta afku a rasa cikin nan" guda baba tabawa ta saki,wadda ta jawo hankalinsu laila safina da salma dake falon annin suna hada wata game "Alhamdulillahi, alhamdulillahi,Allah mun gode maka,ai zama bai kamani ba,Allah dai ya raba lafiya" take tahau shirin tafiya anni tasa aka yiwa driver magana. Cikin lokaci qanqani labarin cikin ya karade gidan,wani irin murna da farinciki suka tsinci kawunansu,amma na falon abbi tana gyara masa laila ta sameta a can tana labarta mata,saita saki duster din da take goge kayan kallon falon,ta sulale ta zauna tana ambatar "Allah na gode maka,Allah na gode maka" sai kuma hawaye ya biyo baya,ta debe tsammanin samuwar ja'afar din a nan kusa,sai kuma gashi bayan daidaituwar al'amuransa harda tagomashi na samun qaruwa. Abbi dake daura links din hannunsa ne ya fito,yaji dukka abinda.laila tace,gaidashi laila tayi ta juya ta fice,shi kuma ya isa wajen amman,ya zauna a hannun kujerar da take zaune a kai,cikin kulawa ya fara mata magana "Ci gaba zamuyi da godewa Allah da yawaita sadaqa,ubangiji ya sake tabbatar da dukka alkhairinsa a tarayyarsu" yayi maganar shi kansa farinciki yana ratsa zuciyarsa,kai ta jinjina tana share hawayenta "Babu abinda zamuce da anni saidai Allah yasa ta gama da duniya lafiya,kaf rayuwarmu da alkhairi take binta,ko yaushe tunaninta yadda zata inganta rayuwar family dinta" kai ya jinjina yana jin dadin yadda ko yaushe tana gaba gaba wajen fadin alkhairin mahaifiyarsa gami da yi mata addu'a "Ameen ameen" ya amsata sannan ya miqe,cikin salon tsokana kuma yace "Ashe dai aishatu anason samun sabbin jikoki,wannan kuka haka?, ja'afar din dai shine na gaban goshin dai,ya kamata anni taji wannan labarin" kunya ce ta kamata sosai,saitayi qasa da kanta tana goge hawayen da batasan sun zubo ba "Ayi haquri yallabai,kada na kasa hada ido da anni" ta fada tana miqewa don yi masa rakiya. Tun ranar da baaba tabawa ta tafi gidan ta koma 'yar kallo,hakanan ta dinga kame kanta waje daya,saboda gaba daya ja'afar din ya kunce mata tunani,ashe haka yake?,ashe lumbu lumbu ne?,wata irin wutar soyayya ke tashi cikin gidan,saidai cikin salo da ban sha'awa da kuma qayatarwa,ya dauki kulawar maimunatu gaba daya ya aza a wuyansa,abinda baaba tabawa kawai keyi kula da gidan da kuma girki. Ta fannin maimunatu kuwa sai yanzu tasan meye ainihin ma'anar gata,gata mai sunan gata,tako ina lelenta akeyi,umma sa'adah nayi,su fareeda cousins dinta sunayi,anni nayi ammi da amma nayi,tsohuwa hajja nayi,umma sa'adah nayi,abbanta nayi,ga kuma afrah dinta data qeqashe taqi komawa makaranta,sai day abbuu ya maidata,wanda a yanzun itama ta koma ce masa abbuu,ya samu cikakkiyar lafiya ya kuma koma kan ayyukansa kamar daa,ya murmure fes dashi kamar babu wata jarrabawa data taba samunsa,a yanzun abu daya ya ragewa hajja shine ya qara aure,shi kuwa gani yake bazai samu mace kamar hauwa'u da shatunsa ba. Ko yaya maimunatu ta motsa sai a kawo mata caffa,tako.ina gata da kulawa take samu,hatta su laila kaman zaayi musu haihuwar jikan fari,kusan ranaku d'ai d'aikune basa zuwan mata a yini ana hira,haka afrah itama fashin kwana daya ko biyu take,ba abinda maimunatu keyi saidai taci abinda ranta keso tasha abinda ranta keso,duk da cikin yazo mata da laulayi sosai,amma tana samun sauqi saboda akwai masu debe mata kewa. Saidai fa duk yadda gidan yakai ga mutane,da zarar oga captain ja'afar ya dawo zai dauke abarsa ya wuce sassansa da ita,hidimarta kuma ta koma wuyansa,ita kanta maimunatu qorafi take masa ya dinga hutawa yaji da aikin office kawai amma yakance "Da da hali zan ajjiye komai ne,nayita rainon cikin nan har sai randa kika haihu zan sake fita na barki" idan kun sake ganin maimunatu yana cikin gidan saidai idan wata muhimmiyar fita ce ta kamashi. Tako ta ina babu abinda zata cewa rayuwa sai godiyar Allah,cikin dare daya Allah Almusawwiru ya canza mata rayuwarta gaba daya,bata da wani sauran qunci ko kuma damuwa kwata kwata,saidai lokaci lokaci takanyi tunanin inna furera,ko yaya take ciki?,me takeyi a halin yanzu,da gaske bata sonta don bata taba waiwayar inda take ba. Abinda bata sani ba shine,inna fureran ta hadu da ibtila'i,bata da lafiya ta fita wani private asibiti da aka bude jikin rugarsu,bayan ta gama fadi tashin neman adreshin maimunatu har gembu amma kowa ya hanata,daga bisani kuma ta samu adress din,saidai har garin gombe ta shigo amma ta bace,tayita yawon neman gidan bata samu ba,qarshe ta hadu da 'yan damfara suka karbe sauran 'yan kudadenta,sai bara tayi ta hado kudin motar dawowa gida.bayan taje asibitin an gama dubata likitan yace "Akwai wani aiki da mukeson bawa.mutane,aiki ne da yanzu yanzu zaki zama.shahararriyar attajira idan kinso" a yanzu ba abinda inna furera keso kamar wannan kalmar ta zata zama me kudi, kowacce hanyace tana jin zata iya binta,don haka tace "Ko meye likita zanyi,zanyi wlh" "Ba wani abu bane mai wahala,jini zamu diba leda biyu,zamu biyaki naira miliyan talatin" jin yawan kudin ya sanyata zamowa qasa,sai gata dabas zaune a qasa tana raba idanu,fillo yaji kudi sama ta ka ba tare daya siyar da kasanarsa ba😝😝😜 "Shin da gaske kake likkita?" "Hajiya ba wasa a maganar nan,jinin muna kaiwa ana taimakawa marasa qarfi a cikin gari,saboda ku fulani kun fisu lafiya da yawan jini saboda yanayin abincinku da nasu ba daya bane" "Aradu likkita ko yanzu ina iya kwanciya ka diba" ta fada jikinta na mazari,don har ta gama hango kudaden da abinda zatayi dasu idan sun samu,lallai magauta da maqiya ganin bayanta ba yanzu ba,ita din me sa'a ce,tayi musu shalll..... 83 Murmushin nasara likitan ya saki,yau da alama ranar sa'arsa ce "Babu damuwa hajiya,zamu baki daki ki kwanciyarki kita baccinki,basai kin koma gida ba bare ki gayawa kowa,ana gama diba zaasa miki kudinki a jaka a baki ki tafi dashi a sirrance saboda gudun barayi da 'yan sane,aidai kinsan miliyan talatin ba qananun kudi bane ko?" Kai ta jinjina "Qwarai kuwa likkita,ai sai na samo.masu tayin irga inajin" "Yauwa to" hankalinta kwance aka bata daki lafiyayye tayi kwanciyarta tana sheqa baccin,tasan gidanta babu kowa sai laulo,gaje kuwa batace ga inda taje ba,jauro kuwa tuni ya sawwaqe mata dama saki guda,saboda yadda tayi silar yawace yawacen gajee,gashi taqi saituwa,hidimar aurensa yake kawai yana fatan zuwan sabuwar amaryarsa ta daidata gidan da yaran,don yasanta tsayayya ce sosai akan tarbiyya. Daga wannan baccin dai inna furera sai tashi tayi ta tsinci kanta ajeji cikin matsanancin ciwo,da qyar cikin masu wucewa cikin dare suka ganota suka daukota zuwa cikin gari,ciwo yayi ciwo har 'yan uwanta daga gembu sukazo,qarshe aka.kaita babban asibiti. Sakamakon bincike ya nuna qodarta guda daya aka cire,dayar kuma ba cikakkiyar lafiya ne da ita ba,haka taci gaba da rayuwa cikin ciwo,idan ka kallo cikinta kamar zai fashe. Duka wannan labarin sai da yuuma tazo take gayawa umma sa'adah,yuman tace "Azabar cin dukiyar marainiyar nan kadai bazai barta ba,hala wutar data ciwa cikinta na dukiyar maraya Allah ya fara azabtar da ita tun gidan duniya" "Haka Allah yake lamarinsa,shi hakki ai yanzu tun a duniya Allah yake sakayyarsa basai anje kiyama ba" umma sa'ada tana fada,sosai maimunatu taji tausayinsu daga ita har gajee,amma data fara maganar ma umma sa'adah cewa tayi "Akul na sake jin maganar wadan nan mutanen daga bakinki,ki fuskanci rayuwarki,banda Allah ya qwaceki da tuni har yanzu kina hannunta,baasan ma a wanne hali zaki kasance ba". °°°°°°°°°°A hankali ta soma bude idanunta,tana jin yadda yake shafar gefan fuskarta a hankali cikin taushi,kafin ta gama.bude idanuwan nata murmushi ya mamaye fuskarta,ta san mutum daya ne ke da wannan aikin,wanda salon tashin da zai mata daga bacci ya banbanta dana kowa. Tarrr ta bude idanuwanta akan fuskar sa dake faman kallonta kamar zai cinyeta "Yaushe ka shigo?" Sai daya langabar dakai gefe sannan ya amsa "Kina can duniyar baccin,baby na ya daukemin ke,na zama abun tausayi,baccin nan ya fara yawa angel" ya fada yana sake shafar fuskarta data yi masa kyau sosai,a tausashe ta riqe hannunsa,a yanzun burinta shine ta samu lafiya ta shiga hidimta masa,tana tuna dramer dinsu da anni shekaran jiya da tayi maganar wai ya maidata makaranta,baima iya amsawa annin ba "Ke maimunatu namiji baida tabbas,idan kika zauna zakiga zaunau,ya maidaki makarnatar daya zaba miki ki qarasa karatunki,koba komai kin tsira da kwalinki" anni ta fada saidai can qasan ranta bata nufin abinda ta fada din "ki qyaleshi don Allah anni,na haqura da makarantar Allah" baki ta kama kamar gaske ta zabga salati "Iyeee,ja'afaru?,yaushe ka iskantamin 'ya?" "Yo ai gaskiya ce,banda abinki hajiya anni,ta yaya matar aure da ciki ruqu qui ruqu qui zata wani dinga tafiya boko?,ta zauna tayi bautar aure shine gaba" "To ai shikenan,duk qoqarin da nake kun watsan qasa a ido?,ya maisheki mara ta ido ko?" Anni ta fada tana tafa hannu,sai a sannan kunya ta kama maimunatu,ta miqe da sauri tana boye dariya tana ficewa a dakin "Bi a hankali!" Suka hada baki wajen fada kowa yana zabura saboda yadda ta kusan yin tuntube wajen fitar. Ashe ja'afar din na labe yana jiranta,tana qarasa fitowa kuwa ya dauketa cak yana dariya "Well done,yau kin biyani,gwara da anni yau tayi ta kanta" dariya maimunatu ta shiga qyalqyalawa "Wato yau itace tayi ta kanta din kenan?,to babu ruwana" "Da gaske nake data sake tada maganar zan fito mata kaina tsaye,ko kuma na daukeki mu bace cikin duniya,kinga babu me takuramu" rungumeshi tayi tana dariya "Ba inda zamu,zamu rayu cikin aminci da yardar Allah cikin ahalinmu". "Me kike tunani?"ya fada yana shafar gashinta, murmushi ta sake "Anni" "The great rigimammiyar kaka" dariya maimunatu ta sake "Maza ta jika" hannu ya bata yana murmushi "Taso muje,abbi ne yazo dubaki" ido ta fidda "Abbi kuma?,ta yaya zan iya kallonsa don Allah hubby" "Am here for you,ba komai,ai shima.uba ne" tanata doddojewa da jin kunyar abbin haka ya rakata ta kuskure bakinta ya zura mata hijab suka fito. Cikin kunya ta sulale gabansa tana gaidashi,mutum ne mai cikakken sanin addini dana zamani,don haka bashi da wata damuwa,ya amsa mata a sake yana tambayar jikin nata,daga bisani ta fita ta basu waje shida ja'afar din "Tunda kacemin zaka samu lokaci banji kace komai ba,ni na samar maka lokacin,na shaidama minister zuwanka,yau basai gobe ba kaje ku sasanta ka dawo da ita,itama ta zauna a dakinta kamar 'yar uwarta" kansa a qasa,gaba daya abbi ya yanke masa hanzarinsa,to amma bazai iya musa masa ba,ya amsa masa da to,yana mamakin dattako irin na abbin,bayan duka tarin aibun daya gani a kanta amma bai bashi qofar rabuwa da ita ba. Sanda ya koma dakin bayan ya raka abbi ya wuce yayi qoqarin danne dukka damuwarsa don kada hankalin maimunatu ya tashi,saidai wayam ya rasata a dakin,ya dinga lalubenta bai sameta a ko ina ba sai a kitchen, tayi zaune tana lodar abinci baba tabawa tana qara mata,sai yayi tsaye rungume da hannuwansa yana kallonta yana murmushi,baba tabawan ce ta fara ganinsa,sai tayi murmushi "Sannu da zuwa manya,qaraso ciki mana" "Baba ke kike sake shagwaba diyar nan taki, abincin nan da take ci dole ta qara nauyi" murmushi tayi "Ba dole ba,ai haka mukeso,alamun samun lafiya kenan" "Gaskiya ne" ya amsa yana sakin qaramin murmushi yana takowa zuwa inda take zaunen,baba tabawa kuma ta ajjiye serving spoon din hannunta tana bar musu kitchen din,don yanzu haka take musu. Yadda take taunar abinda ke cikin plate din ya burgeshi,saboda yadda dan qaramin bakinta yake juyawa,tsigar jikinsa ta zuba,ya matsa kadan sannan a hankali ya riqe fuskarta ya hade bakinsu waje daya. Sai daya tsotse dukka labban nata da sauran maiqon dake kai,tuni plate din hannunta ya yafi yayi nasa waje,abinda yake ciki ya watse,dauke kansa yayi a hankali yana maida numfashi,shi da ita suna kallon farantin dake watse a qasa,tabe baki tayi kamar zata saki kuka tana duban yadda dan waken yayi d'ai d'ai,dubansa ya maida kanta "Meye wannan?" "Dan wake nane fa?,kaga abinda kayimin" ta fadi a mugun narke,da alama qiris take jira ta saki kuka,murmushi ya saki yana dan take yatsunta da nashi "Yanzu tsakani da Allah ni na zubar miki?,ba ke kika zubar da kayanki ba?, mene abun dadi a nan ma fulawa ne ko da menen?,kaman bama" baisan hakan daya fada tunzurata yayi ba,kawai saita sake masa kuka "Ragowarshi kenan fa,Allah saika sakemin wani" ta fada tana hawaye daya na bin daya "Bari na kira baaba tab....." "A'ah" ta fada da sauri tana maqale kafada "Ni kaine zaka yimin" hannu ya dora saman kansa yana dubanta,sai kuma dariya ta kubce masa "Bansan ta yadda akeyi ba" kafin ta amsa baaba tabawa tayi sallama ta shigo ajjiye flask din abincin ta "Subhanallah me ya faru?" Ta tambaya,tana kuka tana gaya mata ja'afar ne ya zubda mata dan wake,kuma tace ya sake mata wani yace zai kirata "Ikon Allah.....sai haquri manya,yanayin nata cikin kenan,yanzu kiyi haquri na sake miki wani" "Shi zaimin Allah,shi ya barar min" "Jeki baaba zanyi" ya fada yana tattare hannuwan rigarsa "An shiga uku toh....." Baba tabawa ta fada taba riqe baki tare da dafe kai,wannan rigimar bata taba ganinta wajen maimunatu ba sai yau,itakam ba zata iya kallon babban mutum mai matsayi da kima kamar ja'afar ya gwaggwafe yana dan wake ba,sai ta fice daga kitchen din tana cewa "Allah ya sawwaqa". Cikin lokaci qalilan ya fuskanci dan waken nan fa bazai yiwu ba,ga maimunatu ta kasa ta tsare,asalima hira ta koma tana masa ko a jikinta,jira take ya.kammala taci,shuru yayi sai kuma ya kashe gas din,kafin tace komai juyo ya dauketa cak,sai ta dubeshi "Baka gama ba fa" "Babban son of beans zan baki,zo muje kiji" ya fada dukka jikinsa yana amsawa,gaba daya ta canza masa,cikin ba qaramin qara mata daraja da martabar da mace ke samu a auratayya yayi ba,duk da dama maimunatun yayi imani da ta dabance,sosai madarar shanu ta ratsata tun tana qaramarta. Ko acan babbar bedroom din shagwabe masa tayi,tanata qwallar shagwaba shi kuma yana biye mata,a sannan kaga yadda lallabarta kamar qwai sam ba zaka ce shine wannan Captain J din ba,matuqin jirgin sama,kuma babban dan kasuwa,maabocin izza miskilanci shan qamshi da jin kai ba,gaba daya ya sukurkuce maimunatu,wani lokaci har tsoro yake bata. Tare sukayi wanka kamar yadda ya saba mata,yakan gaya mata sunnah ne mai qarfi yin wanka tare da iyali,saita koma jikin kujera ta takure kamar wata 'yar mage,don tun dazun tace masa tana jin sanyi. Binsa take da kallo sanda yake taho wa wajenta dauke da wasu fararen socks masu taushi,yayi mata kyau sosai,kayan daya sanya din sun amsheshi ba kadan ba,ko yaushe sake fresh yake da kyau,ko ba'a gaya maka ba hankalinsa a kwance yake. A hankali ya duqa gabanta idanunsa cikin nata,farare sol din qafafunta ya kama ya soma zura mata safar,har ya gama tana kallonsa,sai yasa hannu yaja kumatun ta "Wai duk yunwar dan waken ce?,kada ki cinyeni angel" murmushin ta saki tana lumshe idanu,tuni ya bata abinda yafi dan wake,a hankali tace "Idan na cinyeka kuma wa zan kama?,kawai ka yimin kyau ne,so nake na haifo baby me kama da kai" dan fuska ya bata cikin salon tsokana "Baby ko babies?,biyu ko uku nakeso,kuma masu kama dake ni nakeso" kafada ta maqale tana murmushi "Ban yarda ba,nafison me kama dakai gsky" ido ya zaro "Angel......kina kallon kanki da kyau kuwa,kinsan yadda Allah ya tsara halittarki?,duk sanda na kalleki saina yima daada addu'a da fatan dawwama a aljanna data haifomin ke" murmushi tayi tana sake lumshe idanunta,farincikin samun miji d'aya da d'aya kamar ja'afar na sake kamata,bata da abinda zatace da anni itakam a rayuwa,ta gama mata komai data hadata da d'an jikan nan nata,wanda ya hada komai na rayuwa,ko a aljanna shine zabinta "Ko baki qoshi bane naga kina wani kallona qasa qasa?" Ya fada cikin sigar tsokana yana kai hannuwansa saman qirjinta daya soma cika sosai saboda yanayin ciki,hannuwansa ta ture tana bata fuska hadi da turo baki "Nifa yunwa nake ji Allah,a bani abinci ko kuma na cinyekan" tattausan murmushi ya saki yana dora kansa saman cinyarta ta tadda zai iya ganin fuskarta sosai "Bana gajiya dake angel,bana gajiya da kasancewa tare dake,you are my world angel" a hankali ta dora tattausan lips dinta akan nasa,ta bashi wani hot kiss,sai ya lumshe ido yana fadin "Wash Allah amma,zata kasheni" dariya ya bata sosai har tana qyalqyalawa,gami da sanya hannunta ta rufe fuskarta. Babban hijab ya dauko mata yace suje taci abincin a wani wajen,daga nan tadan tattaka ta miqe qafart,hakan yayi mata,taji dadi sosai,don tunda ta kwanta ciwon bata fita ba. Leqawa tayi ta gayawa baaba tabawa zasu fita,tayi musu adawo lafiya tana binsu da kallo,murmushi kwance akan fuskarta tana mamaki.lallai mata suna da wata babbar baiwa da daraja,mutum kamar ja'afar amma yarinya kamar maimunatu ta sukurkutashi,inda wani na waje aka baiwa wannan labarin zai qaryata,captain ja'afar a kitchen yana sakun dan wake(🤣🤣kadan daga aikin mata,munfi gaban haka,talaka ko mai kudi ko malami dukka a tafin hannun mata suke,Allah dai ya qara mana albarka da juriyar haquri da mazanmu,ya qara mana qauna da fahimtar juna a tsakaninmu,ameen) A hanya yake gaya mata ya sama mata malama da zata dinga zuwa kullum,qarfe sha daya na safe zuwa biyu kullum suna karatu,muhimman subjects da take buqatar samu a waec neco da jamb dinta,in sha Allah karatunta bazaya tsaya ba. Qwararriya ce sosai matar,hasalima hausa kadan kadan takeji,sunanta miss serah,sosai taji dadi, hankalinta kuma ya sake kwanciya,don yanzu babban burinta a yanzu shine ta zama full house wife,ta kyautata masa matuqa kamar yadda taga daadarta tanayi sanda take raye,gata da soyayyar da ja'afar ke nuna mata babu wani abu da zata saka masa dashi face nuna masa zallar soyayya da kulawa. Wannan eatery din mai tsada daya saba zuwa ya kaita,yace yau sai ya qureta,ta zaba duk abinda takeso a kawo mata "Zan baka mamaki" "Haka nakeso" ya fada yana zube mata idanun nan nasa,ta kuwa zaba abinci kamar hauka, waitress din ta kalleshi "Sir,total din fa da yawa" fuskarsa a dan daure kamar yadda ya saba zama boss dinsa duk sanda ya fito ya kalleta "Kiyi aikinki kawai,ba ruwanki da abinda za'a charger" "Ok sir" ta fada tana juyawa a ladabce,cikin zuciyarta tana jin inama ace itace maimunatu,tunda suka shigo idanunta yana kansu,wata irin madarar soyayya take gani suna zubarwa zallarta(haka dan adam yake,a duk sanda kaga wani ya zama wani,ko ya taka wani muqami,burinka kawai dama kaine shi?,shin kasan irin qayoyin daya taka ya wuce a hanya kafin ya iso bigiren da yake kai?,so duk wanda ya zama wani akwai qalubale taf daya haura kafin yakai tudun nasara,jajircewa haquri da juriya gaskiya da amana suke kai dan adam duk wani mataki a arayuwa,kamar yadda amanar maimunatu ta sake baiwa anni sha'awa wajen hada iri da ita). Tun tana ci cikin marmari yana tsokanarta har ta fara zare idanu,dariya irin wadda ya jima baiyi ba ya dinga mata,har sai daya sanya hannayensa dukka biyu ya rufe fuskanshi,Allah yasa babu kowa a kusa dasu. Sautin kukanta kawai yaji,ya daga kai da sauri yaga tana hawaye "Ya salam,me kuma akayi miki?" "Ba kaine ba kakemin dariya saboda ban cinye ba?" Lallai shagwaba ta sake gaba,haka don dole ya danne dariyarsa ya dinga rarrashinta,ya lallaba kayarsa suka biya bill suka wuce. Yanason cika umarnin abbi,don haka ya biya gidan umma sa'adah ya ajjiye maimunatu yace zaije ya dawo,ta gaida umman,cikin murna da zumudi ta shige cikin gidan yaja motar kai tsaye zuwa gidansu unaisa. Yana shiga gidan guard din suka fara rige rigen gaidashi,kafin a shiga cikin gida a gayawa haj Aayah zuwansa,babban parlor din da ake sauke baqi na musamman a gidan tasa aka kaishi,ta dubi unaisa wadda tunda taji ance captain ja'afar ya iso ta miqe ta zauna daram,zuciyarta gaba daya tana gareshi,ta gaji da dakon zuwansa,ta kira wayarsa har sau babu adadi bai daga ba,shi yasa ya samu daddynta da maganar,shi kuma ya gayawa abbi wanda da farko baisan me ake ciki ba. Cikin shigar alfarma haj Aayan koda yaushe take,macace mai izza taqama da fadin rai,duban unaisa tayi,tana jin haushinta yana cikata yadda taga ta rikice daga cewa yazo,tana jin bacin ran yaron a ranta,diyarta kamar unaisa ta zauna wannan auren jeka nayi kan,ga yaran qawayenta 'ya'yan wasu wadanda takeso ta aura mata su amma fir yarinyar taqi sa taimakawar qanwarta anty talatu,yau zata kawo qarshen komai "Ki zauna,ni zanje na ganshi" kai unaisan ta daga badon taso ba,haka kawai taji ita hankalinta bai kwanta da ita ba,amma sai ta koma ta zauna kawai. Ko zama baiyi ba,yana tsaye a falon ya baiwa qofa baya yana duba wata calendar dake dauke da hotuna da bayanan shugabannin da suka mulki nigeria yaji sallamar haj Aayah maimakon unaisa. A nutse ya juyo suka hada ido ita dashi,ta zuba masa idanu tana karanto abubuwa da yawa da suka janye hankalin diyarta a kanshi,bata taba masa kallon tsaf ba sai yau,tabbas ya cika namiji,inda unaisa zata samu yadda takeso a game dashi babu abinda zaisa ta shiga lamarinsu,yayin da shi kuma kallon farko ya karanci akwai abinda ta shigo dashi,sai ya sake dai daita kansa,ya tattara dukka wani izza da kwarjininsa waje guda 84 Kallon kallo suka yiwa juna na wasu daqiqu kafin hajiya Aayah ta janye idanunta,ta sake tabbatar da izzar sa da kuma jin kan da akace yana dashi,ta sani,jinin gidan marwan akko ne,kuma jikoki ga maryam farouq kumo,ta wani fannin kuma shi din jinin sarautar wani yanki ne na qasar gombe daya gada daga kakansa mahaifin aishatu mahaifiyarsa,bai tsintsa a qasa ba "Sai yau suka turo ka ka maidata kenan?......" Ta fada tana dubansa kai tsaye cike da burin nuna nasa martaba da darajae diyarta,daure masa kai maganar tayi,kafin yace wani abu duk da baida niyyar tofawar ta sake magantuwa "Wato ga mara galihu wadda aka gaji da ita aka baka sadakarta,kq koromin diya gida babu abinda ta aikata maka,bayan ka jingineta cikin gidanka ba sid'i ba sad'ad'a.....lallai munubiya tayi gaskiya,duk sai yanzu zancanta ke bayyana sosai,na yarda nayi sake dana bar unaisa tabi zabin ranta......to wai shin ma kai ke aurenta ko wadan can tsofaffin da ka baro a gida?" Kai tsaye ya qanqance idanuwansa cikin nata yana dubanta,mai takeson fada?,martaba da muhibbar mahaifansa take shirin tabawa ko kuwa yaya "To bari kaji,ina raye unaisa ba zatayi zaman boranci ba,yanda suka rayu ba wanda ya takura musu haka 'yata zata rayu,kaje ka gaya musu,indai sun shirya zama da diyata dole su martaba ta su kimantata su kuma daukaka darajar ta,don ita din me daraja ce,indai kanason zamanka da ita dole kasan darajar ta da kimarta" "Idan kuma akaqi fa?" Ya fada yana jin wani abu na tsaye masa a wuya saboda taba masa ababen da duk duniya bashi da kamarsu,cikin mamaki take kallonsa "Saika sawwaqe ma diyata,tunda dai aisha ko maryama ne suka haifamin ita ba" gam ya runtse idanunsa,tabbas da haduwar hanya sukayi da matar nan ba abbi bane sila sai ya nuna mata zallar kuskure da kuma wautar data tafka yau din. Da gudu kuma cikin kuka unaisa data gaza gamsuwa da tahowa mommyn nata ita daya,ta biyo bayanta ta kuma labe tana sauraren abinda ke afkuwa ta afko dakin cikin kuka "Haba mommy.......ya zakice haka?" Da mamaki take kallonta "Ai biyoni kikayi?,to idan bance haka ba me zance,shashasha kin tsaya kamarki namiji na wahal dake kamar shine autan maza,to indai bazai sanyaki a gaban kowacce diya mace ba ciki harda uwarsa wallahi bazan bari kici gaba da zama dashi ba,don ke din mai daraja ce" idanu ya zubawa unaisan yana son hango darajar da hajiya Aayah ke magana akanta tattare da unaisa,hala bata da masaniyar komai,darajar daya tabbatar babu ita sam,amma zai basu assignment mai wahala,zai kuma bar musu tabo,ya zaro hannunsa dake dunqule a aljihunsa,wanda sai sannan yaji saman receipt din da aka basu a wancan eatery din ya dora,ya maida hannunsa ya zaro reciept din tare da ciro wani irin biro mai hade da pen perfume. Yana dora hannunsa saman takardar unaisa ta saki mommyn ta taho da sassarfa tana isowa gareshi "Don Allah kada ka aikata,zan zauna zan kuma zama duk yadda kakeson gani na,wallahi mommy laifina ne,nice nayi masa laifi,ni na jawo yacemin na taho" ta fada cikin kuka gami da dana sanin gayawa haj Aayah duka magangun da haj munubiya ta kitsa mata,hadi da janyo hajiyar tazo har gida ta sake tsarawa mommyn tata zance,duk tayi hakane don a sake azawa ja'afar rashin gaskiya,a kuma yi masa kaca kaca a nuna masa martabarta,ta yadda zai riqeta da kyau,kuma kowa a gidan ya shiga hankalinsa,yasan ita din ba abar banza bace. "It's too late" ya fada a ransa,bai gama ayyanawa ba haj Aayah ta dakawa unaisan tsawa "Kika sake kika isa gabansa ko kika sake furta wani abu sai na tsine miki albarka,nono na kuma da kikasha ban yafe miki ba,ya sakekin,da ana aure kafin a gama idda zakiyi aure". A nutse ya rubuta mata saki uku kyawawa,ya tura kardar gefe,sannan ya maida abun rubutun aljihunsa,har yayi taku biyu ya dakata "Ko gobe kikeso zaki iya daura mata aure,don ban dora mata idda ba,amma ban sani ba ko tana buqatar yin istibra'i,saiki tambayeta" "Istibra'i ba idda ba?" Hajiya Aayah ta fada tana maida dubanta ga unaisa dake riqe da takardar baqinciki kamar zai kasheta,wadda sai dafa fara duba bayanta dake dauke da sunan maimunatu abincin da taci da kudin daya kashe na abinda suka biya,da yake haka tsarin reciept din nasu yake,har yaushe maimunatu diyar ruga baqauyar bafulatana qanwar cikinta ta samu wannan matsayin a wajensa?,gashi ita ta buge da saki sakinma na wulaqanci har guda uku?. Cikin mota ya dinga sauke ajiyar zuciya,har ransa yaji babu dadi karon farko kuma tausayin unaisa ya ratsashi,saidai ci gaba da zama da ita abune da bazaiyiwu ba,inda batazo da alfasha ba,bata kuma dauki maganganu ba da zai iya haquri taci darajar soyayyar da take masa,a hakan ma sai idan ta yarda zata zauna dashi din,saboda yasan kansa da zuciyarsa,wani mahaukacin so ko qi garesu,wanda shi kansa baisan ta yadda zai canza kansa ba,indai zasu zauna tarenma cutuwa zatayi,bazai taba iya adalci ba,shi yasa ya yima kansa alqawari,indai ba wata babbar lalura ba ba abinda zai sashi zama da mata biyu,kamar yadda alqur'ani ya bawa maza shawara ga wanda yasan bazaiyi adalci ba,shima zai aikata hakan ne don gujewa azabar Allah ranar gobe qiyama. Kai tsaye ya karya kan motar tasa zuwa unguwarsu,ya duba lokaci qarfe tara na dare,ya tabbatar abbi yana gida,gwara yakai.kansa da kansa,ya kuma shaida masa abinda yayi da kansa,duk hukuncin da abbin zai yanke masa ya yanke masa. Tun a gate ya hadu da khadim,ya kuma gaya masa abbin yana ciki wajen anni,don haka ya bude murfin motar ya doshi sassan anni kai tsaye,ko kadan baya jin wata fargaba,yana da wannan tsaiwar tun quruciya,yana da juriyar karba da fuskantar hukunci,kuma a duk sanda yayi irin wannan din zaiyi wuya idan ba shine ke da gaskiya ba. Da fari anni ta tsorata,ta dauka wani abune ya faru ganinsa qarfe tara na dare,sannan yanayin fuskarsa ba cikin walwala yake ba,kai tsaye ya zube gaban dr marwan "Abbi......kayi haquri ka yafemin,nasan na maka na dai dai ba,na saki unaisa saki uku,gani a gabanka,kayimin duk irin hukuncin da kaga ya dace dani" duk da anni taji maganar wani iri,amma kuma batayi mamaki ba,tasan dama za'a rina,manya ne fa?,wanda zuciyarsa ke tsaiwa kan abu daya "Innalillahi wainna ilahi raji'un" abbi ya fada,sannan ya dubeshi "Mai ya kaika aikata irin wannan mummunan aikin ja'afar,abgadul halalu ilallah fa?" Fada sosai abbin ya rufeshi dashi, duk da yasan komai,amma bai nuna goyon baya ba "Ya isa marwanu" anni ta dakatar da abbi,don batason fadan da yaketa faman yi, "Kayi gaggawa manya,baka kuma kyauta ba,nan gaba koda wasa billhuwallazi karka ce zaka kwata,koda mummunan kallo kuwa" can qasan ransa dariya ta kamashi,yasan jirwaye mai kamar wanka take masa,kashedi kan maimunatun ta take bashi a fakaice,batasan a yadda yakejin maimunatu a ransa ba,zai iya sadaukar mata da rayuwarsa bama "In sha Allah,a yafemin" "Tashi kaje,Allah ya kiyaye gaba" anni ta fada,sai yaji wani abu mai sanyi yana saukar masa,kamar kuma an zare masa qaya,qaunar anni da martabarta na qaruwa a ransa,haka ya miqe ya fice yana yiwa Allah godiya da komai yazo masa da sauqi. "Marwanu" anni ta kirashi bayan fitar ja'afar daga falon,ganin yadda yayi shuru yana nazari "Na'am anni" "Kada ka saka wata damuwa a ranka,duk da baka gayan ba nima nayi bincike akan yarinyar,kwata kwata ba kinin manya bace,kuma kaima ka sani ka boye ne kawai,to Allah ya dubi zuciyarsa,baida hakkin diyar kowa ya rabashi da aurenta,saboda haka kada ka wani damu,Allah yasa hakane yafi alkhairi" kai ya jinjina "Tabbas anni,ni kaina na sani,amma minister yana da kima a idanuna,hakanan shi din na gari ne,bansan me zance masa ba,wanne bayani zanyi masa" "Allah zai duba zuciyoyinmu ya kawo.mafita" da wannan suka rufe zancan sukaci gaba da lissafin nisabin zakkar da anni zata fidda a shekarar cikin dukiyarta data mallaka. Washegari abbin yana zaune yana duba wani babban littafin fiqhu bidaayatul mujtahid wayarsa tayi tsuwwa,ya duba yaga minister ne,sai yaji nauyin dagawa "Subhanallah,dan yau,dan yau sai addu'a" ya fada,har wayar ta katse bai samu qwarin gwiwar dagawa ba,sai kuma yaga gwara ya kirashi da kansa,don haka yaja wayar yabi kiran. Bugu daya ya daga,yadda suka saba faran faran suka gaisa,saidai muryarsa sam babu karsashi,wannan ya tabbatarwa abbi akwai damuwa "Ni naso na fara kiranka,kunya da nauyi suka hanani" "Wallahi kada kaji komai doctor,kai ya kamata na bawa haquri,bansan haka diyata take ba na dauketa na bawa tsakakakken danka ba,abinda yaron ka ya aikata kuma shine dai dai,Allah yayi masa albarka,dama lalatacciya sai lalatacce,tsarkakakku sai tsarkakakke haka qur'ani ya fada" cikin rashin jin dadi abbi yace "Subhanallah,wanne irin zance kake haka yallabai?,ka daina fada bai kamata ba" "Dole na fada haka doctor,ace matar aure sa bin wani yaro zuwa dubai kwana da kwanaki?,ko sanda zasu dubai din su duka munafuntata sukayi akace an gayawa mijinta shi ya amince,ashe satar hanya tayi,ta kuma sake komawa a randa suka dawo din ba tare da sanin kowa ba ita da yaron,nima ina da laifi da giyar mulki ta rudeni na sakar musu daula suke zabar dukka qasar da sukaso karatu ko zama,duk da cewa yaran daya dakin aiba haka suke ba,kaga naga izina naga ishara ko?,ni banga laifin ja'afar ko in zargeshi ba ko kadan,ita kanta jiya ta fadi komai da bakinta,tsahon zamanta a gidan bai wulaqantata ba,bata rasa ci sha ko suttura ba, kulawar auratayya kuma tun kafin ta aminta da aurensa akayi mata bayanin sai tayi haquri ta koya masa sonsa ta jashi a jikinta,tunda kowa yasan matsalarsa,ta amince da hakan,ta yarda ko shekara nawa ne zata iya zama,kuma ya bata zabi tunda ya fuskanci ba zata iya jurewa zama dashi ba,duka ta fada,yanzu abokiyar zamanta ta tsinci kanta a wannan halin?" "Ya salam,ya Allah, jarrabawa ce yallabai,ka daina fadan magangun da zasu sake munana abun" maganganun masu kwantar da hankali abbi yayi masa kafin daga bisani suyi sallama bayan sunyi dogayen maganganu,abbi ya ajjiye wayar tare da littafin hannunsa a gefe,sai yaji shima gaba daya hankalinsa ya karkata ga aurar da yaransa dake gabansa,sai yanzu yake sake ganin gaskiyar anni data tashi hankali kan a aurar dasu,duk da baya shayi ko shakkar tarbiyya ko daya daga cikinsu,dai dai gwargwado ya tsare yi musu addu'a da tarbiyya bakin gwargwado,yana musu kyakkyawan zato. *BAYAN WATA BAKWAI* Yammaci ne dake dauke da wani lullumi saboda haduwar hadari a garin,dai dai lokacin cikin private hospital din dake government house road din,dakin dake dauke da sunan amenity one,daga doguwar qawatacciyar varender data qunshi dakunan,tun daga amenity one zuwa four da asibitin ke dashi kana iya jin tashin hayaniya sama sama daga dakin. Idan ka samu nasarar sanya kanka cikin dakin,zaka hangi mutane zaune cikin dakin,dukkan wanda ka kalli fuskarsa a cikinsu zai bayyana maka zallar farincikin dake kwance tun daga saman fuskarsa tasa har zuwa zuciyoyi. Anni ammi anty maama,hajja su laila gaba dayansu harda matan kawun nan maimunatu guda hudu,a hannuwan laila da salma fararen shawula ne dake dauke da wasu kyawawan baby boys a ciki,wadanda dukka wanda ya kallesu bazaya so dauke idanuwansa daga kansu ba,wani irin kyau suka dauko daga uwa da uba suka cakude,duka duka basu haura awa guda da zuwansu duniya ba,saidai soyayyar dake kewaye dasu mai tarin yawa ce. A hankali qofar toilet din ta bude, maimunatu ce tare da umma sa'adah,gefe kuma afrah ce,suna riqe da ita a hannu tana takawa a hankali,sai kuma duka hankula sukayi kansu,kowa yana zabga mata sannu "Anya maimunatu ba zaki bar kukan nan haka ba?,ko babies dinne bakiso?" Hajja ta fada tana kama baki,dubanta umma sa'adah tayi "Daadarta take tunawa,wai dama haka tasha wahala ta haifeta?,ta sake shan wahala.bata haifa abinda ke cikinta ba ta rasu?" Kowa saida jikinsa yayi sanyi,suka fara bata baki cikin nuna kulawa. A mugun sukwane motocin guda biyu suka dira farfajiyar asibitin,motar farko bata ko kai ga kammala tsaiwa ba aka bude murfinta aka sauko da wani irin kuzari hanzari da kuma sassarfa. Captain ja'afar ne,sanye da wani farin kaftan da aka qawata shi da dimki na musamman,tamkar yana da masaniyar yau din rana ce ta musamman a rayuwarsa,biye dashi kuwa manyan ma'aikatansa ne,don ya baro company ne babu shiri. Dukka baya suka rufa masa,jabir ya qara hanzari ya cimmasa "Relax mana captain,ance lafiya qalau fa ta sauka" "I know dude,na qagu na ganta ne" ya fada yana sake qara hanzarinsa harda sassarfa. Daga baya dukka suka tsaya,banda jabir da yaci gaba da binsa har suka isa bakin qofar, ja'afar dinne a gaba,don haka yana bude qofar hankalin kowa yayi kanshi,yayin da shi kuma idanunsa gaba daya suke kan maimunatunshi dake zaune saman gado,umma sa'adah na qoqarin bata tea tasha ko za'a samu ruwan nono ya samu,don yaran sun fara qananun rigingimu. Suna hada idanu sabbin qwalla suka cika mata idanu,abubuwa ne mabanbanta cikin zuciyarta,farinciki takeji mara misaltuwa da a yau ta bawa ja'afar din muradin ransa wato 'ya'ya,tunda cikinta ya girma baya cikakken bacci,don ta fishi samun barci me kyau ma,kullum cikin addu'a yake ba dare ba rana,hidima yake mata da jikinsa da aljihunsa,ya qwallafa rai matuqa akan cikin,har ta dinga jin anya ba mutuwa zasuyi ita da yaran ba?,anya itama ba wucewa zatayi yadda daadarta ta rasu ba?,sai gashi komai yazo ya wuce kamar ba'ayi ba. Abu na biyu zallar shagwaba ne da kuma tuna irin wahalar data sha,yazo yanzu zaa sauke masa nasa rabon da bai samu ba a dazun d tana labor. Dukka gaidashi suke,yayin da manyan ke masa barka,yana amsa musu amma hankalinsa ya karkata gaba daya a kanta,miqewa sukayi suka fara basu waje,afra da laila suka isa gefan gadon suka ajjiye yaran suma sukabi bayansu. Shuru dakin ya dauka bayan ficewarsu, hannayensa saye a aljihun rigarsa yana qare musu kallo daga nesa,yana jin komai tamkar a mafarki,idan ya kalleta sai ya maida dubansa ga yaran,duk da baya iya ganin fuskarsu sosai "Angel" ya kirayi sunanta a tausashe,yana jin wata sabuwar soyayyarta tana ratsa qashi bargo da kuma jijiyar jikinsa,kasa daga kai tayi ta kalleshi,sai ya haqura da kiran saboda yadda yakeji kamar ana fusgarshi zuwa gareta ya soma takawa a hankali,har ya isa bakin gadon,jikinta na gogar gwiwoyinta data zubo qafafunta qasa ta jingina da bangon. Hannayensa ya sanya ya daga fuskarta da kyau yana kallonta,sai itama ta zube masa idanuwanta da sukayi wani tarwai, tausayinta ya kamashi,yaso ace dukka gwagwarmayar naqudar data sha yana tare da ita,sai gashi ya qunsa mata ciki ya barta da wahala ita kadai 85 "Angel ya kika yimin haka?,kinajin naquda kika bari na tafi na barki?,bayan alqawari ne muka yiwa juna,dadi ko wuya zamu rabasu tare?" Kyakkyawan murmushi ta sauke masa duk da har yanzu da qwalla a idanuwanta "Banason raba maka hankali ne ko na tashi hankalinka,kayimin dukka wani abu daya dace kayi din" "Duk da haka angel,ki yafeni" ya fada yana sanyata cikin jikinsa yana kuma shafa bayanta a hankali. Yadda taji zuciyarsa na bugawa ya alamta mata zuciyarsa ta motsu da soyayyarta,hanya mafi sauqi kenan da take gane hakan "Ka cancanci dukka yabo da kuma jinjina" ta fada masa murya can qasa,sai kuma ta zare jikinta a hankali,da kallo ya bita "Banyi wanka bafa,jikina duka warin asibiti yakeyi" "Yafimin qamshin dukka turaren dake duniya" ya amsa mata yana narkar da idanunsa cikin nata,yana sake jin ta zama mallakinsa. Motsawar da daya daga cikin yaran sukayi shi ya tuna musu da wanzuwar yaran a wajen,ya saki wani qawataccen murmushi yana juyawa zuwa inda suke,yasa hannu ya fara dauko wanda yafi kusa dashi ya dorashi saman cinyarta,sannan ya sake dauko dayan shima ya jerashi da dan uwansa,yasa hannu a hankali ya bude fuskokinsu da kyau. Idanu ya zuba musu kamar yadda itama taketa kallonsu,cike da mamakin yanzun wadan nan yaranta ne?,mallakinta ne?,ita da ja'afar dinta?. Gani yake kamar sun masa nesa duk da kusa dashi suke,kamar zasu kubcewa idanuwansa,kawai sai ya ranqwafo dab da fuskokinsu yana sake qare musu kallo,dai dai sanda dayan shima ya motsa ya tura hannunsa a baki ya fara tsotsa. Dago kansa yayi sai suka hada ido,ta tabe baki gami da yamutse fuska "Kaga kura da shan bugu ko?" Wata qawatacciyar dariya ce ta subuce masa "Wonderful,na dauka idanuna kemin gizo,ashe da gaske ne photocopy na na baki, alhamdulillah,kinga tun yanzu suna alamta miki da daddynsu sukeyi ba dake ba" rigimar ganga ta saka masa shi kuma ya lalace wajen lallashi,kamar ba mutane ke jiransa a waje ba "Kin manta yanzun kin girma ne?,maman twins ce ke fa?" Ya rada mata a kunne,saita sunne kanta a kafadarsa tana dariya "Karki damu,next year photocopy dinki zamu ajjiye,kinga shikenan rigima ta qare" ido ta fidda tana dubansa "Mutuwa kakeso nayi hubby?" "Ba zaki mutu ba,saikin haifan kamar haka kamar haka sau shida,suma sun bani jikoki kamar hakan" ya qarasa maganar yana debesu ya maida su gadonsu dake kusa da nata,sannan ya dauko tea din da umma sa'adah ta ajjiye ya dawo kusa da ita ya zauna sosai cinyoyinsu na gogar na juna,har sannan binsa take da kallo,idan suka kebe ya sake mata kamar hakan nan saika rantse da Allah ba shine ja'afar marwan akko ba "Haaa.... bude bakin ki karba" hankali kwance ya zauna yana bata tea din,tana sha yana mata tambayoyi game da haihuwar tata tana bashi amsa,gab da zata shanye dr noor ta turo dakin ta shigo,kanta tsaye bata wani koma da baya ba,don itama wayayyar 'yar boko ce,wannan din ba baqon abu bane a wajenta,sai suka gaisa tayi masa barka sannan ta wuce wajen yaran kai tsaye tana sake kallonsu,yaran sun bata sha'awa matuqa,bama itaba,duk wanda yaji labarin an haifa twins yaran captain ja'afar akko sai ya leqo ganinsu,ya kuma tafi da kyansu da girmansu a baki,wannan yasa tuntuni hajja ta tofesu da addu'o'in tsari "Bakin dan adam bashi da kyau,wasu jariran da yawa tun a nan ake nakastasu,wasu suke rasa rayuwarsu,wani ma zai tanka abu baisan yana da kambun bakan ba,sai musiba ta fadawa abu yayita lalacewa a rasa dalili"(haka zancan hajja yake,don Allah komai zamu gani ya burgemu bama akan mutum kawai ba mu dinga shuru da bakinmu koda zuciyarmu ta yaba,idan ma ya zama dole sai.munyi magana mu hada da tubarkalla.ma sha Allah,wasunmu da yawa basusan suna da kambun baka ba,da yawa qila sun zama silar lalacewa ko mutuwar wasu amma basu sani ba,mu kula,kambun baka daban maita daban,a musulunci babu maita,amma akwai kambun baka,mu zama masu yawan fadin ma sha Allah,kome muka gani ya burgemu,ko uwa baason ki fiya yaba kyan danki ko wani abu nashi,zai iya yiwuwa kina da kambun bakan ke a karan kanki amma bakisan kina dashi ba,sannan mu iyaye mu dinga kula da yawaita yiwa yaranmu addu'a,musamamn idan zamu fita wani waje,musamman kuma idan Allah ya musu baiwar kyau ko wani abu,ga masu zuwa kasuwa su dinga haquri suna aje yaran a gida,mu rage yabon yaranmu da rage yawan fadin baiwarsu,kamar baiwar wayo ko basirar karatu,wani da ya tanka shikenan,sai kiga karatun yaro nata komawa baya a rasa daga inda matsalar take,karmu manta da addu'ar da annabi kewa jikokinsa sayyadina hassan da hussain,Allah ya kare mana su daga mugun ido da mugun baki ameen summa ameen). "Allah ya raya su,ya albarkacesu captain, congratulations" ta fada tana duba maimunatu "Thank you dr noor" ya fada shima yana jin dadin kulawar da take bawa familyn nashi. "Yauwa komai lafiya lau,zaku iya tafiya nan da awa biyu,amma ya kamata su fara shan nono yanzu,saboda wannan yellow din nonon kada lokacin samuwarsa ya wuce,yana da amfani sosai a jikinsu". Cikin awanni biyun suka gama shirya komai sai tafiya gida,a nan fa aka fara dambarwa,anni na cewa gidan dr zaa wuce da ita,hajja na cewa gidan wajenta zata je,yayin da umma sa'ada ma ke ganin ita yafi cancanta ta karbeta,saidai shi ogan ba wanda ya cewa komai,sai tsintarsu sukayi a sabon gida,ainihin gidan da shaheeda ta zauna,wanda aka sake gyarawa aka kuma sake canza masa fasali,tuni ya gama aikinsa an zuba komai,suturun sawar maimunatu kawai zaa dauko,don twins dakinsu ya dade da kammala,an sanya komai da yara zasu buqata,da gadajensu na kwanciya kowa nashi daban. "Shikenan dan uwana ya raba magana" anty maama ta fada tana dariya,don ita kanta yadda yaran suka shiga ranta,inda zaa bata maimunatu karba zatayi da gudu,shuru tayi dai kawai ganin masu son karbar nasu nada yawa,kuma duka sun fita cancanta. Cikin kwanaki shidan da suka biyo baya kusan kullum gidan cike yake da 'yan barka,masu wuni da masu zuwa su tafi,yaran sunzo da wani albarka da kuma farinjini na musamman,ba daga dangin maimunatu ba daga dangin ja'afar ba,ga 'yan uwan amma suma da baa barsu a baya ba,don wadan nan sune jikokin fari a wajenta. Baaba tabawa ke zaune a gidan,sai wata mai aikin yasira da anty sa'adah ta kawo mata,gefe daya ga afrah da take wuni sai dare take tafiya,kullum akwai driver da zai daukota ya kuma dawo da ita permanent wannan umarnin captain ja'afar ne. Tun afra na iya irga kayan barka da abinda maimunatu da yaranta suka samu har ta bacewa lissafi,saidai ta karba takai dakin yaran ta ajjiye kawai,ita kanta batasan adadin mutanen da sukazo mata ba suka mata alkhairi,bata taba sanin ja'afar mai mutane bane har haka sai data haifa 'yan biyu,tarin tururuwar mutane,wasunsu shi kansa bai sansu ba,duk da haka ba'a hana kowa shiga gidan, saboda anni tace albarka ce,kuma lokaci ne. Hatta abbu da abbi baa barsu a baya ba,kowanne sai daya tako qafa da qafa yaga jikokinsa,kuma kowannensu sai daya ajjiye musu barka mai nauyi,bama kamar abbuun da yakejin su kamar 'ya'yansa,yana ji kamar shi aka yiwa haihuwar shi da yake da qarancin zuri'a. Kayan lefen da aka ranta masa kudi aka masa aka sanyashi biya su ya maimaitawa maimunatu wannan karon,akwatina yayi mata sosai kamar yadda kowanne yaro a cikinsu aka masa nasa,duk da komai nasu iri daya ne,kasa cewa komai maimunatu tayi,saboda gatan da ja'afar din ke gwada mata har gani takeyi yayi yawa "Kadan daga aikin manya,indai zuciyarsa naso....to babu algus a soyayyarsa,da dukka zuciya ruhi da gangar jikinsa yakeyi a aikace" baba tabawa ta fada,jinjina kai kawai maimunatu tayi,don ita din ganau ce ba jiyau ba. Hankulan abbuu hajja da umma sa'adah ya kwanta sosai,iya soyayyar da ja'afar ke nuna mata da danginsa kadai ya tabbatar musu koda babu su maimunatu ba zata wulaqanta ba. Ranar suna tun asuba abbi da abbu kowa yayi radin suna a masallacin unguwarsu,akayi rabon goro da alawa aka fadin sunan yaran,marwan abbinda abubakar saddiq abbu,a nan gida afrah ta zaba musu nickname da (sa'ad da as'ad). Gidan dr kuwa suna sukayi sosai,yayin da gidan captain ja'afar sukayi nasu sunan,fadin irin kyan da maimunatun tayi bata baki ne,don kusan sau hudu ja'afar yana dawowa gidan ta boyayyar qofar baya,don kawai yazo ya sake ganinta ita da yaran nashi masu zubin diyan larabawa kamar yadda baaba tabawa kan fada idan ta gama musu wanka ta shiryasu tana dan musu rawa. Dukka danginta sun amsa kira,abinka da mai dashi,tun daga gembu har adamawa,abun farincikin tron suna ya watse lafiya,gift data samu kuwa tattarasu tayi tace ba zata iya budasu ba sai ta huta sosai. Kwanaki biyu rak gidan ya zamana iya na masu shi,sai baaba tabawa da kuma yasira,saidai duk da haka lokaci lokaci daga can gidan abbunta ko gidan dr marwan suna shigowa dubata tare da ganin yara. Cikin wani irin gata da kuma kulawa ta shiga rainon yaranta,gefe daya kuma hajja tana tsumata da gyara na musamman,dukka wata kulawa ta buri ta dorawa jikokin nata biyu afrah da maimoon,kasancewar bikin afra ya matso,sai ya zamana duk wani gyara da za'a yi mata tare da maimunatun take hadawanata gyaran har yafi na maimunatun,sosai hajja ya bude tsohuwar ajiyarta na tsohuwar babarbariya,ta shiga gyaran jikarta da kyau,duk wani gata daya dace tayi mata lokacin biki da bata sameshi ba yanzun take zubeshi,daga ita har abbun,shi kansa garar da yayi mata mai uban yawa abar kallo ce,duk da ja'afar din yace baya buqatar komai amma kuma abbun yace ya sani yayi haquri,aladace,kuma alada mai kyau ce wadda musulunci baiyi suka ba. Sosai itama ta hada hankalinta da kyau wajen kula da jikinta yaranta dama mijinta,a yanzun take jinta a matsayin cikakkiyar macen aure kamar kowacce diya mace,tayi kwance kwance tana debe tsaffin dabarun kama miji ba boka ba malam daga bakin hajja sa baaba tabawa,sannan tana samun sabbabi daga wajen afreen dinta da kuma fatiman jabir wadda tuni ta haife nata boy din don har ya fara wayo. Kafin tayi arba'in gaba daya ja'afar din ya sukurkuce mata,kulawar da take bashi kamar wani fami da kuma qwalele take masa,tako ina ta cika sosai,ta qara kyau da haske,ga wasu fitinannun turaruka da take amfani dasu,randa ya ritsata a daki akaso yin aika aika Allah ya qwaceta da qyar,tun daga ranar take takatsantsan,don so take itama saita cika kwanakinta sannan ta rikeshi yadda zata ida rikitashi da kyau. _sai muce Allah ya qara danqon qauna moon din captain🥰😊😊,muje zuwa ga page din qarshe in sha Allah_ 86 *BAYAN WASU SHEKARU* Babban dakin taro ne wanda ya cika maqil da zallar mata,manya mata masu ji da aji da kuma jin sun kai wani matsayi sun kuma taka mataki na rayuwa. Daga can step inda mai gabatarwa take,ta qarashe bayaninta da fadin "We will call our star that we have gathered here to honor her......maimoon abubakar muhammad" ta qarashe kiran da madaukakin sauti. Shuru dakin taron ya dauka,kowa ya tattara hankalinsa gami da zuba idanuwansa yana jiran ganin bullowarta,wasu sun santa,amma kuma ako da yaushe basu gajiya da ganinta,ita din ta dabance,tun daga yanayin halitta zuwa suttura da kuma yadda tasan mutuncin dressing,idan akace dressing to dressing mai nuna zallar kamala da kuma aji a rayuwa,dai dai da qamshinta na musamman ne,baa maganar sauran abubuwa,wadanda kuma basu santa din ba,zumudi suke suyi tozali da kyakkyawar fuskar da labarinta ya cika kunnuwansu kafin zuwan wannan rana,fuskar data zama ta alkhairi kuma jirgin fito ga duk wani mabuqaci mai neman taimako,fuskar data hadu da qalubale da gagwarmayar rayuwa iri daban daban,amma tayi hobbosa ta tabbatar bata koma baya ba. Cikin nutsuwa sautun takalman qafarta dake da tsinin dunduniya maras tsaho suka ratsowa ta cikin mutane,sai ta dauki hankulan mutane da dama nima na juya don ganin tahowar tata. Kyakkyawar farar bafulatanar usul,mai wani irin haske daya cakude da surkin jaja jaja,tamkar jini zai diga a jikinta saman lallausar fatarta mai santsi da sheqi,wadda ke nuni da zallar hutu wadata da kuma jin dadi,ma'abociyar wani irin kyau mai fusgar hankali da wani irin kwarjini daya cakude da zallar kirki da son jama'a dake saya mata soyayyar mutane duk inda ta tsoma qafarta. Sanye take da dark blue din wani yadi na mata,wanda aka yiwa ado da light blue da kuma yarfin gold din zare,kalar data sake fitar da kyanta,wani lafiyayyen mayafi ne a jikinta da bashi da shara shara ko kadan mahadin lafiyayyan takalmin qafarta mai madauri,hannayenta kana iya hangen warwaraye masu fashion masu tsadar gaske,wanda zaka tsammaci gold ne,amma ba shi bane,kasancewar sam bata da sha'awar amfani da gold din. Ci gaba tayi da takowa har ta iso wajen,ta karba abun maganar tana duban fuskar mc din,tata fuskarta dauke da murmushi,sanna ta maida dubanta ga matan dake gabanta,gyara zaman fararen eye glasses din data sanya don qawata adonta tayi,sannan tayi bismillah ta fara magana cikin tataccen turancinta daya cakuda da zazzaqa kuma lallausar muryarta. Duk wata hayaniya tsaiwa tayi,muryarta tacu gaba da tashi har ta gama ta koma yarenta na fillanci,a nutse ta waiwaya tana miqawa mc din loud speaker din tana dan kare fuskarta da hannunta da yasha jan lalle saboda hasken flashes na kyamarori,karban abun maganar tayi tana kiran sunayen wasu matan manya da sukayi fice wajen bada taimako,suka qaraso wajen suka miqa mata dukka kyaututtukan da aka tanada saboda ita. Fuskarta dauke da murmushi da kuma hawayen farinciki ta sake karbar abun magana "Inama mijina yana kusa!" Maganar da taja hankalin kowa a wajen,sai suka maida dubansu gareta,dan qaramin murmushi ta saki "Eh haka nace,inama mai gidana yana kusa,shi yafi cancanta da ya karba dukka wadan nan karramawar....kunsan dalili?" Kusan hada baki sukayi wajen fadin "A'ah" "Saboda da bazarsa nake rawa,hakanan shine tsanin dana taka har na zama abinda na zama a yau,da shawarwarinsa taimakonsa da kuma gudunmawarsa nake dukka wasu abubuwan yabawa da kuke gani a yanzu,ina fata a duk inda yake Allah ya karemin shi da kariyarsa ya dawomin dashi gida lafiya don sirrin hasbunallahu wani'imal wakil" kabbara duka matan suka saki,dai dai da sanda ja'afar ya lumshe idanunsa yana lafewa a bayan mota,live yake kallon yadda taron ke gudana,da taimakon d'ansa as'ad dake dauko masa komai ta wayar hannu video call ta watsapp. Sai yaji.kamar lokaci yaqi gudu,awa hudun da zaiyi kafin jirgi ya saukeshi a nigeria saita koma masa kamar shekaru hudu,wani kewar matar tasa ta dinga ninkuwa cikin ransa,shikam da dan adam yana kyautar aljanna a duniya,tabbas da ya yiwa maimunatu kyautarta tun a nan halak malak,baisan wanne irin so take gwada masa ba sa kullum qara gaba yake.maimakon yayi baya,baisan wacce irin kulawa bace wannan tamkar jariri sabon haihuwa. Duk yadda mutane suka kai ga tsareta suna son gaisawa da ita,wasu suna daukan hoto da ita hankalinta yana kan lokaci,duk bayan mintuna sai ta duba agogo,yau rana ce mai.muhimmanci a wajenta,kuma lokacinta mai tsada ne a yau din,saboda ja'afar zai dawo daga tafiyar da yayi,bayan ya kwashe wata guda baya nan,normally koda office yaje ya dawo bata wasa da bashi kulawa,koda kuwa tare da waye take,zata katse komai ta bashi hankalinta tunaninta jikinta dama lokacinta,takan ce shine kadai dan abinda zata iya masa,tunda ta fuskanci a duniya abinda yafiso kenan,ya jita ko yaushe a kusa dashi,koda zama tayi masa hira ne ya wadatar. PA dinta taja gefe ta kuma yi mata bayanin uzurin da take dashi,da qyar ta samu ta sulale ta qofar baya ta samu ta fice inda driver yake kiranta,sauke wayar dake hannunsa as'ad yayi yana duban fuskar mahaifinsa ta cikin screen din wayar yana murmushi "Abyy.....ummu ta gudu fa" murmushi ne ya subucewa masa yana gyada kai,yasan ta gudu ne saboda shi,a duk sanda yace mata gashi a hanya zuwa gida.....kome takeyi hankalinta yabar kansa ya koma gidan,har sai ta tabbatar ta samar masa da duk abinda zai iya nema ko buqata "Kace ina mata sannu tare da ban gajiya kafin na iso" "Zataji abby....amma abyy,pls saqona fa?,baka manta ba?" Kai ya gyada "Ina sane ranka ya dade✊🏽" ya fada yana dunqule hannunsa "Thank you aby" ya fada yana dariya gami da kashe wayar,ya kuma fella yana bin bayan mahaifiyarsa da sauri. Daga nesan farfajiyar wajen take iya hangensu,gajee ce goye da nasma tana riqe da hannun nasim tana musu 'yar tsere,fuskarta dauke da dariya sosai,dukkan alamu sun nuna tana jin dadin kasancewa da yaran. Daga gefe kuma saman kujerun da aka tanada a farfajiyar dai,sa'ad ne zaune riqe da tab dinsa shi daya yana faman dannawa,kamar mahaifinsa,shi ko da yaushe ba mai hayaniya bane,hakanan ba mai son damu bane,yafi ganewa zaman shuru,rashin son hayaniyarsa ya sanyashi baro hall din,ya gwammace surutai da maganganunsu nasim akan qarar amsa kuwwar hall din. Daga gefe asim ne yake musu tafi yana biye da waqar da gajee keyi musu,shikam kusan halinsu daya da as'ad din,ba ruwansa,dan wasa ne,ya dauko kawunsa uncle JB kamar yadda suke ce masa. Idanuwanta ta maida kan gajee,gaba daya ta canza shekaru biyar kenan da suka shude,tun bayan mutuwar inna furera wadda ta rasu saboda lalacewar qodarta guda daya data tabu,dayar kuma an yanke an dauke,bayan ta rasun gajee data auri saurayin ta bayan ta gama zuba rashin kunya da diban albarka kan shi takeso,wata biyu kacal ya ajjiye mata saki cikin dare suka kada shanunsu suka qara gaba,haka ta dawo gida cike da nadama da darasin rayuwa,rasuwar inna furera ta sanyata tattara ya nata ya nata ta koma gembu,saboda tana ganin babanta bazai yarda ta zauna dashi ba,tuni ya qara aurensa,kuma amaryarsa ta riqe laulo da kyau,tunda dama matsalarsa kadance,kuma zuwanta sai yasa yaron ya daidaita,bayan ta koma wajen inno mahaifiyar furera wadda tuni ta makance sai zaman yaqi yiwuwa,kaf 'yan uwan furera da suka fito ciki daya aka rasa me riqeta,hakanan ta dawo gidansu. Da farko.jauro yace bazai zauna da ita ba,amma amaryarsa ta tsaya tsayin daka kan nan din gidan uban gajee ne,bata da inda yafi nan,haka ya haqura,dama kuma shima ba yayi hakane don tauna tsakuwa don aya taji tsoro. Zamansu lafiya lau,gaba daya gajee ta canza,saidai tun dawowarta babu wanda ya nuna sha'awar aurenta,don kowa yasan yadda abubuwa suka kaya,har wasu na mata qazafin cuta mai karya garkuwar jiki,tayi kuka ta sake dadawa,ta kuma ji yadda sharri da qazafi yake,ashe haka maimunatu keji duk sanda suka jefeta da kalmar mayya?,ko barauniya?. Lokacin da maimunatu tazo garin yiwa yuuma ta'aziyyar rasuwar baffa labaran taga gaaje sai taji hankalinta ya gaza kwanciya,zuciyarta kuma ta kasa samun nutsuwa,daga bisani tabi shawarar da wani gefen na zuciyarta take bata,domin cikar dan adam ya zamana me yafiya,saidai ba lallai ne ko kuma tilas zuciya ta manta nau'in azaba ko cutarwar da wani dan adam yayi mata. Kasa tsaiwa ta saurareta gaaje tayi,saboda tsananin kunya nadama da kuma dana sani,sai data saka akayi mata tara tara,sannan ta tsaya ta saurareta cikin matsanancin kuka "Bazan iya hada muhalli dake ba maimunatu,iya girman cutarwar da mukayi da yafiyar da kika mana ma kawai ta isa,kiyi tafiyarki kici gaba da rayuwarki cikin farinciki,ki barni naci gaba da karbar sakamakon abinda na shuka" maganar gaaje ta sake karyar mata da gwiwa,sai taji hawaye kawai yana sauko mata,meye rana ko ribar cutar da dan adam?,indai kyautatawa riba ce ga rayuwa tabbas zata kyautatama gaje,baa saka sharri da sharri,da wannan tayi magana da jauro,wanda shima da farko yace ta barta kawai a haka har Alllah ya sake fidda mata miji,saidai daga baya titi matar daya aura ta saka baki gaaje ta biyo maimunatu,wannan shine asalin zamansu tare,gaba daya rayuwar gaaje ta sauya,idan ka ga yadda ta canza kai baka ce ita bace, maimunatu bata barta da duhun jahilci ba,ta maidata islamiyya ta manya,saida ta sauke ta kuma iya litattafai da dama,wanda wasunsu a wajen maimunatu take daukan karatun,tana musu karatun ne ita dasu as'ad duk dare na litafin hadith da kuma fiqhu,gaajen bata da sha'awar karatun boko sam,don tace iya na addini ya isheta rayuwar duniya,gaba daya ta tashi daga gajen ta koma barira(asalin sunanta),saidai gajen bata bace ba a bakinsu. Kusan ita ke taya baaba tabawa aikace aikacen gida da rainon yara,duk da maimunatu da baaban sunso hanata amma tace wannan kadai take ganin zatayi ta sakawa maimunatu,ta kuma shafe munanan abubuwan da suka aikata mata ita da innarta wadda har yau nema mata gafara takeyi. Abu guda ke damun maimunatu,shekara goma sha uku kenan da auren ita maimunatun,amma babu zancan aure wajen gaaje,yanzun haka su asad shekarunsu sha biyu kenan,takanyi murmushi kawai duk sanda aka mata zancan aure. Ana haka himu ya bayyana a matsayin ma'aiki a qarqashin dr marwan,gaskiyarsa jajircewarsa da riqon amanarsa ya sama masa matsayi wajen dr,randa suka fara haduwa da maimunatu kamar bai taba saninta ba,duk da sun gaisa cikin mutunci,shima yayi aure amma sun rabu da matar sai yaransa guda biyu dake hannun daadarsa,wadda nauyin kulawarta take wuyansa tun bayan rasuwar mahaifinsu baffa labaran. Yana yawan zuwa saboda yuuma data dawo gidan wajen anni,burin annin kenan na shekara da shekaru sai yanzu Allah yayi sanadin mutuwa,sanin alaqarsa da yuuma ya qara masa matsayi a wajen dr marwan,ya sake jansa a jiki,tare da matsayin da yake samun albashi da kyau. Kuka sosai daadarsa ta dinga yi sanda taga abinda Allah ya yiwa himunta,ya samu rufin asirin da kai tsaye zaa kirashi da mai kudi a yankinsu,duka ta dalilin yuuma da maimunatu,mutanen da bata kallonsu a baya a matsayin wasu abubuwa masu daraja. Yuuma ce ta bashi shawarar idan ya gama gininsa ya nema aure,ya kuma dauko daada ta dawo nan,amma kunya tasa daada tace ba zata iya zama kusa dasu ba,batasan da wanne ido zata kalli anni ba,hakan ma da suke ci susha daga alfarmarsu ba tare da sunyi duba da dabi'arta ba godiya take musu. To shima himun tsoron zabar matar aure yake a yanzun,don baiji dadin aurensa na fari ba,duk da sauqinta zabin daada ne,yuuma dai nata bashi shawari tare da jan hankalinsa akai. To gaurayen marasa auren nada yawa,cikin ikon Allah hankalin maimunatu afrah da anni ya karkata akan yiwuwar hada yuuma da abbuuun maimunatun aure,suka kuma gabatarwa da abbi wato dr marwan "Na dade ina qiyasta hakan a raina,saboda dacewa da sukayi da junansu,zan jarraba,Allah yasa a dace,Allah kuma ya sanya alkhairinsa da albarkarsa a ciki". Cikin ikon Allah kuwa dukkaninsu suka bada hadin kai,abun ba qaramin dadi ya yiwa su maimunatu ba,hadi kuwa yayi albarka,cikin wata qudurar ubangiji isa tsarki da kuma buwayarsa saiga yuuma da ciki,abunda ya girgiza tunanin kowa,yuuma da ciki?,ita kanta ba qaramin girgiza tayi ba,ta kuma qaryata har sai da laulayi ya kankama "Allahu akhbar,Allah buwayin sarki,duk zaman nan ashe rabon yana ta wani waje daban yana jiranki ramatu?" Anni ta fada tana qwallar farinciki,ita kanta yuuma kuka ta dinga yi sosai,kafin daga bisani kuma ta dinga jin kunya,takan kalli kanta,taga yadda shekaru suka fara tarar mata amma wai ciki gareta?. Ta fannin hajja kuwa kamar ta zuba ruwa a qasa tasha "Allah mun gode maka,ashe abubukar akwai sauran qwanka a duniya" shiko abbu fadin irin farinciki daya samu kansa ma bata baki ne,haka ya dinga bawa yuuma kulawa dai dai da shekarunsu,cikin girma da kulawa,har Allah yasa ta haife abinda yake cikinta ta hanyar CS da akayi mata,aka samu yaro namiji wanda kai tsaye abbuu ya sanya mata sunan mahaifinta ita yuuma din,yace shi 'yan uwansa sun saka sunan nasa mahaifin,wannan ya isar masa,itakam gwara a bar mata abinda zata dinga tunawa. Ajiyar zuciya maimunatu ta saki,yadda gaaje kewa yaran kawai zai gaya maka zallar shaquwa dake a tsakaninsu,tausayinta yana cikata,shekarunsu sun fara turawa,a qalla yanzun dukkansu suna neman shekara talatin da hudu zuwa da biyar,so ya kamata ace ta ajjiye itama zuri'ar da zata tuna da ita ko bayan ranta. "Ummeee" nasim wanda ya fara hangota a cikinsu ya fada da qarfi yana wara hannayensa gami da qoqarin gangarowa zuwa wajenta,abinda yaja hankalin sauran kenan,asad ya ajjye tab din hannunsa ya taso a nutse ya karba hand bag dinta yana cewa "Sannu ummee,amma an gama ko?" Dubansa tayi da murmushi bayan ta duqa ta dauki nasim "Ka gaji kenan?" Shafa kansa yayi kamar wani babba "Hayaniya....hadisan da kika kara mana shekaran jiya da daddare naketa qoqarin haddacewa,so gurin ba dadin zama na kasa riqewa" murmushi tayi tana duba hannun nasma dake nuna mata wai ya baci da qasa "Mun gama sai tafiya gida" ta fada tana sauke dubanta ga gaaje "Antyn yara,basu barkima kin shiga ciki ba bare kiji duka abinda aka tattauna" murmushi tayi "Na jiyo wasu abubuwan ta nan....." "To Allah yasa mu amfana" "Ameen ya hayyu ya qayyumu" gaaje ta amsa,sai maimunatun ta fara takawa a hankali tana cewa da as'ad ha hado kan yaran gaba daya anty barira ta huta "Amma gidan yuuma zamu tafi ko?,kwana biyu bamuje ba" da murmushi maimunatu ta kalleta "Zaki fake da haka dai ki gudu,aikin saba duk sanda daddy zai dawo a tafiya saiki tarkata kansu ku gudu da sunan ziyara" murmushi tayi mata "Aiba laifi bane,sai sunfi barinki kin sake kin hadawa daddy hankalinki waje daya" murmushi kawai maimunatu tayi,gaajenta ta canza,ta yadda kullum mamaki take sakeyi. "Ki bari ya iso,kuyi masa sannu da zuwa,sai na tambayar muku zuwan tunda gobe ba school,an shiga hutun makaranta" "To shikenan" ta amsawa maimunatun,tana takawa zuwa inda motar ke girke tana jiransu,asad ne kawai a ciki. lafiyayyar motar suka shige gaba dayansu driver yaja,yaran sunata hirarrakinsu,kowa na fadin sautun daya bawa captain J din,a haka suka dauki hanya. Sai da suka biya ta wani babban guri,ta karba saqonta a wajen sannan suka isa gida,a gaggaucw ta fita a motar ta barsu da gaajen,yau ko rabiyar fadan da sukanyi sanda zasu fita a mota na "kin takani" bata tsaya bi ta kansu ba, mayafinta ma dashi ta wuce kitchen din. _ZAFAFA BIYAR_ _ZAFAFA BIYAR_ _ZAFAFA BIYAR_ _ASSALAMU ALAIKUM JAMA'AR KWARAI MASOYA MABIYA, KUMA MAKARANTA ZAFAFA BIYAR..._ _ALBISHIRIN KU... INA MASU JIRAN *COMPLETED DOCUMENTS NA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR DA AKA KAMMALA WANNAN KARON* ?_ _KU MATSO.. DOMIN JIRAN DA KUKE YA KARE... LITTATTAFAN NA ZAFAFA SUN KAMMALU DAGA FARKO ZUWA KARSHE CIKIN FARASHI MAI RAHUSA..._ _GA MASU TAMBAYA.... ZAFAFAN DAI GA SU KAMAR HAKA_ _*FARHATAL QALB* (NA NANA HAFSAT MSS XOXO) NERA 400_ _*GURBIN IDO* (NA SAFIYYAH HUGUMA)NERA 400_ _*SANADIN LABARINA* (NA HAFSATU RANO)NERA 400_ _*INAYAH _RIBA BIYU* (NA MAMUH GEE)NERA 400_ _*BABU SO* (NA BILLYN ABDULL)NERA 400_ *_DUKA COMPLETED DOCUMENTS DIN AKAN NERA DUBU BIYU 2K (2,000)_* _YADDA ZAKU BIYA_ _IDAN BANKI NE_ _ACCOUNT NAME: HAFSAT UMAR KABIR_ _ACCOUNT NUMBER: 2270637070_ _BANK NAME : ZENITH BANK_ _SAI KU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902_ _ZAFAFA BIYAR_ _ZAFAFA BIYAR_ _ZAFAFA BIYAR_ _ASSALAMU ALAIKUM JAMA'AR KWARAI MASOYA MABIYA, KUMA MAKARANTA ZAFAFA BIYAR..._ _ALBISHIRIN KU... INA MASU JIRAN *COMPLETED DOCUMENTS NA LITTATTAFAN ZAFAFA BIYAR DA AKA KAMMALA WANNAN KARON* ?_ _KU MATSO.. DOMIN JIRAN DA KUKE YA KARE... LITTATTAFAN NA ZAFAFA SUN KAMMALU DAGA FARKO ZUWA KARSHE CIKIN FARASHI MAI RAHUSA..._ _GA MASU TAMBAYA.... ZAFAFAN DAI GA SU KAMAR HAKA_ _*FARHATAL QALB* (NA NANA HAFSAT MSS XOXO) NERA 400_ _*GURBIN IDO* (NA SAFIYYAH HUGUMA)NERA 400_ _*SANADIN LABARINA* (NA HAFSATU RANO)NERA 400_ _*INAYAH _RIBA BIYU* (NA MAMUH GEE)NERA 400_ _*BABU SO* (NA BILLYN ABDULL)NERA 400_ *_DUKA COMPLETED DOCUMENTS DIN AKAN NERA DUBU BIYU 2K (2,000)_* _YADDA ZAKU BIYA_ _IDAN BANKI NE_ _ACCOUNT NAME: HAFSAT UMAR KABIR_ _ACCOUNT NUMBER: 2270637070_ _BANK NAME : ZENITH BANK_ _SAI KU TURA SHEDAR BIYA TA: 07040727902_ 87 K'awataccen kitchen ne na wadanda suka samu duniya da kyau a hannunsu,iya tsaruwa ya tsaru,hakanan an wadatashi da dukkan wani nau'in kayan wuta,bedroom da kitchen dinta suna daya daga cikin muhallan da maimunatu bata wasa dasu,don duniyar gidan aurenta kenan,tana iya kashe ko nawa ne ta qawatasu,don faranta ran captain dinta. Da sallama a bakinta ta shiga kitchen din a dan gagggauce,mutuniyar kirki baaba tabawa na tsaye tana aiki,yayin da yasira kuma ke zauna tana tayata suna hirarsu kadan kadan. Da murmushi saman fuskarta ta waiwayo tana yiwa maimunatu sannu da zuwa,yayin da yasira ta miqe itama cikin girmamawa uwar gijiyar tata mai tsananin kirki da adalci itama tana mata barka da zuwa,gami da yunqurin karbar mayafinta da take qoqarin zarewa "An karbo kambun andawo kenan?" Murmushi maimunatu tayi yana buda kwabin alkubus din da tayi kafin ta fita "Mun dawo baaba,amma naso manyan naki yana kusa,shi yafi cancanta ya karba min" kai ta jinjina tana murmushi,yanayin soyayyarsu koda yaushe abar burgewa ce,kullum sake kusanci suke da juna "Dake dashi din duk daya ne maimunatu,idan kaga zahra ai kaga wata,kema kuma kin cancanci ki karba,alkhairanki ga al'umma masu tarin yawa ne,Allah dai ya jiqan mahaifiyarki,ya raya miki zuriyarki,ya kuma qara danqon qauna tsakaninki da mai gidanki" "Ameen baaba,na gode,Allah ya qara nisan kwana da lafiya me amfani" "Ameen ameen" daga nan suka kama aikin gadan gadan,wanda kafin wani lokaci sunyi nisa a aikin. Suna falo sunata hayaniyarsu,lokaci lokaci suna shigowa kitchen din,wannan ya kawo qarar wancan,wancan ya kawo qarar wannan,kasancewar gaaje ta fita islamiyya bayan dawowarsu,sai su kadai,asad dake ta aikin alqalanci ya gaji,shi kuwa as'ad dama ba kasafai yake kula fitinarsu ba,idan yayi magana daya biyu ana uku baka jiba jikinka ne zai gaya maka, maimunatu na yawan masa fada,shi yasa bai fiya zama cikinsu suna wannan shirmen ba. Sai data tabbatar komai ya hau saiti sannan ta saki ajiyar zuciya tana duban agogon dake kitchen din,akwai sauran minti arba'in a gabanta,waiwayawa tayi ga yasira "Nan da minti ashirin ko da biyar haka,don Allah ki kunna dukka burners din gidan nan a saka turaren wuta ko ina" "To ranki ya dade,turaren wajen aisa?" Idanu ta fidda tana dubanta "A yau din?,ai karkimin gangancin nan,turare idan bana hajiya na'ima ba banason kowanne a gidan nan" "Gaskiya ne,na jima banji turare irin nata ba wallahi,kamar kyauta ake bata kayan hadin,komai a wadace kamar yayi.magana,rannan fa asad naga yana murza turaren a jikinsa,nace me ya hadaka da turaren icce?,wai qamshin turaren ne baya gajiya dashi" dariya dukkansu suka saka maimunatu ta fara takawa zuwa gaba tana cewa "Kinsan qasan kwalaben iya ruwan turaren dake kwanciya ya isa azuba wani sabon turaren ya tsumu,kiyi a gida kiyi a kayan sawa gaba daya,gaskiya yanzun ban gane kowanne turare idan ba nata ba" "Ai ta hadu wallahi matar" yasira ta sanya musu baki,don ita kanta tafi son maimunatun tace ta kunna turaren hajiya na'imar saboda yadda gidan ke daukan wani tattausan qamshi (Tasted and trusted,ba biya tayi ayi mata talla ba,nayi hakanne don mata su amfana,saboda naga yadda yake zaunarwa da gidanki da jikinki qamshi,na tabbatar duk wadda tayi amfani dashi saita godemin,turaren wajenta shine turarena a yanzu,na bar amfani da turaren wutar kowa idan ba nata ba zaki iya tuntubarta ta wannan number (803 212 7953) if u are interested,idan kinji dadinsa kiyimin addu'a kawai). Sai data fara komawa sassansa tayi masa barin turare sosai,ta duba lungu da saqo ta tabbatar komai yayi neat tun daga katafaren falonsa zuwa lafiyayyen bedroom dinsa,ta ajjye masa dukka siyayyar data yi masa kowanne abu a muhallinsa sannan ta wuce nata sassan. Bedroom ne itama mai lafiya,wanda ya zamanka a ciki ya isa samar maka da nutsuwa, yadda aka shiryashi kadai ya isa gaya maka matar gidan tasan abinda takeyi,tasan kuma me ake kira da aure da kuma soyayyar miji,toilet dinta ta shiga ta fara shirya kanta. Cikin minti talatin kacal komai ya zama ready,ba abinda jikinta ke fiddawa sai daddadan qamshin turaren hajiya na'ima mai taushi da sanyaya rai,cakude da wasu lausasan bidy mist. Wani fitananniyar atamfa ta saka wadda aka yima wani zaunannen dinkin girma,da yayi masifar fidda haibarta da kuma kwarjininta,kallo daya idan kayi mata ba zakaso sauke dubanka daga gareta ba,don ita kanta data fito falo yaran binta da kallo suka dinga yi,duk da sun saba ganin irin hakan a tare da ita,amma kwalliyar yau din ta tafi dasu,gaaje ma sai data yi comment akai,saboda sosai gayun maimunatu ke burgeta. Tana tsaka da musu fada akan rashin fita da abincin masu gadin gidan da wuri,sannan ta koma wajensu asim tana masa maganar yadda suka fidda dukka games dinsu suna bazasu a wajen qarar bude gate da shigowar motoci gidan suka baqunci kunnuwanta,sai ta lumshe idanu bugun zuciyarta yana sake daduwa,wanda ya tabbatar mata da dawowar masoyinta uban 'ya''yanta kuma rayuwarta gaba daya zuwa gareta,ta sauke wani siririn murmushi dake dauke da tarin saqonni daga zuciya har zuwa saman fuska. Tana jin nasma da nasim na rige rigen fita zuwa gareshi,saidai ta tabbatar kafin su isa ya shigo,kusan haka al:adarsa take,duk sanda yadda suke sauri wajen ganin sun cimmasa sai ya rigasu,don shima a d'okance yake dawowa kuma a qagauce da son ganin iyalin nasa. Kamar yadda ta zata kuwa a bakin qofar falon sukayi clashing da yaran,the handsome and adorable captain ja'afar marwan khalid akko,cikin wata shiga data bayyana zallar izza kyau kwarjini da kuma qasaitarsa,sassanyan matashi wanda yake kan ganiyar quruciya kyau da kuma arziqi,wanda ya dace da macen qwarai haziqa daya tamkar da dubu irin maimunatu,wadda a kowanne mataki na rayywarsa tana biye dashi tana kuma riqe hannuwansa zuwa kowanne mataki a rayuwa,nasara ko kuma akasinta. "Assalamu alaikun warahmatullah" ita ya fara fada hancinsa yana shaqar masa qamshin da yafiso a duniya fiye da kowanne qamshi,zuciyarsa na masa wani irin motsi tana tabbatar masa da wanzuwar mace mafi soyuwa cikin duniyarsa,wanda a duk sanda kusanci irin haka ya samu tsakaninsu sai sautin bugun zukatansu duka sun sauya. A tausashe ya durqusa gaban yaran nasa saboda ya basu damar hawa jikinsa kamar yadda suke da buri,yayin da muryarsa ta aike da saqo zuwa ga zuciya da kuma gangar jikin maimunatu,sai ta gaza jurewa ma shigowarsa,itama tabi sahun yaran nata wajen yin tattaki zuwa bakin qofar. Daraf kuwa suka hayeshi,ya miqe dasu duka su biyun,kowanne a hannunsa guda daya "Banda kun samu qaqqarafan uba,ta yaya zai iya dagaku duka ku biyun?" Ta fada a ranta tana murmushi,saboda nasma da nasim din ba goyon da tayi sukayi qiba kamarsu. Miqewarsa tayi dai dai da hada idon da sukayi dashi,wasu irin abubuwa suka soma yawo a qwaqwalwar kowannensu da kuma zuciyarsa,a tare suka aikewa juna saqon murmushi mai dauke da tarin ma'anoni "Barka da zuwa,barka sa dawowa daddy" ta fada tana daurewa yadda ta qagautu ta jita cikin ingarman jikinsa da bata sake gasgata tayi kewarsa ba sai yanzu data ganshi a gabanta "Barka kadai ummul aulad hayati baitiha wa zaujiha" murmushi ta sauke masa tana basarwa saboda asad da as'ad dake wajen,wadanda suka fita parking space dauko jakankunansa,tunda suka tasa suke wannan aikin,bai bari kowa ya riski inda iyalinsa suke. Zama tayi daga hannun kujera tana kallon yadda ya sake yana wasa dasu,kai kace tsakanin sako da sako ne,wannan din ba baqon abu bane a wajensa,a waje ne da fagen aiki yake zaaki,amma cikin gida tamkar mage yake komawa da 'ya'yanta,duk sanda ta zuba musu idanu tana mamaki yakanyi murmushi yace "Khairukum khairukum li ahlihi,wa'ana khairukum li ahli(mafi alkhairinku shine mafi alkhairi ga iyalinsa "wanda yafi kyautata iyalansa kenan",sai annabi yace nine mafi alkhairinku ga iyalaina)" takan sake murmushi tana jin dadi har cikin zuciyarta,lallai ya tabbata diyan Dr marwan babban limamin qasar gombe,hakan kuma yana qara mata nutsuwa sosai,tana ji a rai da zuciyarta lallai bata da haufi ba zata wulaqanta a hannun mutumin dake qoqarin koyi da sunnar ma'aiki ba. Da taga abun nasu ya miqa saita miqe tayi daki,ya bita da kallo a sace yana jan numfashi,yaran sun hanashi motsawa kwata kwata,ruwan wanka ta hada masa,amma har ta dawo yaran basu barshi ba,har sai data fara masa sign sai yayi mata alama data wuce dakin gashinan zuwa,tana dan tura baki gaba alamun complain ta miqe ta wuce din,shi kuma ya saki dariya cikin ransa yana cewa "Zakiyi bayani" . Sai daya bude jakarsa dole ya fiddawa kowa tsarabarsa,sannan ya sanya asad ya tattara kan yaran yace su wuce dakinsu,nan da awa daya kowa ya daura alwala zai fito su wuce masallaci sannan ya samu kansa. Murmushi ya saka sanda ya bude dakin,tana tsaye harde da hannayenta,ya taka a hankali yana jin shauqi yana dibansa tare da wani magnet mai qarfin gaske zuwa gareta. A hankali ya isa bayanta,ba bata lokaci ya jata zuwa jikijsa a tausashe ya manneta da jikinsa,rigima taso yi masa sosai kan yaqi sallaman yaransa da wuri,amma kuma saita kasa,suka sauke ajiyar zuciya a kusan tare lokaci kuma daya,kowannensu yayi shuru yana sauraren bugun zuciyar dan uwansa "Ya rabb,ka fini sanin yadda nakeson wannan halitta taka.....ka fini sanin girman kyautatawarta gareni.....ka fini sanin girman soyayyar da takemin......" Kafin ya qarshe ta datsi numfashinsa ta amshe addu'ar gami da juyar da ita kansa "Allah ka soshi fiye da yadda yake sona,ya ubangiji ka faranta masa fiye da yadda yake qoqarin farantawa iyalinsa da sauran al'ummar annabinka,ya Allah.....ka ninka soyayyata a zuciyarsa" da hanzari ya juyo da ita suna fuskantar junansu,ya waro idanunsa waje,zubawa juna idanu sukayi kowa zuciyarsa tana narkewa,sai ya kama hannunta ya sanya saitin zuciyarsa "Angel.....indai soyayyar da nake miki a yanzu akwai qarin wata......to inajin mutuwa zanyi,ko a yanzun nakan rasa inda zan sanyaki na boyeki a zuciyata,inaga idan soyayyar tafi haka?" A tausashe ta sakar masa murmushi ta zagaya hannuwanta a bayansa ta rungumeshi sosai cikin jikinta,duk da duka duka tsahon nata iya qirjinsa ne "So nake kayita sona.....kayita sona.....kayita sona.....saboda ni ina da tabbacin bazan taba iya daina sonka ba" "Nima da soyayyarki zan mutu angel,saboda ke aka halicceni,kamar yadda nake da tabbacin saboda ni aka halicceki....." Yayi maganar yana yiwa bannunsa masauki a tsakiyar bayanta da ya zuge zip din rigar tata har zuwa qasan rigar,kafin ta samu cewa komai ya balle brazier dinta ya kuma soma zameta tare da rigar gaba daya sannan ya maidota cikin jikinsa ya manneta yana sauke numfashi da sauri. Kisses masu zafi ya soma sauke mata,kamar zai cinyeta danya,babu inda bai sumbata ba a jikinta,kafin ya dauketa cak zuwa duniyar da kullum yake mararinta,yake kuma jin maimunatun tashi kamar ranar ya fara saninta,tana da wata baiwa ta musamman,wadda sai an tara dubunnan mata baa samu mai irinta ba,sai tsananin dace. Anan suka taru suka lalace,har lokacin sallar magrib ya gota basu sani ba,tuni su asad suka daura alwala suka sanya asim a gaba suka fice masallaci ganin daddyn nasu bai fito ba,basu nemeshi ba suma,yaran nada tsananin hankali da kuma tarbiyya,nasma da nasim kuwa na wajen baaba tabawa da gaaje da suketa hira,tana bata labarin mutumin dake ta binbinin binta yana sonta "Yuuma tanata qorafi dama,ya kamata ki bashi dama,bakisan abinda Allah zaiyi ba,ni zan shaidawa maimunatu da kaina" wannan karon gaajen bata musa,don tana jin ya kamata ta saukewa mutanen da suka dauki nauyinta nauyin dake kansu ta matsa zuwa gaba itama. Wasu irin hirarraki suka dinga yi a tsakaninsu bayan kammalar komai,hirar dake ratsa zukatan masoya tare da kawo shaquwa a tsakaninsu,tana kwance a qirjinsa suna jin dumin fatar juna(skin to skin). Ita ta fara zabura zata miqe ganin lokaci yaja,yayi caraf ya riqeta yana kallon qwayar idanunta,saita narke masa da shagwabarta wadda bata girma sam a wajensa "Lokacin magariba ya gota hubby" sake tsomoshi tayi,sai ya lumshe idanu,ya motsa tausasan labbansa yana cewa "Astagfirullah" ya sake bude idanuwan nasa a kanta,wani qawataccen qaramin murmushi na fita a fuskarsa. Biye masa tayi itama tana kallon fuskar tasa,irin wannan yanayin koda baiyi magana ba idanuwansa kadai sukan isar da saqo zuwa ga zuciyarta mai dimbin yawa,irin saqon da fatar baki tayi kadan ta isar dashi "Bana gajiya dake angel moon,wai meye sirrin?" "Kaine hubby" ta fada tana zamowa daga gadon da hanzari,ta riga ta kubce masa,sai ya bita da kallo "Zamuje mu gaida abbi amma da abbu da yuuma,don Allah ki gayama anni,tayi haquri,na tuba nabi Allah na bita,ta daina ce miki gurbin ido,idan ta fada kaman zan mutu nakeji" dariya ta tuqe maimunatu sosai amma ta cinye gami da bata fuska "Ba ruwana,aikai ka fara sakamin sunan,donme zaace ta daina yanzu?" Zamewa yayi da gwiwoyinsa a gabanta "Wallahi wallahi ba ma kinfi qarfin ido ma a yanzu bare gurbinsa,ke din fuskace.....ke gangar jiki da ruhi ce gaba daya" dole dariyar da take dannewa ta fito,ta shiga qyalqyala masa,yayin da ya bita da kallo yana murmushi dariyarta tana burgeshi sosai "An daina fada tuni,kula ne bakayi ba,dama tana yine don ta tono ka" "Na tonu kuwa sosai" saita tsaya gabansa tayi saluting nasa,kafin ta sauke hannuwanta yakai hannunsa saman qirjinta wanda kullum tsole masa ido yakeyi,cikin muryar rad'a yace "please idan mun dawo a sake sanmin don Allah" ya fada yana narke mata,kai ta girgiza kawai tana dariya ta shige bandaki da sauru,sai ya boye fuskarsa a tafin hannunsa yana jin zafin sonta a ransa,daga bisani kuma ya yaye bargon da sauri ya sauko shima yabi bayanta bandakin fuskarsa ta gaza boye murmushinsa. Yana daga tsaye tana hada musu ruwan wankan yana qarewa bandakin kallo,tunda ya shigo ya lura da yadda ta canza wasu kayyaki na dakin zuwa toilet din, maimunatu ta musamman ce,ta dabance,komai nasa mai muhimmanci da kima ne a wajenta,sai ya qarasa ya karbe lallausan sabon towel din da take shirin ajjiye masa a gefan bathtub,ya dagota yayi kissing goshinta "Thank you,thank you my moon" "For what?" Ta tambaya tana murmushi "For loving me and for everything you do and everything that you are" bai bata damar tofa tata ba ya jata zuwa bathtub din,nan ma suka bata lokaci wajen wanka saida tayi da gaske. Ko kanta bata tsaya busarwa ba ta zura riga sukayi sallah,sai da suka idar sannan ta dauki waya ta kira baaba tabawa tace yaran su shirya zasu fita,ta sauke wayar tana zame dankwalinta ta sauki hand drayer ta jona zata busar da gashinta. Zameta yayi daga hannunta yana fadin "Ya zaki shiga aikina bayan gani na dawo?" Kai tsaye ta miqa masan,don ya sabar mata da hakan muddin yana nan. Yana busar matan suna sake taba hira,dalilin da yasa aikin ya daukesu tsahon lokaci,ya gyara mata tsaf,sai yaja da baya yana kallonta,tayi masa kyau matuqa da gaske "Gaskiya da matsala,zamu ajjye yaran nan a gidan abbuu" "Daka gama farantama khalipha(yaron da yuuma ta haifa da abbu)" "Amma daddy wai baka girma ne?,next month fa amnee zatayi candy" murmushi ya saka,sai ya juyar da ita tana kallon madubi,shi kuma yana tsaye daga bayanta yana dubanta ta cikin mudubin "Soyayya bata tsufa,koda masoyan sun tsufa angel,jin nakeyi kamar yau na fara ganinki cikin kayan saqi kina koro shanu,kamar yau na fara saninki diya mace a johannesburg...." Maganarsa ta qarshe ta bata kunya matuqa,har sai data sanya hannu ta rufe fuskarta,yana tayata dariyan yasa hannunsa ya zame hannun nata "Banson wata kunya malama,johannesburg tana da kima da babban tarihi a rayuwarta,ki shirya bayan amnee ta gama exams dinta,za'a dauran auren gaaje da himu,na gama magana dashi tun ina can ya kuma amince,zamu wuce umra gaba daya da yara,harda baaba tabawa,daga can zasu dawo gida,mu kuma zamu sauka johannesburg,inason na sake dasa wasu 'yan biyun a can" juyowa tayi tana qanqame shi,dadi yana cikata kamar yaune zuwanta umara na farko,saidai shi din wajene da dukka musulmi,gefe guda farincikin yadda burinta ya cika,himu ya yarda zai auri gaaje,ta tabbatar har yanzu gaaje nason himu,saidai tana ganin kamar ya mata nisa,sai gashi cikin haquri dattako da kyawun hali nasa ya amince zai auretan duk da abubuwan da suka biyo baya. Hannuwansa dukka biyun ta riqe,tana sake jin duk duniya babu macen data kaita sa'ar miji,addu'o'i ta dinga jero masa,wanda ta kasa yankesu har sai da ya hade bakinsu waje daya,bada gangan yayi ba amma sai gashi sun sake rikita juna saida suka koma ruwa,sannan suka dawo suka sake sabon shiri,ita ta shirya shi tsaf da kayan da suka kasance zabinta kamar tadda ta saba masa,ta zauna a gefansa ta ci dashi ya qoshi,sannan suka fito. Wani irin perfect match couples wanda duk wanda ya kallesu sai ya sake waiwayowa ya kallesu,saboda zallar dacewa da juna da kulawa da kuma soyayya dake fita daga idanun kowa zuwa ga dan uwansa,wani lokaci ba tare da sunsan suna aikata hakan bama,haka suka dauki yaran nasu,sunata hirarraki a tsakaninsu,hira dake nuna fahimtar juna da qaunar juna a tsakaninsu,asim nata murna zaije ya tsokani anni,ya boye dan qaramin qadangaren wasaya radawa asad a kunnensa "Yau anni zatayi ta kanta,saina tsoratata,ladan tallemin qeya data yi rannan" karaf a kunnen maimunatu,ta waiwayo ta watsa masa daquwa "Akul dinka da tabamin uwa,ranka zai baci,zakayi ta kanka ne indai naji labarin hakan ya faru" dariya suka sanya gaba daya,dukkansu suna qaunar tsohuwar,har yanzu rigimar nan tata tana nan,saidai kuma tana tsananin son jikokin nata,musamman ace an hadu gaba daya,yaran hisham salma laila safina da fa'iza,ranar bata da katabus sai nasu. A motar kuma hirar sai ta koma ta anty amna,asad da as'ad nata hirar graduation party da suka shiryama amnan ba tare da amnan ta sani ba,ko maimunatu ma sai lokacin takeji, murmushi kawai ta saka tana jin dadin yadda Allah ya hade kawunansu,babu wanda zaice ba ita ta haifi amna ba,captain ja'afar kuwa hannunta ya lalubo kawai ya sanya cikin nashi,yasan ko mene yaran suka zama qoqari da jajircewarta ce,soyayyar data gwadama amanan tsahon shekarun da suke tare ko mahaifiyarta sai haka,yana alfahari da maimunatu matuqa a rayuwarsa,tayi masa komai,ta kuma zame masa dukkan abinda yakeson matarsa ta zama,tana kan zama din ma. *Tammat bi hamdillah* *A nan na kawo qarshen labarina mai suna GURBIN IDO,ina fata Allah yasa al'umma sun amfana,kura kuran ciki Allah ya yafe mana,ya bamu ladan ciki,abinda muka manta kuma bamu rufe dashi ba sai ayi mana afuwa,ajizanci ne* *Masoya masu siyan litattafan mu a koda yaushe,bawai don baku da inda zaku samu ba,mun gode qwarai da gaske,ubangiji ya yalwata arziqinku,ya bar zumunci a tsakaninmu,muna matuqar godiya a gareku,haqurin da kuke damu Allah ya saka muku da alkhairinsa,Allah ya sadamu da alkhairin sa* *ZAFAFA BIYAR NA MATUQAR GODIYA DA JINJINA A GAREKU* *Subhanakallahumma wabi hamdika,ash hadu an la'ilaha illa anta,astagfiruka wa'atubu ilaika*