[9/25, 2:37 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU🗿1 Batul Mamman(Mrs)💖 Bismillahir Rahmanir Rahim Mal Bashir dattijo mai kimamin shekaru hamsin da takwas na shigowa cikin layinsu yara suka fara binsa suna oyoyo Baban yara. Da yake kullum haka suke masa shiyasa baya rabo da yar tsarabar da zai kawo musu. Hannunsa daya yasa a aljihu wanda daga tsintsiyar hannun a yanke yake ba yatsu sakamakon zarton da ya fada kai har ya tsinka masa jijiyoyin hannu. ya sha wahala sosai likitoci suka ce hannun ya mutu dole a yanke shi. Duk da haka bai dena zuwa wurin sanaarsa ba ta kafinta. Da dungulmin hannun ya bude aljihunsa ya saka mai lafiyan ya zaro carbin malam ya mikawa yaran. Suna ta murna suka tafi su raba. Yayi gaba yana dan murmushin suka hada ido da wani matashi a layin. Da sauri ya taba na kusa dashi kai don ubanka kashe ga Baban yara nan. Tare suka tashi suna karkade jikinsu. Baban yara barka da yamma suka fada da ya karaso kusa dasu. Ya dan bata rai bazan amsa ba Sani. Yanzu don Allah baza kuyiwa kanku fada ba da shaye shayen nan? Ya kalli katon ciki Anas so kake ciwon babanka ya sake tashi saboda kai ko? Wanda aka kira Anas ya girgiza kai. Kayi hakuri in Allah Ya yarda bazamu sake ba. Yayi murmushin takaici Allah Ya bada ikon denawa. Kuna ta batawa kanku rayuwa a banza. Idan baku sani ba abinda mutum yayi da kuruciya yakan bishi har girma. Na tabbatar babu wanda zai so nan gaba a bawa dansa labarin ya taba busa wiwi a tarihin rayuwarsa. Sani ya dan yi murmushin jin abinda ya fada. Baban Yara ya ce au dariya na baka ko? Ya kama bakin ya murde. Muna nan da ku idan baku dena ba wata rana kwata zaku shiga ku kwanta kuce gado ne. Yayi gaba abinsa yana ta mitar halin da yara ke saka kansu a yanzu. A kantin kofar gidansa ya tsaya suka gaisa Munkaila mai shago. Mal Bashir ya dauko naira dari ya mika masa. Gashi nagode sosai. Munkaila ya karba na meye kuma wannan Baban Yara? Darin da ka bawa Zuhra mana da safe. Ina shirin fita ta tambayeni kudi zata je karbo sakamakon jarabawarta. Lokacin bani da chanji shiyasa nace ta karba a wurinka. Munkaila ya mika masa kudin, ai yau ko sau daya banga fitowarta ba. Mal Bashir ya karba ya shiga gidansa da sallama. Zuhra na yanka yakuwa taji muryar Babanta a soro. Hantar cikinta ce ta kada sosai ta tashi da gudu ta shiga bandaki. Garin sauri ta zubar da yakuwar da take yankawa. Ummanta ta soma fada ke lafiyarki kuwa. Mal Bashir ya karasa shigowa tsakar gidan. Ina ta sallama babu mai amsawa kamar babu kowa a gidan. Atine Umman Zuhra ta ce yi hakuri Baban Zuhra. Wallahi bari tayi min nake fada banji sallamar ba. Takalmansa ya cire ya zauna kan tabarmar dake shimfide a tsakar gidan. Fitsari ta bari ya matseta shine take wannan gudun ko. Umma tace anya kuwa? Hira mukeyi fa kana yin sallama ta tashi kamar wadda ta ga abin tsoro. Baban yara na jin haka yasha jinin jikinsa. Yace da Umma ta karbo sakamakon jarabawarta kuwa?Umma tana kwashe yakuwarta ta ce bana jin amma ga wasu takardu can akan taga wanda Hajara ta kawo mata dazu. Mal Bashir ya tashi ya dauko a sanyaye...ai tunda ta gudu yasan bana ma bata kitsa abin arziki a makaranta ba. Ai kuwa yana budewa yaga abin haushin da yasa rai da gani. Ta 48 tayi cikin su 52. Ransa ne ya sosu. Ya rasa yadda zaiyi da yarinyar nan. A fusace ya tashi ya tafi kofar bandakin. Zuhra me kike yi ne ya tambaya da daga murya. Daga ciki ta ce ehem ehem! Ya sake bugawa idan ba so kike na bude ki ba gara ki fito tun wuri. Zuhra ta gwammace ta yini a bandaki da ta fito ta sha fadan Baba. Ta sake cewa ehem..... ya ce bari na fita tunda mun koma wasan buya da ke. Sai da ta kara kusan minti biyar sannan ta fito duk ta hada gumi. Ta dubi Ummanta, wai yau da Baba ya kamani bansan....saukar rankwashi taji a tsakar kanta ta durkushe a kasa tare da rike kan ta soma kuka. [9/25, 2:38 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU🗿2 Batul Mamman(Mrs)💖 Baban Yara yace idan baki rufe min baki ba sai na kara miki. Da kuka Zuhra ta mike tsaye tana turo baki ko saboda rankwashin nan ba dole na kasa kokari ba. Idan kana taba min mandula oblongata dina haukacewa zanyi nan gaba kadan. Baban Yara yace kece mandular ai. Nan kika fi kauri dama. Kin iya haddace 'yan kalmonin turanci kizo kina barazana dasu kamar wata wadda tasan abinda take yi. Zuhra dai kuka ta cigaba da yi har sai da Umma tayi mata tsawa. Wallahi idan kika tara min makota yau jikinki sai yayi tsami. Jin haka ta soma tsalle tana kara kukan. Baban Yara yace bari na dauko wayar chaja na yi miki mai dalili. Ai kamar anyi ruwa an dauke haka ta hadiye kukan. Takardun jarabawarta da aka hada da report card din ya soma dubawa. Wasu har zero ta ci. Maths(lissafi) tace arbain da takwas, Arabic tace casa'in da hudu sai Hausa ta taci sabain da daya. Dama sune darrusan da suke dan taimakawa bata daukar ta karshe gaba daya. Sai ko rubutu da ta iya mai kyau idan ka gani zaka dauka na wata mai kokarin ne. Yana dubawa yana tsaki sai daga baya ya kula da yadda take rubuta suna. Kansa ya rinka girgizawa kawai don takaici. Ko shi da iyakarsa aji hudu a secondary ga shekaru sun mika amma yasan idan suka shiga aji shi da yar tasa sai yafi ta kokari. Zo nan ya yi mata tsawa. A hankali ta ja kafa ta je ta tsugunna a can gefe. Yanzu kin tabbatar duka takardun nan naki ne? Nawa ne Baba duba sunan da rubutun mana. Yace ai na duba. Wasu ki rubuta Zuhra Bashir wasu kuma Fatima Bashir don tsabar rainawa malamai hankali. Yana cigaba da dubawa yayi karo da wata. Takalminsa ya raruma ya kwada mata. Ya daga takardar yana nunawa Umma. Kinga wulakancin yar nan wai Fatima Basiru. Ya nuna kansa nine BASIRUN??? yadda yayi yasa ta soma dariya Umma tace Allah Zuhra zanci mutumcinki. Ana miki fada kina wa mutane dariya don shakiyanci. Zuhra ta kara matsawa gefe tana sharar hawaye to ba haka naji su Kawu Sabiu da Innar Ajingi suna kiranka ba. Baba ya cije lebe saboda takaici. Da kika ji sun fada ba sunan gida bane?. A nan wa kika taba ji ya kirani Basiru? Tace to yi hakuri wallahi daga yau na dena. Ki ma kara ya fada yana tattare takardun. Yana yi yana mita. Yarinya sau nawa ana miki repeating gashi kin kusa shekara ashirin. Amma kanki kamar kifi, nasan duk ajin kece mamansu ko. A'a Baba ga Hajara, ka manta ajinmu daya. Yace ina fa zan manta...an tara dakikai biyu a aji daya. Baku da aiki sai cin awara da wainar flawa. Zuhra da baki baya shiru tace to ba kai kake bani kudin ba. Umma tace kaga ka dena kula yarinyar nan sai jininka ya hau. Takardun ya miko mata jeki ki ajiye min a dakina. Ni ina ta kokarin hada kudi na biya miki kudin WAEC saboda kada a rufe amma naga kamar asara zanyi. Sau biyu kina qualifying din nan amma kin kasa hada credit uku. Zuhra tasan yadda babanta ya damu tayi karatu amma duk yadda ta dage a cewarta ko kadan bata ganewa. Zama tayi kusa dashi kaga Baba kawai ka kaini makarantar koyon sakar nan. Har na tambayo matar tace a wata biyu zata koya min sau uku a sati zani. Kuma a dubu shida. Ai kaga yafi sauki akan WAEC din. Ta nuna kanta ni da ka ganni bani da abinci a boko. Kan baya dauka yadda kasan an zuba dusa a kwakwalwar haka nake. Shi din ma ya kusa dariya sai ya dan dake. Tashi ki bani wuri ni. Ko damuwa ba kya yi yan ajinku zasu tafi makarantun gaba ke kina son koyon saka. Ta dan tura baki to ya zanyi Baba. Suma fa duk harkar ta koma satar amsa. Idan sakar ma bazata yiwu ba kawai kayi min aure ka huta. Shi da Umma a tare suka yo kanta suna mata fada. Da gudu ta tashi tayi hanyar waje tana dariya tare da jan mayafin Umma a igiya. [9/25, 2:39 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU🗿3 Batul Mamman(Mrs)💖 Mal Bashir Ibrahim mutumin Ajingi ne ta jihar Kano. Su biyar ne maza a gidansu shine na biyu. Mahaifinsu manomi ne kuma yana kiwon shanu da tumaki. Da farko sun fara karatu har ya kai aji hudu a makarantar gaba da firamare sai babansu ya matsa akan basa samun lokacin taimaka masa a gona. Shi a son ransa duk su hakura da karatun. Ko kadan Bashir baiji dadin hakan ba, sai da ya hakura shi da wansa da mai bi masa suka koma gona. Sauran biyun suka cigaba. Akayi rashin saa autanma ya dena zuwa don shi yafi son kiwo. Wanda ya karasa kuma kan nasa kamar na Zuhra. Ba wani sakamakon kirki ya samu ba. A halin yanzu ma masinja ne a wani company. Mal Bashir ya dawo birni shima aikin kafinta a nan ya hadu da Atine yar kwanar Diso ya aura.sun jima basu sami haihuwa ba gashi yana da son 'ya'ya ,sai daga baya aka haifi Fatima wadda taci sunan mahaifiyar Mal Bashir kuma sunan Atine shiyasa suke kiranta Zuhra. Zuhra na fita gidansu Hajara ta nufa tana ta mita ta jawo mata fada a gida. Da sallama ta shiga sai dai babu kowa a tsakar gidan. Daga dakinsu Hajara ta ji an amsa ta shiga. Kwalliya Hajara take yi anyi wankan yamma tana shirin fita unguwa, mudubi ne a hannunta tana zana gira. Zuhra ta sakar mata dundu a baya...shegiya kin hada min zafi a gida kin zauna kwalliya. Hajara na sosa bayanta suka ji muryar mamanta. Ta shigo dakin haba Zuhra sau nawa za'a hanaki zagi ne? Zuhra ta sunkuyar da kai tana hararar Hajara. Mama tace idan na sake ji Allah da yayanku Lawal zan hadaki. An kwana biyu ba kiji bulala ba shiyasa kika dawo da yi mana zagi. Zuhra tace don Allah kiyi hakuri na dena daga yau In sha Allah. Mama tace da kin kyautawa kanki sannan ta fita. Hajara ta cigaba da kwalliya suna hira tace ke ni fa Sahabi ya dage sai nayi karatu. Yace zai rinka yi min lesson kafin a fara WAEC don har ya biya min kudin a wata makarantar. Zuhra tayi dariya zaiyi asarar kudi da lokaci kenan. Baki fada masa kina sahunmu bane? Bana son wulakanci wallahi tunda na fahimci yana son nayi karatu na soma dagewa. Wannan karon mutum shida na doke harda ke. Zuhra ta daga hannu alamar jinjina kaga su Fropesa Hajara kenan. Hala irin su Ligan dinnan zai nema miki. Kanwar Hajara da ke tsakar gida sai dariya ta leko ta taga...Yaya Zuhra kin fiye abin dariya. Wai Ligan...Legal ake cewa. Zuhra ta hade fuska tace in ba tsoro ba ki shigo dakin nan ki fada mana kiga yadda zanyi dake. Marar kunya kawai. Hajara ma dai dariyar take ta dauko dankwali zata daura. Sai da ta daura wani dakal dakal din mayafi karami. Ta daure shi da ribbons har biyu manya sannan tayi dauri. Daga karshen daurin ta zaro wani ribbon din mai gashi dogo daga jikinsa ta makala taga ya zauna sosai sannan ta tura shi a jaka. Duk abinda take idanun Zuhra kyam a kanta. Tace Hajara gashin doki kika koyi sawa? Da sauri Hajara ta toshe mata baki. To sarkin karadi kada ki fada da karfi sai na fita zan saka. Zuhra tace wallahi babu kyau kuma kema kin sani. Ga acuci kin dora wannan wari ma ya isheki. Hajara tace ke ba yau zan saka ba fa. Yanzu ma gidan Anti Faiza zani tayata aikin abincin da zasuyi a makotansu. za'ayi party ne a gidan. To gobe zansa idan zaa wurin party din. Zuhra tace happy bazday tuyu zasu yi? Oho nima ban sani ba. Tace dai yan gayu ne a gidan. Zuhra tace duk da haka bani gashin na kona ko na fadawa Mama. Da kyar Hajara ta bata ribbon din. Za ta fita Zuhra tace ke kamar kwailin kike ko, kinga fuskarki kuwa? Sai yanzu na lura. Hajara ta dora hannu a ka. So kike dai Mama taji tayi fada kike wani daga murya. Kuma bleaching ake cewa ba kwailing ba kalmar ko dadin ji babu. Tana murmuahi tace wani mai na samu mai dan kyau na gyaran fata. Kinsan tunda biki ya matso gara na shafa na dan washe. Zuhra dai tabe baki tayi...wallahi Hajara ki kiyaye sabon Allah. Ga acuci, ga bleaching ga karin gashi. Shi Sahabin zaki ha'inta da farin karya ko danginsa. Naga dai duk a unguwar nan kuka tashi to meye basu sani ba. Karasa hada jakar tafiyarta tayi tace to malama zuhra idan kin gama waazin ki zo ki rakani bakin titi. Kuma wallahi kika fadawa su Mama sai munyi fada. Zuhra tace mun dade bamuyi ba...ni akan irin wannan ba sai dai aji kanmu ba. Lokaci guda kika tsiri irin wadannan abubuwan kawai don zakiyi aure. Hajara tace to in kinji haushi kema ki fitar da miji mana. Ran Zuhra ya soso ta dan yi murmushi miji dai Allah ke bayarwa. Kuma da yardarSa idan na tashi aure sai na sami miji na gani na fada. Daga nan tayi tsaki ta fita Hajara na kiranta tana bata hakuri. A tsakar gida suka tarar da Mama tace har anyi fadan ne kajin Mama? Ku zo nan...suna harare hararen juna suka durkusa gaban Mama. Tace duk naji abinda kuke fada. Ke Hajara akan an fada miki gaskiya kike gayawa yar uwarki magana ko? Duk canjin halin da kika koya yan kwanakin nan ina lura dake. Shiru nayi so nake farin naki yafi haka yawa sannan nasa yayyanki maza suci ubanki a gidan nan. Zuhra ta kwalo ido....lah Mama kema zagin kike yi. Mama tace ban kuma ce kiyi ba, nima kuskure ne. Ta cigaba da yiwa Hajara fada kije gidan Yayar taku ki dawo zanyi maganin rawar kan nan naki. Ita ma ba kyaleki zata yi ba kin sani sarai. Idan na sake jin kuna fada kuma ni daku ne. Ki wuce ki rakata ta hau adaidaita tace da Zuhra. Sum sum suka tashi suka fita. Zuhra ke rike da jakar kayan amma har suka je titi ko tari basuyi wa juna ba. Sai da adaidaita sahun ya fara tafiya Hajara ta leko tana dagawa Zuhra hannu. Itama dagawa take tana tambayarta yaushe zaki dawo. Hajara tace sai yanzu zaki tambaya? Kwana goma zanyi.....Zuhra harda dan hawaye ta koma gida. Irin wannan fadan sun saba yin shi da Hajara. Sai dai suna sake haduwa zancen ya wuce kenan. [9/25, 2:39 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU🗿4 Batul Mamman(Mrs)💖 Hajara na sallama gidan yayarta ta hadu da babban dan Anti Faiza Abba zaune a bakin kofar gida. Hannunsa ta gani a nade alamun gyaran karaya ko gocewar kashi. Yana ganinta ya rungumeta A dan tsorace tace Babana me ya sami hannunka? Yace fadowa nayi daga kan babur din Baba. Ba dai hatsari kukayi ba ko ta tambayeshi suna shiga cikin gidan. Yace a'a jiya ne da daddare na hau sai na fado. Anti Faiza na jin muryarsu ta fito tana mata sannu da zuwa. Tace kafin ki fara korafi jiya abin ya faru ni kuma bana son tadawa Mama hankali sai ya dan ji sauki. Hajara tace ba komai Allah Ya sauwake. Sauran yaran uku suka zo suna mata sannu da zuwa. Mai bin Abba ce ta kalli Hajara da kyau sai tace Anti Hajara kinga fuskarki tayi fari, kafarki kuma baka. Ko kema mai bleaching ce irin ta fim dinnan.... Gaban Hajara ya fadi, Anti Faiza ta bar raba kayan wanki da take yi tace bazaki make mata baki ba kina jin abinda take fada. Nabila ta ce Allah ki kalli kafarta da fuskarta ki gani. Anti Faiza ta taso zata kaiwa Nabila duka sai taga Hajara na jan siket dinta tana kara rufe kafa. Anti Faiza tace su fita tana mata wani kallo. Gaba daya cikin Hajara ya duri ruwa. Tun kafin ta tambayeta tace wallahi Mama tayi min fada dazu kuma bazan kara yi ba. Anti Faiza tace da kina hauka ne kika fara shafe shafe. Ta fizge jakar kayan Hajara ta zazzageta a wurin tana duba kayan tana fada. Hajara a hankali ta gode Allah da Zuhra ta karbi ribbon din mai gashi a jiki. Anti Faiza kuwa ta kare mata tas sannan tace ke da Zuhra kuke yi ko? Hajara tana matsar kwalla tace a'a ni kadai ce. Ba wani nan, abokin barawo ai barawo ne kuna tare wata rana zata koya ne. Ta fara laluben wayarta. Zan kira Umma ince a turo min ita ko zuwa asabar ne in ja muku kunne da babban baki. Ba don hannun Abba ba ai gidan zani na hada ku. Wato kun girma zaku nunawa duniya baku da mafadi. Ita dai Hajara sai bada hakuri take. Bayan kwana biyu Zuhra na zaune kan karamar kujera a kofar kitchen Umma na ciki tana duba miya da yar karamar fitilarta gwamnati ta gaza. Zuhra ta rike ciki ta fara waka. Dan kanzo Iya ko dan dago dago Iya yunwa bata da hankali Iya yunwa taci mutum tara Iya..... Umma tace Zuhra ko in miko miki kwano ne? Ta washe baki Umma kin gama girkin. Umma tace a'a wai da ki tafi makota bara. Baki Zuhra ta turo tana rike ciki ni shiyasa bana so kice zakiyi girki Umma musamman tuwo sai ki dade. Miyar nan tun kafin magariba kika dora gashi har an idar da isha. Umma tace ni kuma kinga bana son danyen girkin nan naku. Sai ayi tuwo da miya cikin rabin awa. Suna magana Baban Yara ya shigo. Zuhra tana matse ciki tana masa sannu da zuwa. So take yasa Umma ta kada miyar haka. Dariya yayi musu ya shige ciki. Ga mara juriyar yunwa , ga mai dadewa a girki. A falo suka zauna suna ci. Da yake ba wuta Zuhra kasa jira tayi nata tuwon ya huce tasa mafici tana fifitawa tana ci. Ta cika baki da tuwo tace Ummana kin iya girki sosai sai dadewa. Umma tace bazaki yaba min ba sai kin hada da mita. Wannan mijinki sai yayi da gaske wurin noma. Baba yace to dai kada ki takurawa babata. Ya fito da wata leda daga aljihunsa. Ya danne ta da dungulmin hannunsa sannan ya bude da dayan ya dauko gasashshiyar kaza. Umma tace yau dadi zamu ci BabanZuhra. Yace Ya'u ne ya siya shine ya debar min yace na kawowa Zuhra. Dadi ya kamata taje ta durkusa a gabansa. Cinya ya dauko mata da fikafiki biyu. Ta karba da murna ta koma wurin zamanta. Kamar ance ta daga kai ta hango hannuwan iyayenta a gefen kwano suna kokarin raba wuya su ci. Duk zumudin da take a lokacin wani daci taji a wuyanta. Hawaye ya sauko mata tayi saurin gogewa. Ta dan gutsiri naman kadan tace washhhh. Umma tace kin kone ko? Dama cin abinci kin kasa jira ya huce. Zuhra tace hakori na ne yake min ciwo daga nasa naman a baki. Baba yayi mata sannu. Ta tashi ta mayar da duka naman gashi ku cinye bakina zafi. Baba yace ki ajiye zuwa gobe mana. Idan ya lalace ai sai nayi kuka Baba. Ta dauki tuwon bari na kai kitchen bazan iya ci ba. Ta fice tana fifita baki. A bakin rariya ta tsuguna ta cinye tuwonta ta wanke baki. Umma tace ya naji shiru ko bakin ne. Tace a'a almajiri na nema a waje. Wuraren shadayan dare su Umma sun kwanta Zuhra ta lallabo ta fito falo. Tayi sa'a kuwa ledar naman tana nan kan dan tebur din da suka ajiye tare da jug din ruwa. Zuhra ta bude ledar a hankali ta sami yan kasusuwan da basu cinye ba duk ta tsotse don naman yayi mata dadi. Baba ya taso Umma suka tsaya ta yar kofar jikin tagar dakinsu suna kallonta. Hawaye Umma take sosai a hankali tace bar mana tayi muci. Baba yace muna tausayinta tana tausayinmu. Allah Ya albarkaci rayuwarki Fatima. Suka koma suka kwanta. Da safe Umma ta riga ta tashi. Ta fito suka gaisa ta dauko tsintsiya zata fara shara. Umma tace kamar na bar ledar naman nan a falo. Zuhra ta dan tsorata sai tace ai da asuba na dauke saboda beraye. Umma tayi murmushi kawai ta fita tsakar gida. [9/25, 2:39 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿5 Batul Mamman(Mrs)💖 Kafin karfe tara ta gama duk ayyukan da zata yi. Wanka tayi sannan tayi shirin islamiyya tunda asabar ne ana yin ta safe. Ta gama shirinta tsaf ta yiwa iyayenta sallama ta tafi. A darasi na uku Malama Rabia ta shigo. Ita kadai ce mace da ke koyarwa a islamiyar tana koya musu Nahawu. Zuhra jira tayi sai da aka kammala darasin gaba daya sannan tace tana da tambaya. Yan ajin har sun soma dariya sannin halinta. Wata tambayar idan tayi sai kaji kamar shirme. Ita kuwa sai ta dake, sai an bata amsa tace nasan ku ma kun karu. Malama Rabia tace ina jinki Fatima. Zuhra tace menene hukuncin macen da ke karin gashi ko bleaching a musulunci. Malama tayi dan murmushi ai hukuncinsu a bayyane yake, babu kyau. Zuhra tace ai nima nasan babu kyau ina nufin akwai wata aya ko hadisi da yayi nuni an hana ko kuwa fatawar malamai ce kawai. Malama Rabia tace to bari mu fara da maganar karin gashi tunda shi tabbas akwai ingantattun hadisai a Sahihul Bukhari da Sahihul Muslim da suka nuna anyi hani da yinsa. Manzon Allah SAW yana cewa Allah SWT Ya tsinewa mai karawa wata gashi da wadda tace a kara mata. Ki duba hadisi na 5934 a Bukhari da 2122 a Muslim. A wani hadisin kuwa, Asma'u bint Abubakar(RA) tace wata mata tazo wurin Annabi SAW tace masa ta aurar da yarta amma lalura tasa gashin kan yar ya zube. Shin zata iya saka mata gashi? Sai Annabi SAW yayi kashedi ga mai karin gashi da wadda aka karawa. Bukhari 5479, Muslim 3962. Malamai sun dauki karin gashi a matsayin yaudara sannan suka yi hani dashi. Akwai hadisin Mu'awiyya RA wanda yace Annabi SAW yace karin gashi yaudara ce. Sahihul Bukhari 3229. Ta koma ga sauran daliban gaba daya. Ku kanku a ma'aunin hankali kunsan cewa akwai ha'inci a karin gashi. Banda asarar kudi da kuma warin da yake yi a kan mai sawa. Sannan duk mai karin gashi bata taba rufe kanta gaba daya domin tayi ne don a gani. Asali ma a shekarun baya muna ganin mace da karin gashi mun san ba musulma bace. Sai gashi a hankali mun dauki al'adu da dabiun wasu muna yi. Allah Ya shirye mu baki daya. Sai tambayarki ta biyu akan masu shafa mai su canja kalar fatarsu daga baka ta koma fara. Wasu masu zalamar ma fararen ne suke kara kode fatarsu. To duk wannan yana cikin nau'in canja halitta wanda Allah Ya hana. Shaykh Ibn Uthaymeen yayi bayanin canja kalar fata na dindindin kamar bleaching a matsayin laifi kamar masu yin tatoo(zane da wuta ko abu mai kaifi a jiki) da kankare hakori ayi wushirya. Irin wadannan laifukan Annabi SAW ya sanar damu tsinuwar Allah ta tabbata ga masu yinsu. A bangaren lafiya kuwa munsan cewa babu wani nauin bleaching wanda bashi da illa ta kusa ko ta nesa. Wanda munsan Allah Ya hana mu cutar da kawunanmu. Ga zubar da mutumci da kimar mai yi a idon wadanda suke da hankali suke amfani dashi. Ga asarar kudi da sauran abubuwa marasa kyau. Allah Shine mafi sani daga kurakuran da muke aikatawa. Allah Yasa duk abinda zamuyi mu tsaya a iyakar da Yayi mana. Laifukanmu kuma Ya Yafe mana. Gabadaya ajin suka ce Amin. Jikin yan matan duk yayi sanyi saboda ba'a rasa masu dan shafe shafe da masu dora gashi ko da a jikin acuci ne irin na Hajara. Zuhra tayi godiya ga Malama Rabia sosai. Duk bayanan da tayi kuwa ta rubuce su a yar takarda wanda zata nunawa Hajara shaida. Ta so ace Hajarar na nan tayi tambayar. Daga kofar daki 'yan matan biyu suka ce Mama mun tafi. Ba tare da ta dago kanta daga laptop din gabanta ba tace Allah Ya kiyaye hanya ku gaishe su. Shiru taji ba amsa...tana dagowa taga sun tafi. A ranta tace na rasa saurin me yaran nan suke yi haka. Hajiya ta fito daga dakin Alhaji taji karar mota. Sauri tayi kada su tafi ta basu sako su siyo mata a hanya idan suna dawowa. Kayan da ta gani a jikin Adabiyya ne yasa ta kara sauri tana kwala musu kira. A tsorace Adabiyya mai shirin shiga mota ta juyo. Hamida tace shikenan mun gama yawo. Ko kadan ba haka suka so ba. Hajiya na dakin Alhaji suka ki zuwa yi mata sallama. Ita kuma Mama daga bakin kofa suka yi mata basu bari iyayen nasu sunga kayan jikinsu ba. Hajiya ta fito har wajen rai a bace tace duk su shigo ciki. Mama ta fito daga daki tace Hajiya lafiya? Kafin ta bata amsa yaran suka shigo. Ya Salam...Hamida? Adabiyya? Meye hakan kuma? Hajiya tace kema basu ce miki zasu tafi ba ko. Nima karar mota naji na fito da sauri ashe rabon idona ya gane min ne. Hamida yar shekara ashirin da biyu jeans ne a jikinta da top wadda ko rabin cinya bata rufe mata ba. Duk ta dameta sai tayi rolling da karamin mayafi. Adabiyya mai shekaru shatara kuwa skirt ne a jikinta amma itama ya matse har shatin pant dinta ake gani. Shima don tafi yayarta jiki ne ta saka. Sai riga matsatstsiya karama har da wata belt a samanta an kara tamketa. Da dan karamin mayafinta. Hajiya ta kalli yayansu Nura. Kai mahaukacin ina ne da kana ganin sun fito a haka kake shirin jan mota. Ku fada min gaskiya ina kuke shirin zuwa. A tare suka ce gidan Yaya. [9/25, 2:39 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU🗿6 Batul Mamman (Mrs)💖 Mama tace ni na rasa gane me ake yi a gidan Yayan naku ne? Jiya kunje kun ce aiki zaku taya Izzatu yau ma kun ce aikin zaku kara yi. Ko packing suke yi ne zasu tashi bamu sani ba, ta zauna akan kujera kusa da Hajiya tace ni a iya lissafi na ma ai sai karshen August za'ayi birthday din Nana. Kuma ita ce ta rage anyi na yayyenta. Hajiya ta tabe baki kina ma kokarin rikewa. Sun mayar da birthday tamkar wata ibada. Duk shekara sai anyi sau uku a gidan. Allah Ya kyauta. Mama ta ce Nura fada min gaskiya me ake yi. Indai birthday ne an saba yi mun kuma hakura mun zuba ido. Tunda shima Hamzan bai ji maganar mu su dena ba ai matarsa bazata ji ba. Shiru yayi har sai da Hajiya ta daka masa tsawa...baka ji ana tambayarka ne? Adabiyya ta soma kuka dama ita akwai tsoro tace Hajiya party din wedding anniversary zasu yi na shekara goma da aure. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun shine abinda su Mama ke fada. Hajiya ta mike tsaya tana magana a hankali...lalacewar Yayanku har ta kai nan? Allah Ya shirya. Daga nan dakin Alhaji ta koma ta cigaba da gyarawa. Mama ta dubi yaran. Yanzu don Allah waye ya ce ku saka irin kayan nan? Yaushe ma kuka siya? Adabiyya tace jiya da muka je ne Anti Izzatu tace kananan kaya zamu saka yau. Shine muka ce bamu da masu kyau. Sai ta kaimu wani kanti ta siya mana. Mama tace eh lallai yarinyar nan bata nemawa kanta zaman lafiya a gidan miji. Shirun da taga munayi don bama son zama iyaye masu sa ido a lamarin gidan 'ya'yansu ne. Amma wallahi idan na bullo mata ta bayan gida sai ta gane karyar rayuwar turai take yi. An gayyaci su Mariya? Hamida tace eh duk su biyun. Har Yaya Ibrahim ma an gayyace shi da Anti Umma. Mama tace suma duk kananan kayan aka ce su saka? Hamida tace bamu sani ba. Mu da kannenta tace mu saka dai jiya. Mama tace duk su je su canja kaya tana zuwa. Nura yace harda ni Mama? Ta harare shi ban sani ba. Dakin Alhaji ta shiga ta tarar da Hajiya a zaune a kan gado tana kuka. Mama tace haba Hajiya kukan iyaye ga 'ya'yansu bai taba zama alkhairi ba. Hajiya ta share hawaye da gefen dankwali. To ya zanyi Kaltume? Yaron nan ko kadan ban goyi bayan zuwansa Canada karatu ba amma Alhaji ya dage. Karshe yaje ya hadu da mata itama tashin can. Mama tace shekara hudu fa kawai suka yi da babanta yaje aiki. Hajiya tace to ai dai ta zauna ko. Gabadaya sun dauko wasu al'adu daban da namu. Wadanda basu dace da addinmu ba. Kina kallo duk shekara sai sunyi party nasu da na yaransu. Sati kusan uku da suka wuce ba ya kawo mana laces ba wai na Mother's day. Na Alhaji kuwa na Father's day ai kinga bamu taba gaya masa dalilin bayarwa ba kila da zaginsa zaiyi ma. Duk wata rana da turawa suke bawa mahimmanci Yaya da matarsa suna yi. Ko da ba kowanne muke gani ba amma munsan anayi. Su a dole rayuwar turawa sukeyi. Mama tace kiyi hakuri yanzu zan kira shi a waya yazo. Dole mu sake masa magana ko mu hadashi da Alhaji. Wannan karon sun wuce gona da iri tunda suna son batawa yaranmu tarbiya. Hajiya tace Allah Ya shirya mana. Amma don baki ji yadda raina ke baci ba idan su Khalifa na kirana Granny dinnan. Mama ta kwashe da dariya. Ai gara naki ma. Nida ake kira Grams fa. Yau da bamuyi boko ba ai da mun sha kunya tunda sai kiyi musu magana ma amma su amsa da turanci. A dole sai an bambanta su da 'ya'yan yan uwansu. Sani masinja ya dauki wayar landline din office dinsu da aka kira. Muryar mace yaji tace matar Hamza ce. Ji yayi tana kuka tace ya fada masa Junior ya fado daga kan kujera ya karye a hannu. Sani ya tashi da sauri sai ya tuna meeting din da suke yi mai mahimmanci ne. Har ya koma ya zauna ta sake kira a fada masa yanzu ya taho gida. Ta kira wayarsa a kashe. Dole Sani masinja ya shiga hall din da ake meeting din. Architect Hamza Nasir Hamza ya juyo a fusace yace meye haka Sani? Manyan baki gareshi turawa masu son hadin gwiwa da kamfaninsa na zane da ginin gidaje da hotels da sauran manyan gine gine. Sani masinja yace ranka ya dade uwargida ce ta bugo tace Jiniya ya fado daga kan kujera ya karye a hannu. Hamza ya tashi da sauri....what? Ya dubi bakinsa yace da turanci kuyi hakuri dana ne ya karye a hannu. Sun tausaya masa suka ce zasu dawo a karasa meeting din. Amma ya daure yasa hannu a takardar shaidar amincewarsa da sharudansu. A gaggauce ya karanta ba tare da ya fahimci kalma ko daya ba yasa hannu a duka biyun. Daya tasu dayar ta kamfaninsa. Sunji dadin amincewarsa sosai suka tashi. Yana ta sauri a hanya wayar Mama ta shigo. Ya dauka a gigice a zatonsa Izzatu ce. tace Yaya kana ina ne? Mama ke ce? ina hanyar zuwa gida. Tace to maza kazo ina son ganinka. Yace Mama Izzatu bata kiraku bane? Junior ne ya karye a hannu. Yana hango wani dan sanda ya nufo motarsa saboda yana amsa waya yana tuki da gudu yaja motar kafin a bada hannu har ya kusa karawa wani. Mutane suka bishi da zagi da bakaken maganganu. Mama ta dubi Hajiya tace bamu ga ta zama ba wai Junior ya karye a hannu. A tare suka fito daga dakin suka kiran Nura yazo ya kaisu gidan Yaya. Hamida tace Mama me ya faru? Junior ne ya karye a hannu. Yanzu yayanku yake fada min. Adabiyya tace ba gaske bane. Jiya ne Anti Izzatu tace bata san da yadda zata sa Yaya ya baro office da wuri ba. Partyn surprise take son yi masa. Bai san komai game dashi ba. Ana haka wata makociyarsu da aka bawa aikin meatpie ta shigo take cewa danta ne ya karye kuma ya kwana da zazzabi shiyasa bata aiko ta karbi kayan yin meatpie din ba. tana fita ne shine Anti tace ta sami idea din abinda zata fada masa. Hajiya ranta ya kara baci. Mama kuwa ashar ta dannawa Izzatu saboda yadda zuciyarta ke mata zafi. Ta kalli su Hamida duk sun saka material ne da mayafansu manya tace Nura ya kaisu amma ya fadawa Yaya tana son ganinsa komai dare. Sai bayan fitar bakin sakataran Hamza yana hada takardu ya duba wadda ya saka hannu a kai. Jikinsa ne ya fara rawa ya soma salati. Wani cikin yan office din yace menene. Inuwa Sakatare yace ai bana jin oga ya karanta takardar nan da kyau. Ta nuna ya amince ya karbi kudin da suka bashi saboda haka nan da wata shida duk ribar da aka samu tasu ce. Daga wani wata shidan kuma sai su rinka raba ribar gida uku. Su kaso biyu shi kuma daya. [9/25, 2:41 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿7 Batul Mamman(Mrs)💖 Alhaji Nasiru Hamza dan kasuwa ne mazaunin Kano amma asalin iyayensa mutanen Kumo ne na garin Gombe. Sana'ar siyar da shanu da tumaki ya fara wadda a hankali har ya fara fitar da fatar dabbobin kasashen waje yana sayarwa. Shiyasa ma aka fi saninsa da Nasiru maifata. Halima wadda suke kira Hajiya ya fara aure yar kanwar babansa. Sun fara zama a Kumo kafin kasuwancinsa ya bunkasa ya dawo Kano. Lokacin ta haifi danta na fari Hamza suke kiransa da Yaya. Suna zamansu lafiya da mijinta. Kuma suna yawan zuwa gida ganin iyayensu. Hamza na da shekara biyu ta haifi Ibrahim sai Mariya. Alh Nasiru ba karamin soyayya yake nunawa yaransa ba. Yana da amini kuma abokin kasuwanci Alh Sabiu. Kowa ya sansu tare hatta iyalinsu suna mutunta juna. Matan Alh Sabiu biyu. Kaltume ce uwargida sai Sahura. Kaltume bata taba haihuwa ba a shekarun da sukayi da mijinta. Tana dai karatu a lokacin. Ita kuwa Sahura 'ya'yanta shida. Da kamar gaske suke zaman lafiya. Sai daga baya Sahura ta rinka daukar zigar yan uwa da kawaye ta fara yiwa Kaltume habaici da gorin haihuwa. Tun bata kulawa har dai ta fadawa mijinsu akan ya yiwa Sahura magana sai cewa yayi ai ba matsayinsu daya ba. Idan taji haushi ta haihu mana. Da kadan kadan suka juya mata baya. A lokacin tayi shawara ta sanar da Halima halin da take ciki lokacin tana da ciki na hudu. Ita kuma sai ta fadawa mijinta. Ko kadan Alh Nasiru baiji dadin faruwar hakan ba. Ya zaunar da abokinsa yayi masa nasiha. Sai dai duk a banza. Wata rana Kaltume zata tafi makaranta ta shirya ta rufe dakinta sannan ta leka dakin Sahura tace ta fita. Tana dawowa da yamma ta tarar da Alh Sabiu da Sahura har da wasu makota a kofar dakinta. wasu samari ne suke kokarin balle kofar. Kaltume duk ta rude ta tambayi abinda ke faruwa. A madadin amsa sai mari da duka da Alh Sabiu ya rinka kai mata. Sahura na kuka tace muguwa saboda baki haihu ba shine zaka kashe min nawa 'ya'yan. Tunda kika fita nake neman Ihsan banganta ba. Sai dazu kawai naji kukanta a dakinki. Ba yadda banyi ba na kasa budewa, tun tana kuka har muka ji shiru. Ta cigaba da kuka ina jin ma ta mutu Alhaji. Shi kuwa sai dukan Kaltume yake har sai da aka bude dakin. A kwance suka tarar da Ihsan yar wata takwas. Sahura tace ai kawai ta mutu ko ta suma. Alhaji Sabiu ya cire babbar rigarsa yana ta dukan Kaltume. Babu mai hanashi har Allah Ya kawo Alh Nasiru. Yayi ta rokon abokinsa amma sam yaki dena dukanta. Alh Nasiru ganin babu yadda zaiyi ya ja hannunta. Sahura tace shikenan Alhaji dama tunda yake kare mata kwartonta ne. Ji yadda yake rike mata hannu a gabanka. Alh Sabiu yace ko Sahura, to ke Kaltume na sakeki saki uku in kin gama idda ki auri kwarton naki. Kai kuma Nasiru bani ba kai. Da haka abokan suka rabo. Ashe mukulli Sahura ta sata na Kaltume ta durawa yarta maganin bacci ta kaita dakin. Halima taji tausayin Kaltume sosai barin ma da aka rinka yadawa a gari abokin mijinta ne kwartonta. Gashi ya gujeta bayan aurenta ya mutu. shi kanshi sai da abin ya shafi kasuwancinsa. Sai da ta kai ko makaranta ta dena zuwa. Har yan uwanta wasu suna kyamarta. A wannan halin ne Halima ta bawa mijinta shawarar ya auri Kaltume domin ta tsira da mutumcinta. Da kyar Kaltume da Alh Nasiru suka yarda. Bayan anyi auren saboda Halima ta lura Kaltume na son 'ya'ya ta dauki Hamza da Mariya ta kayansu ta mayar dakin Kaltume. Wannan abu ya kara musu zaman lafiya sosai. Kaltume har kullum bata yiwa Halima kallon kishiya sai yar uwa. Haka suka zauna lafiya Halima ta haifi Jidda. Daga nan Kaltume ita ta sami ciki ta haifi Nura da Adabiyya. Sannan Halima ta haifi auta Hamida. Gidansu abin sha'awa saboda kan 'ya'yan a hade yake. Daga baya asirin Sahura ya tuno Alh Sabiu yaji tana bawa yarta labari. Har gida yazo bawa Kaltume hakuri domin ya gane bai kyauta ba. A yanzu ma dai komai ya sukurkuce musu shi da Sahura don yaran babu wani mai abin kirki gasu har su shadaya. Tun daga farkon layin gidansa yake hango motoci. Hankalin Hamza ya sake tashi sosai. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun kawai yake fada. Shikenan Junior ya rasu.........jikinsa duk a mace yayi parking din motarsa daga can baya ya fito. Sai kawai ya kasa karasawa gidan. Kifa kansa yayi a saman motar. A wannan yanayin Ibrahim ya iso. Yana neman gurin parking don layin ya cika ya hango yayansa a tsaye ya kifa kai. Ibrahim ya fito da sauri da matarsa Ummahani da yaransu uku. Hannu yasa ya taba Hamza a kafada. Hakan yasa ya juyo da sauri. Muryarsa a raunane yace ashe kuma kunji. Ummahani tana gaishe shi yace mata shiga ciki Umma ai dukkanmu mukayi rashin. Ibrahim yace rashi kuma Yaya? Nifa tun jiya Izzatu tace muzo da yara yau. Nayi tunanin irin partyn da kuka saba ne na kawo su don kada ace ina raba zumunci. Amma wallahi barnar kudin naka tayi yawa. Hamza yace ina maganar party Ibrahim. Junior ne ya rasu. Baka ga mutane da yawa ba. Ummahani na kokarin bude gate Junior ya bude tare da wasu yaran. Sun sha sababbin kaya. Hamza ya kura masa ido sannan ya dubi Ibrahim. Ibrahim yace kai wa ya fada maka ya rasu? Hamza a rikice yace Izzatu tayi waya Office tace a fada min ya karye a hannu. To ina zuwa naga motoci nayi tunanin ya rasu ne. Ibrahim yayi tsaki cike da bacin rai yace Allah Ya kyauta ni na tafi. Zuciyarsa na kuna yaja motarsa yayi gaba. Ace babban mutum kamar Yaya dan shekara talatin da bakwai ya bari mace na karanta masa yadda zasuyi rayuwa. Kodayake ba laifinta bane. Tare suke yin komai. Daga nan Ibrahim gidansu ya tafi. A hankali Hamza ya tura karamar kofar gate din ya shiga. Kawai sai ji yayi mutanen wurin sun ce SURPRISE!!! farfajiyar gidan ya gani ya sha kwalliya an jera kujeru da tebura. Ga fitilu suna ta haskawa an kunna inji. Kida aka kunna yana tashi a hankali. Bai gama tantance abinda ke faruwa ba Izzatu taja hannunsa suka shige cikin gida. Muje ciki ka canja kaya. Suna shiga daki ta rungume shi. ....HAPPY ANNIVERSARY MY BABY. [9/25, 2:51 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿8 Batul Mamman(Mrs)💖 Hamza ya yiwa Izzatu kallon rashin fahimta. Izzy me yake faruwa ne? Kince Junior ya karye but it seems lafiyarsa kalau. Fari tayi masa da ido irin yadda tasan yana kara dauke masa hankali, sai a lokacin ya kula da kayan jikinta. Wani irin yadi ne mai matukar santsi aka yi mata doguwar riga wadda ta dameta daga sama har gwiwa sannan ta bude sosai. Ga wani abu kalar takalminta da sarka anyi mata dauri. Tamkar wata amarya ta fito. Jikinta mai kyau ne ba kace ta haifi 'ya'ya uku ba. Tana lura da yadda yake binta da kallo tayi murmushi. Dama nayi ne kawai don ka dawo gida akan lokaci. Na gama komai na shirya mana anniversary dinmu na shekara goma. Ya shafi gefen fuskarta amma Izzy ba kya ganin abin ya danyi yawa. Ki ce dana ya karye kinsan zan tsorata. Kiss tayi masa a kumatu to yi hakuri daddyn Junior. Kaga ana jiranmu a waje. Tare suka fito rike da hannun juna. Sunyi matukar kyau sosai ga yaransu suma sun sha ado. Babban shekararsa biyar suna kiransa Khalifa mai sunan Alhaji Nasiru. Sai Junior mai shekara uku sunan baban Izzatu gareshi Sunusi sai kuma Nana(Halima) mai neman shekara ta biyu. Sunan Mama yaso saka mata sai dai Maman taki saboda Ibrahim da Mariya duk sunyi mata takwarori. Hajara tana ta binsu da ido duk inda suka yi ana ta gaisawa da daukar hotuna. Ga masu rabon abinci suna ta yi su ma. Tace kai Anti Faiza ina ma Zuhra tazo muci son ran mu. Ji kaji kamar su suke kiwonsu. muma dai Allah Ya bamu kudin nan muji dadin rayuwa mu rinka party duk shekara. Mariya tace ba amin ba kanwata. Anti Faiza da Hajara suka juya suna kallonta. Hajara tace kinji min mata da bakinciki. Faiza ta kai mata duka to shashasha baki san mutum ba zakiyi rashin kunya, yi hakuri baiwar Allah. Ko ba'a fada ba daga shigar Mariya an san tana da kudi. Murmushi Mariya tayi ba komai ke dai kiyi adduar arziki mai albarka ba na party ba. Daga nan ta tashi ta hada kan 'ya'yanta sukayi waje. Haka aka cigaba da taro har wurin karfe takwas na dare. Nura ne suna shirin tafiya dasu Adabiyya yazo ya fadawa Hamza sakon Mama kan cewa tana son ganinsa a yau. Sai bayan fitarsu ya duba agogonsa. Subhanallah ya fada da karfi tare da mikewa. Izzatu tace yaya akayi? Ya nuna mata lokaci. Kinga har lokacin isha yayi bamuyi magriba ba. Ta dan tura baki idan an watse ba sai muyi ba. Bana son a fara shiga ciki ne azo a bata min toilets. Hamza yace ni dai bani key please. Ta dan daure fuska Allah bazan bayar ba. Kana shiga mutane zasu fara bin bayanka. Ya girgiza kai yana murmushi Izzy baki da dama. Wani famfo ya zagaya a bayan gidan yayi alwala sannan ya fita masallaci. Duk lalacewar lamarinsa bai tashi da tarbiyar sakaci da sallah da gangan ba. Ana gyaran wurin jamaa sun watse sauran kadan Hamza ya fito zuwa gidansu. Izzatu ta bashi manyan kuloli cike da abinci, nama da snacks. Ga katon din juice da na ruwa ya kaiwa su Hajiya. Kula daya ya dauko maigadi ya biyoshi da sauran. Da sallama ya shiga babban falon. Mama da Hajiya ne a wurin sai Jidda da ta biyo su Nura tana jiran mijinta. Duk suka amsa sallamarsa sannan Mama tace maraba da Mungo Park. Turus Hamza yayi ya kasa furta gaisuwar da yake shirin yi musu. Hajiya tace Jidda tashi mu shiga ciki uwa da danta zasu gana. Dama zamanta a wurin ta kara tunzura mama da bayanin abinda ya faru a wurin partyn. Hamza yayi murmshi da wuya kaga fuskarsa a hade sai dai idan yana cikin tashin hankali. Mama nasan nayi laifi ko baki fada ba. Amma wallahi nima bani da masaniyar wannan party din. Surprising dina tayi nima. Mama tace ai naga alama. Zaka ce iyayenta basu da labari ne? Ka hado kuloli ka kawo wa mayunwatan iyayenka abinci ko. To duk ka kwashe abinka bama so. Yace Mama ita da kanta ta bani na taho dashi. Tace kaga ni ba wannan ke gabana ba kaji ko. Yanzu don Allah Yaya yaushe zaka san ka girma? Wace irin rayuwa ce kuka daukarwa kanku kai da iyalinka. Kanka aka fara zuwa kasar waje karatu ne da zaka dauko al'adun da ba naka ba kayi ado da su. Sau nawa muna yi maka fada ni da Hajiya akan birthday partyn da kuke wa yaranku duk shekara amma ka share. Irinsu valentine dinnan ma duk kuna yi ko? Shiru Hamza yayi don yau kam ya san ya batawa Mama rai. Tace ba tambayarka nake ba. Yace munayi. Ta cigaba da fada....duk wani dan iskan day da yahudu da nasara ke girmamawa kaima ka girmama. Ka iya kashe kudi mai tsoka ka shiryawa yara party kawai don suji dadi. Irin sadakar nan ta abinci ko kudi kuwa sai karshen ramadan. Baka tunanin halin kuncin rayuwa da mutane ke ciki yanzu. Alhamdulillah muna da rufin asiri ci, da sha da sutura babu wanda Alhaji baya saukewa amma ai ihsani yana da dadi ko. Ko kasan duk wata sai Ibrahim ya kawo buhun shinkafa gidannan sannan ya bamu dubu biyar biyar ni da Hajiya. Ya san ba kudin ko abincin muka rasa ba. Amma yana neman albarkar iyaye. Mariya da Jidda suma suna nasu kokarin da dan abinda sukeyi. Duk cikinsu kafi kowa morar Alhaji kuma ka fisu kudi amma daga kai sai iyalinka. Kawaici kawai mahaifinka yake maka irin na bafillatani amma ko kadan baya jindadi. Shin ka taba zama ka tambayeshi a halin da kamfaninsa yake ciki? Ko ka tambayi Hajiya me take bukata ko da ba na kudi bane? Hamza ya girgiza kai a hankali. Mama bata san cewa tana fadan ma hawaye take yi ba. Tace to girma ya kama babanku. Ibrahim lecturer ne amma daga wurin aikinsa yana zuwa kamfanin taya shi aiki. Nura yanzu yake ajin karshe a jamia amma tun yana level one yake zuwa. Hamza yayi mamaki wai Nura har ya kai level four yanzu sai dai bai nuna ba kada fadan ya karu. Ita kuwa Mama cigaba tayi da fadanta. Yan uwanku na Kumo makusanta. Ina nufin yan uwan Hajiya da na Alhaji kasan halin da suke ciki? Ko kasan a rage maaikatan banki harda kanin Hajiya. Hamza ya dago kai wanne? Tace Nafiu. Gashi yana da mata biyu da 'ya'ya goma sha uku. Watansa kusan bakwai ba aiki. Akan Nafiu Hajiya ta soma kukan rashin taimakon da kake yi. Maganganun sun ratsa Hamza sosai. Ji yayi kamar wanda aka tasa daga bacci. Mama tace ni dai lahirarka nake duba maka Yaya. Rayuwarka nema take ta sauka daga turbar addini. Har yau ban manta yadda Izzatu tasha maganin hana haihuwa ba wai sai ta gama karatu. Allah ne ma Yaso kuna da rabon haihuwar daga baya. Ka tashi ka je ka bawa Hajiya hakuri ka tafi dare yayi. Hamza yayi godiya sosai tare da sake bata hakuri. Har ya kai bakin kofa tace Yaya....naam ya amsa. Nasan saura baifi sati biyu ba birthday din Nana. Kwana hudu kafin ranar ka dawo dasu nan. Wallahi ka sake celebrating birthday a gidanka zaka ga fushina sosai.. Allah Yayi muku albarka [9/25, 2:51 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿10 Batul Mamman(Mrs)💖 Zuhra ta shigo layin gidan Anti Faiza sai ta hango mai tsamiyar biri yana turawa a baro. Tsallakawa tayi bangaren da yake zata siyo. Dama tana ta tunani yar tsarabar da zata kaiwa su Abba. Hamza da Izzatu suna mota suna hira tana fada masa Inuwa sakatare ya kira yaji ya jikin Junior fa. Dariya sukayi yace kin mayar dani makaryaci dai. Khalifa ne ya hauro daga baya ya dawo gaba ya zauna kusa da Izzatu. Ta juya ta harari maiaikinta. Ke Tala garin yaya kika bari ya taso har ya dawo nan. Oya Khalifa koma wurin zamanka. Ko kulata baiyi ba yace daddy ka kawo na tayaka driving. Hamza yace not today Khalifa kaga anyi ruwa jiya titin babu kyau. Kuma akwai mutane a nan. Khalifa yace ko sau daya ka bari na dana. Izzatu ta kama shi zata mayar bayan mota yasa ihu tare ta riko wuyan Hamza. Iyakar karfinsa yasa yana jan babansa. Garin ya cire hannun Khalifan ya dan dauke ido daga kan hanya. Tana tura ledar tsamiyar birin a jaka taga mota ta yo kanta. Hantar cikinta ta kada ta rasa ina zata yi ma. Gabadaya ta rude kafafunta sun kasa daukarta. Da kyar Hamza ya iya tsayar da motar bayan ya shigar da ita cikin wani ruwa da ya kwanta a gefen titi. Har fuska ruwan ya watso wa Zuhra sannan ta zame ta fadi a zaune cikin ruwan. Karshen bacin rai kam taji shi a lokacin. Musamman da ta hango mai tukin da yaro suke kicikici da sitiyarin motar. Da sauri Hamza ya tura Khalifa wanda yake ta kuka cinyar Izzatu ya sauke glass din motar yana duban Zuhra. Leko da kansa yayi zai bata hakuri sai dai akayi rashin sa'a kwalliyar fuskarta ta bashi dariya. Izzatu da Tala ma da suke cikin motar sai da suka yi saboda yadda lebenta ke daukar ido. Ita kuwa Zuhra haushi ya kara kamata. Hamza ya dan daure amma fuskarsa dauke da murmushi yace don Allah kiyi hakuri kinji. Yaro ne ya rike sitiyarin Allah Ya kiyaye ban tabaki ba dai ko? Zuhra ta tsuke baki ban sani ba...don tsabar wulakanci kayi min wanka da kwatami sannan ka wani kame a mota kana tambayar ko ka tabani. Hamza ya dan sha kunu jin abinda ta fada yace to naji kiyi hakuri don Allah. Ya zaro kudi a aljihunsa ya mika mata dubu biyar. Gashi ki sayi sabulu. Ganin ya tayar da motar ta kama hannun gefen inda yake zaune ta soma masifa. Amma kai baka da mutumci wallahi...tana kallonsa tana kallon kudin. Kudinka me zasu min. Malam ka fito ka duba ko naji ciwo ka kaini asibiti. Izzatu ta dan leko kiyi hakuri kinji, kinga yaron da ya jawo, ta dungure Khalifa. Maganar Zuhra ta bawa Hamza haushi yace idan bazaki karbi kudin ba sauri nakeyi. Kin samu na tsaya zaki rinka yi kin rashin kunya. Zuhra tace anyi din, nace anyi din kuma Allah Ya isa abinda kayi min. Ka wani makale a mota kai mai kudi ko. Yadda take magana ya sake bawa Izzatu dariya. Haka kawai yarinyar ta burgeta. Hamza kuwa harararta yayi sannan cikin fushi ya fito daga motar. Tun kafin ya karaso tsoro ya cika mata zuciya. A gabanta ya tsaya ta daga kai ta kare masa kallo. Tabdijam...da kyar in kanta zai kai kafadarsa ma. Ta hadiyi yawu da kyar. Mutumin duk da bashi da kiba amma dai baya sahun masu rama, gashi da tsaho. Idanunta suka kawo ruwa don kallon da yake mata ba na wasa bane. Idan ya dake ta kuwa ya daki banza. Ya dan rage sautin muryarsa ke kinga nayi kama da sa'anki ne? Ta girgiza kai. Yace to ina baki hakuri sai ki rinka yimin rashin kunya. Izzatu ta dan bude kofa tace babyna ka taho mu tafi kawai. Zuhra ta zaro ido ta kara kallonsa....baby kuma? Katon gardi da kai a kiraka baby. Lallai an cuci kalmar nan al'quran. Ran Hamza ya sake baci ya daga hannu zai mareta. Tace kana tabani zanyi suman karya a wurin nan sai mazan can sun taru. Kuma in fada musu abinda kayi min. Daga kai yayi ya kalli kofar kantin da ta nuna yayi murmushi yace bismillah. Zuhra ta dan ja da baya da gaske nake fa...shima ya kara matsawa gabanta ai ban hanaki ba. Ta tabbatar dai ba wasa yake ba kawai sai tace Allah Ya isa da karfi ta kwasa da gudu. Binta yayi da ido sannan yayi tsaki. Idan ya sake ganin yarinyar nan sai jikinta ya gaya mata. Shi zata yiwa Allah Ya isa har sau biyu. Yayi kwafa ya shiga mota. Izzatu sai dariya take. Yarinyar kamar wata clown. Ita fa gani take tayi kwalliya karshe ko? Hamza yayi tsaki yanzu duk abinda ta fada min bai dameki ba Izzy sai ki rinka dariya. Tace ai abin naku ne da ban dariya. tayar da motar yayi don idanun Izzatu suna ga yarinyar da ke gudu ba maganar da yake ba. Tana kallo har Zuhra ta fada gidan Faiza.... [9/25, 2:52 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿9 Batul Mamman(Mrs)💖 Tunani ne duk ya ishi Hamza har ya isa gida. Tabbas ko makaho yasan kasarmu tana cikin matsi a wannan yanayin da muke ciki. Sai fatan Allah Ya kawo mana sauki. Amma a haka duk shekara basa rasa dalilin yin taro a gidansu. Duk da hakan ba ra'ayinsa bane tun farko amma ya goyi bayan Izzatu akan duk abinda take yi. Dole ne kuma ya nuna mata kuskuren rayuwar da suka daukarwa kansu ko don inganta tarbiyar 'ya'yansu. Kila mutane suna ta zaginsa bai taba tunanin haka ba sai yau. A haka ya isa gida zuciyarsa duk ba dadi. Izzatu ta gama gyaran dakin yana ta kamshi ita kanta ta yi kyau sosai tace ya shiga yayi wanka. Inuwa Sakatare ya karanta takardun gabansa yafi a kirga. Yana son sanar da ogansa amma yana tunanin kada ya zama ya nuna rashin damuwa akan lalurar Junior. Daga karshe dai text ya tura masa wanda ke dauke da cikakken bayani dangane da yarjejeniyar dake tsakaninsu da turawan. Kusan minti goma ba reply sai kawai ya kira wayarsa. A lokacin Hamza na wanka. Izzatu na kallo har wayar ta tsinke aka sake kira har sau hudu. Tayi tsaki ta dauka. Bata son abinda zai bata romantic night din da ta tsara musu ita da mijinta. Gashi baya yarda da kashe waya komai dare. Inuwa ya gaisheta ya tambayi jikin Junior tayi dariya kawai tace da sauki. Yace na turowa Oga sako ne nake son tambayarsa ko ya gani. Izzatu tace yana wanka amma zan sanar dashi. Inuwa yayi godiya yace sai da safe. Har ta ajiye wayar ta dawo ta dauka. Tasan halin Hamza kafin ya kwanta sai ya duba sakonnin wayoyinsa mai bukatar reply ya tura. Ita kuwa daren yau na tunawa da ranar aurensu ne. Bata bukatar duk abinda zai dauke masa hankali. Duba sakonnin mail dinsa tayi duk ta bude su a matsayin an karanta haka ma na whatsapp. Text kuwa banda na Inuwa duk sauran na etisalat ne da mtn. Gabadaya ta hada ta goge harda na Inuwan saboda daga farkonsa taga an rubut RANKA YA DADE YA JIKIN JUNIOR......iya nan ta gani ta goge ta saka masa wayoyin a chaji. A tunaninta text din dubiya ne. Da ya fito ya duba wayar babu wani abu mai mahimmanci sai kawai suka yi shirin kwanciya.... Zuhra ta dawo daga islamiyya tana ta zumbura baki. Sallamar ma a ciki ciki tayi. Umma tace waya taba uwar masu gida? Jakarta ta jefar a kan tabarma ta cire hijabin ta kwanta. Umma yunwa nake ji kamar naci babu. Baba ya fito daga bandaki da buta a hannu yace Allah Ya rabamu da babu. Shine zaki wani kwanta kina turo baki. Ji don Allah kamar ba mace ba. Kin wani kwanta a kasa. Ji gaban rigarki ma kamar manja. Ya taba kitsonta da tsagar har ta bace don tsufa...yanzu kan nan yaushe rabonsa da ki wanke shi? Wai wa zan samu ya aureki a haka? Ba kwakwalwar karatu ga rashin jure yunwa. Gaki ba wani kyan azo a gani ba. Da nayi kudi ne ma sai a aureki ko don nauyin aljihuna. Zuhra ta soma shura kafafu Umma kinji Baba ko? Ai dai kai na biyo wallahi. Yace wa? Ni? Haba yarinya don kinzo na fara tsufane. Tambayi Ummanki lokacin da nake matashi yadda mata ke bina. Umma tana wanke shinkafa tana musu dariya. Zuhra tace har tafiyarmu iri daya fa. Baba yasa dariya ai kuwa da kinji kunya ace budurwa kamarki tana tafiyar maza. Maganin farinjini zan nema miki. Tunda karatun yaki sai ayi auren. Maganarsa ta sake tunzura Zuhra har ta soma hawaye tace Umma ina kama dake ko? Umma ta rike baki tace ta ina? Ni duk gidanmu babu mai kyau na. Ke kuma da Babanki kike kama. Kaga Sima yar gidan Malam Basiru. Dariya sosai suke yi mata tana ta kuka. Ta tashi ta shige daki. Baba yace kinga kin batawa uwata rai ko. Umma tace don na tayaka?. Amma maganar gaskiya rashin saurayin Zuhra na damuna. Maikifin bakin layi ne kawai yake zuwa kuma tace bata son shi. Baba yace nima abin na damuna. Bata son kula da tsaftar jikinta ne kuma da laifinki. Umma tace akan ta tsefe kanta har dukanta nayi. Lokaci na bata zuwa wani satin tana bacci zan sa mata almakashi kowa ya huta. Baba yace wallahi ban yarda ba. Da nayi saa ta gado irin gashinki mai dan tsaho kuma sai ki aske. Ba gidan Faiza zata ba bayan azahar...Umma tace can zata je. Baba yace to kice ta tafi da kaya ko biyu ne ta kwana. Kinsan halin Faiza ko taki ko taso sai tayi tsifar nan. Zuhra na jinsu daga daki ta leko ta taga na fasa zuwa gidan Anti Faizar. Umma tace kunfi kusa ai. Sai da ta gama cin abinci ta sha ruwa sannan ta dauko hijab ta saka da kullin kayanta a dankwali tace Umma zan tafi. Baba ya harareta a haka Zuhra... Islamiyya fa kika je ko wanka bakiyi ba ki ka saka kaya. Ji hijab din ko guga babu. Ke ko irin gayun mata baki iya ba. Ki dan saka kayanki a yar leda zaki kulle a dankwali. Yarinyar nan da a kauye muka tashi bana jin zaki taba wayewa. Gaskiya Umman Zuhra bakya kyauta min. Kin bar min yarinya ta zama borar karfi da yaji. Umma tace ai kana gidan kana ganin yadda nake fama da ita. Baba yace zo ki zauna kinji Fadimatu. Ta zauna bakin nan kamar ya zunguri kofa saboda yadda ta turo shi gaba. Yace yanzu don Allah idan ke namiji ce kika ga mace irinki zaki so ta? Tace eh to ya danganta da namijin. Baba yace ni bance sai mai kudi ba amma dai Zuhra a sami rufin asiri. Ke kadai fa Allah Ya bani dole na so ki da alkhairi. Dazu kina cin abinci lomarki har tafi tawa. Itama dariya maganar ta bata. Ta sunkuyar da kai. Baba yunwa naji sosai a lokacin. Yace to abinda zai faru nayi miki alkawarin waya mai kyau harda kemara indai zaki rinka tsafa. Alhamdulillah Zuhra tace da karfi tare da fadawa jikin Baba tana godiya. Yace dagani duk gidannan kinfi kowa nauyi saboda cin ki. Ta mike tsaye tana tsalle daga yau zaka ga canji Baba. A wurin ta cire hijab da dankwali ta kama zanin zata kwance Baba yace shiga daga ciki dai yana kawar da kai. Ta wuce da tsallenta kamar karamar yarinya. Baba yace da Umma kin kula da hannun rigar mamanta kuwa? Dandakuwa..... Umma tace Baban Zuhra ka fiye gane gane kaima. Allah Yasa canjin ya dore dai. Kusan minti goma sai gata ta fito da daurin kirji da gashinta buzu buzu. Ta dauko kwandon wankanta da yar robar shampoo ta wuce bakin rijiya ta debi ruwa bokiti biyu. Suna nan zaune ta fito bayan kusan rabin awa tayi wanka da wanke kai. Umma tace har kin danyi haske kuwa. Bata ce komai ba ta shige daki. Tasha wahalar taje kanta sosai saboda tsabar cikarsa. Ta shafa mai a ko ina ta raba biyu tayi kitso manya. Ta shafa mai a jikinta da body spray din da Baba ya siyo mata. Ba wani abu ke sawa bata amfani dasu ba, ita a tunaninta idan basu kare ba Baba zai ajiye kudinsa yayi wani abin dashi. Tana matukar tausayinsa saboda lalurar hannu da ta same shi. Sai da akayi laasar ta fito fes da ita. fuska tasha hoda da janbaki orange, har girarta ta gyara. Baba kuwa baki yaki rufuwa da ya ganta bayan ya dawo daga masallaci yace ko ke fa. Allah Yasa ayi gamon alheri a hanya. Umma tace iyayen zamani ba kunya. Dari biyu ya bata kudin mota tayi godiya ta fita. Tafiyar ma kokarin daidaita kafarta ta rinka yi kada Baba yace tayi ta maza. Sai da ta fita Umma tace ba naga ka siyo wayar ba. Yace eh kyaleta muga zuwa kwana biyu sai na bata. Ki rinka sa ido tana gyara kanta. Ga iya zuwa islamiyya daukar karatu amma bata damu da tsafta ba. [9/25, 3:23 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿11 Batul Mamman(Mrs)💖 Su Anti Faiza sun sha dariya da Zuhra ta basu labarin dalilin shigowarta a guje. Anti Faiza tace lamarinki sai addua Zuhra. Yanzu meye na rashin kunya bayan an baki hakuri? Zuhra tace yana daga mota fa yake bani hakurin. Ni dariyar da suka yi min ita yafi bani haushi. Hajara tace to ba dole suyi ba kin kama fuska kinyi mata zane. Ji girarki kamar an miki fenti. Zuhra tace wai haka Anti? Yau baki ga yadda Baba yayi murna ba har alkawarin waya yayi min. Daga nan suka cigaba da hira. Anti Faiza ta sako zancen bleaching tana musu fada. Zuhra tace nima hanata nayi har malama Rabia na tambaya hukuncin mai yi. Ta zauna tayi musu bayanin yadda suka yi da malama. Anti Faiza tace ato ni dai nasan kuna tare naji tsoro kada ta koya miki hali kinsan ance zama da madaukin kanwa..... Bayan kwana biyu suna cin danmalele a falon Anti Faiza suka ji sallama. Zuhra ta kwaye zaninta har ana ganin cinyoyinta. Anti Faiza sai fada take mata basu ji sallamar ba. Abba ne ya amsa sai ga Izzatu ta shigo. Da yake Zuhra na fuskantar kofa tana shigowa suka hada ido. Sai da ta kware don tsoro sannan ta tashi da gudu ta shige daki. Anti Faiza cikin mamaki tace sannu da zuwa Maman Khalifa. Ganin Izzatu na kallon kofar dakin tana dariya tace wata kanwata ce mai shirmen tsiya. Izzatu tace ai mun taba haduwa. Ta baki labarin an kusa kadeta da mota shekaranjiya ko? Zuhra daga daki tana lasar hannunta da ya sha manja tace na gama yawo yau. A falo Anti Faiza tace ba dai Alh Hamza ta yiwa rashin kunya ba? Ke Zuhra fito. Izzatu tace ba kararta na kawo ba. Ni ta burgeni ne ma. Don baki ga idanunta ba da ya fito daga mota. Yadda kika san ta saki fitsari a wajen amma duk da haka bata dena magana ba. Anti Faiza tace ai indai Zuhra ce ta wuce nan. Sai ki fito ki bata hakuri ta kira Zuhra daga daki. A sanyaye ta fito ta gaishe da Izzatu sannan tace ku yi hakuri. Hajara tana gefe tana musu dariya. Izzatu tace ba damuwa. Ai ranar baki ga yadda yaji haushi ba. Har muka je muka dawo yana mita. Ni da zaki bini gidana ma ai da saka ku zanyi a gaba ina samun abin nishadi. Zuhra ta kalleta da mamaki. Yanzu nufinki baki ji haushin duk abinda na fada masa ba? Izzatu tace not at all. Zuhra dai bata gane dangantakar turancin da tambayarta ba, sai tace da nice wallahi fitowa zanyi daga motar in saita bakin mara kunya. Hajara ta dan taba Anti Faiza sannan ta kallo Zuhra alamun ayi mata magana. Izzatu ta ce ni bana son hayaniya nasan he will handle everything shiyasa na kyale ku. Maganar ta bawa Zuhra mamaki sosai. Ace wata tayiwa mijinki rashin kunya kice baki damu ba. Gaskiya ke a mata daban ce....anti Faiza tayi saurin toshe mata baki. To sarkin shirme ance abinda kika yi babu komai kin dage sai neman jawo magana kike. Maman Khalifa don Allah kiyi hakuri. Izzatu tayi dariya ke babu komai fa. Haka suka cigaba da hira Zuhra tana basu labarin Baba na son yi mata aure amma yace yafi son miji mai ilimi. Ni kuwa indai gida da abinci bani da damuwa. Hajara tace amma kika ki maikifi? Baki taba tsayawa gabansa bane shiyasa kike magana. Banda karni babu abinda yake. Anti Faiza tace wai kura ce zata ce da kare maye. Ke da ba kya minti uku kin gama wanka ai bai kamata ki guji dan uwanki kazami ba. Zuhra tace baki ji na fada miki Baba zai bani waya bane..ai daga yanzu zan rinka wanka sosai. Ita dai Izzatu har ranta shirmen Zuhra yana bata shaawa. Dalilinta kenan na zuwa gidan ranar don idan tana neman Faiza waya take yi mata. Kwana hudu Zuhra ta yi a gidan suka koma tare da Hajara. Baba ya bata dubu shida yace ta kaiwa mai koya mata sakar. Cikin dan kankanin lokaci ta fara kwarewa saboda abu ne da take so. Ga tsafta an dore da wanka. Kwalliyar ce dai har yanzu da sauki. Baba ya cika alkawari ya bata wayar. Ranar murna ba'a magana. Haka ta rinka shiga makota tana nuna musu. Mamansu Hajara ma tayi murna. Don duk makotansu sunfi shakuwa sosai tamkar yan uwa. Tecno ce second hand ya siya a wurin wani dan layinsu. Da yake suna ganin girman Baban Yara kamar yadda suke kiransa ba karamin sauki mai wayar yayi masa ba. Arch Hamza na zaune yana duba wasu takardu a office dinsa Inuwa sakatarensa yayi sallama ya shigo. Bayan sun gaisa yace ranka ya dade naji baka ce komai ba game da text da wayar da nayi maka. Hamza yace yi hakuri wasu abubuwan ne suka dauke min hankali. Izzatu ta fada min komai. Babu matsala nagode. Har kunya yake ji ace matarsa karya tayi. Inuwa yace ranka ya dade babu matsala? Hamza ya ajiye takardun ko dai akwai wani abu ne Inuwa? Shi a tunaninsa Inuwa ya gano Junior lafiya yake. A'a babu komai, dama wannan maganar ce kawai. Daga nan ya fita. Tunda Oga bai damu da yanayin contract din ba gara ya dena damun kansa kawai. [9/25, 3:29 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿12 Batul Mamman(Mrs)💖 Da daddare yana bacci yaji kamar ana taba shi. A tsorace ya tashi ya lalubi fitilar gefen gado. Zaune ya ganta ta dora pillow a cinyarta. Sweetheart ka tashi muyi magana game da birhtday din Nana. WHAT??? Shine abinda ya iya fada a hasale. Izzatu tace maganar birthday din Nana nace. Ya nuna mata agogo Izzy kinga time fa, uku saura na dare. Ta dan kwanta a jikinsa kullum ina son mu tsara komai baka dawowa gida da wuri. Jikinsa ya janye sannan yace saboda haka sai ki tasheni da tsakar dare? Haba Izzy! Tashin miji ayi magana a irin wannan lokacin ai sai a film. Indai maganar kirki ce ai ido biyu ake yinta. Ni naga irin haka is normal tsakanin couples. Idan abu na damun daya sai suyi discussing at night. Kasan kuwa na sake ganin yarinyar da kuka yi fada saboda ka watsa mata ruwa. Ashe kanwar Faiza ce. A wannan lokacin Hamza ji yayi tamkar ya saka ihu. Fuskarsa ko kadan babu annuri yace yanzu Izzy ki tasheni a tsohon daren nan saboda zancen birthday sannan ki ce kinga yarinyar nan? Did I ask you? Gobe meeting gareni da sassafe kuma na fada miki. amma sai kika zabi yanzu ki hanani bacci kuma ki bata min rai. Kallonsa kawai take yi....yau me ya sami baby dinta yake irin wannan fadan. Shi kuwa Hamza banda bacin ran gani yayi dama ta samu na bin umarnin Mama a soke maganar party. Yace ki manta da maganar wani party don an dena. Kina iya dafa abinci ki kawo a kai asibiti ko makarantar allo sadaka. Wannan karon ita ce nata ran ya baci. Wace irin magana kake yi ne? Yarinya duk na gama sa mata rai. Har kayan da zata saka ranar duk na gama siya. Hamza yace indai kaya ne ko gobe ma ki saka mata. Izzatu ta soma hawaye kada kayi min haka Hamza please. Yace meye na daga hankali, shekara biyu zata yi ai ba wayo gareta ba. Hawaye take sosai ya rungumeta yana rarrashi. Tace indai don na tasheka ne kayi hakuri amma kada kasa yan gidanmu suyi min dariya ko aga kamar baka da kudin ne. Bai san haka suka daukaki abin ba sai yanzu. Yace na gama magana Izzy no more parties. Ki duba a family dinku mai bukatar taimako sai mu bashi jari. Su Mama basa son abinda muke yi kuma nima na fahimci kuskurenmu. Ai ture shi tayi ta tashi tsaye. Dama nasan zugoka aka yi tunda ka fara magana. Na rasa meyasa 'yan gidanku basa sona. To wallahi sai anyi ko kana so ko baka so. Hamza yace ni kike fadawa haka Izzy? Yau daya don na hanaki abu shine zaki nuna min ban isa ba. Ba tare da ta bashi amsa ba ta fice daga dakin harda buga kofa. Kansa ya rike ya zauna a bakin gado. Lallai yayi sakaci da har abin ya kai haka. Dole ya nemi yadda zai gyara gidansa don a zauna lafiya. Cikinsa ne ya murda alamun yunwa. Yau kamar sauran alhamis Izzatu batayi girkin dare ba. McDonald's tayi musu order. Soyayyan dankali aka kawo musu da kaza harda Tala da maigadi. Ko kadan Hamza bai koshi ba sai dai an saba irin haka wanda tun kafin suyi aure yayi mata alkawarin ware rana daya a sati kada tayi girkin dare zasu rinka ci a waje ko ayi order a kawo musu gida. Tashi yayi ya bita dakinta sai dai a rufe yaji dole ya koma ya kwanta. Da kyar ya iya bacci saboda yunwa. Washegari saboda tana fushi bai sami breakfast ba. Da yayi magana tace ta dena girki sai ya janye maganar party. Shi kuma yace ta bashi atm card dinsa na wurinta maganar soke party babu fashi. Baram baram suka rabu. Har mamanta ta kira a waya ta fadawa tace kada ta damu idan bata da kudi ne zata turo kaninta ya kawo mata. Hamza gani yayi an cigaba da shirye shirye. An siyo katons din lemo da ruwa. Ga gifts duk an gama hadawa a wata jaka mai hoton Nana duk an ajiye a store. Ya sake wa Izzatu magana tace ai ba kudinsa bane. Maganar Mama ya sake bi ya kwashe yaran ya kaisu gidansu. Su Hajiya sunyi mamaki da farinciki ganin Hamza yaji maganarsu. Aka sa Ibrahim dasu Mariya suka kawo nasu yaran. Tuni su Khalifa suka saki jiki cikin yan uwansu. Idan suna Hausa sai ka rantse daga turai suka dawo. Kwatakwata basu iya sosai ba ,sai turanci. Nana kuwa dama bata iya magana sosai ba. Tunda suka zo ta likewa Adabiyya take kiranta Anti Adab. Izzatu tayi mamaki da ta dawo daga supermarket ta tarar yaran basa nan. Tala ce ta sanar da ita sun fita da daddynsu. Sai dai tasha takaici da ya dawo shi kadai yace a can zasu kwana. Tasan saboda maganar party ne. Tayi ta rokonsa da koke koke duk a banza. Har zaunar da ita yayi yana mata nasiha amma ta kafe. Shi kuwa yace indai zata iya zuwa gidansu ta dauko yaran shikenan. Bata san gatse ba ta tafi ana sauran kwana biyu sai dai ta tarar duk sun tafi Kumo. Babu kowa a gidan sai maigadi. Kuka kam ranar ba'a magana. Izzatu tayi fushi sosai da Hamza tare da alkawarin sai ta rama duk ranar da dama ta samu. [9/25, 3:31 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿13 Batul Mamman(Mrs)💖 Fada sosai Hamza da Izzatu suka yi sai da kyar ya samu ya rarrasheta suka daidaita. Amma kudirin ramuwa yana nan a ranta, dama kawai take jira. Kusan wata biyu suna zamansu lafiya. Architect Hamza na kokari wurin cigaba da kulawa da iyalinsa. Su Hajiya ma yana wadata su da abubuwan bukata. Hatta kawunsa da aka kora aiki sai da ya aika masa da dubu dari. Hajiya taji dadi sosai har waya tayi masa abinda bata yi sai da dalili saboda dan fari ne tayi masa godiya. Wannan wayar tasa shi jindadi mara misaltuwa. Shiyasa ya cigaba da yin abinda zai kyautatawa iyayensa. Itama Mama taji dadi ya dauki shawararta don Izzatu bata nuna musu bacin ranta game da tafiyarsu Kumo da 'ya'yanta ba. Zuhra an gama koyon saka Baba ya kukuta ya siyo mata injin saka tsoho ne ma amma bai lalace ba. Tayi murna sosai shiyasa sakarta ta farko shi da ummanta ta fara sakawa rigunan sanyi masu kyau da kauri har uku uku. Duk da suna tsokanarta taki karatu amma sakar tayi kyau sosai. Umma ta bata shawarar duk lokacin da aka bata kudi ta sayi kulu tayi sakar ta ajiye kafin lokacin sanyi tunda ya kusa sai tq sayar. Wata rana Hamza ya fita zuwa gidansa da suke shirin komawa tun safe saboda aikin yazo karshe. Gida ne da ya tsara komai na ginin da kansa sannan kamfaninsa ke ginin. Izzatu tana kitchen yayarta dake aure a Alaska ta kirata a waya. Suna hira ne Izzatu ke tambayarta ina yaranta. Zeenatu tace sun fita da babansu siyan kayan da zasuyi amfani dasu na HALLOWEEN. Izzatu tace kai sis har kin tuna min lokacin da muke siyan namu da Daddy. Gaskiya ba karamin missing America nake yi ba. Zeenatu tace ba kinga dan fillo duk kin rude ba. To amma meyasa bakiyi a nan? Hmmm kinsan yan Nigeria da kauyanci kada ma yan kauye suji labari. Gidadancinsu yayi yawa...ko kin manta yadda muka yi da inlaws dina game da birthday din Nana? Zeenatu tayi dariya haba Juliet din Romeo duk soyayyar taku har zakiyi korafi. Ba haka bane sis, abin ya bani haushi sosai. Amma gaskiya zamuyi halloween this year. Ba don yana wani aiki ba ai da dole mu taho sai muyi celebrating tare. Zeenatu tace muma zamu taho nan da December a gida zamuyi new year. Bayan kwana biyu da wayarsu zancen halloween ya tsayawa Izzatu a rai. Lokacin da suna Canada da iyayenta suna celebrating tare sa sauran turawa. Nan da nan ta fara shirye shiryen yadda zasuyi nasu a gida. Hamza ta tambaya kudi don ya dena bata atm card dinsa. Tunda tace kaya zata siya bai hanata ba saboda rigimarsu ta party ta wuce. Washegari ta debi yara suka je manyan shopping malls din Kano da kyar ta sami abinda take so ta dawo rai a bace. Me zaayi da Nigeria abinda bai taka kara ya karya ba sai ka nema ka rasa. Washegari Khalifa ya tashi da zazzabi dama mura yake suka fita wannan siyayyar. Abu kamar wasa sai da suka kaishi asibiti da daddare, sai da safe aka sallamesu bayan an gama kara masa ruwa. Da suka dawo ne wurin karfe takwas ya kira Mama ya sanar da ita. Ranar ta dace da talatin da daya ga watan october wadda a irin wannan ranar ne turawa suke yin halloween. Izzatu bata fadawa Hamza ba domin bata dauki abin a cikin irin wadanda ya hana ba tunda ba gayyato mutane zata yi ba. Ita da 'ya'yanta zasuyi abinsu a gida. Bayan Hamza ya fita tasa Tala tayi musu wanka ta koma kitchen. Ita kuma ta dauko musu kayansu da ta siyo ta saka musu. Harda Khalifa mara lafiya. A ka'idar wannan rana ta halloween wadda take da sunaye da yawa harda Day of the Dead ana yin abubuwa masu yawa. Nasara mabiya addinin kirista suna celebrating wannan rana ne domin tunawa da matattunsu. Kamar waliyai, manyan masu bauta da shahidansu. Ana saka kaya na ban tsoro a ranar kamar riga mai alamun jini, fuskar shaidanu, yin shigar da baza'a gane mutum ba, tsorata mutane a gidajensu ko waje, zuwa wuraren ban tsoro kamar makabarta, tsohon kango ko gidan da babu mutane. Kai hatta horror films(fim na ban tsoro) ana gani a wannan ranar ko ka ziyarci malamin duba da sauran abubuwan firgici dai. Haka halloween yake ko kadan bashi da alaka da musulunci. Amma wani lokacin musulmai yan uwammu idan suka sami kansu cikin yahudu da nasara sai kawai su dauki al'adunsu suna ado dasu ba tare da sunsan ainihin dalilinsu na girmama ranar ba. Zama a kasar waje ba shine dalilin da zaisa mu dauki dabiar nasara wadanda suka bata da yahudu wadanda Allah ke fushi dasu ba. Allah Ya tsare mana imanimmu. Amin Izzatu ta sakawa Khalifa da Junior kayansu. Rigace mai dogon hannu da dogon wando duk sun dame musu jiki ga kuma fuska wadda aka fitarwa hudar idanu da wurin numfashi. Kayan bakake ne. Idan daga nesa ka hangosu zaka rantse kwarangwal ne saboda zanen kayan da yanayinsu. Bayan ta shiryasu ta daukesu hoto ta turawa Hamza a waya. Daga nan taje ta dauko na Nana. Su kuma jajaye ne harda safar hannu mai alamar farata zako zako. Fuskar(mask) kuwa kamar ta aljanu harda kaho biyu a sama. Nana tana ta dariya Izzatu ta gama shiryata ta daukota zasu fito falo sai Nana tace Mummy poo. Izzatu ta san halin Nana bata kashi a pampers duk yadda za'ayi da ita. Dole ta cire mata ta zame mata wandon ta dorata a po ta tafi kitchen duba girki don shabiyun rana ta wuce. Junior da Khalifa suna falonsu suna kallon cartoon. Tana kitchen taji sallamar su Mama. Da sauri ta fito tana musu sannu da zuwa. Duk su biyun rungume su tayi yadda ta saba. Hajiya sai dan yake take don wannan halin na Izzatu na bata kunya. Bayan sun zauna ta gaishesu Mama tace ina Khalifan? Ashe baiji dadi ba. Izzatu tace eh amma yau da sauki sosai. Zazzabi ne da mura. Hajiya tace to Allah Ya bashi lafiya. Mama tace kirawo shi mu ganshi. Dazu babansa yayi min waya da safe shine muka zo duba shi. Izzatu tace Tala ta dauko musu ruwa da lemo. Tala na tashi Nana ta fara ihun Mummy na gama da dan gwarancinta. Izzatu tace jeki kiyi mata tsarki bari na kawo musu. Tashi tayi tana kiran su Junior su zo ga su Hajita ta shige kitchen. Ba'a fi rabin minti da shigar Tala ciki ba ta fito falo tana ihu. Gabadaya jikinta rawa yake sosai tana kuka. Hajiya da Mama suka tashi a firgice suna tambayarta abinda ya faru. Cikin kuka tace mutanen boye sun bayyana. Mama tace su wa? Tala tace aljanun. Yau na gansu da idona ra'ayil aini har su biyu. Wallahi sai ga yarsu zaune akan po din Nana dayan kuma yana mata wasa. Na higa uku na lalace kwarankwatsa ko a kauyenmu ban taba gamo ba he yau. Izzatu ce ta fito da sauri daga kitchen tace ke Tala bana son rashin hankalin nan naki. [9/25, 3:33 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿14 Batul Mamman(Mrs)💖 Tala ta zazzaro idanu tana kallon Izzatu. Na rantse ba karya nake ba. Hajiya da Mama sai kallonsu suke yi. Tala na maida zance suka ji kukan Nana tana kiran Izzatu. Tare duk suka yi hanyar inda suka ga Tala ta fito. Hajiya ce a gaba. Sai da cikinta yayi mugun kadawa saboda abinda ta gani zaune akan po yana miko hannu alamar ta dauke shi. Na kusa dashi kuma mai siffar kwarangwal ya rugo da gudu zai rungumeta. Da kyar ta iya cewa Hasbunallahu wa ni'imal wakil sannan tayi baya kamar zata fadi. Mama tayi saurin tareta itama a tsorace har ta fara tunanin kada aljanun su rufe kofar gidan su hanasu fita. Tala tace kun gani ko Hajiya ai na fada muku. Nana dai tasowa tayi ta nufo su shima Junior haka. Khalifa da yake kwance a daki shima ya fito saboda hayaniyar da yaji. Mama ta karewa aljanun uku kallo tace Hajiya gidan Yaya ba lafiya. Izzatu ce karshen shigowa tana ganin abinda ya kidima surukanta ta kyalkyale da dariya harda hawaye, karshe sai da ta kai kasa. Hajiya da Mama sai kallon kallo a zatonsu ma ko aljanun sun taba ta. Sai da tayi mai isarta suna kallonta sannan tace Hajiya su Nana ne fa. Kaya ne na saka musu yau halloween. A gabansu ta cire musu fuskar kayan tana mai cigaba da dariya. Ransu Hajiya yayi matukar baci. Tala kuwa karasawa tayi gaban yaran tace Khalifa kaine tana tattaba musu jiki. Ta dago kai tace Hajiya ai kuwa su din ne. Mama ta dubi Izzatu, hallo...me kika ce? Izzatu tace halloween. 31st October ake yi. Lokacin da muna Canada muna yinsa sosai. Tsabar bacin rai Hajiya ta kasa magana ma. Karshen wulakanci da cin mutumci Izzatu tayi musu. Mama tace Hajiya ai sai mu tafi ko, don banga dalilin zamanmu ba. Su Junior suna ta binsu suna cewa zasu bi su. Cikinsu babu wadda ta iya kula yaran saboda yadda zukatansu ke kuna. Izzatu tace muje falo ku sha ruwa don ita bata dauki shirunsu a matsayin bacin rai ba. Sun kai bakin kofa zasu fita idon Mama ya kai kan wani mutum mutumi mai siffar mutum kafarsa ta akuya ga kaho har a saman hanci. Shima duk cikin kayan kwalliyar gidan ne na halloween. Cikin Mama har murdawa yayi, gabanta ya fadi don abin ya bata tsoro har kafarta ta goce ta fadi kasa. Hajiya tayi saurin durkusawa ta taimaka mata ta tashi. Junior da Khalifa ma suna ta cewa sannu Grams. Ita kuwa Izzatu wata dariyar ce ta subuce mata. A ranta tace ko ba komai ta rama abinda suka yi mata na sa Hamza ya hana su party. A fusace Hajiya ya dago kanta cikin zafin rai zata yiwa Izzatu magana Hamza yayi sallama. Ganin Mama na kokarin mikewa yayi saurin karasawa gabanta yana tambayar abinda ya faru. Dama zuciyar Hajiya a kusa take maimakon ta bashi amsa ta kwashe shi da mari. Falon a take yayi tsit Tala tayi saurin komawa dakin su Khalifa ta ga an mari ubangidanta. Falon yayi tsit Izzatu ta hadiye sauran dariyarta. Shi kuwa hannuwansa biyu yasa ya dafe kumatunsa ya dubi mahaifiyarsa a razane. Mama tace haba Hajiya ya zaki dauki hukunci kan wanda baiji ba bai gani ba. Murmushin takaici Hajiyan tayi tace tunda nake ban taba ganin wulakancin da yayi min ciwo irin wannan ba. HAMZA ka guji ranar da zanyi maka baki.....idanunsa sunyi jawur yana mamakin sunansa da ta fada da kuma dalilin bacin ranta. Yace da Izzatu me ya faru? Ta dan tabe baki babu komai. Don basu dade da zama ba suka tashi. Hajiya da Mama suka yi hanyar kofa yana ta basu hakuri da son jin abinda ya faru sunki sauraronsa. Har bakin mota ya biyo su. Sai da dreban ya tada motar sannan Hajiya tace wallahi in dai da raina da lafiyata Hamza bazan kara taka kafata nazo gidanka ba. Mama da yake tunanin zata bata hakuri ko kallon inda yake bata yi ba. Sai ma kwalla da yaga tayi saurin sharewa kafin motar ta fita daga harabar gidan. Da sauri ya shiga gidan yana kwalawa Izzatu kira. Ta fito hankali kwance tace sweetheart abinci zaka fara ci ko wanka. Izzy kina da hankali kuwa? Ya dubi su Junior kai ku koma dakinku. Sai da yaran suka tafi yace idan naki iyayen ne suka fita haka zaki musu? Ki fada min gaskiya me akayiwa su Hajiya. Izzatu tace ni ban sani ba. Suna ganin su Khalifa suka kama hanyar fita. A daidai can ne mama ta dan fadi. Hamza yace ta fadi? Ya karasa yaga gunki a wurin ya dago shi..meye wannan kuma? Izzatu tayi yar dariya na halloween ne. Ka tuna sanda akeyi a Canada? Akwai da yawa naso gama jerasu kafin ka dawo. Ya ce wane irin hoto kika turo min dazu? Ni abinda ya dawo dani kenan. Izzatu ta riko hannunsa zo mu zauna babyna. Ta kira yaran sai a lokacin ya kula da kayan jikinsu. Na nana yafi tada hankali ya mike a fusace izzy dont tell me haka su Mama suka ga yaran nan. Tace haka suka gansu mana. So what? Dafe kansa kawai yayi yana karanta Innalillahi a zuci. A hankali yace Izzy don Allah ki ajiye al'adun wasu a gefe mu zauna lafiya. Yadda Hajiya ta rantse ta bar zuwa gidana na miki rantsuwa da Allah idan kika sake dauko min wani abu da bai dace da dabiar musulmi ba sai na bata miki rai. Bacin rai wanda sai kinyi nadamar aurena. Iya nasihar da zanyi miki nayi nima na gane rashin kyautuwar abinda muka yi a baya. Kina zaune lafiya da iyayenki baki isa ki rabani da nawa ba. This....ya nuna ta da dan yatsa is my last warning. [9/25, 3:33 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿15 Batul Mamman(Mrs)💖 Yana gama magana ya tashi yana kwalawa Tala kira. Da yake tana labe a bayan kofa da gudu ta fito jiki na rawa yace jeki ki cire musu kayan nan ki kawo min mota ina jiranki. To kawai tace ta kwasa da gudu tayi ciki. Izzatu ta kalleshi itama rai a bace kudi fa nasa na sayi kayan nan. Me zakayi dasu?. Ya dan daga gira daya Allah ko? Tunda kudin nawa ne babu ruwanki da abinda zanyi. A iya zamansu basu taba samun sabani kamar yadda suke yi yan watannin nan ba. Kirikiri iyayensa ke nuna mata kiyayya amma zata yi maganin abin. Ta yanke shawarar bazata taba bari maganganunsu suyi tasiri a ranta ba har ta dena rayuwarta yadda ta saba. Ita tasan iyayenta sun bata tarbiyya irin wadda ta dace kuma ga yayarta da mijinta suna zamansu lafiya sai ita kadai ce zasu takurawa. Horn Hamza ya rinka dannawa da karfi sai ga Tala kamar an jeho ta. Ta mika masa kayan. Har ya dan ja motar sai ya dawo ya sake kiranta. Ke fada min gaskiya me ya faru da su Hajiya suka zo dazu? Ai kamar jira take ta soma bayani dalla dalla. Dama banda tsoron da taji ba karamin mamakin Izzatu tayi ba da tayiwa surukanta dariya. Fuskar nan ta Hamza kamar bai taba dariya ba ya ja mota ya nufi gidan iyayensa. Hankalinsa a tashe ya gyara parking din motarsa saboda yaga alamun Alhaji na gida. Yana shiga falo Adabiyya da Hamida ya gani suna kuka. Gabansa ya fadi yace ku meye haka? Adabiyya ta taso ta rungumeshi tana cigaba da kukan. Dama duk ta fisu raguwar zuciya. Hamida tace Mama akeyiwa gyaran kafa. Me kika ce??? A razane yake maganar tace gocewar kashi ta samu. Matsar da Adabiyya yayi daga jikinsa ya shiga falon Alhaji. Mama ya gani zaune a kasa tayi gumi sosai Hajiya na rike da hannunta. Kafarta ta hagu daure da wani farin yadi. Gefe kuma mai dori ne durkushe gaban Alhaji zai karbi kudinsa. Mai dorin yace in Allah Ya yarda gobe da safe zan dawo na duba. Allah Ya kiyaye gaba. Tamkar wanda kwai ya fashewa a ciki haka Hamza ya karaso cikin falon. Mama ce kawai ke kallonsa, ita Hajiya kawar da kai tayi gefe. Alhaji Nasiru ya hade fuska kana ganinsa kasan yana cike da bacin rai. Kusa da Mama Hamza yaje ya zauna ta riko hannunsa kawai sai ta soma kuka. Hajiya ta tashi zata bar falon Alhaji ya dakatar da ita. Hamza yace Alhaji barka da rana. Muryarsa har rawa take bata fita sosai. Alhaji yace Hamza.....toh fa yau duk su biyun sun kira shi da sunansa. Allah gani gareKa yace a zuci. Naam Alhaji. Alhaji yace dago kanka ka kalleni. Kasawa Hamza yayi. Alhaji yace ashe kana da sauran kunya. Dubi yadda iyayenka suke kuka saboda bacin ran da suka kwaso a gidanka. Yau Mamanka ce a zaune ana mata gyaran gocewar da tayi a gidanka matarka tayi mata dariya. Wace irin rayuwar aure kuke yi kai da iyalinka? Me kake son nunawa duniya game da tarbiyar da muka baka? Ba don tsarewa ta Allah bace duk kannenka koyi zasuyi da irin dabiun da ka kwaso a turai. Alhaji ya cigaba da cewa duk irin abinda kuke yi babu wanda ban sani ba amma na kawar da kai saboda iyayenka basu tunkareni da maganar ba. Na basu damar su ta iyaye mata su saita ka a hanya kuma nasan sunyi iya kokarinsu. Amma yau saboda abin yayi yawa Halimatu da kanta ta sanar dani abinda yarinyar nan tayi musu. Wulakanci na karshe Izzatu tayiwa iyalina amma bazan umarceka da rabuwa da ita ba. Sai dai ka sani wallahi nayi maka rantsuwa ranar da duk kuka sake aro daga munanan al'adun wasu har kunnena ya jiye min ko ido ya gani zanyi maka hukuncin da baka taba tsammani ba. Da sauri Hamza ya kalli mahaifinsa don Allah kuyi hakuri Alhaji. Nasan nayi kuskure tunda da goyon bayana komai ke faruwa. Amma in Sha Allah zan gyara kuma yanzu zan daukota tazo ta bada hakuri. Hajiya tayi saurin cewa ban yafe maka ba muddin kace mata tazo bada hakuri. Indai hankalinta da tarbiyarta basu nuna mata abinda ya kamata ba shikenan. Alhaji yace ina zaune kike irin wannan zancen Halimatu? Tace ayi hakuri. Hamza ya dubi Mama wadda kanta yake a kasa ki yafe min Mama don Allah. Abinda ya faru yau ko kadan bani da masaniya a kai. Alhaji yace halo me ma kuka ce sunan abin? Hajiya tace yo ni ina zan rike. Kamar ba kalmar turanci ba, yau na fara jinta ma. Hamza ya sake dukar da kai ko a da bama yin wannan ranar bansan dalilinta na yi ba yau. Alhaji yace dalilinta ya wuce ta tozarta min iyali ne? Ka tashi ka tafi Allah Ya kyauta. Hamza dai kin tashi yayi ya kara matsawa jikin Mama yana rokon ta yafe masa. Murmushi kawai tayi tace masa ka tashi ka tafi ba komai. Duk yadda yaso Mama taki tsawaita magana. Hajiya tace ka tashi ka bamu waje magana ta kare. Idan ka fita ka turo min Adabiyya da Hamida. Jiki ba kwari ya fita ya turo su. Hajiya tasa Adabiyya sake gyara gadon Mama , ita da Hamida suka kamata suka kaita daki. Zuwa dare su Ibrahim duk sun zo gidan da iyalansu. Kowa yayi bakin cikin jin abinda Izzatu tayi musamman dariyar. Ummahani matar Ibrahim tace ni Yaya tausayi yake bani. Jidda tace tausayin me? Ba fa auren hadi bane da kansa yaje ya kwaso mana ita. Mariya tace kuma dashi suke komai ba. Dama matsalar ka fara abu kenan. Sai kaso denawa mabiyanka suce basu san zance ba. Motoci hudu ne a gidan Yaya amma ko keke bai siyawa ko da Nura ba da yake karatu. Irin abinnan ka daukewa iyaye wani nauyi ko a jikinsa. Daga shi sai iyalinsa. 'Yan kwanakin baya ne ma naga abin ya dan canja. Mama dai tana daga kwance tace ku bar zancen nan haka. A haka sai da Mama tayi sati uku a kwance saboda banda gocewar tayi ta fama da zazzabi. Kullum safe, rana da dare Hamza sai yazo. Da daddaren ma da su Khalifa yake zuwa. Izzatu kuwa tunda baice tazo suje dubiya ba itama ta share. A ganinta yan uwansa ne bazata masa shisshigi ba. Wani lokacin ya hadu da kannensa wadanda suka hade masa kai. Daga gaisuwa basa kara yi masa wata maganar. Su Hajiya suna amsa masa gaisuwa amma suma daga nan magana ta kare. Rashin kula shi da Mama keyi duk yafi komai tada masa hankali. Bashi da aiki sai bada hakuri sai dai tace masa babu komai. A haka rayuwarsu ta cigaba da tafiya har suka dan daidaita. Mama ce dai har yanzu bata yi masa kamar da. Shi kuwa bai kosa da yi mata siyayya ba kullum. Domin yanzu ya dauki irin abinda Ibrahim yake yi tun bayan yayi aure. Kullum sai yazo gidan ya gaishe da iyayensa ko da safe kafin yaje aiki ko bayan magariba. [9/25, 3:34 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿16 Batul Mamman(Mrs)💖 Wata asabar da safe Izzatu ta nemi izinin Hamza tana son zuwa Abuja tunda su Junior na hutun makaranta wurin iyayenta. Ya amince har ya bata dubu hamsin ko zata yi siyayya sannan ya cika mota da mai yasa dreba ya kaisu. Ashe new year celebration taje gani. Sauran shekarun duk tare suke yi da Hamza, ganin yadda lokaci guda ya canja mata yasa bata sanar dashi gaskiya ba. Da yaran ta tafi suka je kallo tare da kannenta. Bayan sati daya suka dawo gida. Zuhra ce take tafe da katuwar ghana must go shake da kayan sanyin da ta saka. Yanzu ta kware sosai don sanyin da ya wuce tayi ciniki sosai. Da yake farkon March ake gari ya soma zafi. Sai dai mijin Anti Faiza ya samar mata wata makarantar primary sun bata kwangilar sakar rigunan sanyin dalibai. Murna sosai su Baba suka yi. Ta gama na farko shine zata kai musu. A daidai wani lungu zata wuce bakin titi ta hango Anas da abokinsa Sani suna busa wiwi. Idonunta kyam a kansu, Anas ne ya fara hangota yayi saurin taba sani. Dukkansu kashe tabar suka yi suna murmushin yake. Fitowa suka yi daga lungun Sani yace kaga manyan yan mata. Zuhra ina zuwa haka da rana? Ta karkace kai tana kallonsu wai nan bagarar dani zakuyi. To nagani kuma sai na fada. Anas yace don Allah kada ki fadawa Baban yara. Kinga muje mu rakaki inda zakije ma. Sani ya karbi jakar zai daukar mata. Da sauri ya mayar ya ajiye...ke yanzu tun daga gida kika dauko jakar nan. Zuhra tace eh menene? Sani yace Anas dauki ka ji. Anas ma dagawa yayi ya mayar Zuhra haka kike da karfi. Wani murmushi ta saki da yasa duk munin kwalliyarta tayi kyau. Au ku da rainani kuke yi? Ai kada ku taba bari dambe ya hada mu don kasa zan kaiku. Sani yace ke dalla can wa ya fada miki maza na son mata karfafa. Ko ni naji nauyin jakar bare ke. Wallahi ina baki shawara idan kika yi aure ki nunawa mijinki ke raguwace. Sai yafi sonki. Amma yana ganin kin fara aje kwanji wata zai dauko a mayar dake maigadi. Zuhra ta sha kunu amma ka zage ni Sani, kai Anas kayi wa abokinka magana wallahi. Anas yayi dariya ai gaskiya ya fada miki. Daukar abu mai nauyi ai ba na yanmata bane. Fizgar jakar tayi ku bani kayana yan wulakanci. Kun tsayar dani kuna ci min fuska..kuma sai na fadi abinda naga kuna yi. Anas yace to yi hakuri. Yanzu ina kika nufa mu daukar miki kayan. Dayake dama ta gaji sosai tace bakin titi. Gidan yayar Hajara zani. Sani ne ya dauko jakar Anas yace yaushe ne bikin Hajara. Nan da sati biyu Zuhra ta bashi amsa. A bakin titin suka tarar mata adaidaita sahu. Anas ya mika masa dari biyu yace ya kaita har kofar gidan da zata je. Tayi musu godiya suka juya. A hanya Sani yace Baabaa yaushe zaka fadawa yarinyar nan kana sonta ne? Anas yace haba Sani. Zuhra tafi karfina. Sani yace Zuhran?yarinyar da ko kwalliya bata iya ba. Ko sakandare bata gama ba fa. Anas yace amma ai tana da tarbiya. Kuma sau nawa Baban yara na kama mu a wurin nan. Ai da kunya nace ina son yarsa. Sani ya bigi kafadar Anas to tun wuri gara ka sani ni zan mata magana. Dama don naga kamar ka rigani fara sonta shiyasa na kyale. Anas ya daure fuska kasan Allah bazan bari ka aureta ba. Zuhra sai mutumin kirki mai rufin asiri. Sani ya soma gudu bari kaga har gida zan sami mahaifinta. Da haka suka tafi suna dariya. Su Zuhra sun kawo kwanar layin gidan Anti Faiza wasu mata uku suka tsayar da mai adaidaitan. Suka yi ciniki yaji kudi yace Zuhra ta sauka. Rai a bace tace haba malam ba haka mukayi da kai ba. Jakar nan nauyi gareta kuma gidan yayi dan nisa daga bakin titi. Naira hamsin ya miko mata gashi ki nemi wani ya karasa da ke. Ba yadda zatayi dole ta fito tana kunkuni. Ta kalli matan sunsha ado da gani biki zasu je ta dan murguda baki...ku ma Allah Yasa ku hadu da wanda zai muku abinda kuka yi min. Dankwalinta ta ciro daga kanta ta gyara hijab din sannan tayi gammo da dankwalin. Tana kicikicin dora ghana must go din taji horn din mota a gefenta. matsawa tayi tana tunanin ko ta tare hanya ne. Horn din ta sake ji sai ta dan juyo taga ko da ita ake. Ba karamin mamaki tayi ba da taga matar mutumin nan mai fadan tsiya. [9/25, 3:35 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿 17 Batul Mamman(Mrs)💖 Zuhra ta washe baki tana murmushi tace ke ce? Izzatu itama murmushin take tace nice. Kingane ni ko? Zuhra ta gyara jakar kanta tace eh mana. To shigo na rage miki hanya Izzatu ta fada tana bude mata gaban motar. Allah Ya sani kayan da nauyi ba musu ta sauke tace ina zan saka jakar? Izzatu ta bude mata booth ta saka sannan ta dawo gaba ta zauna. Sai da ta zauna sannan ta gaishe da Izzatu. Sanyin AC yasa ta wani lumshe ido don har ta fara gumi. Izzatu ta ce gidan Faiza zaki je ko? Kai Zuhra ta daga don ji takeyi kamar tayi bacci. Ba karamin dadi take ji ba yadda sanyi ke busowa ta gaban motar. Ko da suka tsaya tace da mun saba dake cewa zanyi ki sake kunna min sanyin nan ko da na minti daya ne. Izzatu sai dariya tace ai mun saba idan kina so sai na kunna miki amma idan zaki bini gidana. Da sauri Zuhra ta bude kofa, wa ya aikeni naje na hadu da mijinki. Rufa min asiri. Tare suka shiga gidan tana jan jakar kayan Izzatu na binta a baya. Anti Faiza tayi mata godiyar taimakon Zuhra da tayi. Izzatu tace ai ba komai. Kanwar taki ce akwai ban dariya. Ta dauko wayarta daga jaka, dan bani number dinki sai mu rinka gaisawa. Anti Faiza tayi saurin rike hannun Zuhra da take kokarin duba numbarta a cikin wayarta don bata haddace numbar ba. Tana dan yake tace rabu da lamarin Zuhra damunki zata rinka yi da flashing. Zuhra ta zumburo baki haba Anti Faiza nima fa yanzu ba zaman banza nake ba. Da sana'a ta, dan kudin gaisawa dai ina dashi. Izzatu tana dariya tana kallon kayan da Anti Faiza ke dubawa. Daya ta dauka ta bude daga cikin ledarta tace amma sakar nan tayi kyau. A ina kuka siya? Zuhra tayi caraf tace ni nayi. Da gaske Izzatu ta tambaya. Anti Faiza tace eh sanaarta kenan. Izzatu na jin haka tace lallai sai ta karbi numbar Zuhra. Kizo muje gidana ki gwada su Nana sai kiyi musu. Zuhra tana ta zumudi ta bada number sannan ta amince zata je gidan Izzatu tunda ta tabbatar mijinta baya gida. Cikin daki Anti Faiza ta kira Zuhra. Naga kina ta rawar kai akan matar nan. Tunda nake da ita bata taba zuwa gidana ba sai kwanakin baya da suka kusa bige ki a mota. Daga ranar ban kara ganinta ba sai yau duk a dalilinki. Don Allah ki kama kanki nima ba wani sabawa mukayi ba. Aikin kayan flawa take bani tana biyana. Kuma kodayaushe ni nake zuwa gidanta. Zuhra tace to ko dai na fasa zuwa kawai. Nace ta kawo yaran nan. Anti Faiza tace ba haka nake nufi ba. Kije amma ki kula kinji ko. A hanyarsu ta zuwa gidan Izzatu tana ta yiwa Zuhra tambayoyi ita kuma ta dena yar fara'ar da take yi saboda maganar Anti Faiza. Izzatu duk ta damu don ita tsakani da Allah shirmen Zuhra na burgeta. Tace ko dai nayi miki wani Zuhra? Eh to ba wai wani abu kika yi ba, Anti Faiza ce tace na kama kaina a gabanki itama bata saba dake sosai ba. Izzatu tace kuma a sirri ta fada miki ko? Zuhra tace eh....au tayi saurin rufe baki. Kuma wai sai na fada miki. Kai amma banji dadi ba. Izzatu tace bazan taba nuna mata kin fada ba. It's going to be a secret. Zuhra tace uhmmm tana dan murmushi. Turancin yayi tsauri kuma gashi kamar na yan TV ba'a ganewa sosai. Shiyasa tayi shiru kawai. Gida ne mai kyau suka shiga sai dai ga kaya a kwaleye ko ta ina. A falon ma babu kujeru sai carpet kawai. Zuhra tana ta kalle kalle tace tashi kuke ko tarewa? Izzatu tace tashi zamuyi. Babyna ya gama gininsa. Zuhra ta rufe fuska da hijab tana dariya. Wai baby....Izzatu tace shine kike min dariya to ya kike kiran naki saurayin? Zuhra tace bani dashi amma ko na samu ni ban iya irin wannan abin ba. Kunya zanji wallahi. Izzatu tayi dariya sannan ta tashi ta kirawo yaranta daga dakinsu. Zuhra kallonsu kawai tayi tace ta gane yadda zata yi sakar. Suna tafiya tace 'ya'yanki kyawawa kema kyakkyawa. Ke kam kinji dadinki. Ga gidanku ma mai kyau. Yanzu idan kuka tashi wanda zaku koma ya kai girman wannan? Izzatu tace yafi wannan ma. Hira sosai suka yi har Zuhra ta fahimci Izzatu tana da kirki. Har kyautar turare tayi mata da zata tafi. Bayan ta koma gida ne take bawa su Umma labarin Izzatu da kyautar da tayi mata. Sunji dadi amma anyi mata fadan karbar turaren. A nata bangaren Izzatu ta bawa yayarta Zeenatu labarin Zuhra ta waya suna ta dariya. Zeenatu tace irinsu idan kika yi fooling dinsu bazasu gane da wuri ba. Izzatu tace kwarai kuwa. Ita da akayi sirri da ita shine ta fada min. Ina jin APRIL FOOL din shekarar nan da ita zanyi. Zeenatu tace ke da mijinki ya kafa miki doka. Mtsw rabo dashi wannan ai ba harkar kudi bace bazai damu ba. Ke ni har dashi ma zan hada ta fada tana dariya. Dama nace zan rama hanani party da yayi. Zeenatu tace zamu zo Kanon da su Mummy cikin next month kafin na koma Alaska. [9/25, 3:36 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿18 Batul Mamman(Mrs)💖 Bayan kwana biyu Izzatu ta gama tsara yadda zata bullowa Zuhra. Murmushi keta tayi don ta tabbatar ba karamin shan dariya zasuyi ba. Hamza ya dawo gida a gajiye 'yan kwanakin nan baya samun hutu sosai. Wani aiki ne ya sasu gaba, ga shirin tashi sunayi. Duk abin ya rincabe masa. Yana kwance necktie dinsa Izzatu ta shigo dakin ta rungume shi ta baya. Sannu da zuwa my darling. Murmushi yayi mata..kema sannu Izzy. Duk na barku da aiki ko. Ba komai, how was your day? Alhamdulillah ya bata amsa. Amma ina jin yunwa sosai. Me kika dafa mana yau? Ban fahimceka ba, ka manta yau thursday. Ga yara sun dawo daga school kowa yunwa muna ta jiranka. Naso kiranka na tuna maka a kawo na rana sai nayi bakuwa. Tun kafin ta gama magana ya rufe idanunsa saboda ransa da ya baci. Ba rashin girkin ne ya dame shi ba kamar yunwar yaran. A hankali ya kalleta Izzy ina ganin lokacin canja wannan tsarin yayi. Ga 'ya'ya Allah Ya bamu. Ki duba irin ayyukan da suke gabana kinsan dole na manta. Kuma su yaran ba kya jin tausayinsu ne. Ko indomie sai ki dafa musu. Ta harare shi wasa ma kake yi Hamza. Duk tsarin da muka yiwa rayuwarmu tun kafin aure yanzu a hankali kake soke komai. Don kawai kaga ina hakuri. Tana magana sai kuka ya kwace mata. Kada ka bari soyayyarmu ta ja baya saboda sabon ra'ayinka. Ni ba wannan Hamzan na aura ba. Wanda na aura ya damu da farincikina. Tausayi ta bashi ya rungumeta yana bata hakuri. A hankali yake magana. Izzy ya kamata mu fuskanci rayuwa a yadda take. Na daukar miki alqawura da dama ba tare da dogon tunani ba. Ba kullum ne zamu sami abinda muke so ba. Kinga saboda bana son tsegumi da kaina nake siyo mana abinci duk alhamis. Yau na gaji ga ayyuka. Ki daure ki rinka girkin ni kuma duk lokacin da nake da time sai na siyo a waje mu ci. Ta dago fuska sharbe da hawaye to naji amma sai ka amince ranar da zamu tare zamu danyi walima mutane su tayamu murna. Izzy na dauka mun rufe irin wadannan abubuwan. Tace walima nace ba party ba. Ko kida bazamu kunna ba I promise. To ba komai amma har yaushe zaki shirya wata walima. Tace ka bari sai nan da kwana tara mu koma. Jumaa ta sama kenan, mu sami albarkar Jumaa. Yayi dariya to naji amma please kafin nayi wanka abinci....tana tafiya tace Jumaa 1st April tayi kwafa. Su Zuhra ana ta shirye shiryen bikin Hajara zama ya gagare su. Kullum sai sun fita. Sune kasuwa ko wurin mai dinki. Ana saura kwana biyu kamu ta dawo daga raka Hajara saloon din unguwarsu taji Baba da Umma suna magana a tsakar gida. Allah Yasa Hajaran ta wuce gida. Baba ne yake cewa...ina farinciki da auren Hajara amma lamarin Zuhra na damuna. Duk samarin da ke zuwa sai kiga babu na aure. Bana son tayi ta zama a gida tunda ba karatu take yi ba. Umma tace haka ne, kuma abin ba zai dameta ba yanzu sai taga an kai Hajara dakinta. Amma da kake damuwa yarinyar nan ko shekara ashirin da daya bata cika ba. Baba yace to ai dai ta kusa. Shekaranjiya da naje Ajingi baki ji fadan da Inna tayi ba wai mun sa yarinya a gaba munki yi mata aure. Yaya Sabiu kuma sai cewa yayi ko Garzali ne na wajensa a hada su tunda shima yaki karatun. Zuhra tana daga soro ta dafe kirji....Yaya Garzali kuma? Allah Ya kiyaye. Mutum mai shegen ji da kai kamar wani mai mulki. Baba taji yace duk da ba kudi gareni ba bana fatan yarinyar nan ta auri mara ilimi irinta. Ba mai kudi nake jira ba amma ina mata fatan samun rufin asiri a rayuwarta. Umma tace Allah Yayi mana zabi nagari. Idan ta dawo sai kayi mata maganar Garzalin tunda a gaban Inna akayi ya kamata ta sani. Hawaye ne suka saukowa Zuhra ba tare da ta sani ba. Allah Sarki Baba da Umma. Sai yanzu take jin inama ta dan mayar da hankali a makaranta. Wayarta ta zaro daga yar jakarta ta bude sakonnin da yau kwana uku kenan kullum sai anyi mata safe da dare. Ta rasa ko waye yake mata wadannan sakonnin soyayya. Lokaci yayi da zata dena sharewa kila alkhairin da Baba ke jira ne ya tunkaro ta. Ta goge fuska ta shiga ciki. Jikin Umma ta fada tace wash Allah nagaji sosai. Umma ta ture ta to dagani kada ki karasa kashin tsufa. Zuhra ta tashi ta koma kusa da Baba. Tana dan daga gira tace in kwanta a jikinka Baban yara? Rankwashi ya kawo mata ta goce...yarinyar nan kin gama rainani. Wayarta ta mika masa Baba sirri nazo muyi. Umma tace ai sai dai idan na fita amma babu inda zani ayi a gabana. Shi kuma Baba yana murmushi yace to ko daki zamu shiga. Dariya kawai tayi ta bashi wayarta ta nuna masa sakonnin text da ake yi mata. Baba ya karanta yafi sau uku uku murmushinsa na fadada yace waye wannan? Zuhra tace nima ban san shi ba. Amma kaga a sakon karshe yace yana jiran amincewata ne ya gabatar da kansa wurinka. Da izininka zai fara zuwa. Duk dadi ya kama Baba sai murna yake. Umma tace kuyi min bayani mana. Baba yace saurayi muka yi. Umma tace kai Baban Zuhra akan yar nan ka iya rufe ido ka manta kai babanta ne. Yace to da 'yar wani kike so nayi. Kinga Zuhra ki tura masa da amsa mai dadi...banda shirme kinji ko sannan kice kin amince ya gabatar da kansa. Tunda yace yana aiki a wani kamfani ai kinga ko ba komai da dan iliminsa ko da na sakandare ne. Karfe tara na dare text ya sake shigowa wayar Zuhra. ** Kewarki ta dameni, ki amince na nuna miki soyayyata gareki** Wani juyi Zuhra ta rinka yi cike da tsananin jindadi. A yan kwanakin nan ta tsinci kanta da jiran text duk safiya da dare. Reply ta tura kamar yadda Baba ya bata shawara ** Na amince** Har Izzatu ta kwanta taji shigowar text. Hamza ya kai hannu zai dauki wayarsa tayi saurin dauka. Yace ni da wayata zaki min kwace? Tayi murmushi ta bude ta karanta. Dadi ne ya kamata. Hamza yace text din waye ne kike murmushi. Kamar yadda ta saba saurin gogewa tayi tace kyale tallan MTN ne. [9/25, 3:37 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿19 Batul Mamman(Mrs)💖 Su Zuhra an fara biki. Sunyi kamu ranar laraba a wani fili nan cikin layinsu. Yan makarantarsu da yawa sun zo bikin. Wata cikinsu mai suna Ikilima ce tayiwa amarya kwalliya. Zuhra tana daura dankwalin ankonta Ikilima tace don Allah ki bari nayi miki kwalliya. Wannan fuskar taki duk kin bata ta. Tissue tasa ta goge fuskar Zuhra sannan tayi mata kwalliya. Nan kawayensu suka rinka cewa tayi kyau sosai. Washegari da babu abinda zasu yi amma an dan taru a gidansu Hajara. Yan mata kuma suna gidansu Zuhra. Tana zaune ana yi mata kitso wayarta tayi kara. Ta daga taga sunan Izzatu. Hankalinta ya dan tashi bata gama mata sakar yaranta ba. Hakuri ta soma bata tana daga wayar. Izzatu tace ba komai ai nasan kuna bikin kanwar Faiza. Ni magana daban na bugo muyi. Zuhra tace to ina ji. Izzatu tayi yar dariya, dama ranar da kika zo gidana kina fita kanina ya shigo kila ma kin ganshi. Zuhra ta dan yi tunani kai babu kowa a hanyar. Izzatu tayi saurin gyara zancen kada Zuhra ta gane. Cewa yayi ya ganki don yana shigowa tambayata yayi ko kina da aure. Nace a'a. Shine ya dame ni har na bashi numbarki. Ina tsammani ya kiraki ko yayi text. Daga daya bangaren Zuhra taji wata murya mai dadi ana cewa haba Izzatu na fada miki ban fara yi mata waya ba sai naga babanta. Zuciyarta har wani saurin bugawa tayi, ba dai mai yi mata text dinnan bane. Izzatu ta katse mata tunani yace sai gobe zai zo gidanku magana da babanki bayan magariba. To a ranar zamu tashi shine za'ayi walima a sabon gidan. Don Allah kizo in nuna miki shi. Ni a ganina gara ku fara haduwa kafin maganar taje ga iyaye. Kuma sunansa Hamza don yace bai fada miki ba ko. Lallai da gaske Izzatu take don jiya yayi mata text yace zai zo ranar Jumaa. A take taji tana jin kunyar Izzatu. Ashe ma dan gayu ne indai kanin Izzatu ne. Ji tayi ance Zuhra zaki iya zuwa din ko ma hadu a gida? Farinciki fal zuciyarta ta rike wayar tana murmushi. Wai ita ce saurayi ke mata magana irin haka. A hankali tace zanzo in sha Allah. Daga nan ta ajiye wayar. Izzatu ta kalli kaninta Walid tace gobe akwai show a gidan nan. Walid yace amma sis sai naji ba dadi kuma. Dungure masa kai tayi...to kill joy idan ka ga dama kada ma kazo. Ya gyara face cap dinsa da ta karkace wai da yaya kike daukar wayar Hamza ne bai sani ba? An gaya maka ni din ta wasa ce? Baya amfani da wayar sosai sai nace ya bani aronta don kada Zuhra tayi text ko waya yana office. Bayan an watse ne ta sanar da Umma yadda suka yi da su Izzatu. Umma tace ba komai amma idan kinje kada ki dade saboda lanchin din Hajara. Ku ne iyayen biki. Haba ai bazan dade ba Umma. Don tana ta rokona ne ma. Umma tace ba komai ki yi sauri dai. Daga nan fita tayi taje ta sanar da aminiyarta Hajara. Amma fa ban fadawa Umma zamu hadu dashi ba. Hajara tayi mata dundu tana dariya tace yarinya ta fara sanin soyayya. Tana dawowa gida ta tarar da Umma tana wanke wata farar shaddar Baba mai kyau. Zuhra tace gobe zashi daurin aure ne? Umma tace ba kince yaron nan Hamza zai zo gaishe shi ba, ai gara a ganshi da kwarjininsa shima. Wani dadi Zuhra taji tace to kawo na karasa wankin. Umma tace bari dauraya ta rage min. Biyun dare ta wuce sannan aka kawo wuta. Zuhra ta tashi tana magagin bacci dama jiran wutar take yi. Da sanda ta lallaba ta dauko kayan Baba daga shanya tazo ta goge masa. Itama cikin kayanta na bikin Hajara ta sake gogewa. Daya zata je gidan Izzatu walimar tarewa, dayan kuma sai da yamma idan Hamza yazo. Rigunan sanyin da ta karasa sakawa ta saka a leda ta gama shirinta tsaf. Shigen gyaran girar da kawarta tayi mata a kamun Hajara ta kokarta tayi. Sai dai tata tayi girma da baki da yawa. Leben nan yasha janbaki purple don ance mata shi ake yayi yanzu. Tayi daurin dankwalinta sannan ta kawo katon mayafi ta dora a kai. Umma ta yaba da kwalliyar tace idan kin kai mata kayan kada ki karbi kudi tunda kinga inda rabo kaninta zaki aura. Zuhra tayi dan murmushi tace to Umma. Ko daga nesa ka hangota za ka san tana cikin nishadi. A haka ta je gidan anti Faiza don tare zasu tafi. Anti Faiza tace naga alama dai Izzatu na ji dake. To dai muyi sauri kinga akwai sauran shiri a gabanmu. Ni ba don aikin meatpie dinta ba ai ba inda zani. Sai dai ta bani fiye da kudin aikin shiyasa na karba. Dreba Izzatu ta turo ya dauki su Zuhra saboda kulolin da Anti Faiza ta zuba meatpie har uku ne. Hamza ya gama magana da lauyansa an gama komai a takardun tsohon gidansa. Da daddare in Allah Ya yarda zai kaiwa Alhaji a bawa kaninsa Nura. Idan yaso in ya tashi aure sai a kara gyara gidan. Ya dan shafi kansa yasan yau iyayensa zasuyi farinciki da abinda yayi musamman Mama. Sakonnin email dinsa ya bude yana karantawa don yau bazai koma gida da wuri ba sai sun gama walimarsu. A firgice ya tashi yana kiran Inuwa sakatare. Inuwa ya shigo da sauri yana tambayar ko lafiya. Hamza ya nuna masa wani sako da aka turo daga Mr Peter wakilin turawan da suka hada gwiwa dashi. Gumi ke keto masa ko ta ina yace Inuwa mutanen nan sunsha kwaya ne da zasu ce wai suna yi min tuni akan basu ribar da muka samu a watannin nan shida gaba daya. Ya ture takardun tebur dinsa. Ni ban fahimce su ba kwata kwata ina aka taba kasuwanci haka.. Inuwa yace ranka ya dade ka manta a contract din ance ribar wata shidan farko tasu ce. Daga nan kuma sai ku rinka raba ribar kai da su. Hamza ya daka tsawa inji uban wa??? Inuwa ya zabura ya matsa gefe. Wata tsawar ya sake yi jeka ka dauko min copy din contract din. Inuwa jiki na bari ya bude wata drawer a cikin office din Hamza ya dauko masa. Karantawa yake yana maimaitawa. Ya dago idanunsa da suka yi ja yace Inuwa garin yaya nasa hannu a takardar nan? Inuwa ya tausayawa ogansa yace ranar da Junior ya karye ne. Nima bayan ka fita na sake karantawa shiyasa na turo maka da text a daren. Hamza yayi saurin dago kai. Text kuma? Eh text na sake maka bayanin contract din ko zaa gyara tun kafin abin yayi nisa. Kuma ka tabbatar min ka karanta. Don kace Hajiya ta sanar da kai na bugu waya ma. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Izzatu kin kasheni shine abinda Hamza ya iya fada a hankali. [9/25, 3:40 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿20 Batul Mamman(Mrs)💖 Lokacin da suka isa gidan cike yake da mutane tamkar ana biki. 'Yan gidansu Izzatu har da mamanta duk sun zo. Ga kawayenta da makota da wadanda ma ba'a sansu ba 'yan cin ta tsotse. Kannen Hamza kuwa Mariya ce kadai taje sai Ummahani matar Ibrahim. Su Hamida suna Kumo ita da Adabiyya da Nura. Gidan ya tsaru sosai kana gani kaga gidan babban architect. Sama da kasan ko'ina mutane hawa sukeyi ana kallon yadda aka kashewa gidan kudi. Zuhra sai rakube rakube take yi ita tazo gidan surukai. Anti Faiza tana mata dariya don Hajara ta tsegunta mata zancen kanin Izzatu. Izzatu na ganinsu sai murna tasa aka shigo da meatpie din aka hada shi cikin kayan rabo. Zuhra ta mika mata kayan sanyi tace bari na dauki miki kudinki. A kunyace Zuhra tace ta barshi. Tayi murmushi ta fita bari a kawo muku abinci. Hamza ta fita ta kira tana rokonsa yazo gida Mummynta tana son ganinsa. Muryarsa a dashe saboda tsananin bacin ran da yake ciki yace mata ya kusa karasowa gidan. Da sauri ta koma dakin da ta bar su Zuhra tace mata dan sake gyara fuskarki muje. Anti Faiza tace ina zaku ake magana bama ganewa? Izzatu tace sirri ne. Kawayenta na dakin kuwa sun gane suma dariya suke yi. Yan kayan kwalliyar jakarta ta dauko ta sake shafa hoda da janbaki. Fuskar nan ta fita daban da sauran jikinta saboda kyallin foundation. Tun a dakin kannen Izzatu da yayarta Zeenatu ke dariya kasa kasa. Ita kuwa uwar gayya ko a jikinta tace da Anti Faiza yanzu zata dawo su tafi. Mamaki Hamza yayi yadda gidan ya cika da mutane haka. Yadda yake ji idan Izzatu bata yi da gaske ba zai iya marinta. Sanadiyar bin al'adun wasu ta janyo masa asara mai girma. Ita ta tada masa hankali yasa hannu a takardar ba tare da yasan me yake yi ba. Kuma ta goge masa messages. Tsaki yayi ya shiga gidan ta baya. Wani karamin falon ya shiga shiga ya kirata a waya. Bata kawo komai a ranta ba jin yanayin muryarsa. Burinta kawai taga yadda zasu kwashe da Zuhra idan sun hadu. Its Zuhra zaman jiran da take yi a falo ya fara isarta don ma da mutane. Da sauri Izzatu tazo da tray a hannunta dauke da juice da soyayyan nama a karamin plate ta mika mata. Muje ku gaisa ku tafi Faiza duk ta damu. Zuhra ta dan gyara mayafi ta karbi tray din. Sai da suka je kofar falon duk taji kunya kamar kada ta shiga. Izzatu ta turata tare da komawa falo tana sanar da mutane su shirya dariya zata yiwa wata April Fool. Mariya na jin haka ta mike da sauri tace da Ummahani kila yarinyar nan ce. Na rasa abinda ke damun Izzatu. Bata kara magana ba suka ji karar fashewar tangaran. Lokacin da Zuhra ta shiga falon da sallamarta. Hamza ya taso a fusace yana cewa Izzy kinsan abinda kika jawo min yau? Zuhra tayi saurin daga kai suka hada ido, bata san lokacin da ta saki tray din ba. Mutumin nan da ya kusa marinta ta gani. Bakinta har rawa yake tana cewa yayi hakuri ta durkusa tana tsince sauran jug da kofin da ya fashe. Dama a harzuke yake yace me ya shigo dake falona? Waye ya bude miki? Duk ta kidime tace Anti Izzatu ce. Zuwa lokacin kofar falon ta cika da yan gidansu Izzatu har da ita. Sauran mutane ma jin ana daga murya suka zo kallo. Hamza yace ita Izzatun ce ta bude miki falona tace ki shigo. Zuhra tace eh. Hamza na daga murya yace ba kece mara kunyar yarinyar nan ba, wato sata kika zo yi. Da sauri ta girgiza kai tace a'a wurin Hamza nazo. Daga shi har Zuhra babu wanda hankalinsa ke bakin kofa bare su ga yadda mutane ke kallonsu. Yan gidansu Izzatu da suka san komai sune suke dariyar yadda jikin Zuhra ke rawa. Yace Hamza? To nine Hamzan ya akayi? Zuhra tace ba kai Hamzan ba. Kannin anti Izzatu ne yace yana sona shine yake min tes. Ita tace na zo nan yana jirana wallahi. Hamza ya runtse idanunsa yace idan na bude baki bace min a wurin nan ba sai na bata miki rai. A gigice ta juya ta hango Izzatu. Ta karasa gabanta tace yi hakuri na fasa miki kaya. Amma ni ban gane ba mijinki yace shine Hamza. To waye kanin naki? Wata irin dariya taji sun kwashe da ita suna cewa APRIL FOOL!!!. Ko da bata gane me suke nufi ba amma dariyarsu tayi mata ciwo sosai. Hawaye kawai take yi ko gani bata yi sosai yadda hawayen ke zubo mata tace Apre..me? Kanwar Izzatu ta sake cewa April Fool. Da wannan fuskar taki kike tunanin yin saurayi dan gayu. Ina ji kuna hirar da matar da kuka zo. Anti Faiza tace Izzatu wai me yake faruwa ne. Na zata kuskure kikayi da kika ce a nan kanin naki yake jiranta. Ba sai kiyi musu bayani ba. Da kyar Izzatu ta tsayar da dariyarta tace ni nake yin text din. Hamza kallon Izzatu yake yi tana dariya ita da yan uwanta. Sauran mutanen wurin kuwa kadan ne abin ya basu dariya. Sauran tausayin Zuhra suke yadda rashin sani yasa ta fuskanci wulakanci. Anti Faiza ta rungumo Zuhra wadda bata san inda take jefa kafafunta ba. Sautin dariyar da aka yi mata kawai take ji a kunnuwanta. Izzatu ta cigaba da cewa april fool nayi mata na rinka tura mata text din soyayya. Ta zata saurayi tayi har ta amince. Ta dafa kafadar Zuhra ta sake cewa april fool. Kada ki damu it was just for fun. Saukar mari taji mai kamar wuta a kumatunta kafin Hamza yace kowa ya fice masa daga gida. Mata suka tsaya kallonsa ya daka musu wata tsawa. Ba shiri suka fara bacewa. Izzatu na dafe da kumatu ta juya taga ba Hamza, Zuhra da Anti Faiza. Anti Faiza jan hannun Zuhra kawai take yi har suka fita daga gate din gidan. Ummahani ce tayi musu horn Mariya na gaban motar suka ce su shigo. Anti Faiza tace su tafi kawai. Mariya tace kiyi hakuri ku shigo kada a rinka kallonta kinga an fara fitowa.. Anti Faiza tana ta cewa su tsaya zasu sauka a hanya amma Ummahani taki tsayar da motar. Mariya tace ki kwantar da hankalinki zamu kaiki inda za'a bi muku hakkinku. Anti Faiza ta cije lebe tana kallon yadda Zuhra ke zubar da hawaye tace Allah zai isar mana ku ajiyemu kawai ba sai munje wurin yan sanda ba. Ummahani tace gidansu Hamza zan kaiku. Ni matar kaninsa ce, wannan kuma kanwarsa ce. Sai a lokacin Zuhra tace ku ajiye mu don Allah. Mariya ta juyo ta kalleta. Dole Zuhra ta baka tausayi. Wannan karon Izzatu ta wuce gona da iri. Kiyi hakuri mun kusa zuwa gidan. Anti Faiza tace kunga bama son wani wulakancin ku barmu kawai. Ummahani bata tsaya ba sai a cikin gidan don tayi saa an budewa Alh Nasiru gate zai fita kenan suka shigo. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [9/25, 3:40 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿 21 Batul Mamman(Mrs)💖 Ummahani na tsayar da motar Mariya ta fita da sauri ta tari Alhaji. Su Anti Faiza kuwa fita suka yi daga motar suka yi hanyar gate zasu fita. Muryar dattijo suka ji yace don Allah su tsaya. Kuka Zuhra ta cigaba tana jan hannun anti Faiza. Mariya ta zo gabansu tace don girman Allah ku tsaya. Ba yadda zasuyi dole suka biyo bayanta. Amma duk yadda aka yi Zuhra ta kafe bazata shiga cikin gidan ba. Kukan da take yi yasa Alh Nasiru yace Anti Faiza da ke mata fada ta kyaleta. Sai a lokacin Zuhra ta kalli dattijon. Ko ba'a fada ba tasan shine baban mijin Izzatu saboda sunyi kama. Da sauri ta durkusa har kasa tace ina wuni? Lafiya kalau ya amsa fuskarsa dauke da murmushi. Kallonta yake yadda take goge hawaye da majinar fuskarta da dankwalin kayanta. Sannan ta nade kanta da jikinta da katon mayafi. Suna nan tsaye Mama da Hajiya suka fito tare da Mariya. Hajiya tace yanzu Mariya ke fada min munyi baki kuma wai sunki shigowa. Anti Faiza da Zuhra suka gaishe su. Mama ta ce ya naga bakuwar na kuka Allah Yasa lafiya. Alhaji yace Mariya ta dan soma fada min. Ku daure mu shiga ciki. Mama ce tazo ta kama hannun Zuhra ta tayar da ita suka shiga cikin gidan ba don tana so ba. A falo suka zauna Zuhra da Anti Faiza suka rakube jikin kujera. Mariya ta bada labarin abinda idanunta suka gane mata a gidan Yaya. Mama da Hajiya sai salati suke. Ita kam Hajiya har kunya taji ace wai Hamza danta ne kuma na fari ma. Alhaji ya dubi su Zuhra yace ko zaku yi mana bayanin yadda abin ya samo asali. Nan Zuhra ta soma basu labari. Tana yi tana kuka. Su Ummahani sunji tausayinta sosai. Alhaji yayi murmushin bacin rai Mariya ku tashi ku kaisu gida. Sai ku gane mana gidan. In sha Allah anjima zamu zo gidan nayi magana da mahaifinki. Amma kafin nan don Allah kada ki sanar dasu komai. Zan gyara matsalar in sha Allah. Mama ta matsa kusa dasu ta rike hannun Zuhra ki yi hakuri kinji 'yata. In Allah Ya yarda Alhaji zai share miki hawaye kuma zai hukuntasu daidai da abinda suka yi miki. Zuhra ta gyada kai ni dama dariyar ce ta fi bani haushi. Anti Faiza tace to ba an baki hakuri ba. Tashi mu tafi. Bayan sun fita Mama tace Hajiya ya kika yi shiru? Hajiya tace hmmm to me zan ce? Kina kallo kullum lamarin gidan yaron nan kara lalacewa yake. Wai april fool sai kace wasu kasurguman kafirai. Na rasa yadda ake suke kwakulo duk wata al'adar banza suna dabbaka ta. Alhaji yace ku kyale ni dashi. Alkawari ne tsakaninmu akan idan haka ta sake faruwa zan hukunta shi.....wani murmushi kawai Alhaji Nasiru yayi. Sai na nunawa yaron nan nima ina riko da namu al'adun nagari. Izzatu ta rike kumatu ta soma kuka. Ita Hamza zai mara a gaban mutane. Sai a lokacin ta kula kowa ya watse sai yan gidansu da mamanta. Da sauri ta nufi wurinta zata rungumeta, sai taga maman tata ta matsa. Izzatu ta zaro ido meye ma'anar hakan. Raliya mahaifiyar su Izzatu ta kalli 'yarta fuskarta na nuna alamun rashin jindadi tace Izzatu that was extreme. Ban taba nuna damuwata ba idan kuna wasanku ke da yan uwanki. Kuma ni mutum ce da ta yarda a bar yaro ya sake yayi abinda ransa yake so. Amma ban yarda da cin zarafin wani don nishadi ba. Me yarinyar tayi miki haka da har zaki kirawota har gidanki ki mayar da ita laughing stock(abin dariya) a gaban mutane? Hawaye ne ya cigaba da sauka daga idanun Izzatu tace Mum har me nayi mata? Kawai ba'a fahimceni bane amma yi nayi don ayi dariya. Raliya tace kada ki manta yarinyar nan nan mutum ce kamar kowa. Ya zaki ji idan kika sa rai da abu kamar soyayya sai kawai ace miki wasa ne har a biki da dariya? ta dubi sauran 'ya'yanta ku tashi mu tafi. Laifinmu ne ni da Dad dinku da muka dora ku kan al'adun da basu dace da society dinmu ba. Gashi mun dawo Nigeria kina ta samun matsala da inlaws dinki. Izzatu na kallo duk suka fita jiki a sanyaye. Share hawayenta tayi ta hau sama. A hankali ta bude kofar dakin ta hango Hamza zaune a kan kujerar gaban madubi ya dafe kansa. Karasa shiga tayi ta tsaya a gabansa, ka kyauta Hamza. You slapped me for no reason. A yadda ya dago kansa sai da ta razana ta matsa baya da sauri. Gani take wani marin zai kai mata. Har wani huci taga yana yi saboda yadda ransa yake a bace. Izzy kinsan abinda kika yi kuwa? Ta dan sha kunu ita a dole bazata nuna masa ta yarda tayi laifi ba. Don kawai nayi april fool shikenan sai ya zama laifi. Har ka manta babu shekarar da bama yiwa juna. Last year kaya ka kawo min wai na fadar kashiya. Sai da na gama yarda nasha kukana sannan kace april fool. Shi inda ya dosa daban da abinda take fada. Saboda tashin hankalin da yake ciki ya manta da wani wasan april fool da tayi. Wannan last year ne, har kin manta nace mun dena duk irin wadannan abubuwan. Tace ban manta ba amma ai wannan ba na kudi bane. Ya rasa yadda zaiyi da ita. Kinga sami wuri ki zauna kin tsaya min a ka. Bakin gado ta zauna tana fuskantarsa. Izzatu ya kira sunanta..... naam. Kin taba goge min text da Inuwa ya turo ranar wedding anniversary dinmu? Dan tunani tayi tace eh, amma na karanta farkon sakon na kuma fada maka abinda nagani. Shine duk ka wani daure min fuska har da mari. To wallahi bazan hakura ba. Ta fadi maganar ne tana tashi. Bata ankara ba taji ya janyota iya karfinsa ya hadata da bango. Da sauri yake numfashi don ji yake kamar zuciyarsa zata iya bugawa. Idanunsa duk sun kankance. Sai a lokacin Izzatu ta ji tsoro tayi tunanin tambayarsa abinda ya same shi. Kafin tayi magana yace daga yau idan kika sake daukar min waya sai nayi miki abinda baki taba tsammani ba. A dalilin wayar karyar da kika yi kika ce Junior ya karye da deleting text dina da kika yi karayar arziki na iya samuna. Ga mamakinta hawaye ta ga ya zubo daga idanunsa, abinda bata taba gani ba. Nan da nan ta rikice, babyna ya zamuyi idan ka talauce? Zamu sami abincin da zamu ci ko sai Daddyna ya taimaka mana? Gashi kayi min alkawarin zaka canja min mota. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun ya ke nanatawa. Zancen ace ransa ya baci da maganarta ma bata lokaci ne. Izzatu dama baki da hankali??? Tace bangane ba. Ya daga murya ya soma fada... ina fada miki matsalata kina zancen canjin mota. To hell with canjin motar taki. Ya dauki kujerar gaban madubin yayi wurgi da ita. Wani irin bakinciki yake ji wanda yake tunanin idan ya taba Izzatu kila sai dai ta kwana a asibiti. Ba talauci ba ko me zai sameni tare zamu zauna. Kin jawo min tashin hankali kala kala kinga ina rabuwa dake shine yanzu zan fada miki halin da zamu iya fadawa kiyi zancen damuwarki ta banza. Gefe ta koma don gaba daya ta tsorata da Hamza. Mutum ne wanda da wuya kaga bacin ransa. A hankali ta soma matsowa kusa dashi zata bashi hakuri sai wayarsa tayi kara. Ita ma wayar ji yayi kamar ya kwadata da kasa sai yaga Alhaji ne yake kiransa. Yana dauka Alh Nasiru yace ana saukowa daga masallaci kazo ina nemanka. Sai kawai ya kashe wayar. Hamza ya rike wayar yana kallonta...Allah Yasa ba gulmar abinda ya faru dazu Mariya ta kai gida ba. [9/25, 3:41 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿22 Batul Mamman(Mrs)💖 Daga masallaci gidansu ya wuce ya baro Izzatu tana ta aikin kuka a gida. Lokaci daya duk ya birkice mata abinda bata saba gani ba. Allah Ya sa su Khalifa ta hadasu da Tala suna dakinta suna cin abinci duk wannan tashin hankalin da ake yi. Baiyi mamakin ganin motar Ibrahim ba don yasan kullum sai yazo gidan. Yana ta sallama yaji shiru ba'a amsa ba. Kande mai aikinsu ce ta fada masa suna dakin Alhaji. Sallama yayi ya shiga ya tarar dasu suna ta hira. A ransa yace babu wanda yasan matsalar da yake ciki. A lokacin da yake jindadi bai kyautatawa iyayensa yadda ya kamata ba saboda haka yanzu bashi da dalilin tada musu hankali ya fada musu halin da kamfaninsa zai iya shiga. Mama na ganinsa ta washe baki ta soma guda. Murmushin yake yayi yace Mama alkhairi muka samu ne? Kwarai kuwa Yaya in sha Allahu alkhairi zamu samu. Ya karasa ciki ya gaishe da iyayensa. Ibrahim ya miko masa hannu suka gaisa suna tambayar juna aiki da iyali. Bayan sun dan nutsu Alh Nasiru yace bayan magriba in Allah Ya yarda zamu je gidan surukan naka. Hamza ya kalli Ibrahim da alamar tambaya. Alh Nasiru yace da kai nake Yaya. Ni kuma Alhaji, wani abin ne ya faru? Mama ta katse shi cike take da murna tace babu komai. Rabon da ta sake masa sosai tun kafin ta karye a gidansa. Alhaji ya ce bani hankalinka nan Yaya. Duk aka yi shiru ana sauraronsa. Dazu Mariya da Ummahani sun zo gidan nan da yarinya tana ta kuka akan cin zarafin da kuka yi mata kai da matarka. Hamza yace wallahi Alhaji ban san da abin ba sai da naje gida. Yau har marin Izzatu nayi akan abinda tayi. Hajiya ta tabe baki sai kace kayi wani abin arziki. Ai ba laifinta bane ita kadai. Alhaji ya cigaba da magana...kasan akwai alkawarinmu na ka amince da duk hukuncin da zan dauka a kanka idan irin haka ta sake faruwa ko? Tuni Hamza ya gano inda Alhaji ya nufa..muryarsa har tana sarkewa yace don girman Allah Alhaji kada kace nema min auren yarinyar nan zaka yi. Kayi min wani hukuncin ba wannan ba. A rana daya abubuwa sai samunsa suke yi. Ba don kada ya nuna karayarsa ba babu abinda zai hana shi fashewa da kuka. Alhaji yayi yar dariya. Dadina da kai akwai hazaka gashi har ka gano inda na nufa. Kamar yadda kuka sawa yarinya rai cewa bayan magariba zaka je gaishe da mahaifinta to tare zamu ayi mai gaba daya. La'ila ha ilallah...Alhaji kayi hakuri. Idan kaga Hamza a lokacin shima sai ya baka tausayi. Yana cikin wannan matsalar ina shi ina aure. Auren ma da wannan kucakar yarinyar mara kunya. Muryar Alhaji ce ta katse masa tunani. Wallahi idan har kaki yarda da auren nan daya hukuncin da zan iya yanke maka shine na zare hannuna daga dukkan abinda ya shafeka. Babana ba fa kai kadai na haifa ba, kuma kaine na fari amma matsalar gidanka ta isheni. Sam ka kasa rike matarka. Hamza yayi shiru yana jinjina kalaman mahaifinsa. Can dabara ta fado masa yace Alhaji nayiwa Izzatu alkawarin bazan taba yi mata kishiya ba. Alhaji ya tashi yana cirw babbar rigarsa yace ashe auren zobe kuka yi bamu sani ba. To kada ka damu yanzu ma alkawarin naka bai tashi ba tunda ba kai ka nemi auren ba. Ita da kanta ta nema maka. Mu nan karashen aikin ta barmu dashi kawai. Ka tashi ka tafi gida ka saka manyan kaya don bazamu gidan surukai da kai a haka ba ka wani ci zanzaro. Ko kazar da kwai ya fashewa a ciki zata fi Hamza kuzari. Daga kafa yake kamar ba'a jikinsa take ba. Ko da ya koma gida dakinsa ya shiga ya rufe. Izzatu tayi bugun har ta gaji. Bai fito ba sai da aka kira magariba. Yayi wanka ya canja kaya. Ba don kuncin da zuciyarsa ke ciki ba sai ka zata sabon ango ne....kodayake ya kusa zama angon! Masallaci ya fara zuwa yayi sallah sannan ya wuce gida. Alhaji da Ibrahim ya gani a shirye suna jiransa. Mama har bakin mota ta rakosu tana musu fatan alheri. da ta shiga gida Hajiya tace wato duk gidannan kinfi kowa farinciki da wannan abin. Mama tayi dariya Hajiya bazan taba manta abinda Izzatu tayi mana ba. In Allah Ya yarda yanzu Yaya zai san yayi auren yar da ta dace da addini da al'adarsa. Yadda Ummahani ta kwatanta masa haka Ibrahim ya bi. Hamza yana gaba kamar ruwa ya cinye shi. Alhaji da Ibrahim sai hirarsu suke yi. Daga bakin layin suka ajiye motar Ibrahim yace daga nan na manta kwatancen, Yaya ya ma sunan yayartawa? Wata muguwar harara Hamza yayiwa Ibrahim kafin yace zanci.....Alhaji yayi gyaran murya don yasan karshenta zagi Hamzan zaiyi. Yau ya zama a lallaba auren zamani. Ibrahim dai dariya yayi sannan ya kira Ummahani ta tuna masa sunan. Da tambaya suka sami gidan domin ba wuyar ganewa. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [9/25, 3:42 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿 24 Batul Mamman(Mrs)💖 Wurin goma da rabi na safe kukan Nana ya tashi Izzatu daga bacci. Tana bude ido ta kalli agogo. Da sauri ta sauko daga kan gadon ta dauki Nana da ke kawo karar Junior ta tafi dakin Hamza. Abin mamaki a rufe taji dakin. Ta tsaya tana bugawa Khalifa yace Daddy ya fita. Ranta ne ya baci. Tunda suka yi aure ranaku kadan ne suka taba kwana daki daban shima sai da dalili mai karfi. Amma akan abinda bai kai ya kawo ba shine jiya yaki tashinta daga bacci ta koma dakinsa kuma yau harda kulle kofar daki. Kwafa tayi zai dawo ya sameta ne. Bayan tayi wanka ta sauko kasa. Tala ta gyara gidan tas kamar ba'ayi taro a cikinsa ba. Hatta su Khalifa duk tayi musu wanka. Da yake asabar ce babu makaranta. Sabon dakin wasansu suka tafi suna ta tsalle tsalle. Tala ce ta rugu da gudu ta kawowa Izzatu wayarta da ke ringing a daki. Bakuwar number ta gani ta dauka suka gaisa. Da jin gaisuwar kasan bata san da wa take magana ba. Mama tace Haj Kaltume ce daga gidan Alh Nasiru uban mijinki. Izzatu ta dan ji kunya tace yi hakuri Mama bangane ba. Mama tace ah ai babu komai idan kina da lokaci kizo nan gida Alhaji ya bayar da sako. Kafin Izzatu ta amsa Mama ta kashe wayarta. Duk da babu mutane sosai a office din saboda weekend ne amma can Hamza yaje. Tunani ne yayi masa yawa bai iya yin baccin kirki ba. Shawara daya ya yanke zai basu ribar kamar yadda suka bukata sannan zaiyi kokarin hada kudin da suka bashi ya biyasu. Yana wannan tunanin Izzatu ta kira shi tana sanar dashi kiran Mama. Yace taje shima zai je anjima kadan. Har zai ajiye wayar yaji tace sweetyna kayi hakuri da duk abinda nayi ba daidai ba. Sai yaji ta bashi tausayi. Basa iya dogon fushi da junansu. Babu komai Izzy, love you. Tace love you more. Dakin Mama ta wuce kai tsaye tunda ita ta kirata. Hamida tana gyaran wardrobe din Mama taji sallamar Izzatu. Wata sabon gani. Anti Izzatu dama kina nan, yaushe rabonki da gidan nan? Izzatu ta dan sunkuyar da kai. Ita kanta tasan tafi wata biyar rabonta da gidan iyayen mijinta. Ko da Mama ta karye kunya da tunanin basa sonta ya hanata zuwa. Kuma Hamza baice taje ba. Mama ta fito daga toilet tace Hamida bana son rashin kunya ko sa'arki ce da zaki zauna ki titsiyeta. Tashi ki fita magana zamuyi. Ki kawo mata dan abinda zata ci. Izzatu ta sami wuri ta zauna tace ki barshi a koshe nake. Hamida ta tabe baki tayi gaba. Mama ta dubeta, gabadaya Izzatu ta fice mata a rai. Mun sami labarin abinda kuka yiwa yar mutane jiya a gaban jama'a. Izzatu na jin haka tasan kila fada za'ayi mata tace Mama don Allah kuyi hakuri. Itama yarinyar zan kirata na bata hakuri. Maybe bata ji haushi ba saboda bata yi kama da mai daukar abu serious ba. Mama tace ga mahaukaciya ko, dole kice bata daukar abu serious. To sakamakon abinda kuka yi jiya Alhaji yaje neman aurenta wurin iyayenta. Izzatu ta zaro ido harda dafe kirji. Yanzu Alhaji Zuhra zai aura? Karamar yarinya ce fa da kadan zata girmi Hamida. Ikon Allah ai da Nura ya nemarwa aurenta. Mama ta tsaya kawai tana kallon Izzatu ranta na kara baci. Ba shi zai aureta ba mijinki ya nemawa aurenta kamar yadda kika fada mata. What? Tashi Izzatu tayi a gigice... Mama don Allah da gaske kike? Hajiya ce da ta shigo dakin a lokacin tace da kuna yar wasa ne da ita. Kan kace meye wannan Izzatu sai kuka. Ta durkusa gaban Hajiya don Allah ku bawa Alhaji hakuri wallahi bazan iya zama da kishiya ba. Bazan iya sharing mijina ba. Daga Mama har Hajiya kallonta suke yi tana kuka wiwi. Mama tace don baki da kunya Izzatu mu kike gayawa bazaki iya sharing miji ba. In sha Allah aure kamar anyi an gama. Tana kuka tace dama kirana kuka yi kuyi min wulakanci. KE IZZATU MEYE HAKA. Ta yi saurin juyawa wurin Hamza daya shigo dakin shima. Rungume shi tayi tana kuka. Kaji abinda suke cewa wai Zuhra za'a aura maka. Duk kunya ta kamashi yana kokarin tureta tana dada kankame shi. Ya daka mata tsawa sake ni mana... iyayen nawa kike cewa suna miki wulakanci? Ba kin iya kiranta ki fada mata Hamza na sonta ba. To zan aureta kinga bukatarki sai ta biya. Idanu sharbe da hawaye tace ni kake fadawa haka Hamza....sai kawai ta fice. Mama tayi murmushi sannan ta nuna masa kofa bita kada tayi wani wurin. Ya yi hanyar kofar Hajiya tace Alhaji yace na fada maka lallai kaje gidansu Zuhra yau ku daidaita. Tsayawa yayi kamar gunki yana kallon yadda su Hajiya ke nishadi saboda za'a kakaba masa auren da baya so. Bai ankara ba yaji tashin motar Izzatu. Da sauri yabi bayanta. Hajiya tace an dai ji jiki. Wallahi Alhaji yayi min daidai. Su Mama za'ayi surika, Allah Ya tabbatar da alkhairi. Mama tace Amin Hajiya tana fadada murmushinta. [9/25, 3:42 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿23 Batul Mamman(Mrs)💖 Yaron da ya rakasu gidan har soro ya shiga dasu sannan ya karasa ciki ya fadawa Baba yayi baki har su uku. Dama a shirye yake shi da baban su Anti Faiza ne a tsakar gidan suna jiran zuwan suriki. Basu san wainar da ake toyawa ba. Baba yayi wa yaron godiya yace da Umma ta dauko juice din nan da ya tanada domin bakon. Manyan kwalin happy hour ne guda biyu sai ruwan roba babba daya. Akan tray ta jera da cups hudu ya mika hannu zai karba babansu Anti Faiza da ake kira Malam yace haba Baban yara bari na dauka. Tabarmi biyu Baba ya dauko suka shigo soron. Da yake akwai wuta yana ganin bakin yadan ji faduwar gaba. Irin wadannan mutanen da gani masu arziki ne. Anya sa'anin auren Zuhra ne kuwa. Ibrahim yayi sauran karban tabarmin ya shimfida musu. Suka zazzauna suna gaisawa. Alh Nasiru ya sake dasu sosai suna ta barkwanci kamar sun dade da sanin juna. Idon Hamza kyar akan dungulmin hannun Baba. A ransa tunani yake Allah Yasa ba kuturu bane. Kodayake ya gama tsara yadda zaiyi ya gujewa auren nan. Alh Nasiru ne ya fara magana. Alhamdulillah tun kafin muyi abinda ya kawo mu kunyi mana tarba mai kyau. Wannan yasa naji dadi nasan yaron nan baiyi zaben tumun dare ba. Malam yace in sha Allahu. Ai Zuhra yarinya ce mai ladabi duk layin nan ko ince unguwar nan babu wanda bai san gidan Mal Bashir ba. Baban yara ake kiransa saboda dan kowa nasa ne. Bakin gwargwado kuma yayiwa tasa yar tarbiya. Alh Nasiru yace haka ake son duk uba nagari. Ni sunana Alh Nasiru Hamza amma anfi sani na da Maifata saboda sana'ar sayar da fata nake yi sannan yayi musu bayanin asalinsa. Ya nuna Hamza da Ibrahim duk ya gabatar dasu. Sai ya nuna Hamza shine mai neman auren Zuhra. Baba ya sake kallonsa yace nagodewa Allah. Dana Allah Yasa kai abokin rayuwa ne na kwarai ga Zuhra. Ita kadai Allah Ya bani kullum adduata ta sami miji nagari. Tun farkon lokacin da ka fara turo mata sako a waya babu abinda ta boye min. Ni kuma a lokacin na yaba da tarbiyarka nake ta addua. Allah Yasa ayi a saa. Kowa yace Amin. Baba yayi musu bayanin matsayin karatunta da sana'ar da take yi yanzu. Alh Nasiru yace duk babu komai. Zai sanar da yan uwansu na Kumo nan da sati biyu idan ya amince sai a kawo kudin aure ayi maganar sa rana don baya son a dauki lokaci. Hamza dai sai yake yakeyi zuciyarsa na zafi. Ya rasa ta ina zai fara kokarin tattaro rayuwarsa da ke neman rugujewa lokaci guda. Suna mota Alh Nasiru yace yanzu da bamu zo ba ai alhakin yarinyar nan kila har jikoki sai ya bika Yaya. Zuhra na dawowa Baba ya sanar da ita Hamza da mahaifinsa sun zo. A zahiri ta nuna musu farincikinta amma a tsorace take da abin. Gashi baban Hamza ya roketa ta rufa masa asiri kada ta fada a gida. Anti Faiza ma tace ko Hajara kada ta fadawa. Haka ta shiga daki ta kwanta tana jin iyayenta suna tattaunawa akan bikinta. Hamza bai sami komawa gida ba sai kusan shadayan dare. Dakin Izzatu ya shiga ya sameta a kwance tana bacci. Hmmm kina jindadinki ya fada kafin ya koma nasa dakin. Yunwa yake ji sosai don rabonsa da abinci tun safe amma baya sha'awar komai. Kitchen din kasa ya sauka ya tarar da kulolin abinci kala kala ga wasu ko budesu ba'ayi ba. Kitchen din tsamin abinci kawai yake yi. Duk da cewa ba'a gama taron ba ya watse amma anyi almubazzarancin abinci. Tea ya hada ya koma daki. Tunanin sa na farko yadda zai biya turawan nan kudinsu gaba daya ya fasa hadin gwiwar dasu. Kudaden kamfanin yanzu da yawa an fara ayyukan ginin dake gabansu. Daya a Jigawa ne dayan kuma a Abuja. Kowanne sai sunyi rabin aiki za'a biyasu gashi duk zasu ci kudi sosai. Nasa kudin kuma ya kashewa gidansa don komai sabo ne a gidan. A gefe daya kuma ga zancen auren yarinyar nan. Gashi iyayensa duk fushi suke yi dashi. Ji yayi kansa yana sarawa saboda tunanin da yayi masa yawa ya tashi ya dauro alwala yana ta nafilfili da adduar samun sauki akan dukkan matsalarsa. Mama ce zai iya fadawa matsalarsa ta bashi shawara to itama yanzu basa dasawa kamar da. Izzatu kuma damuwarta akan abinda ya shafeta ce kawai. [9/25, 3:45 PM] +234 803 040 6305: AL'ADUN WASU 🗿25 Batul Mamman(Mrs)💖 Gidan kanwar Mamanta inda suka yi masauki Izzatu ta tafi. Ko rufe motar bata yi ba ta shiga cikin gidan tana ta rusa kuka. Ana ta tambayarta abinda ya faru taki bada amsa. Sai da kanwar Maman tasu tayi mata tsawa sannan tana shesshekar kuka tace Alhaji ne yace Hamza sai ya auri yarinyar da nayiwa April fool jiya. Anti Larai kanwar Raliya tace kai amma Allah Ya sakawa Alh Nasiru da alheri. Ni dama kinsan duk wannan shirmen naki ba zuwa nake yi ba saboda na rasa wace irin rayuwa kuke yi ke da mijinki. Tun jiya da aka bani labarin abinda kika yi raina ke kuna. Ta mayar da kallonta ga Raliya...Wallahi duk laifinku ne Yaya Raliya. Rayuwar turai ai ba hauka bane. Yara kusan shekara tara da dawowarku kasar nan amma sunki yarda su yar da al'adun da ba nasu ba. Yanzu wa gari ya waya. Raliya ta sunkuyar da kanta kasa. Tasan tabbas gaskiya kanwarta take fada. Ta kalli Izzatu da take ta kuka...sai ki rungumi kaddara tunda ke kika jawowa kanki. Ni bazan shiga zancen nan ba kuma daddynku ma zan fada masa babu ruwansa. Allah Ya baku zaman lafiya. Izzatu tace haba Mum haka ma zaki ce. Raliya tace to ai tsuntsun da ya ja ruwa, shi ruwa ke duka. Daki Zeenatu ta Izzatu tana rarrashi. Kinga Izzatu kiyi hakuri yayi auren nan tunda dama yan gidansu basa kaunarki. Idan kika nuna bakya son auren suna iya sawa ya rabu dake. The way I see it wannan yarinyar bazata kai ko'ina a gidan ba zai saketa. Da haka tayi ta rarrashin Izzatu har ta hakura ta dauki wayar Hamza da yake ta kiranta ta fada masa inda take sannan ta kusa dawowa gida. Bayan ta koma ne suka yanke shawarar yaje gidan su Zuhra kamar yadda Alhaji ya bukata. Maganar auren tasa fushin da yake da Izzatu akan matsalar kamfaninsa ta ragu. Wani light blue din yadi ya saka da aka yiwa dinki mai kyau amma simple style ba ado da yawa. Yasa hula mai ruwan madara da light blue. Yayi kyau sosai don ma bai fiye sa manyan kaya ba. Ya sha turare sannan Izzatu ta daura masa links a hannun rigar da agogo. Yana saka takalmi tace cikin shagwaba ni gaskiya kayi kyau da yawa kamar kada ka fita. Murmushi yayi mata. Kada ki damu bazan dade ba. Da tambaya ya iso gidan domin zuwan su na dare ga ransa a bace ko kallon hanya baiyi ba. Yaro ya tura yayi masa sallama da Zuhra. Yaron na tafiya yabi bayansa ya tsaya a soron inda suka zauna da Baba. Yaron na sallama Zuhra ta amsa. Ita kadai ce a gidan Umma ana la'asar suka tafi kai garar Hajara. Baba ma ya fita tun safe bai dawo ba. Tana gaban murhu zata fara tuka tuwo. Da murmushinta tace Isuhu daga ina haka? Isuhu yace wani mutum ne a waje wai Hamza yace kizo. Wallahi baki ga yadda ya hadu ba Zuhra, motarsa ma abin kallo ce. Ga wani kamshi dan ubansu yana fitarwa. Tunda Isuhu ya fara magana gabanta ya fadi. Ba yadda za'ayi ta yarda da auren nan. Rokonsa kawai zata yi su fadawa iyayensu basa son auren. Ina ita ina wannan mutumim, ita tsoronsa take ji. Isuhu ta kalla kace masa ina zuwa tuwo zan tuka na kwashe. Babu kowa ne a gidan. Duk maganar da sukeyi Hamza na jinsu. Bashi da niyar dadewa a gidan saboda haka dan aiken nasa na fitowa naira hamsin ya bashi shi kuma yayi sallama ya dan shiga daga cikin tsakar gidan. Zuhra bata gama tantance sallamar waye ba taga mutum ya soma shigowa. Gashi ta zuba garin alkama ta fara tuka tuwon. Da sauri ta fara cewa kai dakata kada ka shigo mana. Wani tsohon zani ne a jikinta da koriyar t-shirt sai dankwalin zanin da ta daure kanta tamau dashi. Hamza bai kula ta ba ya shigo har tsakiyar tsakar gidan tana ta kokawa da dankwalinta tana son bude shi ta rufe jikinta. Wani irin kallo ya bita dashi mai wuyar fassara. Kinga yi aikinki ni ba zama nazo yi ba. Magana nake so muyi ina sauri ne. Fuskarta a turbune tace don kana sauri ko sallamarka ban amsa ba ka fado mana cikin gida. Kuma ko lullubi babu a jikina. Dan karamin tsaki yayi, kwantar da hankalinki baki da abinda zai daga min hankali don na ganki ba mayafi. Maganar ta bata haushi sai ta danne tace ina wuni? Kafin ya amsa ta cigaba da tuka tuwonta. Kallo ya bita dashi yadda take zaune gaban murhu zafin baya damunta. Bazaki bani wurin zama ba? Ko juyowa bata yi ba tace na dauka ba zama kazo yi ba. Can gefe ya sake matsawa saboda wutar ta fara hayaki. Ita kanta Zuhran yana damunta ta fara hawaye da majina. Tasa gefen dankwalinta ta goge fuskar ta cigaba da aiki. Da kyar ya hadiyi yawu saboda gabadaya kyankyaminta ne ya kamashi. Gara yayi abinda ya kawo shi ya fita kafin zuciyarsa ta fara tashi. Ji tayi yace Ke,wai baki da saurayi ne?....ta murguda baki duk da ta juya masa baya ni ba sunana ke ba. Kuma ina ruwanka da samarina. What ever taji ya fada da turanci. A ranta tace ban yafe ba idan ka zagen. Alhaji yace yana so na zo wurinki atleast sau uku kafin a kawo kudi. Za'a tambayeki kafin ranar idan kin amince da auren, ina so kice ba kya sona. Mun gama magana da Izzatu tace kina da saukin kai zaki amince. Izzatu da ya fada ya kara bata haushi. Ko kadan bata son sake jin sunan matar. Kinga ni bana sonki kuma idan kika aureni wahala zaki sha. A tsarina mace daya ta isheni. Tunda bana jin kina da saurayi akwai sakatare na Inuwa zanyi mishi tayinki. Idan ya amince kinga shikenan. Ko ba komai na taimaka miki. Kuma nayi alkawarin yi miki kayan daki idan kin tashi aure. Murmushi kawai Zuhra keyi ta gama tuka tuwon ta rufe tukunyar sannan ta gyara wutar. Wato mutumin nan ya raina mata hankali. Shi iyayensa su yabe shi ita kuma ace bata da kunya. Wai har cewa yake zaiyiwa wani tayinta. Ko na sati ne sai ta aure shi ta bata masa rai daga shi har masoyiyar tasa Izzatu. Da wannan shawarar ta dago kanta amma bata hada ido dashi ba. Tace shikenan abinda ya kawoka? Hamza yace eh ko kudi kike so zan iya biya kice ba kya sona kinji. Wannan karon tamkar mai magiya yake magana. hanyar dan karamin falonsu ta kama. Zanyi tunani a kan maganar, ka gaida gida. Shigewa tayi ta barshi nan a tsaye yana mamakin wai itama ta iya jan aji. Ya kada kansa ya fice daga gidan. [9/25, 3:45 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU#26 Batul Mamman(Mrs)# Washegari Hamza ya koma gidansu Zuhra. Soro ta fito ta same shi. Yau zama yayi yana lissafa mata irin mawuyacin halin da zata iya shiga muddin ta yarda aka yi auren. Kanta a kasa har ya gama bayaninsa ya juya ya tafi. A waje ya hadu da Baba yana dawowa gida. Yara ne sunfi goma suke biye dashi yana rarraba musu alawa. Hakan ya bawa Hamza sha'awa. Karasawa yayi suka gaisa da Baba cikin ladabi sannan ya tafi. Yau dai ya karewa hannun Baba kallo ya kula yankewa aka yi ba kuturta bace ta cinye yatsun. Saboda matsalar office dinsa sai bayan kwana biyu ya sake komawa. Umma tasa tayi kwalliya irin wadda ta saba yi tana ta yabon kyan tilon yarta. Zuhra tace don ma banyi wanka ba Umma ai da sai nafi haka kyau. Umma tace to sakarai sai kin fada da karfi yaji yasan cewa ke kazama ce ko. Bata rai tayi haba Umma ki dena ce min kazama. Baba yace na kile. Ai fa naga alama, to wuce ki tafi kin barshi yana jiranki. Tabarma ta dauka ta fita soron. Kamshin turarensa ya cika wurin. Yau suit ce a jikinsa ruwan toka. Zuhra ta gaishe shi ta sami wuri ta zauna don baya zama akan tabarmar. To yau nayi zuwa uku ina fata kina rike da dukkan abinda nake fada miki. Ya dan jima yana magana sannan ya lura ba saurarensa take ba. Shi ta kurawa ido....ke, keee, KE lafiyarki? Bata dawo hayyacinta ba sai da ya dan tafa hannuwansa a gaban fuskarta. Ajiyar zuciya tayi sannan tace yanzu don Allah kana iya numfashi? Ni bansan haka ake saka abinnan a zahiri ba sai yau. Waige ya fara yi don bai gane kan zancen ba. Tace neck tayil dinka nake nufi. Naga ya shake maka wuya kamar mai shirin rataye kansa. Yanayin maganarta yasa shi yin murmushi. Necktie ake cewa sannan bai shake ni ba. Amma dai baka sakewa ko? Dauri irin wannan akwai ganganci a cikinsa. Dole Izzatu tace yarinyar nan tana da shirme. Yace ni zan tafi ina tunanin jibi Alhaji zai zo. Ki kiyaye abinda na fada miki. Har ya juya sai ya dawo...by the way nayiwa Inuwa maganarki sai dai mun makara. An kusa kai kudin aurensa. Zuhra tace babu komai. Nagode.....yadda yaga kamar ta nutsu yasa ya kwantar da hankalinsa. Dubu goma ya dauko yan dari dari sababbi ya mika mata. Ga wannan ki rike. Nagode ta sake cewa sai kawai ta nade tabarmarta ta shige ciki. Mayar da kudinsa yayi aljihu yana mamaki da bata karba ba. Bayan Isha Baba ya kira Zuhra da Umma. Wani katon littafi ya dauko mai hotunan kayan daki irinsu gado, kujeru da kitchen cabinet masu tsada. Kunsan aikina ba wai ina yin kayan daki na masu kudi bane sosai. To amma na sami wani ya bani aron littafinsa nake son kwaikwayon duk wanda kika zaba zanyi kokari na kwatanta miki irinsa uwata. Atine gashi ki tayata zabe. Hawaye ne mai zafi ya saukowa Zuhra. Tabbas iyaye sun cancanci dukkan girmamawa daga 'ya'yansu. Allah Ka sakawa iyayenmu da alkhairi. Baba ne ya fara gani yace meye haka uwata ta kaina? Da yake Umma ma akwai rauni sai kawai suka hadu suna kuka maimakon ta rarrasheta. Baba ma dai ta maza yayi ya fara musu fadan su dena yi masa kuka. Burina Zuhra tayi aure ta sami mai kula da ita. Sai da shekaru suka zo mana muka haifeki dole nayi murna idan na sami wanda zai tayani kula da Fatima kyauta daga Allah. Zuhra fadawa tayi jikin Baba tana kuka. Ni bazanyi aure ba. Saurin tashe mata baki yayi...kul na sake jin irin haka. Aure ai shine rufin asirin kowa. Zaki yi aure cikin gidan mutumci kuma in Allah Ya yarda zaki kawo min jikoki su zo in basu labarin tabara irin ta babarsu. dariya ta rinka yi. Daga baya suka zabi gado da kujeru ita da Umma. Sai da ta kwanta ne a kan dan gadonta maganar Hamza ta rinka dawo mata. Tabbas da niyarta ta aureshi ta kuntata masa. Don duk zancen da yake mata jinsa kawai take yi. Sun dauketa wata gaula daga shi har matar tasa. To amma maganar Baba ta tsaya mata a rai. Duk shirmenta tana kaunar iyayenta kuma bata son bata musu suna. In Allah Ya yarda bazata wasta musu kasa a ido ba. Idan har baayi auren ba sai dai idan Hamza da bakinsa yace baya so. [9/25, 3:46 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #27 Batul Mamman(Mrs)# Bayan kwana biyu Umma ta sanar da Zuhra yau iyayen Hamza zasu zo. Mamansu Hajara ta shigo tayata aiki. Kaji hudu suka soya, Anti Faiza sarkin flour tayi musu cake, meatpie da doughnut. Zuhra ta wanke tsakar gidansu tas dama irin fasassun tiles dinnan ne. Nan da nan wurin ya hau sheki. Bayan ta gama aikin ta hau magiyar a barta taje gidan Hajara. Tunda akayi biki Baba ya kafa mata dokar sai tayi sati baya son yawon gulma. Anti Faiza tace ke da zasu ji ta bakinki ai bai kamata ki fita ba. Kannen Umma biyu suma suna ta zolayarta da matar kanin Baba. Sai bayan la'asar suka watse aka bar Maman Hajara da Umma. Baba ya shigo tare da Malam yace su bakin zasu shigo. Kaninsa da yake aikin masinja ma yazo tunda Alh Nasiru yace indai ta amince to a lokacin zasu bada kudi asa rana. Su Umma daki suka koma bayan an jerawa baki kayan motsa baki. Sai da suka gama barkwancinsu sannan Alh Nasiru ya bukaci ganin Zuhra domin yaji amsarta. Dan karamin falonsu ya shiga tare da Baba. Kanta a kasa ta gaishe shi ya amsa yana mai yabon halayenta. Sannan ya tambayeta domin baya son matsa mata ta auri wanda bata so. Murmushi kawai tayi ta sake sunkuyar da kai. Ganin haka ya mike suka koma tsakar gida. Ya dubi sauran jamaar wurin. Shirun budurwa alama ce ta amincewarta saboda haka idan duk kun amince ina so asa rana nan da sati hudu. Kowa yayi naam da hakan harda Baba. A take suka bada kudin aure dubu dari aka yi addua taro ya watse. Ranar murna a wurin Baba da Umma ba'a cewa komai. Kudin da aka bayar Baba yace zai ajiye mata zuwa lokacin biki. Kinga ko mijinki bai yarda ki cigaba da saka ba kina da dan abin hannunki. Sannan ku shirya karshen sati zamu je Ajingi. Nan Zuhra ta hau murna zata je wurin Inna. Yinin ranar Hamza suna ta meeting da maaikatansa akan yadda zasu samu su karasa biyan kudin da turawan ke binsu kamfanin ya dawo mallakin Hamza shi kadai. Ya sanar dasu dole su zage damtse ayi aiki sosai domin su fitar da kudin kafin watanni shidan da aka basu su cika. Suna fitowa gidansu ya tafi saboda amsa kiran Alhaji. Yasan zancen bazai wuce Zuhra taki amincewa ba ayi masa fadan bai yi abinda ya dace wurin jan raayinta ba. Mama bata gida lokacin da yaje sun fita da Nura. Da Hajiya suka gaisa kafin ya karasa wurin Alhaji. Fuskarsa a sake ya amsa gaisuwar Hamza sannan yace ya kamata ka fara shiri tunda sati hudu kawai aka sa rana. Idan baka son hadasu gida daya sai ka gyara mata tsohon gidanka. A dan daburce Hamza yace wa zan gyarawa? Alh Nasiru yayi murmushi amaryarka mana. Yadda gabansa ya fadi bai san lokacin da yace amincewa tayi??? Alhaji yace ba haka kaso ba ko. Ai nasani Babana. To sai ka dau hakuri yarinya tana neman albarkar iyaye. Hamza yace Alhaji nima ina nema. Don Allah a janye zancen nan. Ko Nura ka aurawa ita. Dariya Alhaji yayi shi kuwa Hamza kamar yayi kuka yace yarinya ce karama. Ya za'ayi na zauna da ita? Alhaji ya gyara zamansa. Kaga ba jan zance nake so muyi ba. Aure ne sai an daura in sha Allah. Ni ban dora maka nauyin komai ba sai sadaki. Tunda na fika son ayi auren na dauke maka duk wata hidima da zata taso. Rasa bakin magana yayi yana kallon mahaifinsa. Mama ce ta shigo tare da Nura da su Hamida suna rike da wasu jakunkuna masu kyau. Seti ne guda shida, tace Alhaji kaga wadanda muka samu. Sai ta kalli Hamza, a'a kaga babban dana angon Zuhra. Ta tura masa daya daga cikin jakankunan. Kaga wannan sunyi kyau? Yanayin fuskarsa bazai fasaltu ba yace Mama harda ke? Nice ma kan gaba ta bashi amsa. Uhm Alhaji gobe da safe zamu je da su Jidda kasuwar, kasan hada lefe akwai cin lokaci. Yana shan furarsa yace Allah Ya kaimu. Share Hamza suka yi tamkar baya wurin. Tunaninsa daya yadda zai fadawa Izzatu plan dinsu bai karbu ba. [9/25, 3:47 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #28 Batul Mamman(Mrs)# Abinda yaji tsoro ne ya faru. Izzatu tayi kuka har ta gaji. Rokon Hamza take yi ya rufa mata asiri kada yayi auren. Tun yana rarrashinta har ransa ya baci da tace duk gidansu babu mai kaunarta. A hasale yake kallonta ke har kina da bakin cewa ba'a sonki Izzy? You caused everything. Lokaci guda kin lalata farincikin gidan nan. Ganin ya soma fada yasa ta rungumeshi. Am sorry baby. Na yarda kayi auren amma bayan lokaci kadan sai mu nemi dalilin da zaisa ka saketa. Jinta kawai yayi. Shi da Alhaji ya kafa masa sharadin indai ba da dalilin da ya sabawa shariah ba bai yarda ya saki Zuhra ba. A bangaren su Zuhra kuwa shirye shirye ya kankama. Makota da abokan arziki kowa yana son gwada bajintarsa wurin bikin tilon yar baban yara. Gudunmawar kudi suka rinka bawa Mal Bashir sai da ya tashi da dubu dari biyu da talatin. Shi kanshi ba karamin mamakin wannan karramawa ta mutanen unguwarsu yayi ba. Anas da Sani ma ba'a barsu a baya ba domin kuwa gas cooker karami suka kawo. Baba yayi murna da godiya sosai. Haka Umma ta rinka shiga gida gida tana godiya itama. Zuhra taje gidan Hajara a nan suke nasu tsarin bikin duk da ba damunta yayi ba don tasan wahala zata sha kawai. Hajara tace wato Zuhra da gaske kike da kika ce idan kika tashi aure sai munyi mamaki. Gashi zaki auri dan gayu dan boko. Wallahi ki dage sosai tunda yana da mata. Zuhra tayi dariya wace irin dagewa kuma. Ai kawai indai zasu bani abinci naci na koshi to suje can su karata. Sahabi da yake daki ya fito ba shiri. Amma dai Zuhra wasa kike ko? Tace da akayi me fa? Maganar da kika fada yanzu nake nufi. Yaushe zaki ce abinci zaki je ci. Wuri ya samu ya zauna yana karanta mata yadda zata yi a gidan miji. Hajara sai dariya saboda Zuhra rufe kanta tayi da mayafi. Irin wannan bayani na Sahabi yafi karfinta. Shi kuwa ya dauketa kanwarsa ne tunda duk unguwarsu daya. An kawo lefe akwati shida da kit. Komai Alhaji ne ya siya. Makota da yan uwa suna ta san barka. Washegari Baba yayi shatar mota suka dauki kayan suka wuce Ajingi. Nan ma kowa yace Zuhra tayi goshi. Yan uwanta suka shiga hada mata abubuwan da zata gyara kanta. Yi kawai take don kada a gane auren da matsala. Cikin wannan lokacin ko text bai taba hada Hamza da Zuhra ba. Har Umma sai da tace naga kwana biyu shiru yaron nan. Zuhra tayi yake muna waya kullum Umma. Wani aiki ne yake son karasawa kafin bikin. Umma tace to Allah Ya bada saa. Alhaji ya sake tuntubar Hamza inda zai ajiye Zuhra. Takardun tsohon gidansa ya dauko ya mikawa Alhaji yace na riga na gama komai ya zama mallakin Nura. A sabon gidan akwai dakuna sai ta zauna a cikin daya. Alhaji yasa masa albarka sannan ya tura Mama ta gano dakin da za'a bawa Zuhra. Dakina ne babba a kasa da toilet a ciki. Mama tace sam amarya ma a sama zata zauna. Dakunan saman uku ne har an gama jera kayan su Khalifa a ciki. Bisa umarnin Alhaji dole aka dawo dasu kasa ba da son ran Izzatu ba aka sabonta fentin. Katon daki ne kamar na Izzatu da toilet. A ciki aka jerawa Zuhra gadonta daga wani gefe da yayi dan tudu. Dayan gefen kuma kujerunta da su tv. Mama tace kuma lallai ayi kitchen kabinet a daya daga cikin dakunan kasan saboda a raba musu kitchen. An fara biki cikin kwanciyar hankali. Baba yana ta yabon Hamza saboda yana yawan kiransa a waya su gaisa. Hakan yasa suka cigaba da tunanin komai lafiya tsakaninsa da Zuhra. Anti Faiza kuma ta sake ja mata kunne akan tayi shiru da bakinta. Sannan tayi mata nasiha akan kwalliya da tsafta. Ni girar nan da kike ja ce bana so Zuhra. A shagwabe tace nufinki bana yin kyau Anti Faiza. Kinsan ni gaskiya zan fada miki. Bata miki kyau don ba iyawa kika yi ba. Kuma babu ruwanki da Izzatu ki kama kanki kinji ko. Zuhra ta gyada kai. Kinga yadda iyayensa suka tsaya miki sosai. Ina so ki kyautata musu daidai gwargwado. Babu fitsara ba rashin kunya. Nagode Anti Faiza in sha Allah zan kiyaye. Anyi kamun Zuhra a unguwarsu washegari alhamis suka tafi Ajingi. Jumaa bayan masallaci aka daura auren Arch Hamza Nasir Hamza da Fatima Bashir Ajingi. Kai ka dauka auren yar wani maikudi ake yi saboda yadda mutane suka zo. Asabar da safe suka dawo kano aka fara shirin kai amarya. Jikin Zuhra a sanyaye tunda aka daura auren. Shikenan zata bar iyayenta ta zauna da mutumin da babu soyayya a tsakaninsu. Ba'a tashi kuka ba sai da motocin daukar amarya suka zo. Aka rasa yadda zaayi a raba Zuhra da Umma. Gabadayansu kuka suke yi tamkar sun rabo kenan. Baba ya shigo yana fadan sun bar mutane a waje. Sai dai Zuhra na rungumeshi ya soma hawaye. Daki yaja hannunta suka koma. Yana kuka yana mata nasiha....uwata ki rinka tsafta kinji ko, ki rike Allah da ManzonSa SAW komai zaizo miki da sauki. Ki rinka taimakon mijinki. Kuma banda katuwar loma a gaban miji. Murmushi tayi hade da kuka ta sake fadawa jikinsa. Baba wa zaku rinka gani a gidan nan idan na tafi? Umma ce ta bata amsa bayan ta fyace hanci cikin yaran Yaya Shafiu matarsa tace na dauki duk wadda nake so. Baba ya dauko wata leda ya damka mata. Ga wannan dubu hamsin ne. Cikin kudin da na samu ne. Zan ajiye miki sauran. Ki rinka amfani dashi. Allah Yayi miki albarka. Basu fito ba sai da Malam babansu Hajara yazo ya buga kofar. Haka suka tafi tana ta rusa kuka ita da Hajara. Anti Faiza tace gulmammu duk wadda bata son auren sai mu koma da ita. [9/25, 3:48 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #29 Batul Mamman(Mrs)# Idan kaga dakin Zuhra baka ce na yar Mal Bashir kafinta bane. Tabbas duk dakunan gidan sunfi nata kaya masu kyau da tsada. To amma itama nata iyayen sunyi kokari sosai. Gida ya cika da yan kawo amarya. Izzatu ita kadai ce a daki dama ita ba mai rakice rakicen kawaye bace. Daga ita sai 'ya'yanta. Duk da tasawa ranta bazata kula Zuhra ko tayi kishinta ba sai da tayi kuka da aka shigo ana guda. Adabiyya da Hamida sunfi kowa rawar kafa Yaya yayi amarya. Hakuri da nasiha aka sake yi mata sannan suka tafi. Hajara da wasu yan uwanta ne karshen tafiya bayan sun sake gyara mata daki. Tashi tayi ta cire mayafin jikinta saboda su hudu ne kawai a dakin. Hajara tayi saurin mayar mata. "Abinda ake son amarya da jan aji. Kin wani cire mayafi, idan wasu suka sake shigowa fa." Sake cire mayafin tayi "ke kyaleni nasha iska. Da zafin gari zanji ko na rabuwa dasu Umma." Tana magana idanunta suka cika da hawaye. Hajara ta ja hannunta suka koma kan gadon. Sake gyara mata dauri tayi aka fesa turare."to mu zamu tafi amarya. Kada ki tashi nasan ango na hanya. Kuma ki dena kukan su Umma haka. Irin haka sai yaga kamar auren dole aka yi muku. A zuciyarta Zuhra tace meye maraba. A zahiri kuwa godiya tayi musu suka tafi. Sai da taji dakin tsit ta tashi tana leka ko ina. Wurin yayi kyau sosai ga kamshin turaren wutar da kanwar Umma ta hada mata. A hankali ta bude kofar toilet ta shiga. Wani murmushu tayi. Irin wannan bandaki kamar a gidan shugaban kasa. Ta mika hannu sink taga ruwa ya fito tun kafin ta kunna famfon. Zabura tayi da gudu zata fita don a zatonta famfon ya lalace ne , kada ace ita ta lalata. Ko da ta juyo sai taga ruwan ya dauke. Gabanta na dukan uku uku ta sake komawa tana mika hannu saman zata kunna sai taga bai sake fitowa ba. Har tayi ajiyar zuciya ta sake saka hannu a wurin fitar ruwa sai gashi ya sake fitowa. Fita kawai tayi ta rufe toilet din. Allah Yasa tayi sallar Isha. Dama nafila take son yi, sai ta hakura. Tun tana jira ko angon nata zai shigo har ta fitar da rai. Dama bata sa a ka ba. Wuri ta samu a tsakiyar gadon tayi kwanciyarta ko kaya bata chanja ba. Bata dade ba bacci mai nauyi yayi gaba da ita. Hamza bai shigo gidan ba sai shadaya da rabi na dare. Tun kayan jikinsa na daurin aure bai dawo gida ba. Babbar rigarsa da hula duk a hannu ya shigo dasu ya hadu da Tala tana ta gyara gidan. Ita kam dole a yaba mata wurin tsafta. A gajiye yake sosai, tayi masa sannu da zuwa ya amsa ya haye sama. Sai da yaji ba dadi da ya kalli kofar dake hagun dakinsa. Wai matarsa ce a ciki. Ko alamar zuwa baiyi ba. Kofar dakin Izzatu ya taba yaji bata rufe ba. Muryarta a shake alamar taci kuka yaji tace "Waye?" Shiga yayi ta taso da sauri ta rungume shi tana kuka. Bai hanata ba sai da tayi shiru don kanta. "Ina su Nana?" Ya tambaya lokacin da yake cire takalmansa. "Suna sabon dakinsu. Tala zata rinka duba min su." Yadda take maganar kasan har yanzu tana bakin cikin canza musu daki da aka yi. Kiss Hamza yayi mata a kumatu." Goodnight Izzy. Kije ki kwanta" Ya juya zai fita. Kansa ke ciwo kamar ya tsage. Yau baici wani abin kirki ba tun safe. Yana son tambayar Izzatu amma yasan idan bata da nutsuwa girki ma baya gabanta. Saurin biyoshi tayi. Ta rike masa hannu" Don't tell me wurin Zuhra zaka kwana". Hannun nata ya saki." No, dakina zani. Na gaji kema ki kwanta haka" Kallon tuhuma take masa." Are you sure?". Kai ya gyada mata. Baya son magana saboda yadda kansa ke sarawa "Ko nazo mu kwana? Ina fargabar ranar da zaka kwana dakin yarinyar nan. Zan iya mutuwa saboda kishi." Ganin baya son magana yasa ta kyale shi. Tasan bazai fadi magana ba yaki cikawa. Bayan ya tafi itama sake gyara jikinta tayi tabi bayansa. Da ya tambayeta abinci tace babu amma bari tayi sauri ta dafa masa wani abin. Jallop din taliya tayi masa. Kafin ta gama yayi wanka. Abinci yaci ya dan zauna ya fada masa. Suka kwanta shi da Izzatunsa. Ba wata hira tsakaninsu domin kuwa akwai abinda ke damunsa. [9/25, 3:49 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #30 Batul Mamman(Mrs)# Zuhra anji dadin bacci saboda gajiyar da ta tara ta biki. Ba ita ta farka ba sai bayan tara. A firgice ta tashi ganin hasken rana a dakinta. Ko sallar asuba batayi ba. Sai da ta shiga bandakin ta tuna da matsalarsa ta jiya. Gashi ta makara sallah. Banda bahon wanka daga gefe wata yar matakala ce mai karamin bene da yayi kasa akwai shower a wurin. Kunnawa tayi ruwa ya watso mata saboda yayi karfi. Da kyar ta iya rage karfin ruwan. Cire kayanta tayi ta koma tayi wanka tare da alwala. Tun kafin ta gama shiryawa cikinta ya soma kukan yunwa. Nan fa ake yinta. Zuhra bata jurar yunwa gashi tunda aka kawota ko motsi bataji a kofar dakin ba. Haka ta gama duk abinda zata yi ta sami wuri ta zauna. Tunanin iyayenta ne ya zo mata ta soma kuka. Izzatu da Tala sun gama hada komai na breakfast suka jera akan dinning table. Sama ta hau ta kira Hamza. Sanye yake da jallabiya light brown sai kamshi yake. Yayi kyau sosai sai dai fuskarsa da ta zama maabociyar damuwa yan watannin nan. Yaransa duk suka yi masa kiss a goshi kamar yadda suma iyayen suka saba yi musu. Sannan suka zauna Izzatu tayi serving dinsu. Lomar farko da zai kai bakinsa ta tuna masa da Zuhra da ke daki tun jiya ko lekata baiyi ba. Tsaki tayi ya tura kujerarsa ya tashi. "Baby what is wrong?" Izzatu ta tambaye shi itama tana mikewa tsaye. Sama ya kalla ya sake yin tsaki "zan kira yarinyar nan tazo taci abinci ne." A take Izzatu ta hade rai. "Ka bari Tala ta mika mata mana. Ai ba sai kaje dakinta ba." "Hakkinta ne na ciyar da ita" yana fadin haka ya hau saman. Ya kusa minti biyu kafin ya murda kofar ya shiga. Akwai kamshi dai saboda dakin amarya ne sai dai zafi sosai duk da tagar a bude take. Ko meyasa bata kunna AC ba oho. A tsaye take tana jera kayanta a wardrobe har ta kusa gamawa taji an taba kofar. Cikinta sai da ya bada sauti saboda tsoro. Ko da ya shigo duk rashin kunyar da taso yi masa sai ta fasa saboda yadda ya cika mata ido. Bata taba kare masa kallo ba sai yau. Da ace zaman lafiya suke yi da ta fada masa yadda yayi kyau. Shima ita yake kallo. Riga da skirt tasa na atampa fuskar nan tasha farar hoda. Kana ganinta ita daban fuskar ma daban. Ga hannun breziya ya fito ta kowane gefen hannun rigarta. Ya dan tabe baki....kai kuma irin taka jarabawar kenan Hamza. "Ke baki iya gaisuwa bane?" Saurin durkusawa tayi tare da jin kunya. "Ina kwana, an tashi lafiya"? Bai amsa ba ya juya"ki sauko muyi breakfast". Kafin ya kai kofa ta biyo bayan shi. Yunwa take ji sosai. Ace yau har shadaya saura bata ci abinci ba. Ita kanta tasan tayi abinda zaa jinjina mata. A baya ta rinka binsa har suka sauko. Izzatu ta kai karshe wurin bacin rai, sai kawai ta danne. Kujera ta samu kusa da yaran ta zauna tare da yin sallama. Khalifa ne kawai ya amsa. Ya kalli Mamansa. "Mummy wannan ma mai aiki ce?" Hamza ya ce masa yayi shiru kawai yaci abinci. Zuhra tana sane bata ji ya gyara masa yace ita ba mai aiki bace ko da bai kirata matarsa ba. Izzatu ko daga kai batayi ba bare ta bashi amsa. Itama Zuhra taki kallonta. Yadda take jin haushin Izzatu ko kallo bata isheta ba. A dalilinta tazo gidan nan da bata da wata kima a idon mazauna cikinsa. Muryar Hamza ce ta katse mata tunani. "Wai ba kya gaishe da mutane ne?" Ta dago fuska suka hada ido. "Na gaisheka a daki" Da kansa yayi mata alamar bata gaishe da Izzatu ba. Amma lallai ya rainata da yawa. Su basu ce 'ya'yansu su gaisheta ba sai ita zata gaishe da matarsa. Kamar bazata yi ba sai kuma tace "ina kwana" Maimakon ta amsa sai kawai ta tashi ta koma dakinta. Hamza ya bi bayanta. Yaran ma suka gama suka tashi. Suna tafiya Zuhra ta janyo flask ta bubbude sannan ta debi abinda zata ci ta hada tea. Sai da taci ta koshi sannan ta tashi daga dinning area din ta koma wurin yaran inda suke zaune suna kallo. Tambayarsu sunayensu tayi suka bata amsa. Junior yace "ke kuma ya sunanki?". Murmushi tayi "sunana Zuhra". Khalifa yace "nice name, will you be my friend?" Ido ta dan zaro "tohhh kun iya turanci tun yanzu..." da haka suka rinka hira da ita tana jansu da wasa. Hatta Nana mai kyuya ta yarda da Zuhra. Hamza ya dauko laptop zai fara aiki sai kuma ya rufe. "Izzy kirawo yarinyar nan, I need to talk to both of you" Wani irin kallo tayi masa. " sweety nice zani dakin Zuhra? Allah Ya kiyaye. Kuma ai bai kamata ta shigo mana bedroom ba. As far as am concerned ni ban dauketa matarka ba." "Gashi kuma na biya sadaki" yadda yayi maganar tasan har yanzu yana ganin laifinta a matsayin wadda ta jawo masa auren. Tana fitowa ta jiyo muryar Junior yana cewa Zuhra ta yi masa tatsuniya. Daga saman ta leka ta kirawo Khalifa. Shi ta fadawa ya rako Zuhra dakin daddysu yana jiranta. Rike da hannun Khalifa suka shiga dakin. Wata irin niima taji. Ita nata dakin sai zafi. Falo ne a farko sannan kofar dakin daga ciki. Wurin ya tsaru sosai ta tsaya tana kallo. Izzatu tace da Khalifa yaje wurinsu Junior. Babu wadda ta kula yar uwarta har Hamza ya fito. Kusa da Izzatu ya zauna. Ita Zuhra kasa ta zauna kan kafet saboda gudun kada ace tayi laifi. Gyara zamansa yayi fuskarsa ta nuna alamun ba wasa. Sannan ya soma magana "Kamar yadda kuka sani dukkaninku matana ne duk da cewa circumstances behind auren kowacce is different...... Zuhra anzo wurin...gabadaya jumlar karshe bata fahimta ba. .....bana son tashin hankali a gidan nan. Izzy kece babba ina so kija girmanki. Ke kuma ya juya ga Zuhra ki bata girmanta. Tun farko na gargadeki akan auren nan kika ki ji. So duk abinda kika gani sai kiyi hakuri. Sannan a yanzu baki da kitchen don sai an gyara miki daki a kasa. For now idan Izzy tayi girki zata baki. Saboda haka babu zancen rabon kwana sai an gama kitchen din." Ya kallesu duk su biyu. "Ko akwai mai magana?" Izzatu tana ta kumbure kumbure tace " ka fada mata ta fita harkar yarana". Bai ce mata komai ba yace da Zuhra tana iya tafiya. Tunda ya soma magana bata daga kai ba. Yayi tsammanin zata nuna bacin rai amma sai yaga tayi shiru. Kanta a kasa ta fita daga dakin ta koma nata. Tana rufe kofar ta suma kuka duk yadda taso daurewa ta kasa....ba son Hamza take ba amma babu macen da zata so a nuna mata ita ba komai bace a gaban kishiya. [9/25, 3:50 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #31 Batul Mamman(Mrs)# Sai karfe uku da rabi Tala ta kwankwasa mata kofa. Ko da ta bude abinci ne a plate an rufe da wani sai ruwa roba daya mai sanyi da cup. Godiya tayi mata ta karba. Gara a rinka kawo mata don ita bata jin zata iya jurar zama tare da mutanen da basa kaunarta su ci abinci. Dama tuni ta soma jin yunwa. Tana budewa taliya ce da miya sai coleslaw a gefe. Kare masa kallo tayi tana mamaki. Abin kuma harda rowar abinci? Abincin dan kukut a plate kamar zaa bawa Khalifa. Tas ta cinye ta sha ruwa rabin robar. In ba haka tayi ba tasan bazata koshi ba. Hamza tun bayan azahar suka fita da wani abokinsa. Gidansu Zuhra suka je yi musu ban gajiya. Su Umma sunji dadi sosai. Har ta cire kunyarta ta tambayeshi ya Zuhra ta kwana. Murmushi yayi sannan yace mata lafiya kalau. Tana gaishe su. Da zasu tafi Baba ya bawa Hamza wayar Zuhra. A jakar Hajara ta manta ta daren jiya. Juya wayar ya rinka yi, banda tsufa ta dade da fita yayi. Da daddare ma har daki aka biyota da abincin. Macaroni ce da vegetable soup. Sai dai Zuhra ta tsani macaroni. Duk yunwar da take ji dole ta hakura. Gudun kada aga kwadayinta ma ko naman dake cikin miyar bata ci ba ta dauki tray din ta sauka kasa dashi. Tana tafiya Hamza da Izzatu dake zaune a dinning table na binta da ido. Bata ko tanka musu ba ta wuce ta ajiye abincin a kitchen. Ta fito kenan Tala ta biyota da sauri. "Naga baki ci abincin ba" Dan murmushi tayi "na koshi ne". Tana wucewa idonta ya kai kan nasu abincin. Shinkafa suke ci, wato ita suka hada da macaroni. Hamza na lura da irin kallon da take musu har ta wuce. Wurin karfe goma da rabi Zuhra tana zaune tunani duk ya isheta gashi ta manta wayarta a gida. Ga uwa uba yunwa. Turo kofar taji anyi tayi saurin tashi zaune ta saka hijab. Daga ita sai daurin kirji saboda zafi ya dameta. Kafin ta rufe jikinta ya kula da daurin kirjin. Ba karamin tsanar sa yayi ba. Bai tsaya jan zance da ita ba yace.. " kina jindadin cin abincin ke kadai ko zaki rinka ci tare damu?" Tasan har ransa ba so yake taci dasu din ba." Zanci ni kadai" "Fine, sai ki rinka fada da wuri idan bazaki ci ba saboda a dena wasting. An kawo miki kin mayar batare da kin taba ba". Idan kika yi shiru zaki kwari kanki shine abinda zuciyarta ke raya mata. Ta dan rage murya "bana cin macaroni ne" "Macaroni kuma? Mtsw ke bana son karya." Turo baki tayi "ni ba karya nake ba. Abinda aka kawo min kenan." Dafa kansa yayi yadda yake idan yana cikin damuwa." Me yasa bakiyi magana ba. Anyway nasan shinkafar bata kare ba idan kina so kije ki ci." Tana kallo ya karaso cikin dakin ya kunna wani abu. Da yake tana setin AC din tuni ta fara jin iska. Yana gani tayi murmushi. Sannan tace. "Don Allah ina ka kunna? Jiya zafi ya isheni na zata da sankarau zan tashi da safe" Ta kusa sashi dariya sai ya gimtse. Idan ya sakar mata fuska zata yi tunanin ta sami karbuwa ne. Remote din AC din ya nuna mata sannan ya miko mata wayarta da chaja a cikin leda. Murna tayi sosai tayi masa godiya. Sai da ya kama hannun kofar ta sake magana tana sosa keya. "uhmmm" Ya tsaya yana kallonta "yes" ganin taki magana. "Dama, dama famfon bandakin ne naga kamar sun lalace." "Kin lalata su dai" ya fada yana shiga ciki. Ya duba duka komai lafiya kalau. Ya fito "wai ni abokin wasanki ne? Babu famfon da ya lalace" Bata ce komai ba tayi saurin shiga. Hannu ta tara a famfon sink da baho duk ruwa ya fito da kansa. Sai da ya tsorata ta duk da ta gani jiya. " ka gani ko, yau tun sallar asuba da shaya nake yin alwala." Wannan karon murmushi yayi. Sannan yayi mata bayanin yadda kan famfon yake. Tun kafin ya fita ta rinka bi tana tara hannu ruwa na zuba. Dariya take yi don abin ya burgeta. Yace to kada ki karar mana da ruwan gidan. Kunya taji tayi saurin cire hannunta ta fito. Shi kuwa tuni ya fice ya tafi nasa dakin. [9/25, 3:51 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #32 Batul Mamman(Mrs)# Haka rayuwa ta kasancewa Zuhra a gidan Hamza. Kullum safe, rana da dare duk zaa kawo mata abincin marowata kamar yadda take kiransa. A kullum zata yi waya da iyayenta. Idan bata kira ba zasu kira ta. Idan aka tambayeta Hamza tace yana nan kalau. Bata taba tunanin fadin komai ba domin Anti Faiza tace zaman gidan miji yana bukatar sirri. Ko Hajara ta hanata ta sanarwa komai na dangane da gidan aurenta. Hamza dai yasan ana bata abinci saboda haka bai taba damuwa da sanin yawansa ba. Idan ta fito sauka da kwanunkan abinci suka hadu da Izzatu zata gaisheta a ciki ciki. Itama da kyar take amsawa. Don Hamza yayi mata fadan baya son gaba ne da ko kallon Zuhra bazata yi ba. Shi kuwa matsalar kamfaninsa tasa shi a gaba, bashi da lokacin gidansa sosai. Ranar alhamis da safe Tala ta kawo mata abinci kamar kullum. Tea ne a dan karamin cup irin mai saucer dinnan wanda kurba biyar zuwa shida zai kare. A plate din kuma sliced bread ne guda uku. Wani irin kallo Zuhra ta yiwa abincin. Ta dauki bread daya taji shi a bushe da tauri. Murmushin yake tayi... Tala yau kuma bushasshen brodi kike kawo min. Tala ta dawo ta dan durkusa gabanta amarya ai wannan tos ne. Tala zata yi sa'ar Izzatu ko ta girmeta da kadan. To...to me? Zuhra ta fada tana yamutsa fuska. Tala tace tos. A tosta ake sakawa sai kiga ya fito ta sama kamar an jeho shi. Har dan bota na shafa miki don kiji dadinsa. Zuhra ta gyada kai, naga alama. To nagode. Bayan fitar Tala tayi ta juya bread din a hannunta. Tunda tazo gidan breakfast dinta na farko ne kawai ta taba koshi. Kullum sai dai rage hanya, gashi bata taba ganin alamar za'a fara aikin nata kitchen din ba. Ba yadda ta iya a dole ta fara cin bread din. Kana ganin fuskarta kamar mai shan madaci. Ko rabi bata ci ba ta shanye tea din. Ta sake kai bread din bakinta Hamza yayi sallama ya shigo batare da ya jira ta amsa ba. Zaune take da tray a gabanta kanta babu dankwali. Doguwar riga ce a jikinta ta wani material. Dinkin dai yayi kyau sai dai wadda tasa kayan ce sai a hankali. Sunkuyar da kanta tayi kasa tace ina kwana? Bai amsa ba yana daura agogo a hanunsa ya dubi plate din gabanta. Ashe ma zaki iya ci. Dama naga toasted bread aka yi nayi tunanin baki saba ci ba a baki wani abincin. Zuhra tayi sauri ta tofar da na bakinta akan tray din. Wallahi bana iya ci, hakan ma dauriya ce kawai. Hamza ji yayi kamar ya amayar da abinda yaci. Wannan wace irin kazanta ce ta gama jika bread a bakinta ta dawo dashi. Fuskarsa na kallon gefe yace naga saura biyu da rabi ki cinye. Tashi tsaye tayi tana karkade hannuwanta...wallahi dama uku ne. Dan murmushi yayi...haka Izzatu take bata son ayi abinci da yawa, a cewarta zasu yi kiba suyi loosing shape. Farkon aurensu har rama ya rinka yi. Daga baya sai yake siyan biskit da cake a ajiye a office. Kyalesu zaiyi, kila idan Zuhra ta dan horo zata nemi komawa gidan iyayenta. Sai ya saketa cikin sauki. Ba tare da ya kalleta ba yace zansa a kawo miki wani abincin. Da ya juya zai tafi yaji tace adawo lafiya, Allah Ya kiyaye, Ya bada sa'a, Ya tsare kuma Ya kare dukkan sharri. Adduar tayi masa dadi yace Amin a hankali. Wannan adduar kullum Umma sai tayiwa Baba idan zai fita wurin sana'arsa. Tunda ya fita bata ga alamun abinci ba sai uku saura aka kawo na rana. Cikin kankanin lokaci ta tayar da abincin. Ta fito daga toilet kenan Tala ta shigo tace amarya kinyi baki. Shikenan anzo wurin.....kullum addua take yi kada tayi baki saboda bata san me zata basu ba, yau gashi wasu sun zo. Tunani ta soma yi lokaci guda idea ta zo mata. Kanta ta rike da hannu biyu ta rufe ido. Tala kaina ciwo yake min sosai kamar zai tsage. Tala tayi saurin karasawa ta riketa har bakin gadonta. Sannu amarya ko na karbo miki magani wurin Anti Izzatu? A'a Zuhra tayi saurin dakatar da ita. Nima ina da shi. Kice su hawo nan bazan iya saukowa ba. Tala duk tausayin Zuhra ya kamata tace ba komai amarya. Kafin ta fita Zuhra tace ki dan taimaka musu da ruwan sha don Allah. Tana fita Zuhra ta gyara kwanciya. Bata san ko su waye ba amma dai tasan gidan amare ana son a bawa baki dan abin kusa da baka. Ita kuma bata da komai, idan za'a bata ma karba zata yi. Ba jimawa yan uwansu na Ajingi suka shigo. Kirikiri Zuhra taki tashi tana ta langabewa ita mara lafiya. Da muguwar rawa gwamma kin tashi. Anti Faiza ce ta rako su. Suna ta mata tsiya ko har an fara laulayi ne na kwana biyar. Ita dai sai murmushi take yi a dole taji kunya. Tala ta kawo musu ruwa harda lemo a jug da kofona. Basu dade ba suka ce gobe zasu koma Ajingi. Tayi musu godiya ta rakasu har kofar daki. Sai da suka sauka kasa Anti Faiza ta dawo da sauri take tambayarta yaya zaman nata. Kuka Zuhra tasa mata ta sanar da ita ko abincin kirki ba'a bata. Anti Faiza tace kiyi hakuri gobe za'a kawo gararki. Akwai kudi ne a wurinki? Zuhra ta share hawayenta tace eh Baba ya bani. Duka ta debo ta bata Anti Faiza ta dauki dubu goma a ciki ta bata sauran. Zanje kasuwa gobe kafin azo kawo garar zan zo in sha Allah. Ta dafa kafadarta...ki kara hakuri kuma kada ki bari Izzatu ta san ba kya jindadin zaman. Daga ita har mijin nata so suke kiyi abinda zai sakeki. Kuma In sha Allah kinzo kenan, yadda iyayensa suka yi miki kokari kema ki dage nemawar kanki wurin zama a zuciyarsa. Zuhra ta tura baki ni me zanyi dashi Anti? Ai kawai idan ya gaji ya sakeni. Anti Faiza toshe mata baki tayi. To banza na sake jin zancen saki sai na fasa miki baki. Biskit ta dauko guda biyu a jakarta ta bawa Zuhra sannan ta sauka kasa suka tafi. Fitarsu ke da wuya Izzatu ta shigo tare da Tala. Zuhra tana kwance akan kujera ta gansu. Tashi tayi zaune tace lafiya cike da tsiwa. Fuskar Izzatu a daure tace ke kika ce Tala ta bawa bakinki ruwa da juice a jug dina? Zuhra ta kalli Tala tayi tsuru tsuru. Kiyi hakuri na zata mijinmu ne ya saya shiyasa nace ta taimaka ta kawo. Izzatu ta soma fada rai a bace...mijinmu fa kika ce? Yanzu Zuhra don baki da kunya sai ki hada baki da inlaws dina ki auri mijina kawai don kinga ina sakar miki fuska. To Tala mai aikina ce ni kadai kuma kada ki sake taba min kaya. Ignorant fool yadda kika zo haka zaki fita ki bar min gida. Zuhra tayi yar dariya ko na kwana daya ne Izzatu kin taba zama da kishiya a tarihin rayuwarki. Izzatu ta tsaya tana kallon Zuhra..dama bata da kunya? Kwafa tayi sannan ta fita tare da buga kofar da karfi. Tala ta dauki tray din Zuhra na bata hakuri tace babu komai. Ita sai mamakin wannan aure na ubangidanta take da yadda suke wulakanta amaryar. Zuhra tayi murmushi ko ba komai yau ta dan gasawa Izzatu magana taji dadi. Daren ranar ba'ayi girki ba ana jiran Hamza ya kawo abinci daga tantalizers. Da yake bai fito office da wuri ba abincinsu ya kare sai snacks ya siyo. Yana wanka Izzatu ta rabawa kowa banda Zuhra. Shima burger yaci ya kwanta a zatonsa an aikawa Zuhra nata. Tala tana son tambayar na amarya tana tsoro don ba karamin fada Izzatu tayi mata ba. Har shadaya da rabi babu abinci babu dalilinsa. Dole Zuhra ta karasa sauran biskit din da Anti Faiza ta bata ta shiga toilet ta sha ruwa sannan ta kwanta ciki na kukan yunwa. [9/25, 3:52 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #34 Batul Mamman(Mrs)# Kafin Hamza ya dawo daga raka su Mama mota tayi saurin shigowa ta hayewarta sama tana murza hannunta wanda ya matse mata harda hawayenta. Tala tana kwashe trays din da aka yi amfani dasu Izzatu ta tsaya mata a ka. Nace Tala ko kin gaji da aikin ne? Ido ta zaro a'a Hajiya wani abin ne ya faru? harara Izzatu ta jefa mata. Jiya banyi miki magana akan yiwa bakin yarinyar nan amfani da kayana bane? Tala tace Allah Sarki ai naga harda maman Alhaji shiyasa na dauko musu. Kiyi hakuri. Izzatu tace ba mamansa bace kishiyarta ce. Kuma na karshe kenan da zaki taba min kaya da sunan karrama bakinta. Wallahi ranar zaki koma kauyenku. Daga nan ta juya ta koma kan kujera ta zauna tana huci. Yadda Mama da su Mariya suka ki amsa gaisuwarta ke damunta. Kwafa tayi inma suna rawar kafa ne sun koma bayan amarya zata bar gidan ne da wuri. Su basu san wasa bane ko abubuwan nishadi da har zasu ji haushin abinda tayiwa Zuhra asa mijinta aurenta. Tana ta karkada kafa tana mita a ranta Hamza ya shigo yayi hanyar sama. Da bibbiyu yake tsallake steps din. Murmushin mugunta tayi Allah Yasa daga nan ya saketa kowa ya huta. Zuhra na tsaye gefen kujera tana hawayen yadda hannunta ke zafi tace kuma Allah Ya isa na....dawa kike taji Hamza ya fada yana shigowa dakin. Duk da ta tsorata cike da tsiwa fuska duk hawaye da majina harda murguda baki tace da wanda ya tsargu. Baki Hamza ya saki lallai yarinyar nan bata da kunya. Shi saboda yadda yaki jinin raini shiyasa baya shiga sabgar autarsu Hamida. Itama tsiwa ce da ita.... Ke, dani kike? Share shi tayi ta cigaba da matsa hannu. Tsawa ya daka mata ke ba kya jina ne. Nace ni kike yiwa Allah Ya isa? Waige ta soma yi hagu da dama ita a dole bata san da wa yake ba. Ransa ya kara baci yayi kanta. Da gudu ta kara shigewa cikin dakin sai da ta kai jikin bango. Kafa yasa ya buga kofar da karfi daidai da bugawar zuciyarta. Sai rarraba idanu take. Wani irin kallo yake mata kafin ya sake cewa wai kina ji ina tambayarki kin kasa bani amsa saboda ki nuna min ban isa ba. Tsoro kam ta gama ji amma ta rantse bazata yi shiru ba tace au dama dani kake? Maganar ta sake sosa masa rai ya biyota har inda take tsaye jikinta ya soma rawa. Tana cigaba da hawaye tace to ai ke naji kace ni kuma da aka haifeni Baba saniya da rago ya yanka ya rada min suna Fatima. Dayake sunan Innarsa ne da kuma Ummana shine ake kirana Zuhra. Ta turo baki sai ka zabi daya a ciki ka dena ce min ke kamar wata...yan lips din nata ya kama da yatsunsa biyu. Taji zafi ta fara kokarin cire hannun nasa. Idan kika ki tsayawa tsinkesu zanyi sai naga na tsiwar . Idanunta duk sun firfito sai hawaye sharrr. Sai lokacin ya kare mata kallo. Ba wani tsahon kirki gareta kuma tana da jiki madaidaici. Kalar fatarta bata da haske sosai amma kuma ba baka zaa kirata ba. Akwaita da idanuwa masu kyau ga hancinta da baki duk yan madaidaita. Banda rashin iya kwalliya da itama zata shiga jerin matan da basu da muni. Hijabin jikinta ya kalla duk yasha hawaye da majina. Sai lokacin yaji kyankyami ya sakar mata lebe. Ta karkace baki ta sake cewa Allah zai saka min. Kan gadon ta haye zata zagaye shi ta gudu. Yasa hannu ya fizgota ta saki kara. Da karfi ya manna ta da bango ta runtse idanunta tana jira ya sake kama leben. Dalli taji masu zafi guda uku ta sake cewa Allah Ya....wani ya kara mata da yafi sauran zafi. Nan da nan ta soma kuka mai sauti. Irin kukan da idan ta fara a gida har makota sai sun leko an bata hakuri take denawa. Hamza huci kawai yake don bacin rai. Me zaisa Alhaji ya hadashi aure da wannan mara kunyar yarinyar. Gashi ta kafeshi da idanu kamar wani sa'anta. Yi min shiru ya fada da karfi. Tsaf ta hadiye kukanta. Ina so kisan cewa ba'a min rashin kunya. Sannan kika kara cewa Allah Ya isa sai na dirje miki baki. Kina jina? A hankali ta gyada kanta domin taji zafi a bakin da ya dalle. Good ya fada, me yasa baki fada min za'a kawo gara ba? Kuma a ina kika sami abinda zaki bawa bakin? A hankali tace Anti Faiza ce ta kawo. Ga gidan yunwa ko, shine abinda za'a bawa baki ma sai kin roka don ki jawo min magana ace bana kula dake. Hannu tasa ta rufe bakinta sannan tace nima bansan zasu zo ba sai jiya. Kuma ban ganka ba bare na fada maka. Ni duk abinda kuke yi min banji haushi ba sai....sai me ya tambaya da yaga ta kasa karasa maganar. Ba komai ta sunkuyar da kai. Zare mata ido yayi bazaki fada ba sai na kara dalle bakin. To ba kaine jiya kace zaka aiko min da abinci ba amma naji shiru. Da daddare ma kuka barni na kwana da yunwa. Wani iri yaji a jikinsa...kika kwana da yunwa??? Nufinki ba'a kawo miki abinci ba. Zaka ce baka sani bane.....auuuu, tayi saurin rufe kanta da hijab kada ya sake mata wani abin. Ga mamakinta shiru taji tana dago kai har ya bude kofa sai ya juyo. Da sauri ta sake rufe bakinta. Key din kitchen din ya jefo mata gashi nan zansa a hada miki gas cooker. Bai kula ba yayi tafiyarsa. Key kuwa a goshinta ya sameta ta soma tsalle tana ihu. Allah Ya isa ta fada a hankali. Kasa ya sauka ya sami Izzatu tana kallo. Tana ganinsa ta taso Baby....hannuwanta ya ture da take shirin taba shi. A wane dalili ne jiya baki bawa yarinyar nan abinci ba? Wani irin kallo ta masa Why do you care? Saboda matata ce hakkinta ne na ciyar da ita. Matarka fa kace Hamza? Har Zuhra takai matsayin da zata hada kai dani. Wallahi sai ka saketa a yau....wayarsa ce ta soma ringing. Yana dubawa yaga manajan bankin da ya tura Inuwa ne ya karbo kudi a cigaba da aikin ginin da suke yi. Izzatu sai fada take yana daga mata hannu tayi shiru taki. Mr Oscar ya gama tsorata tunda manajan yace bari ya kira Alh Hamza ya tabbatar ko shi ya aiko shi. Ya gama hango kansa a matsayin korarre daga aiki kila ma a rufe shi. Bayan sun gaisa manaja yace Alhaji dama na kira ne domin confirming ko kai kayi authorizing cheque na 10 million. Gefe Hamza ya dan matsa amma Izzatu har nan ta biyo ita wallahi ko ita ko Zuhra. Daidai sanda manaja yace ka turo Mr Oscar Hamza baiji ba amma tunda yasan ya turo Inuwa sakatare sai yace eh ya ajiye wayar. Ya juyo ransa ya gama baci Izzatu ki shiga hankalinki dani wallahi. For God's sake ya kike so nayi da rayuwata ne. Daga ke har yarinyar da kika yi sanadiyar zuwanta gidan nan bakwa gabana. Duk kin birkita min lissafi lokaci guda. Da kamfanin zanji ko masifarki? Come on get out of my way ya tureta ya fice don ya kusa makara masallaci. Mamaki ya kama Mr Oscar lokacin da manaja ya bada order a bashi kudin. A tsorace ya karba jiki na rawa yana ta tunanin kada ace ya dawo dasu. A daidai bakin gate suka hadu da Inuwa sakatare. Cikin Mr Oscar ya murda sosai ji yake kamar ya saki zawo don firgici. Inuwa yace Oscar kaima ashe kana banking a nan. Nima sauri nake kada su tashi kasan yau Friday Oga ya aiko ni. Kai kawai Oscar ya gyada yayi gaba yana kankame jakar kudin. Inuwa bai kawo komai ba ya shiga bankin. Shima wurin manaja aka kaishi saboda yawan kudin. Manaja yace kuma kaga yanzu wani maaikacin kamfaninku ya karbi the same amout na 10 million. Hala babban project ne a gabanku. Inuwa sakatare yace Oscar ma kudin kamfani ya karba? Manaja yace eh har da Oganku nayi confirming. Inuwa yayi mamaki dai amma sai ya karbi kudin ya tafi. A iya saninsa shi kadai Oga yake aika banki. [9/25, 3:52 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #33 Batul Mamman(Mrs)# Washegari Jumaa tun bakwai da rabi Hamza ya fita zuwa site din da suke wani gini. Dama a daren Izzatu ta kai masa karar Zuhra wai tayi mata rashin kunya. Da safe ta sake tuna masa yace idan ya dawo zaiyi maganin abin. Yau bakin shayi da bread aka kaiwa Zuhra a matsayin breakfast. Bata nuna damuwa ko kadan a fuskarta ba da Tala ta kai mata. Tasan Izzatu na neman suyi fada ne ita kuwa bazata biye mata ba. Bayan ta gama sha ta dauki kofin ta sauka kasa. Junior ne ya tareta a kofar kitchen din...Zuhra meyasa kika dena cin abinci tare damu? Shafa kansa tayi babu komai nafi son zama a daki ne. Hannunta ya rike to nima zan rinka zama a dakinki. Khalifa ya taho da sauri ayi hirar dashi suka hada ido da Izzatu. Ba shiri ya koma dakinsu don yasan ma'anar wannan kallon. Tsawa ta dakawa Junior tace ya bar wurin. Ya buga kafa a kasa ni Mummy ki kyale ni Zuhra is my new fiyend(friend). Karasowa tayi gabansu ta kalli yadda suka rike hannu. A sakar min hannun yaro ko. Zuhra ta durkusa a gaban Junior. Kaga tunda Mummy tace ka tafi to ka zama yaron kirki kaji. Watarana har goyaka zanyi,amma yanzu idan kana rashin kunya babu ruwana da kai. Murmushi yayi wanda ya kara fito da kammaninsa da Hamza. Pyomis(promise) ya fada yana tsalle. Dariya kawai tayi don bata gane abinda yake nufi ba. Ga mamakinta dage yayi ya mata kiss a goshi tunda durkushe take a gabansa. Izzatu ta fizgo shi tana fada. Muje nayi maka brush, ji yadda ka taba wannan kazantar da bakinka. Ta gallawa Zuhra harara, ita kuwa bata tanka mata ba har suka shige ciki. Mamaki take yadda dan karamin yaro ya iya iskanci a cewarta. Kiss ai sai marasa kunya..... Bata bar wurin ba Anti Faiza tayi sallama. Da sauri ta tarota ganinta da kaya niki niki. Kwalayen juice ne guda hudu, ruwa guda biyu da cake da biskit duk na kwali. Sai da suka gama hawa dasu Anti Faiza ta sake fita ta dauko wata katuwar kula da taimakon mai adaidaitan da ya kawota. Zuhra tace Anti Faiza wannan kayan fa? Bari na sallami mutumin nan ina zuwa. A falo ta jirata ta dawo. Sai da suka gaisa Anti Faiza tace kudin da na karba a wurinki dashi na siya. Kinga anjima zaa kawo gara sai ki bawa baki. Sauran ki ajiye kiyi amfani dasu. Ta nuna kular can kuma meatpie ne da spring rolls shima sai a basu. Da kuka Zuhra ta rungume Anti Faiza tana godiya. Hayaniya Izzatu ta soma ji ta fito falon. Mata ta gani wadanda bata sani ba zazzaune suna ta hira. Ana yan ciye ciye, yan uwan su Zuhra ne da wasu makotansu harda Maman su Anti Faiza. Basu jima ba sai ga su Mama , Mariya, Jidda da Ummahani matar Ibrahim. Cike da kunya Zuhra ta gaishe su. Mama tace duk kannenki ne kike durkusa musu. Tashi abinki kinji matar Yaya. Kunya sosai take ji yadda Mama ke janta a jiki kamar wata yarta. Su Umma sunyi matukar kokari kayan garar da suka hadawa Zuhra. Mama ta basu tukwici suka fara shirin tafiya saboda kada a rufe tituna tunda Jumaa ce. Izzatu komawa tayi daki ba tare da ta sauko sun gaisa ba ta dauki waya ta kira Hamza. Shi da accountant din kamfaninsa ne suke ta lissafin kudi. Duk yadda zaiyi su hada kudin nan kokari yake yi. Sau uku ta kira baya dauka saboda abinda yake yi. A na hudun ne ya dauka Izzy what is it? Honey ni bansan abinda akeyi ba a gidan nan amma ga su Mama da wasu matan da ban taba gani ba a cikin gidan nan. Kamar wata walima suke yi ko me oho. Ana ta ciye ciye dai a falon. Table din gabansa ya buga rai a bace. Ya rasa wani irin abu ke faruwa dashi. Wane irin taro ake yi a gidansa wanda bashi da masaniya a kai. Tunda Izzatu tace harda Mama gara ya kira yaji ko meye. Yayi ta trying din number dinta ba'a dauka. Suna can tasa ana ta shigo da kayan garar cikin falo. Ta tambayi Zuhra tace key din inda akace shine kitchen dinta baya wurinta. Jin shiru da yayi yasa ya hada kayansa yace da accountant din zaije gida ya dawo. Yana fita Mr Oscar ya fara hada takardun da yazo dasu wurin. Cheques ya gani har hudu na miliyan goma goma da Hamza yasa hannu. A take zuciyarsa ta soma rawa. Kamfanin nan na Hamza nema yake ya durkushe duk su rasa aiki. Gara ya taimaki kansa kawai. Guda daya ya dauka ya fita. Shima rufe nasa office din yayi sai banki. Hamza na zuwa gida ya tarar saura Anti Faiza dasu Mama. Duk sauran matan sun watse. Izzatu na ganin shigowarsa ta taga ta fito daga dakinta. Sai a lokacin ta gaishe da Mama. Ko kallonta bata yi ba ta cigaba da tambayar Hamza ya aiki. Baya jindadin yadda iyayensa basa shiri da Izzatu. Tace Mariya ya yara? Itama bata kulata ba. Ai nan Hamza ya soma fada akan me zata share matarsa. Jidda tace Yaya munfi awa daya a gidan nan bata fito ta gaishe da Mama ba sai yanzu. Kallon Maman yayi tace kaga ina key din kitchen din Zuhra a bude a zuba kayan nan a ciki. Sai a lokacin idanunsa suka kai kan kayan. Kamar ya tambayi ko na meye sai ya fasa yace yana daki bari na dauko. Mama tace yi zamanka mu danyi hira yanzu zan tafi. Zuhra jeki ki dauko....dibi dibi ta soma yi don bata san inda zata duba ba. Izzatu ta sha kunu , shi kuma ya dan wayance ki duba bedside drawer ta bangaren dama. A sanyaye ta hau saman. Ita da sau daya ta shiga falonsa ma bata gane inda yake nufi ba. Su Nana ne suka fito daga daki sai murna anga Grams. Shiru Zuhra bata dawo ba yayi dan murmushi Mama bari na bita. A falon ta tsaya kasa shiga dakin. Bata ankara ba taji ya shigo ya rufe kofar har sai da gabanta ya fadi. Hannunta ya ja cikin dakin ya matse shi iya karfinsa. A tsawace yace what the hell is happening a gidan nan? Jikinta a take ya soma bari ga hannu ya matse mata. Idanunta suka ciko da hawaye, ya sake yi mata tsawa nace me ake yi a gidan nan? Kayan garata aka kawo. Tana fada hawayen ya soma digowa. Ransa ya gama baci, kin fada min za'a kawo gara??? Tayi saurin girgiza kai. Snacks da nagani anci a falon daga ina aka samo su? Shiru tayi saboda yadda hannunta ke zugi. Baki da baki ne? Nan ma bata yi magana ba. Sakinta yayi ya dauko key din sannan ya nuna mata toilet maza kije ki wanke wannan hawayen munafurcin. Da gudu gudu ta tafi. Koda ta fito yana jiranta suka sauka tare. Mama tana murmushi tace daga dauko key sai ka shanya mu Yaya. Zuhra yake kallo abu ne ya shigar mata ido na tsaya wanke mata. Kowa sai sannu yake mata ana tambayarta ko ya fita. Budar bakinta kawai sai ta soma kuka. Mama ta tashi da sauri tana tambayarta me aka yi mata. Shima Hamzan tambayar da yake mata kenan a dan tsorace. Tana kukan tace idon ke zafi....Mama ta rungumeta Yaya kace yar tawa sarauniyar shagwaba ce. To sannu kinji Fadimatu ki dena kuka. Idan bai fita ba sai kuje asibiti Yaya. Kai kawai ya daga yana kallon Zuhra cike da tsoron kada ta fadi abinda yayi mata. Sai da aka shigar da komai kitchen din har Mama na fadan garin yaya ba'a fara aikin gyara wurin ba yace sai weekend mai aikin zai zo. Tare da Anti Faiza suka tafi suka ajiyeta a hanya. Zuciyar Mama tana mata wasi wasin dalilin kukan Zuhra. Bata sani ba ko idonta ne amma kamar ta rame ma. [9/25, 3:52 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU # 35 Batul Mamman(Mrs)# Fadan da Hamza yayiwa Izzatu yasa ta kuka sosai bayan fitarsa. Kwana biyu a tsakani yana share lamarinta. Ranar monday ran kowa a bace suka rabu saboda sun kwana da fushi da juna. Ta dage sai ya saki Zuhra idan yana son zaman lafiya. Takaicinsa shine kamar bata san mahaifinsa yayi masa katanga da sakin Zuhran ba. Ita ba ruwanta ko Alhaji zaiyi fushi dashi ita dai bukatarta ta biya. Ko kulata baiyi ba ya fice abinsa. Saboda bacin rai wata jaka ta dauko tana kuka tana watsa kayanta a ciki. Sai da ta gama ta kira mahaifiyarta tana sanar da ita zata taho gida. Idan babu jirgi zata yi shatar mota. Da kyar Raliya ta samu Izzatu ta fada mata abinda ya faru. Tsaki Raliya tayi...ni bansan baki da hankali ba sai yau Izzatu. Yanzu sati daya da zuwan yarinyar har kin karaya? Duk ke kika jawowa kanki ai. Muryarta har ta dashe don kuka tace what do I do Mum? Bazan iya zama da wata mace a gidan nan a matsayin kishiya ba. Raliya tace calm down. Yanzu abinda nake so dake shine ki bude kunnuwanki kiji abinda zan fada miki........... A site din ginin Hamza ya hadu da Inuwa sakatare yace Inuwa hala baka sami zuwa bankin bane ranar Jumaa banji alert ba. Ikon Allah kuma naje ranka ya dade har ma na hadu da Oscar. Sakon yana cikin motata bari naje na dauko. Hamza ya dakatar dashi. Ka bari sai mun koma office. Zuhra tayi mamakin abincinta na rana yau. Duk da bashi da yawa sosai amma yafi abinda aka saba zuba mata. Da laasar ma Izzatu har shiga dakinta tayi tace mata zata je unguwa. A darare Zuhra tace Allah Ya kiyaye hanya. Bayan ta tafi Zuhra ta tashi taje inda Izzatu ta tsaya zuwa bakin kofa ta karanta Ayatul Kursiyy ta tofa a ko'ina. Irin wannan makircin na kishiyoyi ai mun saba jin labarinsa ta fada a fili tana dan dube dube ko an barbada mata wani abin. Kin gama yi min masifa yau kice min zaki fita kamar nice dan gatan mijin nan naki. Ga mamakinta da Izzatu ta dawo tare da yaranta suka sake zuwa dakin Zuhra tace ta dawo. Da dan murmushinta na tsoro tace sannu da zuwa. Zuciyarta ta gama bata akwai abinda ke shirin faruwa ko zai faru. Ranar Hamza bai sami dawowa gida ba sai wajen tara na dare. Gidansu ya biya Mama take tambayarsa yaushe zai kawo amarya. Dammm yaji a zuciyarsa, yanzu jira ake ya dauko wannan kazamar a mota. Cewa yayi weekend in Allah Ya yarda zai kawota. To ka biya da ita taga nata iyayen inji Hajiya. Lokacin da ya shiga gida falon tsit. Yasan su Khalifa sunyi bacci saboda makaranta. Dinning table ya kalla yaga an jere shi da kwanuka kamar ana jiran baki. Ko bi ta kai baiyi ba ya haye sama ya shige daki. Abinda ya kwana biyu bai gani bane Izzatu ta gyare dakin tas sai kamshi ko ta ina. Murmushi yayi yasan tana neman shiri kenan. Jakarsa da takalma ya ajiye yana cire safa ta fito daga toilet dinsa sanye da wata rigar bacci mai matukar kyau. Binta yayi da ido har ta karaso gabansa. Ba karamin kyau tayi ba tasha kwalliya. Safar ta karasa cire masa sannan ta rage masa kayan jikinsa. Bata ce komai ba shima baiyi magana ba. Toilet ta kaishi ta taimaka masa yayi wanka. Abinda ta dade bata yi ba tun kafin tayiwa Zuhra April fool. Sai da ta gama shirya shi suka je kasa ta bashi abinci da kanta. Da ta tabbatar ya koshi sai suka koma dakinsa durkusawa tayi a gabansa gwiwoyinta a kasa ta soma kuka. My sweetbaby nasan na bata maka rai da yawa a iya zaman da muka yi amma ina rokonka don Allah ka yafe min. Hannuwanta ya kama zai tayar da ita zaune taki tashi. Bazan tashi ba sai ka fada da bakinka ka yafe min. Na janyo maka auren da mu duka bamu shirya masa ba sannan itama yarinyar na dauki alhakinta. Kukanta har ransa yake ji. Tayar da ita tsaye yayi ya rungumeta yana rarrashi. Komai ya wuce Izzy tunda kin gane kuskurenki. Kissing dinta ya soma saboda shi kanshi ba karamin missing dinta yayi na. Wani dadi taji yana ratsata ta biye masa. Sun jima a haka kafin tace Hamza dear ina zuwa. Sai da tayi da gaske ya saketa ta fita. Dakin Zuhra taje, lokacin Zuhra tana waya da Hajara suna ta hira kamar bata da wata damuwa. Ganin Izzatu a bakin kofa yasa tayi saurin sallama da Hajara. Da fara'arta kamar Izzatun da ta fara sani tace kizo zamuyi magana a dakin Hamza. I hope ban takura miki ba? Zuhra kallonta take da mamaki ga wata irin riga da ta saka. A ranta tace wasu matan dai basu da kamun kai. Yanzu meye na shigo min daki tsirara. Mayafinta ta dauko ta yafa tabi bayanta. Suna zuwa Izzatu bata daukeshi komai ba ta fada jikin Hamza wanda yake sanye da wandon bacci kawai. Dorawa yayi daga inda suka tsaya. Zuhra tayi saurin runtse ido ta juya baya tace wayyo na shiga uku iskan...... Hamza na ganinta yayi saurin ture Izzatu tare da yi mata tsawa. Idan kika kuskura kika ce iskanci sai na dalle miki baki. Kina hauka ne zaki shigo mana daki babu sallama. Izzatu ta sake rike shi ni na kirawota baby. Rigarsa ya dauka ya saka gaba a baya saboda kunyar da yaji Zuhra ta ganshi a haka. Sabon raini zai shigo kenan. [9/25, 3:53 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #36 Batul Mamman(Mrs)# Bakin kofar Izzatu taje ta riko hannun Zuhra suka shigo cikin dakin. A gefen gado ta zaunar da ita, mugun kallon da Hamza ya watsa mata yasa tayi saurin zamewa kasa, dama a darare ta zauna. Wasu yan siraran hawaye Izzatu ta soma yi tace Zuhra don Allah ki yafeni. I played a cruel joke on you. Zuhra tace eyye...play kuma? Kawar da kai Hamza yayi yayi dan murmushi. Yana ganin da kyar idan Zuhra ta fahimci abinda Izzatu ta fada saboda yadda ta soma yaken karfi da yaji. Izzatu ta cigaba da magana, nasan ban kyauta ba amma don Allah ki yafe min. Babu komai Zuhra tace idanunta na cikowa da kwalla. Ta dai yafe amma bata jin zata taba manta irin dariyar da Izzatu tayi mata a gaban mutane. Tashi ma tayi zata koma nata dakin Izzatu ta dan taba Hamza, baka bata hakuri ba. Ni kuma??? A wani dalili? Dan marairaicewa Izzatu tayi, shi kuma yana kallon Zuhra da ta tsare shi da ido. Dena kallona ya fada yana harararta. Kanta ta sunkuyar dama tasan bazai bata hakurin ba. Izzatu dai da fara'arta tace ni na baki hakuri a madadinsa. Kai Zuhra ta gyada kawai, Izzatu tace to tunda kin hakura ina fata zaki amince ya SAKE ki. Ta juya ga Hamza, daga shi har Zuhra kallon mamaki suke mata. Zuhra tace dama abinda kike so kenan shine kika rinka yi min kirki dazu? Duk abin Izzatu sai da taji kunya. Hannuwan Zuhra ta rike, nasan kema auren nan dole ake yi miki kamar yadda aka yi mana. Ki amince ya sakeki ki koma gida ki auri miji daidai da ke wanda zai so ki. Nasan idan da bakinki kika fadawa Alhaji ke kika nemi sakin bazai ga laifin Sweetyna ba. Sai ta kalli Hamza ta kalli Zuhra duk tunani suke yi. Dan gyaran murya Hamza yayi duka suka mayar da hankulansu gareshi. Idan kin amince da sakin bazan sake ki yanzu ba sai nan da kamar wata shida ko shekara daya saboda Alhaji bazai taba yarda ke kika nema ba. Izzatu ta bata fuska habaaaa Hamza, wata shida is too long. Hankalinsa yana ga Zuhra yana karantar yanayinta saboda ta zurfafa a tunani. Zaman gidan nan ba nata bane saboda babu mai kaunarta. Itama kuma ba son mijin take ba, son kyautatawa iyayenta da nunawa Izzatu kurenta yasa tun farko ta amince. To yanzu idan aka saketa yaya Baba da Umma zasu ji? Waye zai yarda ya aureta idan aka ji aurenta ya mutu bayan wata shida. A sanyaye ta dago kanta suka hada ido da Hamza, saurin kawar da kanta tayi kamar ba itace mai tsare mutane da ido ba. Na yarda amma don Allah kada ku bata min suna idan anyi sakin saboda iyayena....hawaye ne suka zubo mata tayi saurin rufe fuskarta da mayafinta ta fita. Tana jiyo ihun murnar Izzatu ta sake danewa jikin Hamza. Shima duk jikinsa yayi sanyi don baiyi tunanin zata amince da wuri haka ba. Dole ya sami dalilin da zai fadawa iyayensu yadda baza'a ga laifin kowa cikinsu ba. Izzatu yaji tana kokarin cire masa riga yasa hannu biyu ya rike abarsa. Meye haka? Dazu kinzo kinyi hugging dina a gaban yarinya. To meye ta fada tana jan rigarsa. Ai tasan abinda yafi haka ma munayi. Tana dariya tace Baby we need to celebrate bari na samo mana juice mai sanyi da cups muyi toasting. Duk da wata shida is a long time amma ba komai. Fita ta sake yi ta barshi yana tunani. Kamata yayi ya yi murna da amincewar Zuhra sai dai a kasan zuciyarsa yasan abinda suke niyar yi bai kamata ba. Ba jimawa ta dawo da apple juice a wata roba mai kyau ta tsiyaya musu a glass cups. Hamza zai kai nashi baki ta rike hannun, I said lets toast ta kashe masa ido. Tare suka dan buga cups din suka yi yar kara. Izzatu tace TO FREEDOM. [9/25, 3:53 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #37 Batul Mamman(Mrs)# Kwanaki biyu a tsakani Zuhra na zaune a falo don yanzu Izzatu tace ta rinka zama tana sakewa. Hatta su Khalifa tana bari su zauna da ita. Wurin karfe biyar na yamma Hamza ya shigo maigadi ya biyo shi da ledoji. Kofar inda ya kamata ya zama kitchen din Zuhra yace ya ajiye masa. Su Junior da Izzatu suna ta yi masa sannu da zuwa Zuhra ta mayar da idanunta ga kallon tv. Ita yanzu da tasan matsayinta a gidan tana ganin yi masa sannu da zuwa kamar shishshigi ne. Shima a nasa bangaren bai kulata ba suka tafi dakinsa shi da Izzatu. Ba jimawa ya fito da shirt mara nauyi da dogon wando, da gani wanka yayi. Abinci ya zauna ci suna ta hira da Izzatu. Sai da ya gama ya tashi ya bude kitchen din Zuhra sannan yace ke zo. Da farko tayi niyar sharewa sai Izzatu tace mata jeki mana Zuhra kayan miya ya siyo miki. A hankali take tafiyar har sai da yaji haushi. Ya nuna mata kayan da hannu alamun ta dauko. Wato kace na dauka da bakinka ne kake ganin asara....Allah Ya sauwake ta fada a ranta. Dauka tayi gabadaya hudun ta shigar dasu kitchen din. Kallon mamakin da yayi mata yasa ta tuna maganarsu dasu Anas da suka ce mata maza basa son mata masu karfi. Sai kuma ta tunawa kanta ai Hamza ba mijin da zasu so juna bane. Kwalin gas cooker dinta ya farke ya sake fita. Bai dade ba ya shigo dauke da karamar cylinder. Daga can gefe ya ajiyeta sannan ya hada mata gas din. Ya koma kan fridge din shima dan madaidaici ya jona mata. Ita dai tana gefe tana binsa da ido. Sai da ya gama tsaf yace ga kayan miya nan da nama sai ki saka a fridge kada su lalace. Daga yau ki rinka dafa iya abincin da zaki ci. Idan akwai abinda babu a cikin kayanki sai ki fada a siyo. Tsananin farinciki da taji yasa ta washe baki da gaske kake don Allah....daure fuska yayi, na taba wasa dake ne? Nagode, nagode, nagode ta rinka fada tana bude ledojin. Ji tayi yace kuma ki kula kada ki bata wurin nan kinga tun asali ba kitchen bane. Ya nuna mata sink shi kadai zan iya sawa idan kin tafi sai a cire amma bazan miki wani kitchen kabinet ba. Duk da haka ma nagode ta fada cike da murna. Yau zata dafa abinci son ranta taci ta koshi. Hango kanta take da kwano ba ma plate ba shake da abinci. Wannan irin farinciki da take yi yasa shi jindadi. Ko ba komai yana ganin ya tsira daga laifin tauye mata hakki a ganinsa. Zuhra tana susar kai tace uhmmm....yes ya amsa don yasan akwai abinda take son fada. Dama...dama... gajiya yayi da inda indarta yace dama me? Uhmm nace shi gas din ya zan rinka kunnawa? Au dama baki iya kunnawa ba aka kawo ki dashi. Turo masa baki tayi to mu a gida ba da itace muke yi ba ko risho. Ganin ya daga hannu tasan a bakinta zai sauke shi tayi saurin ja da baya. Nufi na fa ban saba dashi ba amma cikin kayana akwai risho din sai na fito dashi. Hannu ya daga yana nunata, ki fito da me? Wallahi kada kuskura ki kunna min risho a wurin nan in ba so kike ki sake min sabon fenti ba. Kinji ko! Gyada kai ta rinka yi kamar kadangaruwa da taji ya fara daga murya. Sai kuma yace matso ki gani..kunnawa yayi sannan ya gwada ragewa da kashewa duk tana gani. Idan kin kasa ki kira Tala ta nuna miki don naga alama kin fita kauyanci. Ni ba yar kauye bace ta fada tana kara turo bakin nan nata. Biyota Hamza yayi zaiyi maganin rashin kunya ta juya da gudu. A bakin kofa suka ga Izzatu tana dariya. Ai tunda naji kana daga murya nasan kun fara fada shine nazo kallo. Ta kalli Zuhra bai dake ba ko...babu wanda ya bata amsa ta cigaba da dariyarta ta kama hannun Hamza suka fita. Tuwo Zuhra tayi niyar yi Izzatu tace kada tayi girki an riga anyi abincin dare da ita. Har ranta bata ji dadi ba amma haka ta daure taci abincin. Inuwa sakatare yana ta hada wasu files zai kaiwa Hamza saboda meeting din da zasu yi sai gashi ya fito daga office dinsa rike da waya da makullin mota. Inuwa yace ranka ya dade fita zaka yi ne? Akwai meeting fa biyu da rabi. Ba jimawa zanyi ba Inuwa in sha Allah. Zanje banki ne tun friday kaga yau alhamis banji alert ba na kudin da ka ciro. Inuwa yace to Allah Ya kiyaye adawo lafiya. Amma ranka ya dade yaushe Oscar yace zai dawo ne muna bukatar sa hannunsa a wasu takardu. Hamza yace nima duk na damu ko jikin mahaifiyar tasa ne sai dai ban same shi a waya ba. Bari nayi sauri na dawo sai muyi maganar dai. Koda ya fita jikin Inuwa sakatare yayi sanyi....Allah Yasa abinda zuciyarsa take kitsa masa ba gaskiya bane. Manyan architects yau da kanka a office dina. Manaja ke magana yana tashi tsaye suka gaisa da Hamza. Kowa fuskarsa dauke da murmushi suka tambayi juna iyali. Manaja yace sai kuma naji kayi aure ba labari. Kai Hamza ya dan sosa yana tunanin yadda zance ke yawo a gari..kayi hakuri abin ne yazo a gaggauce. Babu komai Allah Ya sanya alkhairi. Yanzu dai how can I help you? Tashi Hamza yayi kada ka damu shigowa nayi mu gaisa na riga na sanar dasu a costumer care alert ne bana ji tun last friday. Kuma har a atm da na cire kudi still banji ba. Manaja yayi dariya ai dole ka damu ku masu harka da manyan kudi. Suna magana text ya shigowa Hamza. Yayi murmushi dadina da bankin nan saurin gyara abu. Gashi har alerts din sun shigo. Yanayin fuskarsa ne ya soma canjawa a take. Manaja ya naga alert na an cire ten million har sau biyu a ranar friday din? Manaja ma dena murmushi yayi ai sau biyun ne Architect. Ka turo sakatare dinka sannan ga mamakina ka turo wani Mr..Mr....mtsw na manta sunan amma dai na kira nayi confirming a wurinka kafin a sakar masa kudin. Jiri ne ya soma dibar Hamza daga tsaye yayi saurin dafa tebur din manaja ya zauna. Da kyar ya iya cewa Mr Oscar? Eh shi kuwa manajan ya amsa. Ka tuna na kira na tambayeka kace eh kaine ka turo shi. Tabbas manaja ya kira amma a lokacin Izzatu ke faman daga murya tana masifa sai ya saki Zuhra baiji abinda manajan yace ba ya amsa masa. Wato shiyasa Oscar yace mamansa ba lafiya ya tafi garinsu gashi an kusa sati babu mai samunsa a waya. Allahumma ajirni fi musibati wa akhlufni khairan minha. [9/25, 3:53 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #38 Batul Mamman(Mrs)# A rikice manaja ya fara tambayar Hamza ko sunyi kuskure ne. Numfashin Hamza da kyar yake fita ya dago idanunsa da suka yi nauyi lokaci guda yace babu abinda kayi manaja. Matsalar daga bangarena ne. Sau biyu yana yunkurin tashi amma kafafunsa sun kasa daukarsa. Manajan sai bashi baki yake yana rokonsa ya zauna har zuciyarsa ta daidaita amma sam yaki zama. Ko da ya shiga mota rasa wurin zuwa yayi. Gidansa zai tafi ko office zai koma. Yafi rabin awa a motar kafin ya tayar ya dauki hanya. Lokacin da ya shiga gidan babu kowa sai Kande mai aikinsu. Da fara'arta ta tare shi tana masa sannu da zuwa. Jikinsa duk a sanyaye yake yace ina mutan gidan ne naji shiru. Nura yana daki su Adabiyya kuma sun tafi makatanta. Hajiya da Mama kuma sunje unguwa. To din ma da kyar ya iya fada sai ya tashi ya tafi dakin Hajiya. Babu abinda yake a lokacin kamar yaga mahaifiyasa. Yaji dadi a bude ta barshi kamar tasan zai zo. Gadonta ya nufa ya kwanta abinda ya dade baiyi ba. Yana rufe ido sai wasu zafafan hawaye suka sauko masa. Ji yake kamar komai nashi ya tsaya cak. Cheque din da Mr Oscar ya dauka hade da sauran da suke office dinsa idan an hada miliyan arbain kenan zai hada ya bawa su Mr Peter ya kawo karshen contract dinsu. A dalilin hada wannan kudin gabadaya maaikatansa suka amince da karban rabin albashinsu a wannan watan don kawai su tseratar da kamfanin. Yanzu gashi miliyan goma ta tafi a kudin bai san ta ina zai samu su ba. Ginin gidansa yaci kudi ba na wasa ba. Idan kuma ya tattara kudaden account dinsa tare da sayar da filayensa zai iya biyan kudin to amma rike iyalinsa zai zama da matsala domin kuwa akalla kafin kudin ayyukan da yake su fito zai dan dauki lokaci. Yana wannan tunanin bacci ya dauke shi. Hajiya ta kira Mama ko sun taho daukarta daga tata unguwar Mama tace tun dazu nake kiranki ban samu ba. Gamu a garejin makanike ban je inda zani ba. Amma na fasa ana gamawa zamu biyo. Hajiya tace babu komai bari na bi adaidaita sahu kaina ke ciwo. To ki kira Nura mana yazo ya dauke ki. Hajiya tace babu komai shima yau da mura ya tashi. Sai kun dawo ni zan wuce gida. Tana gama wayar suka yi sallama da kawarta da taje dubawa ta fita ta hau adaidaita sahu. Gabanta yayi mummunan faduwa ganin mutum a kwance a kan gadonta. Alhaji yana Kumo kuma ko shine da wuya ya kwanta a dakinta. Nura kuma sai da ta leka dakinsa ta dubashi sannan ta taho nata. Babu inda baya rawa a jikinta ta ja kafa ta je gefen gadon inda zata ga fuskar mai baccin. Sai da ta dan ja baya saboda wanda bata taba tsammani ba ta gani. A tsorace tace Yaya....shima kansa ke masifar ciwo ya bude idanunsa da kyar. Hawaye ne bushe a fuskarshi Hajiya ta matsa ta taba shi. Bakinta har rawa yake saboda tsoron abinda zai ce tace Yaya me ya faru? Tashi yayi ya gyara rigarsa da ta yamutse sannan ya mayar da hularsa. Yana dan murmushi yace Hajiya babu komai. Zuwa nayi mu gaisa duk bakwa gidan. Bari na koma office sai anjima. Hannunsa ta rike. Itama hawayen take yi....haba Yaya duk duniya idan akwai wanda zaka boyewa damuwarka kasan banda ni ko. Bar ganin ban fiye shiga harkarka ba duk yanayin da ka shiga nakan gane na farinciki ne ko akasinsa. Dawowa yayi yasa mata kuka kamar karamin yaro. Kai bakace Hamza bane dan shekara talatin da takwas mijin Izzatu da Zuhra. Akan kujera ta zauna tana rike da hannunsa ya zauna a gabanta. Kansa ta dora akan cinyarta yayi kukansa mai isarsa. Rabonsa da yi mata irin kukan nan tun ranar da zai tafi Canada. Duk ranar da yayi irinsa to ba karamar damuwa yake ciki ba. Babu wanda yasan yana yi sai ita mahaifiyarsa. Cike da tausayawa irin ta uwa ta rinka shafa kansa har yayi shiru. Ko da ya dago kansa murmushi ne a fuskarsa yace Hajiya na dade banyi miki kuka ba ko. Yau ma sha'awarsa nayi shine na taso daga office. Bari na koma ana jirana meeting karfe biyu da rabi. Lokacin biyu saura kwata. Tunaninsa bai wuce yadda ya mori kudinsa ba lokacin da yake dasu shi kadai. Sai da matsala ta tashi zaizo ya tayarwa da mahaifiyarsa rai. Ya santa bata da magana sosai, ba lallai ko Alhaji ta fadawa amma zata shiga damuwa. Hajiya tace tunda baka son fada min damuwarka zan tayaka addua kamar kullum. Allah Ya kawo sauki cikin dukkan al'amuranka. Ka yawaita ambaton Allah hakan yana yaye damuwa da bacin rai, sannan kayi kokarin sauke hakkin wadanda ke kanka Allah Yayi maka albarka. Wani hawayen ne ya sauko masa yayi saurin gogewa. Amin Hajiya nagode. Tana kallo ya fita ta shiga toilet tayi alwala. Tasan da kansa zaizo ya fada mata matsalar amma abinda yafi dacewa yanzu tayi zata masa. Addua ta dukufa yi masa sannan ta saka dukkan kannensa da iyalansu. Waya yayiwa Inuwa meeting sai gobe baya jindadin jikinsa. Tunani ne fal a zuciyarsa. Sai yanzu yake tunawa cewa Allah SWT Ya na jarabtar bayinsa ta hanyoyi da dama. A irin rayuwar sakaci da addini da yayi ai dole watarana ya fuskanci irin wannan. Sai yanzu ya sake nadamar abubuwan da yayi a baya da wanda yake kanyi yanzu wato sake da hakkokin matarsa don a zahiri suna damunsa. Sonta kawai baya yi. Zaiyi kokarin kyautata alakarsa da Mahaliccinsa da sauran mutane. Itama Zuhra zaiyi kokari ya sake da ita zuwa lokacin da zai saketa. Tunda basa son juna rabuwar ce zata fi. ta yadda bazai cigaba da daukan hakkinta ba. Zai bari sai komai ya lafa masa a wurin aiki sai ya sanar da Alhaji zai saketa saboda gudun kada Allah Ya kamashi. A lokaci daya duk sai ya zama abin tausayi. [9/25, 3:54 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #39 Batul Mamman(Mrs)# Karo na biyar kenan da Zuhra ke dandana ruwan miyarta. Yawunta duk ya tsinke saboda yadda kamshin daddawa ke tashi. Nana na biye da ita a kitchen din har ta gama. Tuwon shinkafa tayi malmala biyar yadda zai isheta taci da rana, da daddare sannan ta sami na dumame da safe. Plate ta dauko mai dan fadi da zurfi ta saka malmalar da tafi kowacce girma da miyar kukarta duk a hade. Manshanu kadan ta zuba ta goya Nana a bayanta ba zani ta dauki plate din da hannu biyu ta tafi falo. Tana tafiya tana cewa Nana rike wuyana sosai fa. Ita kuwa Nana sai murna take tace toh. Sai da ta shimfida tabarma kusa ta dinning table sannan ta zauna cin tuwo. Loma take kaiwa kamar za'a kwace. Tana ci tana bawa Nana a baki. Sun kusa cin rabi Izzatu ta sauko...idanunta kan Zuhra tana bawa yarta tuwo a baki. Har da nan gudunta tayi saurin zuwa inda suke ta dauke Nana tana ta warin kuka da daddawa. Zuhra ya zaki bata abincinki ke da aka ce ki dafa naki ke kadai? Ni ban saba bata abinci da hannu ba kuma bama tuwo sosai saboda yayi mata nauyi. Bata nuna jin haushi ba tace kiyi hakuri ban sani ba. Ganin Izzatu tayi hanyar kitchen yasa Nana ihu tana cewa Mummy sauketa, sauketa abinci. Izzatu tace naji yunwa kike ji bari na wanke miki baki na zuba miki couscous. Bata ankara ba Nana ta galla mata cizo a kafada. Ba shiri ta sauketa tana sosa wurin. Ita kuwa da gudu ta koma gaban kwanon Zuhra. Hannu biyu tasa tana ci bata jira Zuhra ta bata ba. Sake komawa Izzatu tayi zata dauketa sai taji muryar Hamza yana sallama. Yana shigowa Zuhra ta kai wata shirgegiyar loma bakinta. Ido suka hada ai kuwa ta kware saboda kunya. Ji yayi nauyin zuciyarsa ya ragu saboda yadda yaga tana cin tuwon cike da nishadi. Izzatu tace sweety kaga rigimar Nana wai sai taci abincin Zuhra. To ki kyaleta mana ya fada tare da wucewa sama. Ita kanta Zuhra tayi mamakin amsarsa. Bayansa Izzatu tabi tana masa sannu da zuwa. Zuhra ji tayi jikinta yayi sanyi saboda yanayin da taga Hamza. Da gani yana cikin damuwa Allah Yasa ba wani laifin tayi masa ba. Plate din tuwo kuwa sai da suka sude shi tas ita da yarta Nana sannan aka tashi aka wanke hannu. Bayan yayi wanka Izzatu ke tambayarsa ya aiki. A hankali yake magana yace Alhamdulillah. Tana zaune akan kujera tana masa kallon tuhuma tace Hamza ko ka fara sonta ne? Bangane ba shima a zaunen yake don baya jin zai iya cin abinci. Banda damuwar da yake ciki hannun Zuhra yake hangowa miya na binsa ta gefe tana kai lomar tuwo. Yarinyar ta fiye kazanta. Izzatu ta dan sha kunu Zuhra nake nufi. Lokacin da ka shigo ita ka fara kallo kuma ka danyi murmushi. Izzatu kenan,yanzu baki bani komai nasa a baki ba kike tuhumata. To idan naso ta laifi ne? Matata ce fa. Sosai ta daure fuska bana so, Hamza bana son irin wannan wasan. Nan da wata shida zata koma gidan iyayenta mu cigaba da zamanmu yadda muka saba. Daga nan sai kuma ta soma murmushi baka ga yadda take cin abinci ba dazu. Baka ce dan bakin nan tana zai dauki abinda take tura masa ba. Idan ka fita yau pizza zaka siyo mana Baby a matsayin dinner. Ko sau daya bata damu da rashin walwalarsa ba. Hmmm kina bani mamaki Izzy...me kuma nayi Babyna? Murmushi take masa tana kashe ido. Fada mata ma bata lokaci ne don karshenta ta fadi abinda zai kara bata masa rai. Babu komai bari na dan kwanta kaina na ciwo. Tashi tayi to bari na kawo maka magani. Amma kafin nan ga wannan....ta dauko cards har kala hudu na biki. Ni duk matsalar Zuhra yasa na manta next week za'a fara bikin Mardiya cousin dina ta kaduna. Yar Uncle Jibril kanin Dad dinmu. Wai matar da miji ya fadawa yana ciwon kai kenan. Ga naka na daurin aure, ni a son raina ranar saturday na tafi kadunan saboda muna da shirye shirye a gabanmu. Kasan dani suka dogara tunda na zauna a Canada suna son ayi abin da tsari sosai. Kije Allah Ya kiyaye hanya ya fada a takaice....bargo yaja ya rufa har kansa. Bashi da kwarin yi mata fada ko fada mata abinda ya kamata. Sai da ta gama yi masa lissafin kudin da take bukata sannan ta dauko masa magani da ruwa. Sai la'asar ya tashi jikinsa ya danyi kwari sannan kan ya dena ciwo. Masallacin kusa da gidansa yaje yayi sallah ya dawo yaci abinci. Yana gama cin abincin ya dauki key din mota....Izzy ni zan fita ki fadawa yarinyar nan kada tayi abincin dare zan taho muku da pizza din in sha Allah. Duk maganar a sanyaye yake yinta, wani salihanci yake ji tunda Oscar ya dibga masa sata. Tace harda Zuhra kuma? Ba kayi mata siyayyar kayan abinci ba. Yace nasan nayi amma as long as tana gidan nan zanyi kokarin sauke nauyinta. Tabe baki Izzatu tayi to shikenan sai ka dawo. Har bakin mota ta rakashi ya tafi gidansu. Nan ya zauna suka sha hira da kannensa kamar bashi ba. Hajiya taji dadin ganin ya sake ba kamar dazu ba. [9/25, 3:54 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #40 Batul Mamman(Mrs)# Takwas da rabi a gida tayi masa ya shigo da ledar pizza har hudu manya. Ya riga ya kudurce a ransa daga yau siyayyar abincin alhamis ta kare sai lokaci lokaci kuma. Itama Izzatu zai bata kudi taje bikin ta dawo sannan ya sanar da ita halin da yake ciki tunda bata tambaya da kanta ba. Ita da yara suna ta murna da ya dawo ta karba ta rarraba. Yanka biyu ta sakawa Zuhra a plate Hamza yace ta kara mata daya saboda big size ce. Tala ta kirawo ta kaiwa Zuhra daki saboda tun bayan magriba bata sauko ba. Tala ta fito daga kitchen hannunta duk kumfa tana gogewa da tsumma. Hamza ya mika hannu bari na kai mata saman zani. Plate din ta mika masa tana tambayarsa a ina zai ci tasa yace ta kai masa falonsa yau baya son hayaniya. Zuhra na kwance akan doguwar kujerarta tana kallon wani film din Hausa na marigayi Rabilu Musa dan ibro tana ta dariya. Tun daga bakin kofar dakin Hamza yake jin dariyarta. Yarinyar nan bata da kamun kai ya fada a ransa. Ji yadda take dariya kamar ba mace ba. Sallama yayi ta tashi da gudu ta dora hijab a jikinta. Plate din kawai ya mika mata zai fita sai yaji tace ina wuni? Tunawa tayi dazu tana cin tuwo bata gaishe shi ba. Jiya kuwa dama basu hadu ba. Da ya juyo ya amsa sai yaga plate din take karewa kallo. Ta dan kalle shi....shi kuma wannan menene? Pizza ce, baki taba ganinta bane? Tace eh, Allah Yasa da dadi dai. Sai da yayi murmushi sannan yace ci ki ji mana. Yanka daya ta dauko gashi da girma ta dan lankwasa shi biyu ta tura a baki ta gutsiri rabi. Sai da Hamza yasa hannu a bakinsa don mamaki....tabdi! Ke bakinki zai iya yagewa idan kina katuwar loma haka. Dan gayun nan na mata ma baki iya ba. Wani irin dandano taji da bata taba ji ba. Abin dai bazata iya kwatantashi ba. Bata san lokacin da ta furzar da na cikin bakinta ba, wanda bai sauka a ko'ina ba sai kafar Hamza. Wayyo Allah, Wayyo Allah, Wayyo Allah shine abinda yake ta nanatawa ya dage kafar tare da kawar da kansa gefe. Idan ya kalli kafarsa yasan dole ne yayi amai. Kamar yayi kuka saboda da takaici. Yana girgiza kai yace ke kuwa me nayi miki zaki tofa min abin baki. A tsorace ta dago kai zata bashi hakuri. Sauran ya gani a gefen bakinta da habarta. Dan danne fushin da yake yi ne ya gagara ya daka mata tsawa....Goge bakinki mana. Da hijab dinta tayi saurin gogewa sannan ta sake cewa kayi hakuri, shi kuwa sake hade fuska yayi yana ta yatsina hanci....kai so disgusting yace yana rike hanci. Irin kallon bangane ba tayi masa sannan tace SO kuma? Ni yaushe kaji nace so? Ba cewa nayi ina sonka ba hakuri nake baka. A wane dalilin zan ce ina sonka? Mamaki ta bashi ya rasa daga ina taji kalmar. Sai daga baya ya tuna yace SO DISGUSTING. Dariya sosai abin ya bashi, yace anya kin taba shiga aji kuwa? Sosai ma kuwa, har SS3 na kai a sakandire. Tana magana ta durkusa zata goge masa na kafar tasa da hannunta. Saurin jan kafar yayi tare da yin tsaki...kazama da hannu kuma zaki goge, ni bani tissue. Eyye me kace? Ya sake maimaimatawa. Dan murmushi tayi na ta gane zancen. Toli fefa kake nufi, wallahi bani da ita. Jin kafarsa yake kamar ya yanke ta yace to dauko min ta toilet dinki da sauri. Ya dan kalli kafar....Oh God I hate this. Gani yayi bata tafi ba ya dan daga murya nace ki dauko ta toilet kin tsaya kina kallona. Baya ta dan sake matsawa na fada maka babu. Iko sai Allah, yanzu ko a toilet babu? To da me kike amfani. Dariya ya bata ji wata irin tambaya.... tace da tawul mana, ni bansan ana goge jiki da toli fefa ba. Jin bata fahimce shi ba ya kara bashi haushi. Ni ba cewa nayi a goge jiki ba. Shiru yayi saboda kunyar abinda zai fada. Da kyar yace kafin kiyi tsarki nake nufi. Kanta ta dan juyar a kunyace tace tsarki da toli fefa kuma kamar wata arniya. Yarinyar nan duka take so...kwafa yayi sannan yace ke a kazantarki idan kin gama abinda kike a toilet hannu kike sawa? Shi kam Izzatu ta cuce shi da tayi sanadin auren nan. Gaskiya ke kazama ce ta karshe ya fada yana toshe hanci. Hanyar toilet dinta yabi zai wanke kafarsa sai wata zuciyar ta hanashi. Karshenta yaga wani kayan kazantar. Da jan kafa ya fita daga dakin ya tafi nasa. Ya shiga toilet ya sakarwa kafar ruwa. Sai da yaga babu komai a kafar sannan yayi wanka ya fito. Ita kuma Zuhra gyara wurin da abin pizzar ya bata tayi ta sauka da sauran a plate. Izzatu ta kaiwa suna cin nasu dasu Khalifa tace bazan iya cin wannan abin ba. Izzatu tayi dariya dama shi ya dage sai ya baki. Tana karba ta bude plate din da ta saka masa nasa ta kara da sauran biyun na Zuhra. Tana kallo Zuhra ta wuce kitchen dinta ta dumama tuwo ta haye sama zata ci. A bakin bene suka hadu yace mhmmm haka kika iya, ki cika kwano da tuwo. Bata amsa ba ta bashi wuri ya sauka. Izzatu ta biyoshi falonsa da nasa abincin. Biyun saman wanda aka yi da naman kaza ya cinye yace ya koshi. Izzatu tace kuma kai na ajiyewa mai beef(naman saniya) din don nasan shi kafi so. Ruwa ya dauka a cup yana sha tace ashe rabonka ne mai chicken din da Zuhra ta dawo dashi wai bata.......kwarewa yayi sosai tun kafin ta gama maganar ya soma kakarin amai. Idanunsa har ja suka yi saboda wahala yace yanzu Izzy ragowar yarinyar nan kika bani. Tace to meye ai bata ci ba, hannu tasa tana shafa masa baya. Sannu kaji my darling shiyasa ba'a son magana idan an cin abinci. [9/25, 3:54 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #41 Batul Mamman(Mrs)# Washegari meeting din gaggawa ya kira da dukkan maaikatansa. A nan yake sanar dasu abinda Mr Oscar yayi. Inuwa sakatare yace shi yayi mamaki da ya ganshi a banki amma tunda manaja yace da yardar Hamza aka saki kudin shiyasa bai tayar da zancen ba. Maaikatan suka tambayi Hamza garin yaya haka ta faru yace matsalace ta taso daga gida a lokacin. Yana kujerar tsakaya a conference room din yadda kowa zai iya ganinshi a katon zagayayyen table dinsu yace kada ku damu in sha Allah bazan bari kwazonku ya tashi a banza ba. Sauran cheques din ya nuna musu Allah Yasa na rarraba da guda daya ne Oscar ya dauka ba karamar matsala zamu shiga ba. In Allah Ya yarda zan san yadda nayi na fito da wata miliyan goman da zamu hada musu. Next zuwan Mr Peter kasar nan zamu hada musu kudinsu. Ayyukan gabanmu kuma kunga manyan projects ne. Ina rokon kuwa dage ayi ingantaccen aiki. Sannan ina neman afuwarku na kasancewata shugaba mai sakaci da aiki. Muryoyi ne suka rinka tashi suna fada masa babu komai. Wani yace yallabai irin haka shine yake sa bawa ya kara jajicewa da imani. Ba karamin dadi yaji ba da yadda suka yi masa uzuri. Bayan sun gama tattaunawa addua suka yi aka rufe taron. Shima sai ya sake samun kwarin gwiwa tare da yiwa kansa alkawarin bazai sake basu kunya ba. Kafin ya koma Izzatu ta gama hada duk kayan da zata bukata na tafiyar. Idan ta tafi sai lahadi ta sama zata dawo. Sannan ta sanar da Zuhra zatayi tafiya. Tala ma ta hada nata kayan dana yara. Suna zaune a falo daga Zuhra sai Izzatu tace idan mun tafi basai kinyi girki da Sweetyna ba. Zai rinka siyan abincinsa, da zaki yarda ma kawai ki tafi gidanku ki kwana biyu kafin na dawo. Zuhra tace a ranta lallai Izzatun nan ma, daga aure sai tafiya gida a kwana? Wannan ai sai mutane su gane lallai auren babu lafiya. Izzatu tace kinyi shiru ko ba kya son zuwa gida. Nasan dole zaki fi jindadi da sakewa a nan to amma....Zuhra taji haushin maganar tace ba haka bane, su Baba zasu yi tunanin ko akwai matsala. Kinga idan akayi sakin laifinsa zasu gani. Izzatu tayi dan tunani eh haka ne fa. To ki zauna amma ko da wasa kada ki shiga harkarsa nasan shima bazai shiga taki ba don ba sonki yake ba. Murmushi Zuhra tayi tana jin yadda Izzatu ke fada mata bakaken maganganu. Dubu dari Hamza ya bawa Izzatu kafin su kwanta. Tayi murna amma fuskarta ta nuna ba haka taso ba. Yana daga kwance yace ya akayi ne? Juya kudin take yi a hannu babu komai, nayi tunanin zaka karamin ne saboda yara. Ga Tala zan tafi da ita don ta kula dasu. Tashi yayi zaune ba shiri, da Tala zaki tafi amma baki fada min ba? Tunaninsa bai wuce zaman da zaiyi da Zuhra shi kadai ba na kwana takwas. Izzatu tace da bakinka kace ko unguwa zani na dade na rinka tafiya da ita. To zan sami karin kudin? No, yace tare da sake kwanciya. Bani dasu. Idan kin dawo akwai maganar da nake so muyi. Ta tashi ta saka kudin a jaka. Indai ba Zuhra ka fara so ba ko meye babu damuwa. Hamza ya girgiza kansa kawai ya kwanta, halin Izzatu sai ita. Wato gara duk abinda zai faru ya faru akan ta zauna da kishiya. Washegari da wuri suka shirya kafin goma duk kayansu suna mota. Suna gama breakfast dreban da yake kai su Khalifa makaranta ya iso. Tare zasu tafi ya dawo a motar haya ya barwa Izzatu motar. Idan sun tashi dawowa ya koma ya dauko su. Har bakin mota Zuhra ta rako su. Hamza ya rungume 'ya'yansa sannan suka wani manne da juna shi da Izzatu ana kiss a gaban mutane. Kunya duk ta ishe Zuhra. Ita kuwa Tala dama ta saba gani. Nan suka tsaya har motar ta fita maigadi ya rufe gate. Ajiyar zuciya Zuhra tayi tana tausayawa kanta yadda zata zauna ita kadai a gidan. Kasancewar Hamza ba tafiya zaiyi ba bai dameta ba tunda ba harkar juna suke shiga ba. Ciki ta koma zata tafi dakinta Hamza ya shigo yace ki shirya bayan azahar zamu fita. A sanyaye ta dan juyo gida zaka mayar dani? Na fada mata zan zauna a nan saboda kada a zargi wani abu a gida. Hamza yace Izzatu tace ki koma gida ne? Wai ita zai nunawa bai sani ba. Tace eh jiya ta fada min. Dan guntun tsaki yayi. Izzy ta fiye rigima itama. Ki shirya zamu je ki gaisa dasu Baba sannan muje gidanmu. Wani tsalle tayi da yasa ya matsa gefe kada ta bige shi. Alhamdulillah ta fada ta haye sama cike da murna. Wani lokacin sai ya ganta kamar mai hankali, idan abin ya motsa kuma ba kanta. Daga murya yayi yace idan na dawo daga masallaci baki shirya ba an fasa. A hankali tace zaka sha mamaki. Ai kuwa yasha mamakin domin yana dawowa daga masallacin ya ganta zaune kwam a falo ta gama shirinta. Tuna masa tayi da ranar da ya fara ganinta har ya kusa bigeta da mota. Duk zafin da ake a gari fuskarta sai kyallin foundation take. Tabi girarta da pink din jagira ta gyarata, da yake kayan jikinta akwai green sosai har mayafin haka ta saka green din eyeshadow. Sai yan labbanta da ta zanawa bakin lining sannan ta saka jan janbaki da ya fito sosai. Abin bai bashi dariya ba ma, wannan wace irin kwalliya ce. Mtswwww Da taji yayi tsaki ga wani kallo da yake binta dashi sai jikinta yayi sanyi. Shi dama bai ma gama shiri ba don jallabiyace a jikinsa. Muje yace da ita yana shirin hawa bene. A tsorace tace ina???? Sama ya nuna mata da hannu. Kawai gani yayi ta durkusa gwiwoyi a kasa idanunta sun ciko da hawaye don Allah kada mu fasa zuwa. Don Allah ka kaini naga Ummana da Babana. Yayi yar dariya au gorin iyaye zaki min? Girgiza kai tayi da sauri a'a Ummanmu da Babanmu nake nufi. Yace to naji tashi muje yana murmushi. Da gaske sama taga zai hau sai ta dan ja baya. Hannunta kawai ya kama ya ja ta suka hau saman tana ta tirjewa. Wani abu yaji ya soki zuciyarsa da ya kama mata hannu. [9/25, 3:55 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #43 Batul Mamman(Mrs)# Har suka isa gidan babu wanda yayi magana a motar. Ficewarsa ma yayi daga motar ya shiga gidan ya barta. Kwafa tayi sannan ta fito da ledarta a hannu. Hanyar da yabi itama ta bi. Sai ta ganshi a bakin kofa yana tsaye...kinji yadda naji dazu da kika fita baki jirani ba. Bude baki tayi....lahhh wai haushi kaji. Sai kuma yaji haushin kansa meye zai biye mata harda ramawa. Gyaran murya yayu shi a dole a bawa. Shige muje ya nuna mata hanya. Dakin Mama suka fara zuwa bata ciki. A hanyarsu ta zuwa dakin Hajiya suka hadu da Adabiyya. Wani ihu ta saki tare da kankame Zuhra. Oyoyo Anti Zuhra....Hamida naji ita ma ta fito daga dakinsu suna ta ihun murna Zuhra na murmushi. Hamza yace lallai yaran nan. Kirikiri kun nuna min bakwa son uwar 'ya'yana. Hamida tace to Yaya ai itama ba sonmu take ba. Tana fada ta shige daki da gudu don tasan muguntar dallin bakin da yake mata. Adabiyya ta gaishe shi sannan taja hannun Zuhra suka tafi kitchen. Hajiya na dora ruwan tuwo suna hira da Mama. Adabiyya na shiga Hajiya tace wato don kada kuyi aiki kunce zakuyi karatun jarabawa sai gashi kun cika mana gida da ihu. Adabiyya tana dariya ta turo Zuhra da ke makale jikin kofa kinga bakuwar da muka yi. Mama ta taso itama tana mata sannu da zuwa. Kasa Zuhra tayi duk ta gaishesu. Ina Yayan naku Mama ta tambayi Adabiyya. Yana wajen dakinku. Fita Mama tayi tace Adabiyya kaita dakinku zata fi sakewa ki kai mata abinci. Idon Zuhra na kan Hajiya tana bare albasa zata hada ruwan miya. Gabanta ta karasa a kunyace tace Hajiya kawo na yanka miki. Itama Hajiyan ta rasa dalilin da yasa taji kunyar Zuhra kamar yanzu Yaya ya fara aure. Barshi kuje daki da Adabiyya idan na gama zanzo mu sake gaisawa. Adabiyya ta gama hada cup da lemo a tray tace zo muje Antinmu. Zuhra ta mika hannu don Allah Hajiya ki kawo na tayaki. Me zaki dafa nayi miki? Na iya girki fa. Hajiya tayi murmushi tana kallon Zuhra. Mayafinta ta cire ta jefa saman kofar kitchen din. Adabiyya tace don Allah kizo muje idan kika sha ruwa sai mu dawo. Ki tayani zama a nan kawai muyi girki. Ta karbi albasar Hajiya kije ki huta. Sosai Hajiya taji dadi sai dai kuma girkin saboda Alhaji da zai dawo daga Kumo yau take yi. Amma yadda Zuhra ta langabe mata kai yasa ta hakura ta fada mata tuwon semovita zata yi da miyar danyar kubewa wadda tuni Hamida ta gurza. Tana fita Adabiyya tace gaskiya ina taya Yaya murna yanzu yayi aure. Zuhra bata ce komai ba sai dariya tace ta bata roba zata yi rude. Sai ga Hamida da littafi a hannu tace ayi hirar da ita. Sunso sa mata hannu tace ita dai su tayata zama. Komai ta nema zasu nuna mata haka tayi tuwonta wanda ya tuku sosai yayi kauri. A leda ta kulle sannan ta bar ruwan miyar wajen awa daya yana dahuwa wutar kasa kasa yadda Umma ke yi. Hamida tace ita kamshi ya dameta a kada miyar yau tuwo zata ci ba indomie ba. Suna ta barkwancinsu har ta gama hada miyar kitchen din yana ta kamshi. Mama da Hamza suna daki suna hira. Da suka gama yace zai fita sai bayan sallar isha zai dawo. Dakin Hajiya taje tace mu leka yarinyar nan ko? Hajiya tace tana kitchen da yan uwanta wai ita zata yi tuwon. Farincikin Mama bazai misaltu ba tace Hajiya kinga ikon Allah ko. Kina ganin Zuhra kinsan yarinya ce mai tarbiya. Hajiyan ma murmushi take, sai wani koda surika kike a gabana ko kunya babu. Bari nawa dan Nura yayi aure kisha mamaki. Haka suka sha hirarsu gwanin sha'awa har suka ji shigowar motar Alhaji. Ana magariba Hamida ta zuba musu tuwon a katon faranti. Suna ci yan matan na zuba mata santi. Ita duk kunyarsu take ji ta kasa sakin jiki taci sosai. Bayan sun gama Mama tace su rakata falon Alhaji ta gaishe shi. Tuna ranar da ta fara zuwa gidan tayi kunya ta kamata ta rufa katon mayafinta ko fuskarta baa gani. Tana durkusawa ta gaisheshi ya fara miko mata rafar kudi dubu goma. Tayi saurin daga kanta yayi mata murmushi wannan tukwicin ciyar da dan tsoho ne. Itama murmushin tayi Hamida tace Alhaji mun tayata fa. Yayi dariya kin tayata hira dai. Daga shi har Hajiya da Mama duk sun mata karba mai kyau suna ta yabon iya girkinta. Wannan kuwa a wurin Ummanta ta koya. Da zasu koma dakinsu Adabiyya ta dauko turaren ta mika masa gashi inji Baba. Allah Sarki mal Bashir harda wata wahala banda 'ya da ya bani. Ina fata babu wata matsala dai tsakaninki da Yaya da Izzatu. Tace babu komai nagode. Ledar kayan da Umma ta bata ta bawa Adabiyya ta kaiwa su Mama. Tasha addua sosai a wurinsu. Da Hamza ya dawo falon Alhaji yaje. Suna hira ya bude food flask din yaga akwai sauran tuwo a ciki. plate din Alhajin ya jawo ya zuba yaci harda karawa. Alhaji yace Kaltume kiyiwa danki magana ya bar min na dumame. Hamza na dariya yace yau tuwon yayi dadi amma ba jagwalgwalon su Adabiyya bane ko. Mama tace me ka mayar min da 'ya'ya ne. Don kasan matarka ce ta dafa kake mana santi. Cak ya tsaya da shan miyar da yake da cokali yana kallon Mama. Hajiya tace yau kowa yasan sabon hannu yayi mana girki sai yabonta ake yi. To Hamza, ga abinci da dadi ga kyankyamin Zuhra da yake. Amma dole ya yaba mata don ba karya ta iya girki. Da zasu tafi Mama atampa Super Exclusive ta bata mai kyau, Hajiya kuma ta bata dubu biyar. Sai godiya take musu kamar ta ari baki. Su Adabiyya suka yi mata alkawarin zuwa su kwana biyu da weekend don duk cikin satin zasu gama jarabawa. Adabiyya na level two Hamida na level one a jamia. Hamza sai mamakinsu yake basa son zuwa gidansa a iya saninsa. Ba karamin dadi taji ba yadda suka karbeta a gidan. Suna isa gida ya rufe ko'ina yace mata sai da safe. Yana son yaba mata yadda ta kyautatawa iyayensa amma wata zuciyar ta hana shi. Abinda su Hajiya suka bata ta nuna masa yace to Allah Ya saka da alkhairi. Kema an fada min abinda kika kai musu nagode. Taji dadin godiyar tasa ta tafi dakinta zuciyarta fes. Da sassafe ta farka ta gyara wake ta bawa maigadi ya kai mata markade. Haka kawai taji kosai take son yi. Waken ba dayawa ta hada ba tunda nata ne ita kadai amma tayi yadda maigadin zai samu don tana ta tunanin me yaci jiya da rana da kuma dare. Tafi kowa sanin yunwa ba dadi. Kunu ta dama da tsamiya ta dan saka lemon tsami sannan ta soya musu kosan. A dan karamin jug din roba ta zubawa maigadi nasa kunun sannan ta sami wata robar ta zuba masa kosai da yaji. Nata kuma ta kwashe daga mai ra barshi ya tsane kafin ta kaiwa maigadin. Tana juyowa taga Hamza har sai da taji tsoro. Ya gama shirinsa zai tafi wurin aiki. Gaisheshi tayi tace zan mikawa maigadi abinci. Hanya ya bata ta wuce ya tsaya yana kallon kosan. Yana jin yunwa amma bazai ce tayi abinci dashi ba duk da jiya yaci kuma ya yaba. Kamar ya fita daga kitchen din sai ya dawo bari yaci yaji ko ta iya kosan. Izzatu bata yi tace abincin talakawa ne. Daya ya jefa a baki yaji dadi harda dan kurbar kununta dake cikin kofi. Gaskiya da dadi, a hankali ya dawo ya dan leka falon yaga bata taho ba. Da sauri yazo ya dauki wani harda saka yajin da ke wata yar roba ya kuma sawa a baki duk da akwai zafi sannan ya dauki biyu a hannu. Ko taunawa bai fara ba Zuhra ta dawo tayi mamakin ganinsa a kitchen din tace ashe baka tafi ba. A ransa yace me zaisa ta dawo yanzu. Gimtse baki yayi yace uhmm. Kallon rashin yarda tayi masa ko akwai abinda kake so? Uhmm uhmm ya amsa bakin nan a rufe. Ya rasa yadda zaiyi da kosan bakinsa. Daukar plate tayi ta juye kosan ta dauki kofin kunun tace to adawo lafiya ta fice ta barshi a tsaye. Sai a lokacin ya saki numfashi sannan ya sami damar tauna da hadiye kosan bakinsa. Ficewa yayi ya shiga mota ya cinye sauran biyun sannan ya goge hannu ta tissue. A mudubin motar ya kalli kansa....Hamza kaji jiki, satar kosai a cikin gidanka. Murmushi yayi ya ja motarsa. [9/25, 3:55 PM] #+234 803 040 6305#: AL'ADUN WASU #42 Batul Mamman(Mrs)# Iyakar karfinta tasa tana neman kwace hannunta amma rikon da yayi mata ba na wasa bane. A haka ya jata suka je dakinsa ya dauko kwalin tissue sannan suka koma nata dakin. Iyakar tsurewa Zuhra ta gama don bata san abinda zaiyi mata ba sai magiya take yayi hakuri. Yana jinta ya share, sai da suka zo gaban dressing mirror dinta ya jawo stool din ya zaunar da ita. Numfashinta har wani sama sama yake don fargaba. Har tausayi ta bashi sai ya dan sassauta murya tare da daidaita fuskarsa da tata har suna jin numfashin juna...ke, rufe idonki. Ji tayi kamar zuciyarta zata ballo kirjinta ta fito, ba dai hada bakin da ya gama da Izzatu zaiyi da ita ba. Ita ko a litattafan hausa idan tana karantawa ta tsani ace anyi kiss. Turawa dai marasa kunya suyi abinsu amma ita duk yar kazantarta kyankyamin haden bakin nan take yi. Kokarin tashi tayi ya rike kafadunta ya sake zaunar da ita. Kawai sai ta saka masa kuka...don Allah kada kaci amanar matarka. Kamar yau ne zata dawo kuyi abinku. Tissue yake zarowa daga kwali yace me zamuyi? Kanta a kasa tace sumba mana. Bai san lokacin da ya soma dariya ba. Kece sumbar ai....ya nuna bakinta Allah Ya kiyaye nayi kissing wannan dan bakin. Ina miki kallon saliha ashe kema idonki ya bude kinsan kiss. Hannuwanta tasa ta rufe fuskarta don kunya yasa hannu ya sauke su. Rufe ido nace. Ba musu ta rufe...tissue ya ninke ya soma goge mata girarta. Yana yi yana kallon yadda ta bata rai harda turo baki. Bai bar abinda yake ba yana yi yana kallonta. Ya gama da girar ya koma saman idanunta da lips dinta. Takaici duk ya isheta kwalliyar rabin awa an goge mata ita. Hannunta ya sake kamawa ya kaita kofar toilet. Jeki kisa sabulu ki wanke fuskarki. A tsiwace tace bayan duk ka goge min kwalliyata. Daga hannu yayi zai dalle mata baki ta tafi da sauri. Ke dawo ki ajiye mayafin kada ya jike. Kamar bata ji me yace ba sai da ya maimaita da dan fada fada. A hankali ta warware shi. Idanunsa a kanta, dole ta rufe jiki da katon mayafi irin wannan matsatsiyar riga. Doguwar riga ce mai kyau duk ta fito da surar Zuhra. Ta wuyan rigar kirjinta ya dan fito. Tana daga hannu ta ajiye ya hango hammatarta......fal gashi. Saurin kawar da kansa yayi. Yaso shagala da kallon jikinta sai gashin da ya gani ya dawo dashi. Gaskiya lamarin Zuhra akwai gyara. A inda ta barshi ta dawo ta same shi yace ta sake zama a kan stool din. Wani lotion mai kamshi yasa kadan a hannunsa saboda zafin gari ya shafa mata a fuska. Daga shi har ita wani yanayi suka shiga yadda yake shafa mata fuskar. Bayan ya gama ya dauko hoda ya shafa mata. Sai ya duba lip gloss light brown ya sa mata a baki. Har abin taje gira yasa ya kwantar mata da gashin girar sosai. Ita kanta sai taga tafi dazu kyau duk da tana son saka janbaki da eyeshadow. Kallonsa take yadda ya iya sarrafa kayan kwalliyar mata. Da ya gama mikewa yayi yana dan sosa bayansa da ya kage saboda ya jima a duke. Hararta yayi saura kice min dan daudu, kuma ko kice kinyi kyau bare kuma godiya. Murmushi tayi tace nagode. Shareta yayi ganin ta fara dariyar shakiyanci bari naje na shirya ki canja kayan nan kafin na fito ki saka mai zani. Wata atampa mai adon pink da fari ta saka wrapper skirt da riga. Duk Hajara ke kai musu dinki kuma sunyi sa'ar tela. Pink din mayafi ta saka da farin takalmi da yar jaka fara mai kyau. Sake kallon kanta tayi a mudubi tayi murmushi. Mutumin min nan yana da kirki idan yaso. Amma banda wayon ya tabani meye zai goge min fuska da kansa. Tana zancen zuci taji wani kamshin turare mai dadi. Hamza ne sanye da yadi ruwan madara mara nauyi. Ya gyara fuskarsa ya rage gemu da gashin baki. Sai ya kara haske da yi mata kyau. Shima kallonta yayi ta canja kayan yace better...Zuhra tace best. Ta dan daga gira...nima fa na iya turancin nan. Good, better, best waye bai iya ba. Dariya ta bashi ita kuwa ko a jikinta tabi bayansa suka fita. Da kansa ya bude mata gaban motar ta zauna ya rufe. Yana tayar da motar ya kunna AC, ko minti biyar basu yi da fara tafiya ba ta soma gyangyadi. Dan bugun kujerarta yayi, kinji sanyin AC ko, to idan kika yi min bacci jefar dake zanyi a titi na huta. Gyara zamanta tayi tace amma dai wasa kake yi ko? Gabansa yake kallo ki yi baccin sai mu gani wasa ne ko gaske. Waje ta koma kallo. Da shirun ya isheta tace Allah Sarki su Nana suna hanya ko. Kaduna babu nisa sosai tun dazu suka isa ya bata amsa. Daga nan motar tayi tsit ko rediyo bai kunna ba. Motar na shiga layinsu Zuhra yara suka fara binsu ana ga Zuhran baban yara. Hannu bibbiyu ta rinka daga musu. Har su Anas da Sani kowa ta gani sai ta daga hannu. Haka kawai Hamza sai abin bai masa dadi ba. Tana dagawa Munkaila mai shagon kusa da gidansu hannu Hamza yace kika kara daga hannu sai na dalle miki baki. A islamiyya ba'a koya muku kamun kai bane. Turo baki tayi to kuma sai ka hanani zumunci da mutane. Rai a bace ya juyo sai dai ko motar bata jira ya kashe ba ta fice da gudu. Umma na kwance a falo taji an fado mata a jiki. Tana kokarin tashi Zuhra ta soma kuka. Umma tace to meye haka kuma. zuciyarta cike take da farincikin ganin yarta. Baba da ke daki fitowa yayi da jin muryar Zuhra. Shima makale shi tayi tana kuka. Umma tace wai kukan na meye ne? Hamza ne ya shigo dauke da manyan ledoji guda biyu yace kukan shagwaba take yi Umma. Baba ya tarbe shi, har kasa ya durkusa ya gaishesu tare da ajiye ledojin a gaban Baba. Umma tace kai kuwa baka gajiya da wahala. Duk zuwa sai kayi dawainiya. Dan sunkuyar da kansa yayi albarkarku muke nema Umma. Zuhra mamaki tayi wai dama yana zuwa gidansu. Kawai sai taji ya kara girma a idonta. Zata yi kokarin dena yi masa rashin kunya. Hira sosai suka yi da Baba ita kuma suka shige daki da Umma. Duk dadi ya kama Umma taga kamar Zuhra ta nutsu. Zuhra tace sai bayan hutu zaki dauko Safara'u ne? Umma tace eh ance sun kusa fara jarabawa. Zuhra tace yace daga nan gidansu zamu je. To me zaki kaiwa surukan naki? Sai a lokacin tayi tunani ya kamata ace ta kai wani abu tunda yana yiwa nata iyayen. Umma bata jirata ba ta fita kitchen. Kayan kamshi da kayan kadin da kanwarta ta aiko mata da yawa ta zuba a leda ta bata. Da zasu tafi bayan sunyi sallar laasar Baba ya bata wani turare mai kyau yace ta kaiwa Alh Nasiru. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [9/26, 12:31 AM] #+234 803 244 1205#: AL'ADUN WASU #46 Batul Mamman(Mrs)# Ba shiri ya saketa, yana yarfe hannu. sake bude baki tayi zata yi ihu a hankali yace ke nine....ajiyar zuciya tayi da karfi sannan tace da tsoratani kazo yi kake min sanda a daki? Kaima baka da fitila ne? Dukan da tayi masa ya kulle masa ciki gashi ta dame shi da surutu. Da waya na shigo karama bansan inda kika jefar min da ita ba. Yayi kokarin dukawa ya lalubi wayar yaji zafi a cikin....auchhhh. Zuhra tayi saurin matsawa kusa dashi menene ta tambaya a tsorace. A duhun ya harareta naushi na fa kikayi a ciki ga cizo sai kace wata yar dambe. Duk hanyar mugunta kin sani. A wahale take jin muryarsa na fita ta mika hannu tana sannu taji ta taba cikinsa....kamar wadda aka tsikara tayi saurin janye hannun tana cewa yi hakuri. Shima hakan yaji amma bai so ta dauke hannunta ba. Dakin yayi shiru na dan lokaci...Hamza ya kasa gane dalilin da yasa ko yaya jikinsa ya taba na Zuhra sai abin yayi affecting dinsa sosai. Dan gyaran murya yayi bazaki tayani neman wayar ba? Kamar jira take ta durkusa tana rarrafe tana shafa hannu a kasa. Abu taji ta taba tayi saurin janyowa ashe hannun Hamza ne shima yana duddubawa. Da yake da karfinta taja shi kuma baiyi tunanin hakan zai faru ba sai ya fada kanta. Bakon yanayi duka suka tsinci kansu a ciki. Kunya kamar Zuhra ta nutse a wurin, kamshi ne mai dadi yake fita daga jikin Hamza. Yana fadawa ya gane daurin kirji ne a jikinta...a hankali ya soma yi mata magana. Nifa bana son daurin kirji don Allah ki dena. Wai ita yake hadawa da Allah....saurin dawowa tayi hayyacinta ta fara kokarin ture shi. Yana ji ya sakar mata nauyinsa yana mata dariya.....wai kema kina son jin dumin mijinki shine kika janyoni. To saboda ina tausayinki bazan miki fada ba mu kwana a haka. Wayyo Allah, karshen kunya Zuhra ta gama ji. Har wata in'inar karfi da yaji ta fara. Al'Quran....Al'Quran ba...ba haka bane. Ko kadan bashi da niyar tashi don ya soma jindadin tsokanarta yace to yaya ne? Abinda kika ga munayi da Izzy kike so nayi miki? Wani karfi ne yazowa Zuhra ta dage ta ture shi. Tana ji yana dariya ita kuwa sauran kadan ta soma kuka. Bata dade da matsawa ba yaga wayar ya dauka ya kunna tare da soma haska dakin. Can bakin kofa ya ganta ta takure harda jan bargonta ta rufe jiki. Koda ya matso harda dan hawayenta. Kusa da ita ya koma me kuma nayi miki kike min kuka? Sai da ta dan matsa sannan tace ba kaine kace wai...wai...wai....kwafa tayi ta kasa karasa maganar. Dariya shagwabarta ke bashi, dazu fa aljani kika kirani banyi kuka ba sai kece mai arhar hawaye zaki min kuka daga wasa. Kin kallonsa tayi saboda kunyar ganinsa babu riga. Yace kinga fito daga bargon nan kisa rigar bacci bana son daurin kirji. Tana kumbura baki tace ni a haka zan kwana. Mikewa yayi to ya rage naki...wai ma kinyu wanka kuwa kafin ki kwanta. Tsami nake ji a dakin nan....dama zuciya na kusa ta fara kuka wallahi bana tsami. Yace to kinyi wankan..tsakaninki da Allah. Rufa tayi har ka sannan tace banyi ba. Rufe bakinta ke da wuya ya janye bargon gaba daya tana kuka ko kulata baiyi ba. Lokaci daya ya yankewa kansa shawarar abinda zaiyi ya taimaka mata kafin su rabu. Kan gadonta ya jefa bargon sannan ya shiga toilet dinta. Babu komai sai sabulun wanka da omon wanki da wanke toilet. Ficewa yayi ya barta a duhun baiyi magana ba. Ga tsoro tana ji ita kadai amma bata son binsa. Bayan kamar minti biyar ya dawo da wata fitila mai haske wadda tafi karamar wayar tasa. Shima a babbar bashi da chaji sosai. Wani abu ta gani a hannunsa kamar toothpaste tace ina da makilin fa. Wannan ba makilin bane yar kauye zo nan. Baya ta dan matsa tace yi hakuri. Fitilar ya ajiye a kan dressing mirror dinta sannan ya jawota ya zaunar da ita kamar ranar da yayi mata kwalliya. Duk ta tsargu da daurin kirjinta, shi kuwa ya saka kayan bacci marasa nauyi yanzu. Yana zaunar da ita ya kama hannunta duk da yadda yaji ya daga. Allah Sarki Zuhra sai hawaye...ashe dazu bata ga komai a kunyar da Hamza yake shirin bata ba. Kokarin sauke hannunta tayi ya sha kunu zan matseki idan baki tsaya ba. Kuma kinga mu kadai ne a gidan babu mai taimakonki. To me zaka yi min? Yace sa ido ki gani bana son surutu kuma ki hadiye kukan nan. A hankali take hawaye tana gani ya bude abinda ta zata makilin ne ya zuba a wani abu kamar cokali mai dan fadi ya soma shafa mata a hammata. Ji tayi kamar cakulkuli ta soma dariya....girgiza kai yayi kina da matsala, daga kuka sai dariya. Bata dena dariyar ba har ya gama yace ta bar hannunta a bude. Dayan hannun ya daga ya shafa a nan ma. Wurin minti biyu yana dube dubi a dakin har yaga inda ta ajiye turaruka da body spray din lefenta. Tace wai a haka zan zauna ne? Sai da ya dauko wurin kala biyar sannan ya dawo ya dauki yar robar da tisssue a hannunsa ya kwashe duka gashin. Zuhra ta wage baki ....lahhhh kaga gashin ya cire. Hamza murmushi kawai yayi..yar kauye bata san shaving cream ba. Fes ya share mata sannan ya mika mata shaving stick har uku. Shiga toilet kiyi shaving sannan kiyi wanka ina jiranki a nan. Ya Salam yau Hamza so yake ta tona rami ta boye kanta don kunya. Kasa shiru tayi tace can kasa wai yau kunya kake son sani ji? Bata san yaji ba yace yes idan baki wuce ba zanzo nayi miki da kaina. Fitilar ta dauka da sauri ta shige harda murda key. Murmushi Hamza yayi ya dan matsa kofar toilet din...kada ki fito sai kinyi wanka sau uku. Ki tabbatar jikinki ya fita sosai don zan duba. Idan baki fita ba na iya yiwa kazamai irinki wanka. Kuma kiyi brush sosai. QTo an hada Zuhra da aiki, sai da tayi amfani da duka shaving sticks din wurin gyara jikinta sannan ta shiga dirzar jiki. Allah Ya kiyaye ta bari yayi mata wanka. Sau biyar ma tayi harda goge kafa da abin kaushi duk da kafar tata bata da matsala. Brush da toothpaste kuwa sun san Hamza na dakin don sun sha aiki. Katon tawul tasa ta goge jikinta sai taji wani dadi da iska na shigarta. A hankali tace na gama. Yana kwance akan gadon nata yace to fito mana. Lallai ma a hakan? Rigar bacci yake duba mata amma sai yace to meye ya rage da zaki boye min. Shiru yaji bata fito ba ya dan kwankwasa, bude ga riga ki saka. Dan kadan ta bude kofar ta zura hannu. Wata rigar bacci ce mai kyau amma cotton mara nauyi ta wuce gwiwarta ma da karamin hannu. Yace ki goge jikinki sosai kafin ki saka. Dama ta goge ta saka ta yafa tawul din ta fito. A kan stool din yake zaune yace tunda yau akwai zafi sosai ba sai kin shafa mai ba. Har gabanta ya karasa ya cire mata tawul din sannan ya fesa mata body spray kala uku. Don Allah baki ji dadin jikinki ba yanzu ya tambayeta yana murmushi. Kanta a kasa tace naji...yace good, lesson one duk dare sai kinyi wanka kafin ki kwanta kinji ko. A hankali tace to. Wayarsa ya kunna yace to sai da safe ya fita ya bar mata fitilar. Gado ta haye tayi addu'o'in kwanciya sai dai baccin yaki zuwa. Duk abinda Hamza yayi mata tun shigowarsa ta rinka tunawa tana murmushi...... [9/26, 12:32 AM] #+234 803 244 1205#: AL'ADUN WASU #45 Batul Mamman(Mrs)# Amma yarinyar nan bata da hankali. Rai a bace ya tashi ya zaki min haka? Don me bakiyi shawara dani ba kika fadawa maigadi kamar zamansa kike yi? Ni gidana babu aljanu. Dariya take kasa kasa, daga abin arziki sai kayi min fada. A take ta kwabe fuska tana shirin yin kuka....sau biyu suka ci min abinci. Wannan wace sabuwar rigimar ce kuma ya fada a zuci. Sannan ya dan rage murya ni kada kiyi min kuka. Kamar yace yi kukan kuwa hawaye ya wanke mata fuska. Sai dai bai sani ba hawayen dariyar da takeyi ne ta wayance kamar kuka take. Rannan sunci min kosai a kitchen sannan a gabanka ma suka ci min tuwo. Subhanallah.....da gaske wai ta zata aljanu ne? Muryarsa da kyar take fita yace ke banda jaraba meye na kirga kosai har kika san anci miki. Kuma ya akayi kika san anci tuwonki a gabana? Zuhra na kukan karya tace ka manta da suka ci tuwon har suka saki cokalin a kasa. Kawar da kansa yayi gefe, ni banji ba bana son sharri. Da dankwalinta ta share idanunta tace kosan zai kai goma wanda suka ci. Hamza bai san lokacin da yace kiji tsoron Allah uku ne zuwa hudu kawai. Ai kuwa Zuhra ta kyalkyale da dariya sosai. Duk yadda yaso dakewa fuskarsa sai ta bawa mutum dariya. Har yayi hanyar fita ya fadawa maigadi kada a kira malam mai ruqiya sai kawai ya gano tsokanarsa take yi. Ya rufe bakinsa da hannunsa da ya tuna har adadin kosan da yaci ya fada mata. Yana juyowa suka hada ido Zuhra ta kwasa da gudu tayi sama. Binta yayi wato kin mayar dani abokin wasanki ko. Nine aljani me satar abinci.... bata jira ya iso ba ta shige daki ta rufo kofa. Duk yadda taso ta kasa murda key din ta rufe saboda tsoro gashi yana turo kofar. Karfinsu ma ba daya bane sai kawai ya tura kofar. Hanyar toilet tayi yayi murmushi kina shiga zan rufeki a dakin nan sai kin kwana biyu. Can gefen gado ta tafi babu wurin buya....gabanta na dukan uku uku taga ya biyota. Sai kawai ta zauna a wurin ta boye fuskarta a cikin cinyoyinta. A hankali ya tako yazo gabanta yana murmushi sannan shima ya zauna suna fuskantar juna. Zaman nasu yayi kusa da yawa saboda wurin yayi musu kadan. Da wata irin murya mai dadi yace dago kanki. Sake tura kan tayi cikin cinyoyinta zuciyarta na bugawa da karfi. Bata ankara ba taji yasa hannu biyu ya daga kan nata. Babu inda baya rawa a jikinta don tsoro...shi kuwa wani irin yanayi na daban ya tsinci kansa. Kukan gaske yaga tana yi sai ya soma dariya har sai da tayi mamaki. Yayi ajiyar zuciya, kin iya tsokana amma kina tsoron hukunci ko. Shiru tayi yau babu rashin kunya su kadai a gida. Duk laifinki ne baki taba yimin tayin abinci ba, baki damu da inda mijinki yake samun abinda zaici ba. Kunnenta yaji da kyau kuwa? Miji fa yace. Bata iya kallonsa ba tace kai kace na rinka dafa na iya cikina. Kuma itama kafin ta tafi tace kada nayi girki da kai. Hannunta ya kama suka tashi muje na hukunta ki. Sake yin alamar kuka tayi yace kinga ni na dena yarda da kukan naki na karya. Plates din ya dauka yace babu ruwa ne ko juice. Akwai ta amsa da mamakin me zaiyi. Ki dauko ki hado da wani spoon din. Falonsa ya shige da abincin. Sai a lokacin tayi ajiyar zuciya....wai amma ta tsorata. A tray ta dora jug cike da zobo mai sanyi da cup da kuma spoon din da yace ta dauko. Samunsa tayi a falonsa yana zaune a kasa yana cin abincin. Murmushin da tayi yayi masa kyau yace na dena satar abincin a bayan idonki. Gabansa ya nuna mata zauna muci. Dawa??? Ta kwalalo idanu tana kallonsa. Tashi yayi ya zaunar da ita. Punishment dinki kenan na tsokanata kici abinci tare dani. Idan baki ci ba kuma nayi bakinki zan dalle. Don Allah kayi....hannu ya daga mata. Kada ki bata bakinki ki bani hakuri. Daga yau har Izzy ta dawo zaki rinka yin abinci dani. Tace to amma ni bazanci da kai ba. Harara ya sakar mata. Don ma kin samu Hamza zaici abinci plate daya dake...kuma wallahi bana son kazanta. Idan zakiyi na dare zan zo inspection naga yadda kike girkin don nasan halinki. Ba yadda ta iya dole ta zauna suka ci. Sai dai bata iya sakin jiki ba don da ta diba zaice lomarta tayi girma ko kuma tayi kadan. Haka yayi ta mata har suka gama ta kwashe komai ya wanke. Zobon kuwa bayan ya shanye cewa yayi ta hada masa wani...zobo ma yana cikin abinba Izzy bata masa. Shima na masu karamin karfi ne. Da daddare tuwon semovita yace tayi da duk miyar da ta ga dama. Su Hamza an sami sake Izzy bata nan. Miyar kuka ta kada taji wake da nama. Bai iya boye mata santinsa ba. Sai da ta gyara kitchen din tsaf ta tafi dakinta. Wurin shadaya da rabi tana kallo aka dauke wuta. wayarta tayi saurin janyowa daga jikin chaja sai taga ashe bata yi chajin ba. Chajar bata shiga jikin socket din da kyau ba, ga wayar dama bata rikon chaji yanzu. A take ta fara jin tsoro ga zafi. Da bin bango ta janyo bargo daga gadonta da pillow tayi shimfida a gefen kofa. Bata son duhu ko kadan shiyasa take kwana da fitila a kunne ko ta kunna torch light din wayarta. Hamza na fesa bodyspray ya fito daga wanka aka dauke wuta. Wurin minti biyar baiji maigadi ya tayar da inji ba sai ya sauka. Maigadi yayi yayi injin yaki karbar wuta kuma akwai mai a ciki. Dama irin babban nan ne da yake daukar har AC da fridge. Sunyi iya kokarinsu abu yaci tura Hamza ya kira mutumin dake masa gyara yace ko zaizo da safe. Mutumin yace yana kauyensu yaje karbar kudin auren kanwarsa amma jibi zai dawo. Hakan baiyiwa Hamza dadi ba ya yanke shawarar neman wani washegari domin zafin gari sai ya hana mutum bacci. Dakinsa ya koma sai ya tuna da Zuhra yace bari ya doba ko tayi bacci. Tsoro yasa Zuhra ta dukunkune kanta cikin bargo duk zafin da akeyi. A hankali ya bude kofar dakin gudun kada ya tasheta idan baccin take yi. Dishi dishi take ganin inuwar mutum da yayi hanyar gadonta. A ranta tace shikenan barawo ya fado dakinta. Tashi tayi da sauri zata gudu ko da bin bango ne taje dakin Hamza taji anyi saurin rungumota ta baya. Sandarewa tayi a wurin don tsoro kamar ta saki futsari, gumi ya rinka tsatstsafo mata. Hamza bai ankara ba yaji ta kai masa naushi a ciki ta soma ihu...Wayyo Allah barawo. Duk da zafin cikin bakinta ya samu ya toshe da hannunsa ai kuwa ta gantsara masa cizo iya karfinta. [9/26, 8:58 AM] #+234 815 728 4163#: AL'ADUN WASU #47 Batul Mamman(Mrs)# Zuhra na idar da sallar asuba ta sauka zuwa kitchen. A zafin nan da rashin wuta tana tsoron kada naman cikin fridge din ya lalace. Fito dashi tayi tana wankewa Hamza ya dawo daga masallaci ya sameta. To acici me kike yi a kitchen da asubar fari. Muryarsa taji kamar hancinsa a toshe yake. Amma yau gabadaya kunyarsa take ji da ladabin musamman ta gaisheshi. Sannan tace nama zan tafasa na soya kada ya lalace saboda babu wuta. Ta sunkuyar da kanta, ya jiki naji kamar yau murar tafi ta jiya. Hamza yace eh amma da sauki. Yaji dadin yadda har ta fuskanci bashi da lafiya ta nuna damuwarta. Kallonta yake yadda take aiki ga hijab dan madaidaici a jikinta, hakan bai hanashi tuno surarta da ya gani ba daren jiya duk da duhun dakin. Ji tayi kamar ana kallonta ta dan juya suka hada ido. Murmushi kawai yayi mata ya tafi. Flask ta dauko sabo na tea ta wanke sannan ta tafasa ruwan zafi da lipton, citta da kaninfari. Ta soya kwai guda uku da albasa yar kadan saboda bata sani ba ko Hamza na son kwai da albasa. A karamin plate ta zuba ta rufe shi da wani irinsa sannan ta dora mug na shan tea da teaspoon a tray. Bread daya ta bawa maigadi ya siyo musu jiya gashi bata da dankali ko doya. Duka bread din ta dora masa da kayan tea. Kasa shiga falon nasa tayi tana tunanin ko tayi masa karambani ne. Sai da ta gaji da tsayuwa sannan tayi sallama ta shiga. A kwance ta ganshi kan doguwar kujera ya zurfafa a tunani. Ba komai ke damunsa ba kamar harkar office ga mura tayi masa kamu sosai. Sallamarta ce ta tashe shi ya zauna. Batayi magana ba ta ajiye masa tray din a gabansa sannan ta koma ta dauko flask din. Kallon kayan yakeyi har ta dawo...ta ajiye flask din tana dan sosa kai tace uhmm dama nasa citta da kaninfari a ruwan. Idan baka so sai na tafasa wani. Dago kansa yayi jikinsa duk babu kwari sosai yace me yasa kika dafa da cittar? Naga kana mura ne zai bude maka kirji. To nagode da kulawarki, taimaka ki hada min amma kada kisa sugar. Tausayi ya bata sosai bata yi masa musu ba ta hada masa sannan ta fita ta koma kitchen. Kazar dama daya ce tayi mata saura ta wanketa sosai ta hada da kayan kamshi da jajjagen kayan miya tayi farfesu. Yana kan wuta ta wanke shinkafa ta baza a tray sannan ta shiga yanka su cabbage, albasa, attaruhu, karas da koren wake. Harda grating din tafarnuwa kadan. Duk bayan ta gama ta sake komawa falon ko ya gama cin abincin. Ya gama amma fa bread din da rage bazata iya raba musu ita da maigadi ba saboda dama ba wani babba bane. Duk yadda take jin yunwa da ta kwashe kayan kwai biyu ta soya ta hadawa maigadi tea da bread din. Tace idan ya gama zai kai mata nikan shinkafa. Talle maigadi yanzu duk gidan babu wanda yake ganin girmansa kamar Zuhra yace to Hajiya nagode. Kitchen ta koma ta kashe farfesun sannan ta fara soya sauran naman. Tana yi ta hada tea ta zauna a kan kujera tana sha don bazata iya cin kwai zalla ba. Bayan yaci abinci yasha magani jikinsa yayi dan kwari. Shiru babu motsin Zuhra sai yaji babu dadi. Sama yazo hawa yaji alamun har yanzu tana kitchen. Tea ya hangota tana sha shi kadai. Shiga yayi yana kallonta tea kadai kike sha ba bread? A'a na cinye bread din ne. Yadda tayi magabar yasa bai yarda ba ya duba dustbin dinta ina ledar. A zuciyarta tace kaji mutum da bin kwaf. Shiru tayi ba amsa yace bakya jina ne? Na bawa maigadi....kin me? Dama bashi da yawa kika bani, kuma sauran kika bawa maigadi to ke me zaki ci. Baki da Indomie ne? Murmushi kawai tayi ai yanzu zan dora abincin rana bana jin yunwa ma. Mamakinta yake...yanzu kamar Zuhra tasan ta hakura da abinda take so domin wani. Ji yayi ta sami wani gurbi a zuciyarsa. Hannunta ya kama suka koma falo...meyasa baki fada min ba kika yi shiru zaki kwari kanki. Wasa ta soma yi da yatsunta taki kallonsa..ai naga baka da lafiya kuma zan iya jira. Lallai yau ya koyi darasi a wurin Zuhra...shi bai taba bata kudin siyan wani abu ba yasan da kudinta ta sayi bread din kuma ta bashi. Kallon da yake mata yasa duk ta kasa sakewa . Shi kuwa hannu yasa yana shafa gefen fuskarta har sai da tsigar jikinta ta tashi. Nagode kinji, Allah Ya baki lada, kin nuna damuwa da rashin lafiyata sannan kin iya hakura da abinci don wani yaji dadi. Amma daga yau ki rinka fadamin duk abinda kike bukata, tace to cike da kunya sannan ya saketa ta koma aikinta zuciyarta na bugawa da sauri. Sauran naman ta kwashe ta bawa maigadi nikan shinkafar sannan taje tayi wanka. Har ta dauko foundation sai ta tuna da kwalliyar da ya gyara mata ranar da suka fita. Irin yadda yayi mata haka tayi aka dauki deodorant da body spray aka fesa. Sannan kayanta ma suka sha turare mai kamshi. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #48 Batul Mamman(Mrs)# Hamza na falonsa ya gama waya da assistant director akan wasu ayyuka. Duk yayi musu bayanin yadda yake so ayi aikin da alkawarin idan yaji sauki anjima zai shiga office. Bayan ya gama Izzatu ya kira. Hira kadan suka yi ya gaisa da su Khalifa tace masa tana son wucewa Abuja idan an gama bikin. Dad dinta ne zai tafi Japan shine zata je yi masa sallama sai wata lahadin zata dawo. Ransa a bace yace Izzy ba haka muka yi dake ba. I need you here, bama ni da lafiya. Izzy tace kayi hakuri baby amma Dad zaiyi wata biyu kaga ya kamata naje muyi sallama. Idan yace bai amince bama yasan sai taje ko tasa mamanta ta kira shi a waya. Abin mamakin ma tsakaninsa da Allah rashin dawowar tata bai wani dameshi ba. Shi da baya iya nisa da ita...yace to su Khalifa kinsan zasuyi missing school da yawa ko. Eh zasu taho da Tala ranar lahadin amma da Nana zan tafi Abujan. Bye baby, love you. Dip ta ajiye wayar, rike tasa wayar yayi a hannu yana mamakin Izzatu. Ko sau daya bata yi masa sannu ba duk da muryarsa data canja ko bai fada ba za'a gane bashi da lafiya. Har tunani yake yi wai dama haka take masa ko yanzu ne dai saboda bikin da suke yi. Zuhra na saukowa aka kawo wuta. Tsabar murna yasa tayi ihu har sai da Hamza yaji. Da sauri ya fito yaga abinda ya sameta sai yaga tana ta juyi a falo tana kiran nepa, nepa.... baki ya rike yana kallon ikon Allah, sai kace wata karamar yarinya sai tsalle take yi. Riga da skirt ta saka na yadi mai laushi. Dinkin ya kamata tsam ta daura dankwalinta. Duk da ba wata kwalliya tayi sosai ba amma tayi masa kyau. Gabadaya surar jikinta ta fito sai tuna masa daren jiya take. Sannu da aiki yar kauye ya fada yana tsaye a bakin koma. Da farko tsoro taji har zata gudu sai kuma ta tsaya ta fara neman wuyan hijab dinta ta saka. Jira yayi ta saka din sannan ya karasa gabanta ya kama kasan hijabin. Hannunta tasa tana neman kwacewa ya janyota gabadaya jikinsa. A take ta fara rawar jiki tana cewa kayi hakuri na dena tsallen. Sosai ya rungumeta yana kallon fuskarta ya cire mata hijab din cikin nutsuwa sannan ya saketa. Kirjinta ta fara kokarin rufewa yace ke jiki ba jiki ba kiyi ta wani rufewa. Haushi taji ta dan tura baki sai ta fara juyi a gabansa tace a hakan? Wallahi ina da jiki, kaga fa...dariyar da yake mata yana cewa juya na gani da kyau yan mata yasa ta bar abinda take yi ta soma kokarin kwatar hijab dinta. Hannunsa ya daga sama tace to na bar maka bari na dauko wani. Baifi taku biyu tayi ba ya jawota jikinsa. Hannuwansa na gaban kirjinta ya dan rage tsaho daidai da kunnenta...ki hakura da hijab din kinga akwai zafi. Kuma naga ashe kina da jikin da zan kalla. Yana magana taji yasa hannunsa a kafadarta yana mayar mata da hannuwan breziyarta da suka fito. Daga daren jiya zuwa yau Hamza yasa Zuhra tsananin jin kunya. Yadda ya rufe mata jiki gabadaya ta baya yasa ta kasa motsi. Zuciyarta ce kawai take bugawa da sauri. Tana wannan yanayin har ya saketa bata sani ba. Ganinsa kawai tayi a gabanta yana murmushin da yanzu take yawan gani tare dashi. Hada ido suka yi ta kawar da kanta, a hankali tace duk kasa ni jin kunya. Sai ka rinka wayon taba min jiki. Kuma dai kasan babu kyau. Ya daga gira kina matar tawa. Tace to ba sakina zaka yi ba. Tana fada ta wuce kitchen ta barshi a tsaye. Maganar Zuhra tasa ya shiga damuwa sosai. Dambun shinkafa ta hada mai rai da lafiya. Ta rinka yawo tsakanin falo da kitchen har abincin ya dahu. Daya da yan mintuna ta gama ta mikawa maigadi. Shi kam yana jindadin sauyin da ake samu na girki a gidan nan. Gashi harda ruwan sanyi tunda an kawo wuta. Na Hamza ma ta hada masa komai a tray ta shiga falonsa ta ajiye sai dai baya ciki. Yunwa take ji sosai domin yau tayi dauriya. Nata tayi niyar zuwa ta diba a kitchen sai taga wata kofa ta bude ashe da toilet a wurin. Tashi tayi zata gudu yace dawo ki zauna fita zanyi, da alama alwala yayi. Zan canja kaya naje office zaman gidan ya isheni. Ba komai ke damunsa ba sai maganar Zuhra ta saki. Ya rasa gane yana son zancen sakin nan yanzu ko kuwa. Da 'yar damuwa a fuskarta tace amma baka da lafiya, ka hakura mana. Yana jindadin yadda take kulawa dashi yace bazan dade ba in sha Allah. A gaban tray din ya tsuguna Me kika dafa mana ne...yar kazama ta iya girki. Tray din ta dauka tunda ni kazama ce ka nemi wani a waje. Yi hakuri ki kawo kinji, ai kinfi kowa tsafta a gidan nan. Bubbude flask din yayi yaga dambun shinkafa tayi da farfesun kaza. A take yawunsa ya tsinke. Wai me yake damunka ne Hamza da kaga abincin sai ka rude kamar wani mayunwaci. Kinsan abincin da Hajiya tafi so kenan dambu ko wane iri ne. Zuhra tace da gaske? tare da dauke flask din da ta zuba masa nasa. Bari naje na juye sauran ina ga zai kai cin mutum uku idan aka hada. Tana magana tana neman fita daga falon. Hamza yace ke dawo bangane me kike nufi ba? Ya daga kawo min abinci ko tasting banyi ba kin dauke. Buga kafa tayi irin ya ma zai ki ganewa...yanzu fa kace min Hajiya na son dambu. Zan hada da sauran sai ka kai mata. Bari nayi sauri ko taliya na dafa mana tunda kaima fita zaka yi. Tashi yayi da sauri ya kamo wuyan rigarta ta baya ya dawo da ita...haba yar kauye daga magana sai ki dauke abincin. Ya dan yi mata kalar tausayi, nima ina son ci don Allah ki ajiye. Zuhra ta dan harare shi to Hajiyan fa? Flask din ya soma ja itama tana ja. Da taga yafi karfinta sai tace to bari na zuba maka kadan sai ka kai mata sauran. Kaga duk duniya ga namiji bashi da abinda yakai mahaifiyarsa daraja. Kafin na tafi in sha Allah idan kana so kullum duk abinda take ci ka fada min sai na dafa mata. Ummana tace idan nayi aure na taya mijina neman aljanna ta hanyar kyautatawa iyayensa da sauran ayyukan kirki. Kaga yanzu kafin ka sake ni ko dan yaya sai nayi abinda tace ko? Sai kuma ta rufe baki da hannu daya...ka ganni ko? Umma cewa tayi ba fada maka zanyi ba sai dai ka gani a aikace. Don Allah kada kace na fada. A shagwabe take masa maganar wadda tayi matukar tasiri a ransa. Har wani dan dukan bakinta take yi ita a dole tayi laifi. Allah kadai Yasan farincikin da Hamza yaji a wannan lokacin. Yau shine da matar da take nuna damuwa akan mahaifiyarsa fiye dashi. A wannan lokacin gani yake Zuhra tafi masa kowace mace. Bai yarda sonta yake ba amma a shirye yake ya kyautata mata iya karfinsa...a hankali take samun masauki mai daraja a zuciyarsa. Ido ya zuba mata kawai yana kallonta. Ita kuwa kuwa tana kare maganarta tayi gaba da flask din ba tare da ya tareta ba. A dan plate ta zuba daidai yadda zaici ta hada sauran wuri daya. Takaici ma take bata sani da wuri ba ai da tayu mai yawa. Naman da ta soya ta diba ta zuba a kai saboda farfesun tayi shi da yaji tunda Hamza na mura. Tunda Zuhra ta fita yake ta kai kawo....ya tsani ta tayar da maganar sakin. Shigowarta tasa ya sami wuri ya zauna ta mika masa plate din. Jan hannunta yayi ya zaunar da ita a gabansa. Nasan kin fini jin yunwa ki ci ni ga nawa abincin ya nuna mata farfesun....cikinta har wani kullewa yake ta yi murmushi da gaske ka bar min. Hamza yace eh...plate din ta janyo gabanta ta soma ci da sauri. Ya kama hannunta lesson two yar kauye, ki dena cin abinci da sauri kuma banda katuwar loma. Ta danji kunya sai tace to yaya zanyi? Dan madaidaici ya diba a spoon din ya nuna mata. Tace dama Babana yace kada nayi loma a gabanka...Allah Yasa na iya denawa dai. Amma meye kake cewa lesson one da two? Kallonta yake ya rasa me yake ji game da ita so nake ki zama yar gayu kafin lokacin rabuwarmu, yadda zan dena kiranki yar kauye. Washe baki tayi da gaske don Allah? To ai da ka fada min da wuri yadda zan kiyaye duk abinda ka gyara min. Rabin abincin taci ta ture plate din ni na koshi. Hamza yace don nace ki rage loma? Yamutsa fuska tayi a'a cikina ne ya kulle tea zan sake sha. Sannu yayi mata sannan yaja plate din ya ci sauran tare da shan farfesun. Kamar kullum yau ma abincin Zuhra yayi dadi. A zuciyarta kuwa dadi taji ta bashi dambun saboda tana ganin irin kallon da yake yiwa abincin tunda ta soma ci. Yana gamawa ta hada masa wanda zai kaiwa Hajiya a wata yar jaka ta bashi. Yace to daga can zai biya office. Har ya isa gidansu ko na sakan daya bai dena tunanin Zuhran Baban yara ba. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #49 Batul Mamman(Mrs)# Da yake weekend ne a falo ya tarar da mutan gidan suna kallon wani shiri da akeyi a Sunna TV. Kannensa suka gaishe shi ys amsa da sakin fuska. Sannan ya gaishe da iyayensa. Mama tace Yaya yau ina office din? Zama ya fara yi sannan yace mura ke damuna amma tayi sauki. Yanzu ma can zan wuce, aiko ni aka yi wurin Hajiya. Hajiya tace ni kuma? Jakar hannunsa ya tura mata gabanta gashi inji Zuhra. Hajiya dai kunyar bude jakar tayi Mama tace kaga Yaya miko min nagani. Kowa a falon zuba ido yayi yaga abinda ke jakar sai ga Mama ta fito da food flask mai kyau. Tana budewa dambun shinkafa ne ke kamshi mai dadi. Muryarta a shake kamar tayi kuka tace Adabiyya, Nura, Hamida ku shiga ciki. Ba musu suka tashi suka barsu su uku a falon. Mama ta turawa Hajiya flask. Kinga abinda ke ciki kice wani abu. Murmushi Hajiya tayi nagani Mama amma me zance? Ga mamakinsa duka su biyun hawaye sukeyi. Hankalin Hamza yayi matukar tashi ya fara basu hakuri. Mama tace Yaya ko kasan tunda kayi aure abincin gidanka bai taba shigowa gidan nan ba sai yau. Kasan gidan iyayenka babu yunwa amma a tamu al'adar lokaci zuwa lokaci mace takan yi girki na marmari ko da da sallah ne ta aika gidan surukanta. Irin haka yana sa iyayen miji su so matar musamman idan tana da tarbiyya. Shima mijin indai yasan kimar iyayensa dole matar ta sake samun wuri a zuciyarsa. Hannuwansa ta kama gam ta rike...Yaya yanzu kayi aure, nasan zaka ga kamar muna kin Izzatu amma ko kai shaida ne akan bambancinsu da Zuhra. Kwalla ce ta cika masa ido shima ya basu labarin yadda akayi ya kawo dambun. Hajiya dai kasa rike kukanta tayi ta tashi ta bar falon. Ashe tana da rabon ganin Hamza ya auri macen da zata saka shi a hanya..Allah Yayi mata albarka. Ko ba'a fada ba tasan shima ba karamin dadi yaji ba. Tana tafiya Mama ta share hawayenta. Yaya ka rike Zuhra amana Alhaji bai maka zaben tumun dare ba. Idan ka cutar da 'yar mutane saboda dalilin da ya jawo aurenku Allah zai kamaka da hakkinta. Tana gama magana tace jirani ina zuwa. Kafin ta dawo Hamida tazo tace Yaya gobe bayan laasar zamu zo ni da Adabiyya muyi weekend. Yace to Allah Ya kaimu.....shikenan zasu zo su takura masa idan yana tare da Zuhra. Shima weekend din yake jira yini biyu a gida ba fita. Mama dakinta ta tafi ta dauko dubu sababbin dari dari ta bawa Hamza ya kaiwa Zuhra tukwici. Tunda yake bai taba tunanin irin haka na faranta zuciyar iyaye ba sai yau. A hankali yace God bless the day I met you Fatima. Allah Yayi miki albarka. Ko flask din bai jira ba ya fita ya tafi office. Duk aikin baya masa dadi so yake yaji muryar Zuhra tana masa shirmenta ko shagwaba. Har mamakin kansa yake, ga babban abin kunya bashi da numbar wayarta ma. A lokacin ya tuna wayar tata tana da matsala, bayan sun gama cinikin filayensa da wani dillali ya tashi. Beirut road ya wuce ya siyo wata sabuwar waya kirar Samsung mai kyau. Nasa tukwicin kenan na abinda Zuhra tayi masa yau. Daga nan ya biya wani shago yayi yar siyayya ya tafi gidansa. Yana ajiye mota ko gida bai shiga ba ya fita masallaci saboda a hanya yaji kira. Can ya zauna har aka yi sallar Isha sannan ya dawo ya shigo da kayan da ya siyo. Duhun da ya gani ya tuna masa bai nemi wani maigyaran injin ba gashi har dare yayi. Zuhra ce ta fado masa ita da ko wayar kirki bata da ita. Nemanta ya shiga yi daki daki baiji motsinta ba. Abin ya bashi mamaki ko bacci take yi ne? Yana hawa sama tana fitowa daga dakinsa da fitila a hannu daya, daya hannun kuma tsintsiya ce da abin kwasar shara. Har ajiyar zuciya yayi, ita ta fara magana tace sannu da zuwa. Murmushi yake yauwa yar kauye. Me kike yi da tsintsiya a duhun nan? Tsoro na rinka ji ni kadai sai kawai na fara shara da wankin bandaki. Amma dai ban bata maka rai ba da na shiga dakinka ko? Naga yanzu kana min kirki shine nace bari nima na gyara maka daki. Bai amsa mata ba sai da yazo gabanta...baki yi laifi ba yar kauye, nagode. Ki je kasa akwai kaya a falo ki kai kitchen dinki bari nayi wanka. Bai shiga dakin ba sai da ta saukq kasa. Dadi yaji sosai har da turaren wuta ta saka. Ta gyara gadon tayi shara. Toilet din ma ta wanke shi tas har boxers dinsa da vests da suke cikin wani abin zuba kayan wanki duk ta wanke amma bata shanya ba saboda wurin shanyar yayi mata tsaho. Sau uku take niyar wankewa sai ta fasa wai kada yace bata da kunya. Sai daga baya ne ta daure zuciyarta ta wanke su harda kawar da fitilar gefe ita bata kalla ba bare ace mata 'yar iska..... Ba jimawa ya sauko yace mata tayi girkin dare ne tace a'a amma zata dora yanzu. ki dafa mana indomie kawai akwai a cikin kayan da nazo dasu. Cikin 'yan mintuna ta gama ta kawo. A plates daban ta zuba musu. Maigadi kuwa dama ana magariba ta dafa masa taliya. Hamza na kallonta har ta zauna zata fara ci ya dauko nasa plate din ya dawo gabanta, tasa ya juye a cikin natan sannan ya soma ci batare da yace mata komai ba. Ido ta zuba masa ta kasa ci saboda tana gudun tsokanarsa. Ya dago kai suka hada ido....lesson three, yana da kyau mata da miji suci abinci tare. Yana kara musu shakuwa da son juna. Kyakkyawan murmushi tayi...Allah, to amma ba da kai ya kamata naci ba kada mu shaku gashi zamu rab....hannunsa yasa ya rufe mata baki ta daga ido tana kallonsa. Ki dena zancen rabuwarmu akwai sauran lokaci. Just eat. Babu abinda yaki jini yanzu kamar tayi zancen rabuwarsu, idan lokacin yayi sai asan abinyi amma for now so yake yayi enjoying moments dinsu tare. Sai da Zuhra ta gyara kitchen sannan tace masa sai da safe Allah Ya kara sauki. Lokacin aiki yake da laptop a gabansa. Suma yan nepa kamar sunsan injinsu ya lalace suke kim basu wuta sosai. Wanka ta dauki lokaci tayi don so take duk abinda ya koya mata ta rinka yi. Zafin yau da sauki akan na jiya shiyasa ta dan shafa mai kadan sannan ta shiga barnar bodyspray. Har humrarta da bata taba shafawa ba ta dauko kwalba daya mai kamshi ta rinka bin duk gabobinta tana shafawa. Rigar baccin da ta dauko yar karama mai siririn hannu har tafi ta jiya kankanta da rashin kauri. Wani dadi take ji ashe haka tsafta ke da dadi...gadonta ta haye ta ajiye fitilar a bedside drawer tayi kwanciyarta. Zafi baisa ta rufa ba amma ba bacci ma take ji ba. Tunani take ko me Hamza yake yi yanzu....... Kusan rabin awa kenan da yayi wanka ya gama shirin kwanciya sai dai ko alama babu bacci a idanunsa. Zuhra yake son gani amma yana kokarin hana zuciyarsa sabawa da son kasancewa tare da ita. Sakon kudin da Mama ta bashi ya tuna yana wallet dinsa ga wayar da ya siyo mata duk bai bata ba. Murmushi yayi ya tashi don ya sami dalilin zuwa dakinta. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #51 Batul Mamman(Mrs)# Kiran farko na assalatu Hamza ya bude idonsa. Murmushi ne ya bayyana a kyakykyawar fuskarsa saboda jin har yanzu Zuhra na jikinsa. Hannunta ya zagaye cikinsa, ga kanta a wurin wuyansa. Yana jin lips dinta a wuyan nasa. Sake matseta yayi zuciyarsa na fada masa yayi a hankali kada ya fada soyayyar da zata iya zame masa rigima nan gaba. A hankali ya rinka shafa kanta yana kiranta da sabon sunan da ya rada mata. Cutie ki tashi asuba tayi. Sake makalewa tayi a jikinsa batare da tasan halin da hakan ke sake jefashi ba. Cikin dabara ya fara janye jikinsa sai itama ta bude ido. Ji yayi ta tashi da sauri Ya Hamza ba dai a haka muka kwana ba. Mikewa yayi ni bana son gulma kin gama makale min a jiki kamar babu pillow a kan gadon zaki wani wayance yanzu. Kunyarsa sosai take ji ta koma cikin bargo ta dukunkune kanta. Gudun kada ya makara sallah yasa yayi murmushi kawai ya fita. Sai da taji ya rufe mata kofa ta tashi ta shiga toilet. Har addua tayi bayan ta idar da sallah,kada yayi mata kallon mara kamun kai. Tana idarwa dakinta ta gyara da toilet sannan ta sauka ta share falon tayi mopping. Falon ne da girma shiyasa taga gara tayi aikin da wuri. Tun dare ya fada mata bread kawai zaici da safe da tea, wani maidadi ya siyo a Grand square. Ruwan zafi ta dafa ta juye a flask ta hada da kayan tea ta kai dinning table ta ajiye. Ta sallami maigadi ma sannan ta koma daki ta tsefe kitson kanta ta kama gashin da ribbon. Wanka ta shiga ta bata lokaci a bandaki don yanzu an dena jika jika. Ta zauna gaban mudubi ta shafa mai sannan ta rinka feshe jikinta da turaruka. Ta kula Hamza na son kamshi sosai, yau so take ta burge shi yasan tana daukar karatun da yake mata. Wani dogon wando tight baki ta saka ta hada da riga pink wadda ta kusa gwiwarta mai hannu three quarter. Rigar da dan matseta daga sama sannan ta yi fadi kadan daga kasa. Da Hajara suka je kasuwa aka siyo kayan da kudin sakarta. Hoda tasa da kwalli sai dan janbaki kadan pink wanda tayi lining lips dinta da liner pink amma mai dan duhu. Har wani tsalle tayi da tafi ganin tayi kyau. Ta fesa turare a kayanta sannan ta dauko karamin pink da bakin mayafi ta daura irin yadda dai 'yan gayu suke yi. Kasa ta sauka har lokacin Hamza bai sauko ba gashi har takwas da rabi. Tana son zuwa ta duba ko bacci ya koma bayan ya dawo daga masallaci amma tana jin kunyar kayan jikinta. Wayarta da ta dan sami chaji ta duba taga text din Hajara tana sanar da ita zata zo wurin shabiyu ta kira wayar tun jiya taji a kashe. Wayyo dadi, Zuhra sai murna. Kada Hamza yace wannan karon bata fada masa zata yi bakuwa ba ta yanke shawarar zuwa dakinsa. A darare tayi sallama ta shiga falon sai taji ya amsa daga cikin daki. Kanta tsaye ta shiga ciki ta ganshi daure da tawul yana tsaye a gaban wardrobe dinsa yana neman kayan sawa. Kafin ya juyo ta runtse idonta tana cewa yayi hakuri. Dariya yaso yi sai dai shigarta ta matukar daukan hankalinsa. Ji yake kamar ya dauketa yayi hugging. Zata fita yace tsaya a nan ina zuwa. Kayan ya saka sannan ya taho gabanta da coat a hannunsa da necktie. Kamshin turarensa ya sanar da ita isowarsa. Cikin murya mai jan hankali yace bude idonki Cutie. A hankali ta budesu ta ganshi tsaye da shirt dinsa duk maballan a bude. Yace jiya na fada miki ana taimakawa miji yasa kaya ko? Kai ta gyada kawai tana kallon kasa. To balle min buttons dinnan naga ko kin koyi karatun. Ta dan zaro ido tana kallonsa. Come on Cutie ina da meeting kada na makara. Hannu na rawa ta soma ballewa daga kasa. Shi dariya take bashi ga tsoro ga baki. Har tazo na karshen wuyansa jikinta sai bari yake. Bayan ta balle ya bata tie din saura wannan. A sanyaye tace ban iya daurawa ba. Gwada mata yayi sannan ya ware ya bata ta daura masa. Kallon da yake mata yasa hannunta ya kasa tsayawa sosai. Nasa hannun ya saka ya taimaka mata har suka daura tare. Yau duk ta kasa kallon shi ya dago kanta da hannunsa sai kawai ta rufe ido tace Ya Hamza kunyarka nake ji ka barni na fita. Zagayeta yayi da hannuwansa sannan ya matso da ita gabansa. Cutie kinyi kyau. Ta danyi murmushi da gaske? Yace da wasa. Kafa ta buga a kasa cike da shagwaba tace haba Ya Hamza mana kace nayi kyau don Allah. Hancinta yaja sannan yace kinyi sosai shiyasa na saka miki Cutie. Muje muyi breakfast kada na makara. Dan tsayawa tayi yau ban gaisheka ba, sai ta durkusa ina kwana ya jiki? Tayar da ita yayi tsaye kinga irin wannan gaisuwar bata dacewa da miji da mata. Kinga yadda ake yi ko don gaba. Duka hannuwansa yasa a kafadunta yayi kissing din lips dinta lightly. A take taji wani abu yana yi mata yawo a ciki. Shi kuwa jan hannunta yayi suka sauka don yasan ko rabin minti suka kara a wurin abinda zai mata sai ya fi wannan. Yau cin abinci nasu babu wata hira ake yi domin dukkansu tunani suke. Hamza sai tambayar kansa yake ko dai ya fara son Zuhra ne? Itama Zuhra tambayar da take yiwa kanta shin zata iya rabuwa da Ya Hamza. Suna gamawa ya tashi tace anjima Hajara zata zo kanwar Anti Faiza. Yace nima kinga na manta su Adabiyya zasu zo kwana. To da safen nan kuma naga text din Jidda ita da Mariya da matar Ibrahim kanina zasu zo. Inajin duk da yaransu zasu zo anya zaki iya da baki da yawa haka? Ga mamakinsa murna take yi sosai, zan iya mana in sha Allah. Gara na dora girki da wuri saboda yara ma. A dawo lafiya....bata saurare shi ba shige kitchen tana tunanin abinda zata dafawa bakin nata. A hadith na shabiyar a Arba'una Hadith Manzon Allah SAW yace duk wanda yayi imani da Allah da ranar karshe to ya karrama bakonsa. Kuma tarbiyar Ummanta da Baba kenan. Ita yanzu me zata dafa ta burgesu kuma kowa yaci ya koshi? Hamza ya gaji da tsayuwar mamakin irin wannan murna da Zuhra keyi ya dauki jakarsa ya fita. Izzatu bata taba son 'yan uwansa su zo gidansa ba. Idan sunzo ma zasha ruwa ne da juice su koma gida. Zuhra daban take.... Sai da ya shiga mota ya tuna da sabuwar wayarta ya dawo ya dauko har lokacin tana kitchen. A tsaye ya ganta ta rike haba ita a dole tunani take. Tana ganinsa tace yauwa Ya Hamza dan bani shawarar abinda zan dafa mana. Yace naki din, nida kika tafi kika barni daga cewa zaki yi baki. Ta marairaice masa to yi hakuri kaji Ya Hamzaaaaa. Murmushi yayi Cutie kina abinda kike so. Tayi murmushi tana kallonsa. Shima yayi mata kyau. Zo ga wannan I hope you like it. Da dan murmushi tace ina fa dan gane turanci kalma me tsauri ce dai bana fahimta. Amma dan fassara min abinda kace yanzu turancinka ba irin na malamin English dinmu bane. Fassarawar yayi yana dariya ya mika mata wayar. Gashi nan na saka miki wani sim din sai ki saka na daya wayar tunda mai sim biyu ce. Bade baki kawai tayi tana kallonsa. Sai kuma hawaye Ya Hamza wannan tawa ce? Ya gyda kai, tace Allah Ya saka maka da alkhairi Ya baka ladan faranta min. Allah Ya kareka daga dukkan sharri. Nagode sosai. Wayar dubu ashirin Zuhra kewa kuka da wannan addua, Izzatu kuwa dubu dari ya bata da zata yi tafiya amma kirikiri ta nuna ta raina. Matsowa yayi gabanta ya goge mata hawayen da hannunsa sannan yace nagode da adduarki. Su kuma bakin kiyi musu danwake idan kin iya, a iya sanina dasu Mariya duk mayun danwake ne. Yana gama magana ya fita tabi bayansa. Sai da motarsa ta fita daga cikin gidan ta dena daga masa hannu. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #52 Batul Mamman(Mrs)# Zuhra aiki ya kankama. So take ta gama abincin kafin su iso yadda ba zasu zauna da yunwa ba. Katuwar roba ta samu ta dora danwake sai da tayi tukunya uku tana yi tana juyewa a wata roba mai dan girma. A kalla mutum goma sha biyu zasu ci su koshi sosai. A ranta tace idan bai isa ba sai ta kara. Bata san adadin yaransu ba ga maigadi. Bayan ta gama ta dafa kwai guda goma, ta wanke tumatir, albasa, koren tattasai da cucumber ta ajiye bazata yanka da wuri ba kada yayi tsami. Man da ta soya yasha albasa sannan ta duba bata da juice da yawa. Zobo tayi wanda ta dafa da citta da kaninfari. Ta tace ta saka sugar da lemon tsami sai ruwan cucumber da ta gurza ta tace. A leda ta kulla ta zuba a fridge saboda jug bazai shiga ba. Tana sauke mai ne ya tsallo mata a wuya har wuri biyu. Wani uban tsalle ta doka saboda zafin da taji ta soma karanta ALLAHUMMA AJIRNI MINANNAR saboda neman tsari daga azabar Allah. Allah Ya kiyayemu, amin. Sanda ta gama komai shadaya da rabi ta gyara kitchen sannan taje tayi wanka. Riga da zani ta saka tayi irin kwalliyar dazu mara yawa ta sauko kasa. Sabuwar wayarta ta dauko sai dai ta kasa gane kan wayar. Tana ta tabe-tabenta taji sallamar Hajara. Kamar kananan yara haka suka rungume juna suna tsalle. Can Hajara tace ke dena jijjiga ni kada ki barar da danki ko 'ya. Zuhra ta zaro ido tana shafa cikin Hajara. Doke hannun tayi to yar duniya meye na shafa min ciki. Kema ina tunanin akwai fa, ji yadda kika yi haske kika kara cikowa. Zuhra ta kama hannunta zo ki zauna yau tattalinki zan taya Yaya Sahabi. Ah su Hajara daga aure sai ciki. Hajara tace ke bana son iskancinki fa. Kema naki yana hanya idan babu in sha Allah. Ai burina mu shiga labour room tare. Shakiyanci suka yi ta yiwa juna. Daga baya suka shiga kitchen da Zuhra tace kannen Hamza zasu zo. Hajara ta bude taga danwake...anya Zuhra kina da kai kuwa? Yan uwan miji zasu zo ki rasa abinda zaki basu sai danwake? Zuhra tace yayansu ne yace shi suka fi so. Plates suke hadawa da cups suka ji sallama a falo. Dama Zuhra da hijab dinta a hannu saboda kada suzo da maza. Kuskuren da mata da yawa keyi kenan. Yan uwan miji maza ko abokansa su zo sai mu fito babu lullubi ko hijab. Muji tsoron Allah mu kare mutumcinmu. Mota biyu suka yo duk a gidan nasu suka hadu suka taho tare. Zuhra fuskar nan dauke da fara'a sai kunyar su Mariya take yi. Suka gaisa da Nura yace zai tafi sai bayan sallar Juma'a zai dawo. Bajewa suka yi da 'ya'yansu ana ta hira da Zuhra. Ta sake musu sosai kada ma Adabiyya da Hamida suji labari. Ta tambayi yaran sunayensu suka fada mata. Karamin dan da Ummahani ke goyo kuwa Zuhra ta goya shi saboda ya hana mamansa sakewa. Tun yana kuka har yayi bacci. Da taimakon Hajara dasu Adabiyya ta hado musu abinci. Cikin tabarminta ta shimfida manya biyu. Jidda tace ai ki hada mana a tray kawai muci tare yafi kara zumunci. Zuhra na murmushi tace haka Ya Hamza ma yace. Su Ummahani suka hada ido suna dariya. Yaya yaji dadin aure.... Sakewa da jindadin da basu taba yi ba a gidan dan uwansu yau sunyi. Yabo da addua kam Zuhra tasha a wurinsu. Nura yafi kowa santi da ya dawo aka hada masa nasa abincin. Bayan sun gama kuma dukkansu sunsa hannu wurin gyara falon da wanke wanke. Tamkar 'yan uwana jini haka suke jin Zuhra. Sai da sukayi sallar la'asar suka fara haramar tafiya. Ana haka sai ga Hamza ya dawo daga wurin aiki. Shima yau ya gaji sosai. Kudi ya kusa kammaluwa zai sallami su Mr Peter ya rabo da kaya. Dadi yaji yadda ya tarar da kannensa sun cika gidan ana ta hira. Zuhra na tsakiyarsu da goyo kamar sun shekara tare. Suna ta gaishe shi da yi masa sannu da zuwa ita kuwa kanta na kasa. Duk kunyarsu take ji, tana kallo yace bari nayi wanka na sauko kafin ku tafi. Ummahani ce ta dan zungureta Anti Zuhra tashi mana Yaya ya dawo. Indai don wadannan ne, ta nuna Jidda da Mariya suna dariya...duk ki manta dasu kowacce ta iya rike miji in fada miki. Zuhra harda rufe fuskarta da hannuwanta. Hajara ce ta tasheta ta karfi. Zata hau saman Ummahani tace kawo dan nan kada yace zamu bankare masa kirjin amarya. Ita fa ba saba binsa daki sannu da zuwa tayi ba. A falon ta dan tsaya sannan tayi sallama tare da cewa in shigo. Daga ciki Hamza yace yes come in. Kwance yake akan gado amma kafafun na kasa ko takalmi bai cire ba. A tsorace tayi saurin zuwa gaban gadon, cikin sanyin murya tace...Ya Hamza jikin ne? Harararta yayi sai yanzu kika ga damar zuwa. Zuhra tace ina? Zama yayi suna fuskantar juna tana durkushe a gefen gadon. Yanzu mijinki ya dawo ba sannu da zuwa bare ki karbi jakata. Tace yi hakuri, bai kula ba ya cigaba da cewa kuma na taho daki baki biyoni kin cire min kaya kinyi min wanka ba. Zuhra ta mike da sauri....eyyeeee Ya Hamza wanka? Ya kashe mata ido wanka fa. Don Allah kayi hakuri....sai kawai ta soma hawaye. Saurin tashi yayi ya janyota jikinsa. A cinyarsa ya zaunar da ita tayi saurin rufe ido. Wai meyesa Ya Hamza ke yi mata hakane yanzu. A hankali yake magana Cutie you scared me. Na kiraki yafi sau goma baki dauki wayar ba. Dafe kai tayi... ina jin hayaniya ce tasa banji ba amma kayi hakuri. Kokarin tashi take yi ya sake riketa sosai yana kallon wuyanta. Cutie me ya sameki a nan ya fada yana dan taba wurin...auchh Ya Hamza da zafi fa. Cikin shagwaba take magana tana kara narkewa jikinsa ba tare da ta sani ba. Sorry meye ya sameki? Murmushi tayi masa mai ne ya kona ni da har zanyi kuka saboda zafi sai na tuna ba karamin lada aka rubuta min ba. Na kone a kokarin karrama baki... ta washe baki tana murmushi. Hura wurin ya rinka yi yana mata sannu. Zuhra dai duk tsigar jikinta ke tashi ta dan wayance, 'yan gidanku suna da kirki duk ina sonsu. Zanyi kewarsu idan na tafi. Tashinta yayi shima ya mike...tam, zaki fara ko? Ni tashi muje na sallamesu sai na dawo nayi wankan. Suna saukowa su Mariya suna ta dariya. Hamza yace zan hanaku zuwa gidan nan tunda gulma kuka zo yi. Cikin raha suka yi sallama duk suka tafi. Dubu biyu ya bawa Hajara ta shiga mota. Tayi masa godiya sosai. Suna shiga mota mai gyaran inji yazo ya fara aiki. Zama Zuhra ta sake yi suka kafa sabuwar hira dasu Hamida sai ga Hamza ya leko yana kiranta. Tace bari ta sauko sai suyi shawarar abincin dare. A kofar dakinta ta ganshi ya bude tabi bayansa. A ina su Hamida zasu kwana? Zuhra tace ai tare zamu kwana a nan dakin kayansu na cikin kwaba. Sai da ya gama dariya sannan yace don Allah ki dena cewa kwaba sai a zata baki waye ba, wardrobe sunanta. Ta sha kunu sai kayi ta tsokanata ko? To Cutie kauyancinki ne yayi yawa. Yanzu dai har su Adabiyya su tafi a dakina zamu rinka kwana tare. Kinga kada suyi tunanin akwai matsala a tsakaninmu sannan zamu cigaba da lessons dinmu ko. Yana kare magana ya bude wata drawer inda yaga ta ajiye kayan bacci ya dauko mata wasu riga da wando. Rigar dai kamar bra ta sama sai ta bude kadan taga kasa. Wandon kuwa ko cinya bai gama rufewa ba. Zuhra na gani ta kwace kayan daga hannunsa a kunyace, ni gaskiya bazan saka wannan a gabanka ba. Yace to dauko wadda kike so....ta fara neman wata kenan yace amma ki kwana da shiri duk wadda kika saka ko kinyi bacci sai na cireta. Baki bude ya barta ya shiga toilet ya dauko brush dinta. Sannan ya dibi turaruka da body spray harda man shafawa. Ki karo wasu abubuwan idan kina bukata harda kayan da zaki saka da safe. Fita yayi ya barta a tsaye ta ma rasa abinda zata yi. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #53 Batul Mamman(Mrs)# Tunda suka yi maganar nan Zuhra take bata rai ko dakin nasa bata je ba . Ya ma za'ayi yace tasa wannan kayan duk ya gane mata jiki. Ta fasa kwana a dakin nasa ma a falon zata kwana a kan kujera. Sun gama girki sannan suka yi sallar Isha. Bayan sun idar tana daura dankwali Hamida tace Anti Zuhra meyasa bakya saka relaxer a kanki gashi kanki yana da yawa, irinsa yafi kyau. Adabiyya ta taba gashin don Allah ki fadawa Yaya gobe ya barmu muje salon din bayan layin nan. Baki ga yadda suka yi suna ba kuma duk musulmai ne matan wurin. Hamida tace ni da bikin Zayya munje har lalle suke yi mai kyau. Don Allah Anti Zuhranmu ki tambayar mana. Zuhra tayi murmushi nifa bana son Antin nan haka kawai bayan inajin duk kun girmeni. Nan aka fara fadar shekaru Adabiyya ta girmeta ita kuma ta girmi Hamida. Duk hirarsu Hamza yana tsaye a bakin kofa yana ji ya dawo daga masallaci. Zuhra ta sake tana ta hira amma tun bayan dawowarsa bai sami damar kebewa da ita ba. Abincinsa ma a falonsa na kasa ya gani. Gyaran murya yayi sannan ya shigo...kun hadu kun cika gida da hira ko sallama bakwa ji. Hakuri suka soma bashi Zuhra ta kawar da kai. Hakan baiyi masa dadi ba don ba na kunya bane, da gani fushi take yi. Tunanin dalilin fushin yake yi amma ya kasa ganewa. Kiranta yayi sannan ya shige falonsa. Kanensa na zaune bare ya tambayeta a nan. Da ta shiga falon gani kawai tace ta dan durkusa a gefen kujera. Lallai ya tabo Cutie dole ya bata hakuri. Yi yayi kamar bai gane tana fushi ba yace tashi ki zubo mana abinci yunwa nake ji. Ni naci da su Hamida ta bashi amsa a takaice. Sai ya dan kashingida to shikenan ki barshi na fasa ci nima. Kallonsa tayi da mamaki a fuskarta ba yanzu kace kana jin yunwa ba. Ya kada kai tunda kinci ba tare da kin jirani ba shikenan, am not hungry anymore. Duk sai bata ji dadi ba. A hankali ta dan matsa kusa dashi, Ya Hamza nayi maka laifi ne? Yadda take maganar yasan kuka take shirin yi masa. Yace a'a naga kema kina ta bata rai shiyasa na dena jin yunwar. Sunkuyar da kanta tayi sai hawaye...hankalin Hamza ya tashi ya sauko kasan ya matso kusa da ita. Yanzu Cutie me nayi miki kike kuka....cikin kukan tace ba kaine kace sai na saka wannan kayan ba dazu, kuma da nayi fushi baka rarrasheni ka bani hakuri ba. Tasa hannu ta share hawayenta kuma shine yanzu kake fushi dani don Mala'iku su rubuta min zunubi. Zama yayi yana kallonta har ta gama bayanin sannan ya soma murmushi yi hakuri my cute baby ashe fushin duk laifina ne. Kiyi hakuri dazun ma wasa nake miki. A take ta washe baki kamar ba ita take kuka ba...da gaske ka yarda nasa rigar mutumci? Ya dafe kai wato wadancan ba na mutumci bane. To ki saka duk wanda kike so kinji. Yanzu dai bani abinci sai muyi shirin bacci. Tana tashi yayi ajiyar zuciya Zuhra akwai iya rigima. Ji yadda take masa kuka lokaci daya kuma ta dena kamar ba ita ba. Bayan yaci abinci ta koma suka zauna kallo ita da su Adabiyya. Shiru shiru Hamza na jiranta a dakinsa taki hawowa har shadaya da rabi. Duk sai ya damu so yake kawai ya ganta. Gajiya yayi da jira ya sauko ya tashe su suje su kwanta dare yayi. Zuhra na ganin ya tafi tace akwai TV a dakina muje muga karshen film din. Adabiyya tace wane karshen film kuma ki tafi ki kwanta Anti Zuhra kada kisa Yaya ya kora mu gida da sassafe. Suna shiga dakinta taga Hamida ta shiga wanka Adabiyya ta cire kaya ta daura tawul tana jiranta. A ranta Zuhra tace ashe kowa na wankan dare banda ni. 'Yan sauran kayan bukatarta ta dauka tayi musu sai da safe. Tana sallama falon nasa ta ganshi zaune ga laptop a gabansa ya zurfafa yana aiki, TV kuma a kunne ana news a BBC. Zama tayi a wata kujerar tace masa sannu da aiki. Hannu ya daga alamar amsawa ya cigaba da abinda yake yi. Remote ta dauka ta canja tashar zuwa film din da suke kallo kafin ya tashe su. Wurin minti shabiyar tana zaune, idonsa yana kan aikin gabansa yace Cutie tashi kije kiyi wanka. 'Yar shagwaba ta soma yi masa ka bari a gama don Allah. Dago kai yayi yana kallonta to babu komai bari na gama aikin gabana sai nayi miki. Bata jira ya kare zancen ba ta shige cikin dakinsa harda murda key. Girgiza kai yayi yana dariya. Tunda tare zasu kwana ai bashi da damuwa. Sai da ta gama gyara jikinta tsaf ta tuna bata dauko wasu kayan baccin ba. Wadanda ya dauko ta gani akan gadon ta dauk tasa. Kayan sunyi mata kyau sosai ta saka hula sannan ta dauki hijab dinta mai hannu dogo har kasa ta dora a kai. A haka zata kwana a can gefen gadon idan yaki yarda ta koma falo. Tsoro take kada ya sake rungumarta irin na daren jiya ko ma yayi mata kiss irin yadda yayi da safe. Lips dinta ta dan shafa tana murmushi ashe kiss dinma ba kazanta bane. Ji tayi Ya Hamza ya kara shiga ranta sosai. Tunanin me kike yi haka harda murmushi Hamza ya fada yana rufe kofar dakin da mukulli. Hantar cikinta ce ta kada saboda tsoro murya a sarke tace bari na koma falo na kwana. Dan hararta yayi kina son muyi fada ne? Ta girgiza kai yace to sami wuri ki kwanta ni sallah zanyi. Kafin ya fito daga alwala ta shimfida abin sallah biyu a inda take tunanin nan ne gabas. Kallonta yayi tayi masa murmushi nima nayi alwala ai. Zuhra batasan komai tayi kara shiga ransa take yi ba. Dadi yaji mara misaltuwa da yaga ta tsaya akan abin sallah tana jira ya tayar. Da Izzy ce sai dai ta kwanta yayi ya idar da nafilarsa ko ta bijiro masa da bukatarta a lokacin. Sunyi kusan minti arbain da biyar suna sallah sannan ya idar yayi musu addua. Zuhra na ninke abin sallan tace Ya Hamza karatunka dadi wallahi. Yace nagode kinyi min addua kuwa? Yana kallo da hijab din ta kwanta tace sosai ma. Sai da ya kashe fitila suka kwanta kowa na nasa gefen Zuhra tace Ya Hamza ina son tambayarka amma kada kaji haushi na. Idan na bata maka rai kayi hakuri. In sha Allah raina bazai baci ba yi tambayarki. Sauke numfashi tayi da karfi...na kula tun satin da ya wuce wani lokacin sai ka zauna kayi ta tunani. Har ina tsoron ko duk saboda ni ne sai naga kuma kamar abin yafi karfin matsalar aurena da kayi ba'ason ranka ba. Idan bazaka iya fada min ba ma babu komai zan tayaka addua kullum. Amma kasan wani lokacin idan ka dan fadawa wani matsalarka sai kaji nauyinta ya ragu. Ko jibi idan su Khalifa suka dawo sai ka fadawa mamansu. Tunda ta fara magana yake kallon inda take kwance. Zuhra daban ce shine kawai abinda yake tunani. Har tana lura da damuwarsa duk yadda yake kokarin boyewa. Shiru yayi ya kasa magana saboda yadda ta tsaya masa a rai. A hankali ya fara yarda da cewa bazai iya rabuwa da Zuhra ba. Ji tayi yayi shiru tace Ya Hamza nayi maka laifi ko? Ka yafe min. Babana ne yace ana son mata da miji su rinka yiwa juna addua. Naga ko dai a yaya muka yi aure kai mijina ne yanzu shine nake son yi maka addua. Har yanzu bai yi magana ba sai ma haushin kansa da yake ji saboda yadda ya kuntata mata harda sa ranar saki. Hankalin Zuhra ya tashi da lalube take mika hannu saboda dakin yayi duhu sosai sai sautin AC, Ya Hamza kayi magana mana, Ya Ham....hannunta ne ya kai jikinsa ya janyota ya rungumeta sosai suka kwanta. Kanta akan kirjinsa da yake a bude bai balle maballan ba yaji saukar hawayenta. Saurin dagata yayi duk ta dukunkune jiki da hijab yace Cutie kukan me kike yi? Har da sheshsheka tace ba kaine kayi shiru ba na zata wani abu ne ya sameka. Hijab din jikinta yake kokarin cirewa tana rikewa a raunane yace Cutie kin damu dani ne haka. Da muryar shagwabarta tace kaifa Yayana ne yanzu wanda yake min kirki bana so muyi fada har mu rabu. Ta rike hijab din a jikinta don Allah kada ka cire min kunya nake ji. Kyaleta yayi ya rungumta a haka. A hankali ya bata labarin da babu wanda ya sani sai kalilan a kamfaninsa. Amma bai fada mata duk Izzatu ce take yin sanadiyar faruwarsu ba. Har mamakin kansa yake yadda ya iya budewa Zuhra kazamar yarinyar nan mara kunya cikinsa. Muryarta a kasa saboda labarinsa yasa ta kara yin kuka tace Ya Hamza ka godewa Allah da duk wata jarabawar rayuwa. Kaga ni bana sonka aka yi mana aure amma dana hakura na barwa Allah sai gashi ka zama mai kirki har ina sonka sosai a matsayinka na Yayana. Allah baya dorawa mumini abinda yafi karfinsa. Kuma yarda da qaddara yana karawa mutum imani da kusanci da Allah. Kada ka taba jin tsoron talauci Allah shine mai azurtawa. Zan rinka tayaka addua har Allah Ya kawo karshen komai. Hawaye ne suka cika masa ido ba na komai ba sai na karin imani da maganganun Zuhra suka saka masa. Abu daya ya kudurce a ransa zaiyi iya kokarinsa ya koya mata sonsa domin a halin yanzu baiga wanda ya isa ya rabashi da ita ba sai Allah. Idan abin nan da yake ji soyayya ce da bai taba tunanin zai yiwa wata ba bayan Izzatu to lallai ya amince har ransa yana son Zuhra. Ita kuwa duk da kunyar da take ji saboda yanayin kwanciyarsu ta hakura saboda yadda take jin tausayin Ya Hamza. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [10/2, 9:57 AM] #+234 803 220 0468#: AL'ADUN WASU #54 Batul Mamman(Mrs)# A hankali ta dan bude idonta sai taga haske a cikin dakin. Bude idanun tayi gabadaya ta kalli agogo. Karfe bakwai harda minti tara. Subhanallah ta fada tana kokarin tashi daga kan gadon. Rabin jikin Hamza duk ya danne mata hijab tayi kokarin janyewa ta kasa. Tana son taba shi ta tashe shi amma haka kawai take jin wata irin kunyarsa. Baccinsa yake hankali kwance. Karewa fuskarsa kallo tayi tana ayyana irin kamaninnsa da dukkan kannensa. Duk Alhaji Nasiru suka biyo shiyasa kana ganinsu kaga 'yan gida daya. Sajensa yafi komai daukar hankalinta kuma yana karawa fuskarsa kyau da kwarjini. Ga wani tausayinsa da yake ratsata saboda labarin da ya bata da daddare. Shagala tayi da kallon mijinta tana tunanin yadda zata ji ranar da zasu rabu. Idonsa a rufe yace irin wannan kallo Cutie sai na zata irin son nan kike yi min, in ba ni ba sai rijiya. Saurin tashi tayi zata gudu saboda kunyar da taji ya kamata tana kallonsa hijab dinta ya shake mata wuya. Tashi yayi yana mata sannu. Kinga maganin masu kwana da miji da hijab kenan. Kan Zuhra dai yana kasa ta kasa kallonsa ya tashi ya shige toilet yayi alwala. Bayan ya fito itama tayi suka yi sallar asuba tare da salatul duha tunda gari ya waye. Sai da suka gama azkar sannan yace mata yau kin janyo mun makara sallar asuba. Tashi tayi tana ninke abin sallah, babu ruwana ko yanzu ma ai na rigaka tashi. Gadon ta tafi zata gyara Hamza ya haye ya zauna a tsakiya yace ni bacci bai isheni ba kizo mu kwanta. Zuhra tace kitchen zani kaga muna da baki. Kinga zo kiyi kwanciyarki ya fada yana mika mata hannu. Indai wadannan yaran ne sai su kai shadaya suna bacci. Zuhra tace to maigadi fa. Tashi Hamza yayi ya zagaya ta bayanta, bata ankara ba taji ya dagata cak ya sauketa a taskiyar gadon. Tsoro taji ta kankame shi ya kwanto a jikinta yana kallon yadda ta runtse idanunta. Sonta yake ji yana shigarsa ko ta ina. Idan da wani ne ya fada masa zai so ta bazai taba yarda ba. Kamar mai rada yace Cutie ba'a son yiwa miji musu. Mu danyi bacci kadan sai ki tashi. A jikinsa ya kwantar da ita tasa hannuwanta duk biyu ta rufe fuska. Matsananciyar kunyarsa take ji fiye da ta da. Kanta na kirjinsa ya sake sassauta murya. In cire miki hijab din kisha iska? Maimakon ta bashi amsa kama jikinta tayi kam. Bai sake magana ba sai bayanta da yake shafawa a hankali. Har bacci ya soma daukarsa ita kuwa ta zata shima idonsa biyu tace Ya Hamza akan maganar da mukayi jiya akwai shawarar da nake son baka amma don Allah idan hakan laifi ne kayi hakuri. Ina jinki yace cikin muryar bacci. Ta tashi zaune, kayi hakuri bansan ka soma bacci ba. Bude ido yayi yana kallonta, babu komai ina jinki. Komai nata kishiyar na Izzatu ne. A nutse ta soma magana kamar ba ita ba. "Nasan duk wadanda suka san abinda ke faruwa da kai sun baka shawara kila ma irin wadda zan baka ko wadda tafi ta. Lokacin da tsautsayi ya ritsa da Baba a wurin aikinsu mun sha wahala. Sanda yake da duka hannuwansa munfi wadata da rufin asiri. Da aka yanke hannun yana jinya a gida ga kudin magani da sauran abubuwa na yau da gobe ya kasance an koro ni daga makaranta. Ba don Malam babansu Hajara ba abinci ma sai ya gagare mu wata rana duk da a haka Baba ya fishi rufin asiri. Wata rana Umma tace naje makota na sanar dasu zata fara wainar flawa. Ranar baka ga kukan da nayi ba." Hawayen ta soma Hamza ya sa yatsansa ya share mata. Ta cigaba da magana "bakincikina mun talauce har abin ya kaimu ga sayar da wainar flawa. Ina kuka na sanar da Umma bazani ba, ta soma fada nace so take kawayena suyi min dariya. Sai ta zaunar dani ta dena fada tace min. Zuhra aure ba abin wasa bane. Aljannar mace kuma tana karkashin kafar mijinta. Ma'ana samun aljannarta na tattare da yardar mijinta. Lokacin da babanki yake da lafiya ya wadata mu Alhamdulillah. Yanzu kuma lalura ta same shi 'yan uwa da abokan arziki duk sunyi mana kokari amma dole mu yiwa kanmu. Idan miji ya shiga matsala mace ana so tayi iya kokarinta da yin abinda bai sabawa shari'ah ba wurin kyautata rayuwarsu. Idan har bata da hali kuma sai ta taya shi da addua dare da rana har Allah Ya kawo musu sauki. Kada ki taba daukar maganar masu cewa idan mace ta taimaki mijinta wata rana zai saka mata da tsiya. Dama don Allah kika yi saboda haka ki nemi lada a wurinSa. Tun daga ranar na koyi tattali da adana abu saboda na ragewa Baba kashe kudi. Idan ya siyo min turare ko sabulu na rinka janjaninsa har kazanta ta dan kamani. Amma dai yanzu na dena ko " tayi maganar da murmushi sannan ta dago kanta suka hada ido da Hamza." Kasan me yasa na baka labarin nan?" Yace "sai kin fada". Zuhra ta gyara zama." Ni a shawarar da zan baka Ya Hamza kafin komai ya daidaita ka rage kashe kudi. Misali tunda nazo gidannan tun karfe shida na yamma ake kunna inji har tara na safe. Wani lokacin da rana ma sai an kunna duk yadda abubuwa suke tsada yanzu. Kuma na kula ranar alhamis a waje kake siyo abinci. Gashi yawancin safiya kullum za'a soyawa su Khalifa kwai kowa bibbiyu. Suci rabi su bar rabi ya shiga shara." Ta dan daga hannu " ba cewa nayi a takurasu ba amma a rage irin wannan. A koya musu yau su sami yadda suke so gobe su hakura saboda halin rayuwa. Injin ma a barshi sai kamar tara ko goma na dare a kunna. Da duk abubuwan da kasan basu da mahimmanci sai a barsu." Tunda Zuhra ta fara magana Hamza yake kallonta. Kallo irin na tsabar soyayya da mutuntawa. Yarinya ce Zuhra sosai a kanshi da Izzatu amma duk yadda suke ganin shirmenta ta san abinda take yi. Matsalar gabansa bata dame shi ba kamar yadda yake son gina soyayyarsa a zuciyar amaryarsa. Zuhra duk ta tsargu da kallon da yake mata tace Ya Hamza na shiga abinda bai kamata ba ko? Nasan duk aikin Maman Khalifa ne. Dama kawai nayi ne don nima na sami ladan da mata ke samu a gidan aure. Kaga bansan lokacin da zan sake aure ba idan muka rabu. Tayi masa murmushinta mai kyau...shiyasa nake son samun lada a iya zaman da zamuyi. Kasa magana yayi sai mamakinta kawai. Dan taba shi tayi saboda yadda ya kasa dena kallonta. Ba tare da ya dauke idonsa daga kanta ba ya dorata kan cinyarsa tare da rungumeta sosai a jikinsa. Sannan yace nagode sosai Fatima, Allah Yayi miki albarka. Abinda na fada miki jiya babu wanda ya sani sai ke sai mutane kadan a office dinmu saboda haka ki rike min sirrina. Kuma na baki dama ki fada min duk abinda kika ga ya dace na gyara ni Hamza nayi miki alqawari zan gyara. So yake yace mata yana sonta amma baya son tsorata ta don yasan tana tsoron halin Izzy. A hankali zai bi da ita har sai yasa taji irin yadda yake ji game da ita a tasa zuciyar. Ba jimawa ta fito daga dakin ta sauka kasa. Adabiyya da Hamida ta gani sun share ko'ina sun dafa tea. Abinda za'a ci ne basu sani ba. Kunyarsu ta kamata ta soma 'yan kame kame. Yau makara nayi wallahi. Kuyi hakuri....da yake su Jidda sun kawo mata dankali tace rbari a soya dankali. Hamida tace gaskiya Anti dankali akwai bata lokaci kawai muci indomie. Tace to Adabiyya ta dafa musu harda ita, zata soyawa Ya Hamza shi kadai. [10/2, 9:57 AM] #+234 803 220 0468#: AL'ADUN WASU #55 Batul Mamman(Mrs)# Zuhra na hada kayan wanki a dakinta Hamza ya shigo yace su shirya yaji jiya suna zancen zuwa salon ita da su Adabiyya. Taji dadin hakan sosai dama a dalilin bata son auren taki yarda a saka mata relaxer a kanta wai kada ya rinka hanata zuwa tunda yace kuntata mata zai yi a gidansa. Dubu ashirin ya bata ita da su Hamida kowa yayi abinda yake so. Zuhra ta bude baki, wannan kudin yayi yawa har ka manta zancen da muka yi dazu? Ban manta ba baki nayi ki rike a hannunki koda bukata zata zo miki. Tayi ta masa godiya duk da a ganinta kudin sunyi yawa. Shabiyu saura suka fita tare ya sauke su yace zai je unguwa idan sun kusa gamawa su kira shi. Zuhra tace ai babu nisa sosai muna tafe muna hira ma sai mu koma. Su Adabiyya dake bayan motar yacewa su fita su jirata a ciki. Suna tafe suna waige da yiwa yayan nasu dariya har suka shige. Ya mayar da hankalinsa gareta. Akwai abinda kike so na taho miki dashi ne? Ta girgiza kai Allah Yasa kaje lafiya ka dawo lafiya. Allah Ya bada abinda ake nema. Ya nuna mata jindadinsa da adduarta yace nagode sai na dawo. Da ta fito wata mata ta gani ga baby a hannunta ga jaka da zanin goyo duk kayan sun mata yawa. Da sauri ta karasa ta tare mata jakar da ke shirin faduwa. Matar tayi murmushi kai amma nagode miki. Sai da na zo nan hannun jakar ya tsinke ga Muhsina ta min kuka. Zuhra ta karbi yarinyar matar ta hade bakin jakarta da zanin goyon suka shiga tare. Har su Adabiyya sun kama mata layi da yake weekend ne wurin ya cika. Wuri daya Zuhra da matar suka zauna tana ta yiwa yarinyar wasa ita kuma tana dariya. Matar tace ni sunana Sa'adatu ke fa? Zuhra ta fada mata sunanta tace ina son baby dinnan. Sa'adatu tayi dariya ai naga alama kema tana sonki don kyuya take yiwa mutane amma gashi tana miki dariya. Suna hira matar tace ita har lalle zata yi. Hamida ta taso daga inda Adabiyya ke tayata tsifa Anti don Allah kema kiyi lallen wallahi Yaya yana so. Duk sallah baya fashin bamu kudin lalle ko Adabiyya. Adabiyya tace ce eh. A wani daki ake yin lallen Zuhra tabi bayan Sa'adatu ta shiga. Ai kuwa mutum daya suka tarar ana tsara mata ado sosai. Sa'adatu tace ni dai kada kiga ina ta kallonki wallahi kamar na taba ganinki a wani gida. Zuhra tace kila mun hadu, a wace unguwa ne? Sa'adatu ta soma bata labarin wasu da suka tare a unguwarsu ana walima aka yiwa wata April fool. Wallahi sai kuke dan yimin kama da yarinyar duk da ba kare mata kallo nayi ba. Murmushi Zuhra tayi sannan tace nice yarinyar. Sa'adatu ta bude baki don Allah da gaske? Ana ta rade radin mijin matar ya auri yarinyar. Don Allah ke ce? Zuhra tayi ajiyar zuciya. Nice, har an kusa wata biyu da auren. Sa'adatu tace lallai Zuhra rayuwarki ishara ce ga wawayen mata. Duk yawancin matan unguwar nan da Izzatun nan ta gayyata walimar tarewarsu sai da suka zageta ranar da abin ya faru. Yadda kika san kanwata aka yiwa wulakancin nan, har maigidana na bawa labarin abinda ya faru. Mai lallen ce ta fita karo leda Sa'adatu ta matso kusa da Zuhra. Ko baki fada ba nasan aurenku da mijin Izzatu bazai zama na jindadi kamar na kowa ba duba da irin abinda ya faru da farko. Amma zan baki shawara ki rike mijinki sosai yadda har abada idan Izzatu ko mai hali irin nata tayi niyyar daukan al'adun wasu zata sake tunani. Kinga yau muka fara haduwa amma haka kawai naji ina sonki da alkhairi. Zuhra dai sai murmushi take yi. Auren da yake da lokacin karewa wane rike miji zata yi?... Sa'adatu tace kina son mijin naki? Kanta ta sunkuyar kasa kawai tana murmushi. Ai an gama wannan murmushin naki ya isheni amsa. To kalleni da kyau bari na koya miki karatun saye zuciyar mijin matar da bata san inda ke mata ciwo ba. Ina ma da Ummu Sudais muka zo wurin nan. Don baki ga yadda tafi kowa jin haushi ba ranar. Kada kiga kamar cin fuska amma ko ba'a fada ba wayewarki da ta Izzatu ba daya ba. A irin haka tayi miki wayo har hakan ta faru. Abu na farko da nake so dake shine daga yau mijinki ya ga kin canza masa gabadaya. Canji irin wanda zaisa ko fita yayi yana tunanin Zuhra a gida. Ki rike TSAFTA sosai domin ita ce abu na farko da kowane miji yake nema daga matarsa. Duk kyaunki da iya kwalliya idan baki da tsafta ko jiki na wari miji bazai so kusantarki ba. A hankali kuma zaki fice masa a rai ya fara neman wata. Na biyu ki iya KWALLIYA irin ta zamani amma fa ba mai yawa da za'a kasa ganeki ba saboda tsabar fuska tasha fenti. Na uku SHAGWABA,Zuhra ba sai na bata lokaci ba a nan. Duk mijin da zaki mayar da kanki yarinya a gabansa dole ya soki. TATTALI DA ADANI yana da kyau ga dukkan matar aure. Babu namijin da zai so ya auri matar da take da almubazzaranci. GIRMAMA IYAYE da son 'yan uwan miji shima yana karawa mace daraja a idon mijinta. IYA ABINCI wannan kowa yasan shine jigon dorewar zaman lafiya a gidan aure. KULAWA, maza nason mace ta kula dasu tamkar yara kamar yadda muma muke son hakan. Ki rage kunya domin ba'a son don kinyi aure ki ajiyeta gabadaya, ki nunawa mijinki so da kauna ta sigar da zai manta da yadda ya auroki ya rike ki da zuciya daya. Ke kike aurensa saboda haka kinsan bukatunsa, idan baki sani ba kisa ido sosai ki nemi soyayyar mijinki da gaskiya. Abu na karshe kuma mafi mahimmanci shine ki rike ALLAH SWT DA MANZONSA SAW, idan kika yi haka to in sha Allahu komai zai zo miki da sauki. Mu 'yan unguwar nan duk 'yan bayanki ne wallahi. Abinda duk ya shige miki duhu zan baki numberta sai mu rinka zumunci. Zuhra tsaf ta nade shawarwarin Sa'adatu tayi mata godiya sosai. A ranta ta kudurce in Allah Ya yarda zata yi iya kokarinta taga cewa Hamza bai saketa ba domin tsakani da Allah tasan tana sonsa. Karshe ma sai kafin a fara lallen tace ita gyaran jiki zata fara yi tunda suna yi. Bayan an gama aka yi mata lalle da retouching. Idan kaga Zuhra sai ka zata ba ita bace jiki sai sheki yake don ma na rana daya tayi. Hamza sai waya yake Adabiyya na dauka tace ba'a gama ba har sai da ransa ya baci yace wane irin abu suke yi a wurin. Sai karfe biyar Zuhra ta kira shi lokacin ya dade da komawa gida. Yaso yi mata mita sai dai tana zuwa gaban motar ta daga masa hannuwanta tana dariya.. Ya Hamza lallena yayi kyau? Fasa fadan yayi saboda yayi kyau din. Baki da ja aka yi mata tamkar wata amarya. Hamza na son mace tayi lalle amma Izzatu tace kauyanci ne shiyasa bata sake yi ba tun na aure. Wai ya labarin Izzatu a Kaduna??? [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #56 Batul Mamman(Mrs)# Izzatu na tsaye akan Tala ta gama hada kayan su Khalifa suna ta shiri washegari zasu koma Kano. Tuno babban dalilin da zai kaita Abuja tayi tace kinga Tala ki hada harda kayan Nana ku tafi tare. Ga wannan wayar zan rinka kiranki akai-akai kina sanar dani abinda ke faruwa a gidan. Nasan babyna bazai kula wannan yarinyar ba amma dai ki sa ido kafin na dawo. Ki rinka yi masa girki saboda nasan ya wahala a siyan abinci kwanakin da bana nan. Tala tace to Maman Khalifa. Izzatu tace ba to ba aiki zaki min. Idan kika ga zata shige masa ki hanata ni na baki wannan damar sannan ki kular min da yara bana son suna cin kazantar da take kira abinci. Sosai ta karantawa Tala dukkan abinda take so tayi mata idan ta koma. Daga nan suka shirya aka tafi kai amarya. Sai da suka kaita akayi sallar magariba suka shirya aka tafi dinner wadda ango ya shirya. Ko wanka Zuhra bata yi ba da suka koma gida sai da tayi sauce din hanta wanda yaji albasa da kayan lambu sannan ta dafa farar shinkafa. Harkar girki duk aikin Anti Faiza ne shiyasa take son yi mata siyayya mai kyau idan zata je gidanta. Hamida da Adabiyya sun tayata suka hada komai sannan aka fara layin wanka. Zuhra kayanta ta dauka ta fita ta tafi dakin Hamza. Yana falonsa yana aiki shiyasa ta shiga kai tsaye. Bata dade da shiga toilet din ba ta fito zuciyarta babu dadi. Tasan yau da kyar zata sami bacci tunda abin yazo. Matsanancin ciwon mara yake saka mata. Dama kwana biyu kenan tana jin alama. Dakinta ta koma ta dauko pad sannan ta dawo ta shiga wanka. Lallenta ya kara yin fes dashi. Harda humra ta dauko a dakinta tabi duk jikinta ta shafa musamman cinyoyinta. Sannan ta fesa turaren jiki kala daban daban. Dogon skirt ta saka baki mara fadi don ya kama mata jiki sannan tasa wata jar top itama ta kamata sannan hannunta dan iya kafada kawai ya rufe. Sake fesa turare tayi sannan tabi gashin nan da yasha gyara tayi styling dinsa. Ta taje shi baya ta zubo da wani ya rufe mata rabin fuska. Juyi ta rinka yi gaban madubi tana yiwa kanta dariyar yadda zata je gaban Hamza a haka. Kwalliyarta ta dan gyara wadda tayi alkawarin mayar da hankali ta kara koya sannan ta fito daga dakin. Kamar abin kirki har ta fara saukowa ta koma daki neman mayafi. Ai da kunya taje gaban Ya Hamza a haka. Tana shiga dakin su Adabiyya suka fara yaba kyan da tayi. Karfafa zuciyarta tayi ta bi bayansu suka sauka. Sai da ta dan tsaya a kofar falon tana tunanin da tadda zata shiga a haka. Daga baya dai ta tuna yanzu dama ce ta samu da zata yi kokarin samun soyayyar Hamza idan ba haka ba nan da 'yan watanni sunanta bazawara. Muryarta a can kasa tayi sallama sannan ta shiga ciki. Hamza na zaune a kan wata kujera irin mai juyawar nan a gaban wani table daga karshen falon yana aiki a computer. Bayansa take iya gani shima ba tare da ya juyo ba yace ni yau munyi fada Cutie. Duk sai shareni kike yi tunda muka dawo sai yanzu zaki zo. A hankali take tafiya tana gwada yadda taga mata masu ji da gayu suna tafiya. Ta hadu dasu kala kala a salon yau. Cikin nutsuwa ta karasa kusa da shi kamshinta mai dadi ya sanar masa da isowarta. A daidai bayan kujerar ta tsaya tace Ya Hamza bazaka juyo kaga kwalliyata ba? Murmushi yayi amma yaki juyowa. Ni lessons din da na koya miki bamu zo kan jan aji ba amma har kin koya. To nima nawa zanyi miki bazan juyo ba. Turo baki tayi ta soma shagwaba....Allah sai ka gani. Ji yayi tasa iya karfinta tana kokarin juyo kujerar. Ko da ta juyo dashi da kyar sai taga ya runtse ido. Duk kiyi ki gama bazan kalleki ba yau. Murmushi tayi sannan ta matso da fuskarta kusa da tashi har yana jin numfashinta. Ya Hamza don Allah ka bude idonka ka gani. Irin kwalliyar da zanyi ce idan na sake aure. Bukatarta ta biya domin tana rufe baki ya bude idanunsa suka sauka a kanta. Ya tsani ta rinka zancen idan sun rabu balle kuma idan tana cewa ga abinda zata a gidan sabon mijinta. Mikewa tayi ta soma juya jikinta a gabansa. So da kaunar Zuhra ke kara karfi a zuciyarsa. Kallonta yake kamar ba ita ya aura ba saboda yadda tayi masa kyau. Da ya kula tana jindadin kallon nasa amsa take jira sai ya dan tabe baki....to,kin so kiyi kyau amma dai da saura. Muryarta kamar zata yi kuka tace da saura fa kace? Hamza yayi murmushi eh mana. Da akan wannan 'yar kwalliyar kika zo zaki dameni. Ba karamin mamaki yayi ba da yaga ta soma hawaye da gaske tana buga kafa. Baka ga yadda na dade ina yin kwalliyar nan ba shine zaka ce banyi kyau ba. Hankalinsa ya tashi ganin tana kuka yace wasa fa nake miki. Hannunta ya ja ya zaunar da ita a kan cinyarsa a kujerar yace haba Cutie ke kin fiye rigima. Meye abin kuka don na dan tsokaneki. Zuhra ta wani shige jikinsa duk ta kunyar da take ji...to ni ba yau saboda kai nayi kwalliyar ba amma baka ce nayi kyau ba. Hannu ya kai yana shafa gashinta da yake ta sheki...da gaske ni kika yiwa kwalliya? Me yasa? Fuskarta ta dago tare da ware idanunta hawaye na fita ta gefe amma murmushi take yi. So nake na nuna maka nagode da ka zama yayana kake kulawa dani yanzu. Ya Hamza bazan taba mantawa da kirkinka ba a rayuwata. Allah ne Ya hadamu don ka zama yayana ka canja min rayuwa. Sai kuma ta dan harare shi...amma kaga nan, ta nuna lips dinta. Bazasu manta da yadda suka sha dalli a wurinka ba. Kai Ya Hamza ka iya cin zali ko sannu baka taba yi min ba. Komai Zuhra tayi burgeshi take yi, yayi dariya yanzu yanzu kike yabo na kin koma korafi. Turo lips din ta kara yi.... gasu ka basu hakuri sai na janye korafin. Yace naki, lokacin ba tsiwa kike min ba. Wani hawayen yaga ta soma yace oh Cutie baki san wasa bane..to rufe idonki na baki hakuri. Ba musu Zuhra ta rufe ido tana murmushin jindadi zai bata hakuri. Abinda bata taba tsammani ba yayi mata. Da farko ji tayi kamar ya dan shafasu da dan yatsansa har tsigar jikinta ta tashi sai dai kafin ta gudu ya hade bakinsu wuri daya. Kissing dinta yake sosai ta kasa koda kwakkwaran motsi saboda yanayin da ta tsinci kanta. Hamza bai barta ba sai da suka kusa minti biyar a haka yana bin har wuyanta da duk fuskarta yana kissing. Kiran sallar Magriba ne yasa ya kyaleta ba don yaso ba. Kasa kallonsa tayi harda rufe fuska da hannuwanta. Ya Hamza duk kasa ni jin kunya, ni daga yau ko kallonka bazan iya ba. Murmushi yayi mai nuni da tsantsar jindadi da kaunarsa gareta sannan ya sauke mata hannun da ta rufe fuska. Gira ya daga mata kinga kujerar nan ya kamata ki bata mahimmanci a rayuwarki. Kanta a sunkuye tace meyasa? Idanunsa a kanta yace saboda a kanta Ya Hamza ya fara kissing din Cutie kuma yasan taji dadi. Tsananin kunyar da taji yasa ta tashi da gudu ta bar falon. Dariya yayi shima ya tashi yaje yayi alwala ya tafi masallaci. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU # 57 Batul Mamman(Mrs)# Tare ta hada musu abinci bayan isha ta kai falonsa. Dariya yayi yace har kin gaji da wasan buyan ne? To karaso sai ki bani a baki. Dan harararsa tayi Allah Ya Hamza zan tashi. Haka kawai ina zaman zamana kasa duk minti daya sai nayi tunaninka sai naji kamar na tona kasa na shige. Hannunta Hamza ya kama yana mata wani kallo kasa kasa, Cutie da gaske kina tunani na? Tell me, me kika fi tunawa. Sunkuyar da kanta tayi kasa tana wasa da yatsun hannunta. Yace nifa bana son gulma, yarinya taji dadi kina so kina kaiwa kasuwa. Bari muci abinci ni yunwa nake ji sai mu koma kujerar tamu ko. Naga kamar karatun yayi miki dadi. Karshen kunya dai Zuhra ta gama ji ko kanta ta kasa dagawa. Shi kuwa Hamza yana sane yake ta tsokanarta, dariya ma yake mata. Kasa cin abincin tayi ta tashi zata fita. Yace ina kuma zaki? dawo kinji, na dena tsokanarki. A kunyace tace kayana zan kwashe daga dakinka tunda gobe su Khalifa zasu dawo. Damuwa karara ya gani a fuskarta, yasan ba dawowar su Khalifa kawai take son cewa ba. Har inda take tsaye yaje ya riko hannunta suka dawo suka zauna. Cutie kina tunanin idan Izzy ta dawo zan tashi daga Ya Hamzanki? Daga kan da zata yi kawai sai kuka ya kwace mata. Dama ga ciwon mara da ya fara matsa mata sannan ga shagwaba. Kuka take sosai Hamza yana ta aikin rarrashi. Da kyar ya samu tayi shiru ya dan ja hancinta. Cutie baki da dama, daga magana sai kuka. Tace to irin yadda kake yi min da zaka cigaba idan ta dawo? Hamza yayi murmushi ganin cewa Zuhra ta damu dashi. Kada kisa komai a ranki na damuwa. Idan ta dawo zan raba muku kwana saboda bamu gama lessons dinmu ba, ya fada yana murmushi. Ranar girkinki zaki yi abinci dani kuma zaki kwana a dakina. Ya danyi dariya nasan kwanciya kusa dani ne bakya son denawa shine harda kuka. Yarinya ta soma sabawa da jin dumin maigida a kusa da ita. Ji tayi kamar ta nutse a kasa don kunya kawai sai ta soma salati, ni kada kayi min sharri bayan kaine da ka ganni sai ka rinka wayon taba ni. Yace karewar tabaki yau da kaina zanyi miki wanka. Jin haka yasa ta tashi da gudu ta barshi shi kadai. Wurin su Hamida ta koma suna ta hira suna bata labarin samarinsu Haidar da Yasir. Zuhra tace kuce mun kusa shan biki. Haka suka cigaba da hira cikin nishadi hankalin Zuhra a kwance Izzatu bazata dawo da wuri ba. Saboda yadda take fargabar dawowar Izzatun har mafarki tayi wai ta dawo Hamza ya koma yadda yake da. Mararta ce ta soma murdawa sosai hirar ta soma gagararta. Adabiyya ce ta kula da yadda take rike ciki tace Anti Zuhra tun dazu na kula kamar baki da lafiya. Tace marata ce take ciwo bari naje na kwanta. Bayan ta hau sama Hamida tace ikon Allah naji ance da anyi aure ake dena ciwon nan kinga har yanzu bata dena ba. Adabiyya ta kai mata duka to uwar tsurku. Amma seriously naji wasu sunce idan mace bata dena bayan aure ba tana haihuwar fari take denawa. Wanka Zuhra tayi da ruwa mai zafi sosai sannan ta fito ta shirya cikin kayan bacci riga da dogon wando na cotton. Yanzu dai bata sake da kamshi bare kuma ana period dole duk mace ta kula sosai da kanta. Gado ta hau tana juyi saboda ciwon ya fara yawa. Duk wata a gida haka take fama ranar su Umma basa samun baccin kirki. Har shabiyu saura Hamza na aiki Adabiyya ta leka tace masa sai da safe saboda an dauke wuta. Yace yau anyi abin kai baku jira nazo na tasheku ba. Ina Antin taku? Hamida ce ta bashi amsa, Yaya ta tafi daki tun dazu bata da lafiya. Kashe laptop din yayi ya taso meyasa babu wanda ya fada min a cikinku. Suna soma hawa sama maigadi ya tayar da inji. Hamza ya rufe ko'ina ya wuce dakinsa. A kan gadon ya hangota ta nade wuri guda yayi zaton bacci take yi ya je yayi wanka. Yana cikin saka kaya yaga sai juye juye take tsakanin bangaren hagu da dama tana rike da ciki. Rigar ya fasa sakawa ya zo ya dafa bayanta. Cutie me ya sameki? Baki da lafiya kuma shine baki fada min ba. Cikinta ta nuna masa tana kokarin tashi zaune. Shi kuma ya taimaka mata ta tashi yace murdawa cikin yake yi? Ko toilet zaki je bari na taimaka miki. Baza'a rasa flagyl ko imodium ba a cikin first aid box. Takaici ya kama Zuhra me yake nufi da cewa cikinta ya murda, wato a tunaninsa...... kai amma ya cuceta da zaiyi wannan tunanin. Yana kokarin dagata muje na kaiki toilet ta dage ta doke hannunsa harda zumbura baki tace ni ba ciwon shiga toilet nake yi ba. Hamza yace oh kina fama da ciwo kina tsiwa. To me ya same ki? A hankali tace marata ce take ciwo. Yace sai kice min period pain ne, ko muje asibiti? A'a zuwa safiya zai dena ta amsa da 'yar kunya. Gyara mata kwanciya yayi sannan shima ya kwanta a kusa da ita yana mata sannu. Kusan minti shabiyar ciwon ya lafa daga baya ya dawo sosai. Hamza ya rasa me zaiyi mata taji dadi hawaye take yi kawai abin tausayi. Ko kula da cewa babu riga a jikinsa ma bata yi ba ciwo ya isheta kuma tace ita babu maganin da take sha har ya dena. Ruwa ta bukaci sha ya tafi ya debo mata a dispencer din falonsa. Tana gama sha tace Ya Hamza...yes Cutie me kike so? Tace zaka shafa min bayana. Tausayinta ne ya kamashi ta kwanta ruf da ciki ya rinka shafa mata bayan a hankali. Kamar zata yi bacci amma kwanciyar taki dadi ta sake juyawa. Ya Hamza...dan kwanciya yayi ya rankwafo kusa da ita. Yace ina jinki Cutie na, me kike so? A dan kunyace tace zaka shafa min cikina? Umma tana yi min a gida ina jin dadi. Ji yake kamar ciwon ya dawo jikinsa ta dena hawayen da take yi. Hannunsa ya dora akan cikin ya soma shafa mata a hankali. Da ta gaji sake kwanciya tayi ta tura pillow kasan cikinta. Shi dai Hamza duk abinda tace haka yake mata. Daga baya ya dage sai sun je asibiti tace a'a zata warke zuwa safiya. Ba su suka yi bacci ba sai wurin hudu. Ta riga shi yi ma ya gyara mata kwanciya a jikinsa shima yayi. Ana asuba ya farka ya tafi masallaci. Da ya dawo ya kwankwasawa su Adabiyya kofa ya sanar dasu su hada breakfast harda maigadi Zuhra bata jindadi. Doguwar rigarsa kawai ya cire ya dawo ya kwanta. Cikin 'yan mintuna bacci mai nauyi ya dauke shi. Ba su farka ba sai shabiyu saura. Zuhra ce ta fara tashi ta ganta kwance a jikinsa kamar wata mage. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #58 Batul Mamman(Mrs)# Kallo ta kare masa yana bacci. Tasan jiya ba wani baccin kirki ya samu ba shiyasa ta fita daga dakin a hankali ta rufe masa kofa. Wata mahaukaciyar yunwa take ji kamar anyi mata sata a ciki. A gaggauce tayi wanka ta shirya cikin riga da skirt na atampa ta sauka kasa. Banda breakfast hatta abincin rana su Hamida sun kusa gamawa. Shinkafa da miya suka yi, Adabiyya na gyara salad Zuhra ta shiga kitchen din suka yi mata sannu. Tace kuyi hakuri yau na barku da aiki. Adabiyya tace haba dai aiki, ai tun jiya na kula baki da lafiya sosai. Da asuba kuma Yaya yace baki dade da samun bacci ba. A kitchen din ta zauna cin abinci suna hira. Har karfe daya babu motsin Hamza tace bari ta duba shi kada ya makara zuwa masallaci. Tana bude kofar dakin ya fito daga toilet da karamin tawul a hannunsa ya daura wani a kugunsa. Juya masa baya tayi tana bashi hakuri. Har inda take tsaye ya karasa ya rufe mata kanta da karamin tawul din. A bayanta ya tsaya ya rungumeta. Ko motsin kirki ta kasa, yayi kasa da kansa ya sauke akan kafadarta. Cutie ya jiki? Ta runtse ido tace da sauki Alhamdulillah. Rikon da yayi mata ne yasa ta tuna yadda ta rinka makale masa cikin dare. Dan murmushi kawai take yi tana jira ya saketa ta gudu. A hankali ya juyo da ita muje ki shafa min mai yana daga cikin lessons dinmu. Alamar kuka yaga tayi ta kasa daga ido ta kalle shi. Ya Hamza kayi hakuri banda shafa mai. Yadda nake jin kunyarka hannuna rawa zai rinka yi fa. Shiyasa nake so ki koya har ki saba ya fada yana jan hannunta. Idan baki shafa min ba kinsan dai zunubi za'a rubuta miki ni babu ruwana. Tawul din da ya dora mata taja ta sake rufe fuskarta sannan ta mika hannu bani man....yana jindadin kasancewa tare da Zuhra. Kamar gaske tasa hannu a cikin man sai yaga ta lakato shi da yawa kamar mai shirin wasan mai. Saurin yin baya yayi...Cutie me zakiyi da wannan man? Sai da tayi dariya sannan tace shafa maka zanyi. Haba ke kuwa, wannan ai man da zan shafa a wata biyu ne kika lakata. Dan kadan ta rage tace to wannan yayi? Yace kinga jeki kiyi wani abin kafin na shirya. Idan kika shafa min wannan man ai ko Takitse bazata gaya min narkewa ba. Dama haka take so ta cire tawul din ta ajiye sai ta rufe idonta wai kada ta ganshi ba kaya ta mika hannu ni dai sai na shafa maka ko a fuska ne saboda kada ladan ya wuce ni. Da gaske take matsowa kusa dashi yana yin baya yana bata hakuri. Kamar zugata yake kara yi tana ta binsa suna zagaye dakin tana dariya. Da ya gaji yace idan baki fita daga dakin nan ba Cutie zan daukeki muje mu sake yin wanka. Bata jira ya maimaita maganar ba ta fita tana dariya. Shima dariyar yayi ya soma shiryawa. Karfe uku da kwata suka ji horn din mota alamun su Khalifa sun dawo. Murna a wurin Zuhra tamkar 'ya'yan cikinta ne. Yadda take son babansu haka suka shiga ranta su ma. Dreban kamfaninsa ne ya daukosu, yana tsayar da motar suka fito suna ta ihu suna kiran Daddy. Su biyu suka shigo a guje suka rungume shi tare da yi masa kiss a goshi shima yana yi musu. Junior ya rugo wurin Zuhra da ta fito daga kitchen da sauri. Dama tukin tuwo yasa bata fito da wuri ba. Kankameta yayi yace I miss you. Duk rashin turancinta tasan ma'anar wannan kalmar shiyasa taji dadi sosai. Bakinta kamar gonar auduga tace I miss you too Junior. Khalifa ya soma rigima Daddy kaji Zuhra bata yi missing dina ba. Kuma ni har nafi Junior missing dinki. Har sweet na rage miki fa. Zuhra tace yi hakuri kai babba ne shiyasa na fara fadawa kaninka. Hamza duk kunya ta isheshi da Khalifa yace mata Zuhra. Basu taba tunanin gyara musu ba da suke fada a da. Da dan borin kunya yace kada na sake jin kun kirata Zuhra. Junior yace to me zamu fada? Adabiyya ce ta bashi amsa, ku rinka kiranta Maama. Khalifa ya wani rungumeta don ace yafi sonta yace Maama I miss you. Tace nima haka tana dariya. Zuciyar Hamza kamar an masa albishir maidadi ganin yadda yaransa suke son Zuhra. Tala ce ta shigo da Nana a hannunta tana jan jakar kayansu. Har wani tsalle ta soma yi da ta hango Hamza. Ajiyeta Tala tayi da dan gudunta ta taho zata rungume Hamza sai ta kula da Zuhra mai bata abinci. Kwana tayi ta barshi da hannu a bude ta tafi wurin Zuhra ta rike mata kafa. Fuskar nan babu alamun wasa tace zanci tuwo. Hamza ya soma salati ana dariya. Yanzu duk gidanmu ki rasa wanda zaki gada sai Hamida mai cikin zani da babarki Zuhra. Hamida tace haba Yaya don Allah a gaban yara kake fadan wannan sunan. Adabiyya da Zuhra sai dariya suke yi. Hamza yace gashi nan ta gado ki a cin abinci da kiba. Ji yadda take gudu duk jikinta na juyawa kamar wata 'yar shekara hudu. Zuhra ta dauki Nana tace kai dai kawai kaji haushi 'yata tafi sona shine kake hucewa a kanmu. Tala ta gaishe su sannan ta wuce ciki da kayan. Ana la'asar Hamza ya fito zai tafi masallaci su Junior suna ta wasa a falo. Zuhra tace Junior, Khalifa Daddy zai tafi masallaci fa. Khalifa yace mun gani Daddy bye bye. Cigaba da wasan suka yi Zuhra tace kuzo muje kuyi alwala kada ya tafi ya barku. Maza a masallaci ake so su rinka sallolinsu. Junior yace Zuhra sai kuma ya rike baki... au Maama yau sallah babba ce ko sallah karama da zamu je masallaci? Allah Yasa su Hamida sun tafi yin alwala da kunyar da Hamza zaiji sai tafi wannan. Shi yasan bai taba damuwa da nunawa yaransa zuwa masallaci ba sai lokacin Idi. Zuhra ta kalle shi bari muyi sauri suyi alwala sai ku tafi. Ai dolensa ma ya jirasu tunda kanwar bayansa ce take fada masa abinda ya kamata. Yaran kuwa sai murna suka shirya suka bi babansu. Tala ce ta gama ware kayansu ta shiga kitchen din Izzatu zata dora abinci. Hamza na falon yaji motsin kwanuka ya tura Khalifa ya kirawota. Me kike yi a kitchen? Sai da ta durkusa daga gefe sannan tace abinci zan dora. Yace abinci wane iri? Tana dan susar kai tace Maman Khalifa tace idan mun dawo na rinka yi muku girki kai da yaran. Ransa a bace yace kada ma ki soma. A wane dalilin zaki yi mana girki bayan Zuhra na nan? Kema idan ta dafa zata baki so kada ki yi wani girki indai ba ta nemi ki tayata ba. Kuma ki rinka yi mata wanke wanke da sauran ayyuka idan ta bukata. Tala bata iya boye mamakin fuskarta ba. Hamza yace ko akwai wani abu ne? Tayi saurin mikewa a'a. Dayake Hamza yace ana magariba zasu je mayar dasu Hamida gida shiyasa Zuhra tayi girki da wuri. Tuwon shinkafa tayi da miyar agushi. Tala ta shigo kitchen din yana ta kamshi tana tambayarta ko akwai abinda zata tayata Zuhra tace babu komai. Bata manta kashedin da Izzatu tayi mata ba akan Tala. Khalifa ya shigo yace Tala ina sabon takalmi na zan nunawa Maama. Zuhra tace Khalifa kaga Tala babba ce ku rinka ce mata Anti Tala ko. Yace dama Mummy ce tace maiaiki ce ita ba sai mun ce Anti ba. Zuhra tace idan kana fada har aljanna zaka shiga. Da murnarsa yace bari na fadawa Junior ya fita. Tala tace nagode sosai saboda taji dadin yadda Zuhra ta darajata. Murmushi tayi ta dauki abincin maigadi zata mika masa Tala ta karba tace bari na kai masa. Tana zuwa inda yake zaune kan benci yace yau kun kusa saka min hawan jini. Tala tace saboda me? Ya gyara zama, wato ina ganin motarku gabana ya fadi nace Hajiyar ta dawo zamu koma gidan jiya..yunwa salamu alaikum. Tala tayi dariya sannan tace ai ni gidan mamaki ya bani. Dan bani labari meya faru bayan tafiyarmu. Maigadi ya bata labarin yadda Zuhra ke kyautata masa ga abinci a wadace. Tala ta bude flask dinsa taga tuwon yadda zaici ya koshi. Nan ta bashi labarin yadda suka yi da Izzatu kafin ta taho. Maigadi yace bar marowaciya....sai ya rufe baki kada wani yaji. Ai ki kyaleta kawai ni nan kullum addua nake yiwa Hajiya amarya Allah Ya kawo kazantar daki. Tala tace amin amin ai yanzu yallabai yayi aure. Wai har Anti tace su Khalifa su kirani. Gabadayansu suka shirya suka mayar dasu Hamida gida. Yaran sai murna sunga kakanninsu. Zuhra ta tafi gaisawa da Hajiya a dakinta ta bar Hamza a dakin Mama. Hamida ta dauko kudi ta nunawa Maman tace kinga Yaya ya bamu dubu bibbiyu ita kuma Anti Zuhra ta bamu kayan kwalliya. Mama tace Allah Ya saka da alkhairi Yaya mungode. Mamaki ne ya kamashi domin kuwa bashi ya bawa Zuhra kudin ba. Bayan fitar Hamida kasa shiru yayi ya fadawa Mama. Mama tayi murmushi tace Yaya Allah ne Ya hadaka da yarinyar nan domin ta tayaka gyara dukkan abinda ka bata. Har abada tsakaninmu da ita sai addua da fatan alkhairi. Abinda take yi maka shi ake bukata daga duk matar kwarai mai neman rahmar Allah. Cike da farinciki Hamza yake kara jin son amaryarsa. Mama tace idan Izzatu ta dawo sai kayi kokari ku zauna kayi mata nasiha. Idan da tarbiyar gidansu a halayyarta harda sakaci irin naka. Baka taba kokarin hanata ba a da sai ma biye mata da kake yi. Yanzu sai sauke nauyin dake kanka na yiwa iyalinka tarbiya irin ta addini. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [10/4, 12:59 PM] #+234 806 970 6638#: AL'ADUN WASU #59 Batul Mamman(Mrs)# A gajiye Izzatu ta isa gidan iyayenta a cikin garin Abuja. Bayan ta sallami mai motar da tayi shata tun daga Kaduna maigadinsu ya biyota ciki da jakar kayanta. Raliya na zaune a falo tana waya taga Izzatu ta shigo. Ko sallama batayi ba da wadda suke wayar ta tashi a gigice. Izzatu lafiya? Me ya faru?? Ina yaran??? Tambaya take tana kuma leka waje taga ko zata fahimci abinda ke faruwa. Izzatu tayi murmushi Mum kina da rudewa wallahi. Sai watso min tambayoyi kike a lokaci guda. Tayi maganar tana shirin zama akan kujera. Idanun Raliya kamar su fado don fargaba muryarta har rawa take yi tace kinga I..Izz...Izzatu bana son jan rai. Idan wani abinne ya faru ki fada min tun wuri. Hamzan ya sakoki ne ko me? Izzatu tayi jifa da mayafinta, Ohhh Mum ko ruwa ki bari nasha mana. Ki kwantar da hankalinki all is well. Hankalin Raliya bai kwanta ba sai da Izzatu ta gama cin abinci sannan tace Mum nazo yiwa Dad sallama ne fa na tafiyarsa Japan. Ran Raliya a bace tace Izzatu zan ci........ki wallahi. Shine zaki zauna ki tayar min da hankali tun dazu ina tambayarki kinyi shiru. Hawan jini kike so ya kamani ko ciwon zuciya? Kuma ko jiya kafin mu baro Kaduna sai da muka sake maganar nan dake nace an daga tafiyar tasa. Munyi maganar nan yafi sau biyu, ina hankalinki ne? Izzatu ta bude baki Mum da gaske na manta munyi zancen nan. Raliya tace to sai ki kwana yau gobe ki kama hanya ki koma gidanki. Izzatu ta kalleta sannan tace Mum nifa sai next week zan koma. Na riga na tambayi Hamza ya barni nayi sati daya a nan. Dariyar takaici Raliya tayi tace lallai Izzatu baki da kai, sai kace ba kece mai korafi akan auren da yayi ba shine kika basu wuri su sha soyayyarsu hankali kwance. Ya zaki rinka fadin haka Mum? Izzatu ta fada kamar tayi kuka. Ya bazan fada ba Izzatu? Banda satin da kika je kika yi a Kaduna kamar bikin Najah ake yi kanwarki yanzu kuma kin taho nan zaki kara wani satin. Allah Ya baki sa'a, ni yanzu nawa ido ne idan kina wannan rashin hankalin. Tana gama magana ta tashi a fusace ta bar Izzatu a wurin. Itama nata ran a bace yake tace ni nasan waye Hamza kuma na yarda dashi. Bazai taba kula wannan kazamar yarinyar ba. Lokaci kawai yake jira ya saketa kowa ya huta. Washegari tun karfe tara Izzatu ta gama shiri ta tafi dakin Raliya. Rungumeta tayi sannan tace goodmorning Mum. Raliya ta daure fuska. What is good about the morning Izzatu? Izzatu tayi dariya wai har yanzu fushi kike yi don nazo? Kina kallo yadda Dad yaji dadin ganina. Tunda duk yaran nan sun koma school kamata yayi kema kiji dadin zuwana. Raliya tace jindadi na daya ne ki koma gidan mijinki. Ina jiye miki tsoron sharrin kishiya Izzatu. Amma, ki cigaba. Ina zaki da sassafe haka keda bakya tashi da wuri? Izzatu tace aron mota zaki bani cikina ke dan yi min ciwo zani asibiti. Raliya tace ki jira dreba ya kaiki dai. Wane irin ciwon ciki ne? Dan tsaki Izzatu tayi saboda bata son yadda mamanta ke jan zancen. Nima ban sani ba shiyasa zani. Karfe goma da 'yan mintuna tayiwa Izzatu a wani asibitin kudi. Tayi sa'a babu layi sosai shiyasa bata dade ba ta shiga wurin likita. Likitar mace ce Dr Mardiya suka gaisa da fara'arta ta dan kalli file din gabanta. Izzatu Sunusi ko? Izzatu amsa da gyada kai. Dr Mardiya tace to Izzatu meye matsalarki. PT strip(abin gwajin ciki na gida) guda uku Izzatu ta nunawa likitan tace ciki gareni ina jin bazai kai wata biyu ba amma ya dan wace daya. Ina so ayi aborting din cikin bana so. Dr Mardiya tace baki da aure ne kike son zubar da ciki? Izzatu tace ina da aure da yara uku sun isheni. Idan cikin ya zube ina so ko dai a daure min mahaifa ko a cireta gabadaya. Bansan yadda akayi na sami cikin nan ba bayan ina shan pills. Sai da likitar ta gama 'yan rubuce rubucenta sannan tace tunda kina da aure bazamu cire miki ciki ba ba tare da izinin mijinki ba sannan kuma sai munyi bincike mun tabbatar cikin zai iya zama hatsari ga rayuwarki. Ran Izzatu ya soma baci, kinga doctor zan biyaku ko nawa ne a cire cikin nan. Plan dina na haifi yara biyu accidently na haifi ta ukun to sun isa haka. I am just 33 year old amma saboda haihuwa har na fara loosing shape. Boobs dina sun fara kwanciya saboda shayarwa. Dr Mardiya tayi murmushi tace baiwar Allah ashe da gaske ne idan dadi yayiwa mutum yawa sai yace Allah gani kasheni. Ko kinsan mata nawa ke neman haihuwa ido rufe amma irinku da yawa sai suzo zubar da ciki. Har gara wadanda suka yi na titi ko masu talauci akalla duk da hakan ba dalili bane amma suna da abin fada. Ke kuwa saboda kada kiyi loosing shape zaki zubar da ciki. To ai dole shape da kirji ya tafi tunda ko babu haihuwa akwai tsufa. Ina mai baki shawara kije ki sake tunani zaki gane wannan abinda kike son yi bai dace ba. Rai na kuna Izzatu ta fito daga office din likitan. Haka kawai zata sakata a gaba da wa'azi. A Kaduna ta gane tana da cikin shiyasa ta yanke shawarar zuwa Abuja ta zubar batare da sanin Hamza ba. 'Ya'ya uku dai ai sun ishesu. Asibiti biyu taje bayan nan duk sai likitocin su bita da nasiha. Karshe wani pharmacy taje ta siyo maganin zubar da ciki ta tafi gida. Yaushe zata yi ta ciki da haihuwa Hamza ya zo ya dena ganin kyanta. ******** Zuhra da yara ta kwana a dakinta. Tala ta dauko mata pampers har uku da za'a sakawa su Khalifa saboda duk suna fitsarin kwance. Ajiyewa kawai tayi don bata da niyar saka musu. Tsabar son jiki na mata yara sun girma sai muyi ta kakaba musu pampers bama tausayin masu siyowa da jikin yaran. Hamza yazo yace ta bari su kwana a dakinsu da Tala tazo ya cigaba da jinyarta tace ita ta warke. Duk yadda yayi Zuhra taki yarda ta kuma kwana a dakinsa. Ba komai ke hanata ba sai kunyarsa da take ji da kuma soma sabawa da tayi na kasancewa tare dashi. Dawowar su Khalifa ya kara tuna mata idan Izzatu ta dawo dole abubuwa zasu canza sannan uwa uba bata san matsayinta a wurin Hamza ba. Tana so taji ina batun maganar rabuwarsu ta kwana. Cikin dare alarm ta saka sau uku tana tashi ta kai yaran dukkansu suyi fitsari hakan yasa da gari ya waye Junior ne kawai yayi shima da asuba ne ta sauka kasa ta tambayi Tala me ake basu abincin makaranta. Sai da ta gama taje tayi musu wanka. Suna breakfast Nana kuwa bata tashi ba Hamza ya sauko. Kin kula Zuhra yayi wai yayi fushi. Dariya kawai tayi sannan ta gaisheshi. Khalifa na murna yace Daddy yau banyi fitsari ba ni da Nana, Junior ne kawai yayi. Hamza yaji dadi sosai yace da gaske? Khlaifa yace yes Daddy kuma Maama bata saka mana pampers ba kaimu toilet ta rinka yi, tace duk mun girma mun zama big boys. Junior ya fashe da kuka ance yayi fitsari. Maama ba kince sau daya nayi ba. Zuhra ta dorashi akan cinyarta sau daya ne mana kuma gobe bazaka yi ba in sha Allah. Daddy ayi mana addu'a mu dena fitsarin kwance. Duk wanda ya sake yi zamu cinye abin dadi bazamu bashi ba. Wani irin kallo Hamza yake bin Zuhra dashi mai nuni da farincikinsa a fili. Yace to kowa ya daga hannu muyi addu'a. Bayan sun gama suka dauki jakunkunansu da lunch box suka fita waje wurin motarsa. Zuhra tana dauke kayan da suka ci abinci Hamza ya dawo ya dan tsaya a bakin kofa Cutie bazaki rakani bakin mota ba? Yana cikin lessons dinmu fa. Murmushi tayi tace Ya Hamza ka gama fushin? Daga hannu yayi zai dalli bakinta ta goce, zan gamu dake ne idan na dawo ya fad yana murmushi. Kiyi min addu'a kinji. Yau in sha Allah zan biya mutanen nan kudinsu na rabu da bashi. Tace In sha Allah zanyi, sai ka dawo, Allah Ya tsare. Cike da nishadi kamar ba wanda yake shirin gamo da matsin rayuwa ba ya kai yaransa makaranta ya wuce office. Yana ganin indai Zuhra na tare dashi in sha Allah komai zai zo masa da sauki. [10/4, 1:40 PM] #+234 815 728 4163#: AL'ADUN WASU #60 Batul Mamman(Mrs)# Zaman Zuhra da su Khalifa abin sha'awa. Kwana biyu da dawowarsu amma sun saba sosai da ita. Wannan ne ya ragewa Hamza radadin da yake ji a ransa na halin da yake ciki. A yadda ya kukuta ya hada kudin nan kaf gida da account dinsa bashi da kudin da ya kai dubu dari biyu da hamsin. Kudin man inji kadai ya ishe shi banda na mota da sauran abubuwan da zasu iya tasowa. Gashi Izzatu ta sanar dashi motarta da suka tafi Kaduna ta lalace a ta haya a tafi Abujan ta bar motar a gidan Kawunta . Yana cikin tunani Zuhra ta shigo falon da sauri kamar wadda aka biyo da littafi a hannu. Saurin gyara yanayin fuskarsa yayi saboda kada ta gane yana cikin damuwa. Ya rasa yadda ake take sani sai kace mai gani har hanji. Dan durkusawa tayi a gabansa tace Ya Hamza don Allah taimaka ka fitar dani kunya. Mtswwww shiyasa Baba yace na dan maida hankali a karatu ko na koyawa yara homework ne na samu saboda kada naji kunya wata rana. Gashi abinda yake fada yau ya faru. Suma malaman da kyuyar tsiya sai a bawa yaro homework biyar a rana. Tunda ta fara magana Hamza ke kallonta yana murmushi. Zuhra ta iya sawa ya manta da damuwarsa. Lebenta ya hada ya kama da yatsunsa, to aku sai zuba kike yi baki fadi ainihin abinda ya kawoki ba. Hannunsa ta nuna da ya rike mata baki, yana saki ta kwabe fuska shine zaka matse min baki ko? Yace to ko na bashi hakuri ne. Matsawa tayi baya don ta tuna yadda ta kare ranar da ta nemi a bawa lips dinta hakuri., ba sai ka basu ba na hakura. Sake matsowa tayi ta dora masa littafin Khalifa akan cinyarsa. Na kusa minti shabiyar na kasa gano kan aikin nan. Ina tsoron fada masa ba daidai ba yaje yaci zero. Hamza yayi dariya ai kuwa da ya bazaki a duniya yace Maama bata iya homework dinsa ba. Littafin ya duba verbal reasoning na 'yan nursery three. A wata takarda duk ya rubuta amsoshin ya bawa Zuhra taje ta koyawa Khalifa kamar ita tayi. Suna gamawa tasa suka yi shirin bacci kowa yayi fitsari suka kwanta. Ba jimawa suka yi bacci. Kasa ta sauko dibar ruwa saboda Nana sai ta kula Hamza na cikin falonsa har lokacin bai kwanta ba. Sallama tayi ta shiga yasa computer da takardu a gaba yana ta aiki. Da yaji motsinta ya dago kai suka hada ido ta sakar masa murmushi. Doguwar rigar bacci ce a jikinta mara kauri ta daura zani a sama har kirjinta , sai hula a kanta. Hamza yace maman yara me ya sauko dake? Tace ruwa na manta ban daukarwa Nana ba. Da hannun yayi mata alama ta karaso gabansa. Tana zuwa yasa hannu ya kwance zanin dake daure a kirjinta. Cutie bana son daurin kirji. Kunya ce ta kamata saboda rigar bata da kauri ta fara shirin fita ya rike hannunta ya zaunar da ita a kusa dashi. Tun yanzu kin dena damuwa dani saboda yara sun dawo ko? Irinku ne masu mayar da miji dan kallo da kun haihu. A haka ma kina shareni ina ga kin haifi naki. Zuhra ta sha kunu Ya Hamza nufinka ni ba 'ya'yana bane. Ai ko baka fada ba na sani amma a yadda na daukeka dan uwana dole naso 'ya'yanka, ko kara ai kayi min naji dadi. Sarkin kuka tana magana ta soma hawaye. Hamza duk ya rude, ba haka nake nufi ba Cutie ki dena kuka 'ya'yanki ne mana. Ta share hawaye ba wani nan, don kaga ina kuka ne kace nawa ne. Rungumeta yayi sosai a jikinsa, duk abinda kika yi yana sani farinciki da jindadi Cutie amma bazan juri kukanki ba sai ya kara min damuwa. Idanu sharbe da hawaye ta dago kai tana kallonsa. Ya Hamza indai kana so na dena kuka sai ka karbi shawarar da zan baka yanzu. Lallai ma yarinyar nan dama kika samu shine kike kuka mara dalili don ki fake ki fadi abinda ke ranki. Dariya tayi tana share hawayen, ya akayi kayi saurin ganewa don Allah? Amma da gaske banji dadi ba sosai don nasan dai wasa kake yi ne. To ina jinki mecece shawarar taki? Zuhra tace dazu na kula kamar kana cikin damuwa. Hamza ya girgiza kai anya Cutie baki da alaka da sarkin mayu. Yarinya duk yadda na boye abu sai kin gane. Dariya tayi sosai sannan tace to Ya Hamza idan ban gane kana da damuwa ba ai babu amfani a zan tare. Kasan ina yin saka ko? Yace Baba ya fada min. Zuhra tace to idan na hau sama zan dauko kaga irin rigunan da nake yi. Mijin Anti Faiza ya taba samar min nayiwa 'yan wata makaranta. Duk da ba babba bace amma akwai riba. Idan zaka iya ka nemo mana makarantu pravate masu dan tsada ko zasu bani kwangilar sakar rigunan sanyi na makaranta. Idan nayi kaga zamu sami wata hanyar ta shigowar kudi kafin ka gama aikin kwangilarka a biya ka. Zuhra bata san yadda take raunanawa Hamza zuciya da kalamanta da kaifin tunani ba. Yace Cutie ban fada miki matsalata don ki tausaya min ki taya ni neman kudi ba. Tayi dan murmushi Ya Hamza na tabbatar ba fada min kayi ba saboda naji dadin labari. Kullum ina tayaka addua Allah Ya saukaka maka halin da kake ciki, to tunda Allah Ya bani iko sai na taimaka maka da abinda na iya kafin lokacin rabuwarmu. Ya Hamza nima fa ka taimakeni, da taimakonka na san na kula da jikina kamar kowace mace batare da ka nuna min kyama ba. Don Allah ka bani wannan damar nayi maka wani abu. Nan gaba kila ko zumunci bazamu sami damar yi ba idan nayi aure. Tashi Hamza yayi ya tasheta tsaye yana kallonta cike da tsantsar kauna. Cutie nima kin taimakeni da abubuwa da dama ciki harda gyaran tarbiyar su Khalifa. Kada ki wahalar da kanki a kaina. Hawaye ne yake wanke mata fuska tace don Allah ka bincika ko za'a sami masu bani aikin. Wallahi na iya sakar sosai. Hannu Hamza ya mika zai janyota jinkinsa sai ya fasa, yanzu ina tabaki zaki ce wayon tabaki nake yi. Kinyi min izini na rungumeki? Rigar jikinta ta kalla sai taji kunya ta sunkuyar da kai. Ya dan leka fuskarta please Cutie. Kai ta gyada tare da rufe fuskarta da hannuwanta. Hamza ya rage tazarar dake tsakaninsu ta hanyar rungumeta a jikinsa sosai yana mayar da numfashi. Bai san inda zaisa son Zuhra a ransa ba. A hankali yace kin yarda bayi kissing dinki please? Don kunya ji take wani abu na yawo a cikinta ta kara sunne kai a kirjinsa. Ya Hamza kunyarka nake ji. Ya dago kanta a hankali da hannunsa daya. Ko na minti daya kawai Fatima. Bai bari ta sake sauke kanta ba ya hada bakinsa da nata. Ita dai sai yadda yayi da ita kawai. Dukkansu a bakuwar duniya suka tsinci kawunansu. Ko da ya saketa bai dena kallonta ba yace Cutie ko ban sami school din ba bazan taba mantawa da wannar ranar ba. You hold a special place in my heart. Hamza yana godiya da dukkan abinda kike masa na kyautatawa. Ita dai bata iya magana ba ta dauki jug din ruwa ta haye sama ta barshi yana murmushi. ********** Kwayoyin guda hudu ne a hannunta da kofin ruwa. Zuciyarta tana dan yi mata wasiwasi sai dai gaskiya bazata iya yarda ta kara haihuwa ba. Wadannan ukun sun ishesu. Tun kafin ta hadu da Hamza take da ra'ayin 'ya'ya biyu kawai. Rufe ido tayi ta watsasu gabadaya daya. Idan cikin ya zube sai ta fadawa Hamza da iyayenta bata ma san dashi ba. Tana sha ta dauki waya ta kira shi. Lokacin Zuhra bata dade da barin falon ba. Hira sosai suka yi yana fada mata yadda yayi missing dinta. Har zuciyarta Izzatu tasan bata kyauta masa ba amma tasan idan ya gane da cikin nan tilasta mata zaiyi sai ta haifa. Sai da suka gama hirarsu ta masoya ta gyara kwanciya tayi bacci. Karfe biyar da rabi wani matsanancin ciwon ciki ya tasheta. Tana kunna fitila taji danshi a inda take kwance. Hannu na rawa ta bude bargon taga jini ne sosai a wurin. A razane ta kwalla ihu MUMMMMM. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #61 Batul Mamman(Mrs)# Kamar daga sama Raliya da Dad dinsu Izzatu suka ji ihunta. Kafin su karasa dakin kaninta Walid ya rigasu. Kokarin dagata suka tarar yana yi ga jini ya jika zanin gadon. Kuka Raliya ta saka ta soma jijjiga Izzatu sai dai ta suma bata san waye a kanta ba. Dad dinsu yayi saurin dauko makullin mota shi kuma Walid ya ciccibota ya sakata a ciki. Hankalinsu a tashe suka tafi asibiti mafi kusa dasu. Raliya sai kuka takeyi tana kiran sunan Izzatu. A yanayin da likitoci suka ganta theatre akayi gaggawar kaita ana kokarin ceto ranta. Sai kai kawo suke yi a kofar theatre din har gari ya karasa wayewa. Suna kallo nurse zata fito da gudu wata ta shiga. Tsahon lokacin nan babu irin tunanin da iyayenta basuyi ba. Suna nan tsaye jugum jugum Raliya tace idan ka taho da waya ya kamata a sanar da Hamza. Alh Sunusi yace haba Raliya, ya za'ayi mu kirashi a wannan lokacin bayan muma bamu san aininhin abinda ke damunta ba. Ko kin sani? Cike da damuwa Raliya tace ni bansani ba kuma banga wata alama ta rashin lafiya a tare da ita ba. Likitoci biyun dake kan Izzatu ne suka fito a tare bayan fiye da awa daya da sukayi a ciki. Daya daga cikinsu ya dubi Alh Sunusi yace ku biyo ni office. Raliya tace Doctor kawai ka fada mana a nan idan ta cika. Yayi murmushi noooo Madam, ki kwantar da hankalinki. She is stable now. Duk su biyun sun tsirawa liktan ido suna jiran bayaninsa. Glass din idonsa ya cire ya goge fuskarsa da hankice....duk motsinsa Raliya kamar ana tsikarinta take ji. So take kawai tasan abinda ya sami Izzatu. Likita yace "yallabai menene matsayin patient dinnan a wurin ka?" " 'Yata ce" Alh Sunusi ya amsa masa. "Tana da aure ko budurwa ce?" Raliya ta kagu ya fadi abinda ke faruwa tace "matar aure ce harda 'ya'ya uku. Mijinta yana Kano". Sai da yayi 'yan rubuce rubuce sannan yace "patient dinnan tasha maganin zubar da ciki overdose. A ka'idar wanda tasha ma guda daya ake sha amma da kyar ta iya fada mana hudu tasha a lokaci daya". Cikin rashin fahimta Alh Sunusi yake tambayar Raliya dama Izzatu nada ciki tace itama bata da labari. Likita yace to a gaskiya ba karamin ganganci tayi da rayuwarta ba domin da kyar muka iya ceto rayuwarta da ta abinda ke cikinta. Tunda yana da lafiya bamu ga dalilin zubar dashi ba. Sai dai ya zama dole a kula da ita sosai har ta haihu domin mahaifar a yanzu bata da kwari. A takaice ma dai sai dai ayi mata aiki a cire baby din idan ya cika watannin haihuwa sannan ita kanta mahaifar dole a cireta. Dalilin haka yasa muka tabbatar munyi kokari wurin ceto abinda ke cikin." Raliya ta dora hannu a ka tana kuka tunda taji yace za'a cire mahaifa. Alh Sunusi rai duk babu dadi yace muna iya ganinta? Doctor yace su bari ta huta domin ta wahala. Bayan awa uku Alh Sunusi da Raliya ke zaune a dakin da Izzatu take. Farkawarta kenan tace Mum me nake yi a nan? A fusace Raliya tace ubanki kike yi Izzatu. Nace ubanki kike yi. Shashashar banza mara hankali, iliminki da shekarunki basu kara miki komai ba sai hauka. Alh Sunusi yace haba Raliya ya zakiyi mata magana irin haka bayan kinsan halin da take ciki. Tun dazu kike kuka kina addu'ar ta farfado. Ta tashi kuma kin bita da zagi. Raliya tace to ya zanyi da yarinyar nan? Ta hade rai ta kalli Izzatu...har kin iya zubar da ciki ko? To Allah bai nufa ba wannan dai sai kin haife shi. Izzatu ta zaro ido...Mum kina nufin bai zube ba? Meyasa basu yi min wankin ciki ba? Ni wallahi bana son sake haihuwa. Su Khalifa sun isheni. Maganarta sam bata yiwa iyayenta dadi ba. Raliya tace kaji da kunnenka ko? Ni kam nayi nadamar kyaleku da mukayi kuka zama turawan karfi da yaji. Zeenatu ta auri mijin da dabi'unsa tamkar wani bayahude har yau ban taba sonsa ba. Amma saboda mun baku damar yin yadda kuke so a dole muka barta da zabinta. Ke da Allah Ya rufawa asiri kuma kina neman tonawa kanki. Idan Hamza yaji abinda kika yi ya sakeki zaki yi bayani. Izzatu ta daure fuska Mum bana son irin haka. Hamza bazai taba iya rayuwa batare dani ba. Muna son juna kuma ai nayi kokari da na haifa masa har 'ya'ya uku. Alh Sunusi ya daka mata tsawa. Ashe abinda Mamanki take fada gaskiya ne baki da hankali. Duk laifinmu ne da muka baku irin wannan tarbiyar amma wallahi idan kika kuskura kika kara yunkurin zubar da cikin nan sai ranki ya baci. Kuma ni dai bazan kira Hamza na sanar dashi abinda kika yi ba, ai da kunya. Raliya tace nima ai ba fada zanyi ba. Dama karya tayi masa ta taho shine muma zaki ha'incemu ki zubar da ciki bamu sani ba. Izzatu ta soma kuka ni duk kun tsaneni. Kawai don nayi aure shikenan kuma bani da 'yanci na zabarwa kaina abinda ya dace? Tana magana iyayenta suka fice ta cije lebe. Ita bata ga aibun abinda tayi ba. Haihuwa ce ta isheta haka. Tunanin abinda Hamza zaiyi idan yaji zancen nan tayi gara tayi shiru tunda idan ya sani fada zaiyi mata shima. Za dai ta kirashi ya aiko mata da kudi na hannunta sun kusa karewa. ********* Kwanaki biyu da maganar Hamza da Zuhra ya dukufa nema mata makaranta saboda yadda ta dame shi. Da samples biyu data bashi yake yawo. Cikin ikon Allah a rana da uku wadda ta kama Juma'a ya sami wasu makarantu har biyu. Ba karamin farinciki yayi ba da hakan. Har mamaki yake yi yadda yake kwantar da kai a gaban Principal ko Headmaster yana neman alfarmar a bashi wannan kwangilar. Da gaske ba karamin matsi zasu shiga ba shi kuma baya son taba kudin kamfani ayyukansu su durkushe. Tun a hanya ya kira Zuhra ya sanar da ita. Makaranta daya bangaren nursery za'ayiwa dayar kuma secondary ce ma. Har wani tsalle take yi ta tambayeshi kalolin da aka zaba ya fada mata. Kafin ya iso gida a cikin kudinta ta aiki Tala kasuwa ta siyo mata kulu da maballai. Bai dawo gida ba ranar sai tara saura. Bayan yaci abinci yace gobe zan duba sai a siyo kayan da zaki bukata. Inda zai samo kudin yake tunani. Zuhra tayi 'yar dariya tace ai har Tala ta siyo min tun dazu. Wani daki kusa da na Tala a kasan ta nuna masa kayan. Yace wa ya baki kudin? Ya Hamza akwai 'yan kudi a hannuna. Yanzu dai ka huta sai ka nuna min irin yadda kayan nasu suke na fara aiki. Sai wani farinciki take yi zata sami damar taimakonsa. Murmushi yayi yace nagode Cutie Allah Ya baki lada, tace amin. Jikinsa a sanyaye ya tafi daki. Bayan dan lokaci Zuhra ta bi bayansa saboda ta kula da yanayinsa. Rashin kudi a wurin wanda ya saba rike su da tausayi. A bude ta tarar da kofar falon amma baya ciki. Tana kokarin shiga dakin taji muryarsa yana waya muryarsa a raunane. Maganar karshe kafin ya ajiye wayar taji yace " Inuwa kafi kowa sanin halin da nake ciki, idan baku maida hankali sosai akan aikin nan ba karshenta yarana idan anyi hutu bazasu koma school ba.". Izzatu ta kirashi tayi masa karya tace tana bukatar kudi zata asibiti tana zazzabi tun kwanaki biyu da suka wuce ya fada mata bashi dasu ta ranta a nata zai biyata . Tun daga ranar tayi fushi ta kashe waya baya samunta. Ita a tunaninta kuntata mata kawai ya koyi yi saboda iyayensa. Gashi tana son biyan kudin asibiti bata son tambayar iyayenta tunda fushi suke da ita. Banda ita yana tunanin yadda zai biya kudin makarantar yara boko da islamiyya duka masu tsada suke zuwa. Komawa da baya Zuhra tayi tana kuka cike da tausayin Hamza. Inda ta ajiye kudin da Baba ya bata da sauran na hannunta ta duba. Abinda yayi mata saura dubu saba'in da uku har dan kudin sakar da ta taho dashi. Dubu hamsin ta dauko har ta kai bakin kofar dakinta sai ta dawo tana tunani. Idan ta kaiwa Hamza kudin nan bazai taba yarda ya karba ba. A take tayi murmushi da dabara tazo mata. A cikin rigarta ta boye kudin ta koma dakinsa. Kwance ta same shi akan gafo ko kaya bai cire ba bare yayi wanka. Ta karasa kusa da gadon, Ya Hamza ba lafiya ne? Murmushin dole ya kirkiro ya tashi gajiya ce kawai Cutie ke kuma ko tausa baki taba yi min ba. Kodayake nine ban koya miki wannan karatun ba. Tace to yi wankan sai nayi maka. Amma sai ka kawo cin hanci. Dariya take tana maganar domin ta rage masa damuwa. Yace to ki jira na fito zan baki. Shigarsa toilet keda wuya Zuhra ta bude wardrobe dinsa duk ya hargitse ta fito da kayan. Har ya fito daga wanka tana gyara masa kayansa. Yayi murmushi yau Cutie abin kirki ake ji ne. To nagode ki gyara da kyau. Ita dai bata juyo ba don tasan daga shi sai tawul. A hankali ta juya taga ba ita yake kallo ba sai ta fito da kudin dake boye a jikinta harda dariyarta ta juyo, nayi tsintuwa ba sata ba. Hamza yace kinyi satar kenan. Ai ba'a tsintuwa a cikin daki. Kudin ta nuna masa da fara'a a fuskarta. Ya Hamza har a cikin kaya kake boye kudi? Jin abinda tace ya taho wurin da sauri. Mu gani ya fada yana mika hannu. Mika masa tayi tana cewa sai ka bani ladan tsintuwa. Yanayin farincikinsa bazai misaltu ba. Ba karamin dadi yaji ba wanda hakan da Zuhra ta gani yasa wani hawaye kokarin fito mata tayi saurin mayarwa. Hamza yana ta juya kudin yace ni bazan iya tuna lokacin da na ajiyesu ba. Tace a nan gefen na gansu. Kuka ke neman kwace mata saboda yadda taga yana farinciki don ya tsinci dubu hamsin abinda yafi karfi a da. Ta dan wayance bari na duba su Khalifa na dawo. Tana fita nasa hawayen suka sakko..bai yi kokarin mayar dasu ba sai ma sujjada da yayi ta godiya ga Allah da Ya bashi Zuhra. Tunda ya fito daga toilet ya kula da yadda take yawan juyowa ta kalle shi shiyasa a na karshen yayi saurin kawar da kai. Yana kallon lokacin da ta daga rigarta ta zaro kudin. Wai shi zata yiwa wayo kada yace ta bashi kyauta yaki karba. Zuhra ta cancanci duk wata soyayya da kauna daga gareshi kuma wannan dubu hamsin din yana fata Allah Ya bashi ikon biyanta da abinda ya fisu daraja. A hankali ya furta I love you Zuhra. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #62 Batul Mamman(Mrs)# Washegari tun da Zuhra ta tashi sallar asuba bata koma bacci ba. Tana idarwa ta sauka ta shiga kitchen. Breakfast ta fara hadawa sannan ta dora miyar abincin rana, sannan ta yanka dankali 'yan madaidaita ta dafa da kwai. Bayan ta gama ta hadasu wuri daya ta yanka cucumber da koren tattasai ta gurza caras ta saka mayonnaise. Cikin kankanin lokaci potato salad dinta ya hadu ta saka a fridge inda bazaiyi sanyi sosai ba, idan tayi sallar azahar taliya kawai zata dafa. Duk wannan saurin so take ta fara sakarta ne da wuri. Tana gamawa ta tafi daki zata yi wanka ta tarar yaran duk sun tashi. Bata sami nutsuwa ba sai da ta shiryasu har suka gama cin abinci, ta barsu wurin Tala ta shige dakin da ta ajiye kayan sakar. Duba kayan da Hamza ya kawo tayi da irin tsarin da makarantun suka bashi. Cikin dan kankanin lokaci ta soma sakarta hankali kwance. Dayake abu ne da take so ta kware a sarrafa injin sakar. Na 'yan nursery din ta fara wanda zata yi musu guda dari da hamsin a dubu daya da dari bibbiyu su kuma su sayar a dubu da dari biyar. Kokarinta ta gama ko na makaranta daya ne kafin litinin ya fara kai musu. Idan aka biya tasan kudin zaiyi masa amfani sosai. Wayar Izzatu ce ta tashi Hamza tana sanar dashi zata dawo washegari zata biyo jirgin safe. Hamza yace to Allah Ya kawoki lafiya. Tace Amin tunda kaki aiko min da kudi wannan ma Dad dina ne ya bani. Hamza yace to Allah Ya saka masa da alkhairi ya ajiye wayar. Ace ko sau daya zata ce bata kula da yanayinsa da ya canja ba bare ta tambayeshi meye damuwarsa. Tsaki yayi ya tashi ya shiga wanka. Yana fitowa yaci karo da breakfast dinsa a falonsa. Murmushi yayi ya zauna yaci ya koshi. Aiki yake son yi amma yau ko motsin Zuhra baiji ba shiyasa ya fasa ya sauka. Su Nana kawai ya gani a falon suna ta kiriniya yace ina Maama? Junior ya nuna masa dakin da take, kuma Daddy tace kada wanda ya shiga aiki zata yi. Sai a lokacin Hamza ya tuna da zancen saka yace to ku zauna bari naje nace mata sannu da aiki na dawo. Zuhra na kan riga ta bakwai Hamza ya shigo dakin da sallamarsa. Kafadarta ce ta dan rike saboda kwana biyu bata sakar ta dan tsaya tana dukan wurin. Ganin Hamza ya shigo yasa ta murmushi. Ya Hamza har ka tashi? Nayi tunanin sai ka kai karfe daya. Yace saboda ga kasa sarkin bacci ko. Murmushi tayi tace ni dai bance ba, naga yau asabar ya kamata ka huta. Maimakon yayi magana zagayawa yayi ya tsaya a bayanta sai ji tayi yasa hannuwansa yana mata tausa a kafadunta. Da farko kunya taji sai kuma ta soma dariya saboda ji take yi kamar yana mata cakulkuli. Sosai take dariya har ta fara kokarin tashi ta gudu yace ke dai kina da matsala. Kiyi ta dariya kamar shashashan madina. Da kyar take mayar da numfashi tace to ai kaine kasa ni dariya. Daga yi miki tausa sai kice na sakaki dariya? To ajiye ki huta ya fada tare da daukan riga guda daya. Yayi murmushi Cutie ashe dai ba cika baki kike yi ba kin iya sakar. Kanta a kasa tana cigaba da aikinta tace kaima zanyi maka kafin na tafi. Amma dai yanzu ka fita idan na ganka bana iya aikin sosai. Ya dan durkusa a gaban injin yana dariya da gaske Cutie? Ko dai kin fara sona ne? Ta dago idonu a bude ni di??? Rufa min asiri Ya Hamza ina ni ina kai. Nifa har na yanke shawarar wanda zan aura idan ka sakeni. Kamar saukar mari yaji maganarta. Harara ya watsa mata ya fice ba tare da ya sake magana ba. Da taji ya rufe kofar tayi dariya, ita tsokanarsa kawai tayi amma tunda ta ga yaji haushi ta daga hannu sama. Ya Allah Kasa shima yana sona ko dan kadan ne. Ba ita ta fito daga dakin ba sai azahar ta dafa taliya tayi sallah. Har ta idar su Khalifa basu dawo daga masallaci da Hamza ba. Ajiye musu abinci tayi ta kai masa nasa falo ta koma ta cigaba da aiki. Bayan sallar magariba Inuwa sakatare yazo, Hamza ya sanar da ita zasu fita tayi masa adawo lafiya. Ranar gabadaya Zuhra a saka ta tafi sai sallah da girki da take tashi tayi. Wurin karfe goma ta fito saboda yunwa. Su Khalifa duk sunyi bacci Tala ta kaisu dakinsu ganin Zuhra na aiki. Abinci ta diba da ruwa ta tafi dakinta dashi saboda ko sallar isha bata yi ba. Sai da ta zauna zata ci abincin taga babu cokali. Wanko hannunta kawai tayi a toilet ta zauna taci. A gajiye take sosai ga kafadunta da baya duk suna ciwo. Gajiya da bacci ne suka tarar mata a kan doguwar kujerar da taci abincin ta dan kashingida sai bacci ko hannu bata wanke ba. Hamza ya dawo gida bayan ya ajiye Inuwa a nasu gidan. Unguwar su Mr Oscar suka je ko akwai wanda yake da labarin inda ya tafi basu samu ba. Dakin da Zuhra ke saka ya duba ya tarar da riguna birjik a kasa ga fitila bata kashe ba ga dukkan alamu zata dawo ta cigaba da aikin ne. Bashi da niyar barinta ta cigaba a ranar saboda yasan ta gaji. Dakinta yaje ya tarar da ita tana bacci a zaune ga plate din abinci a gefenta a kan kujera. Ya duka zai tasheta ya kula da hannunta duk miya har ta soma bushewa. Da gani tana jindadin baccin sai yaki tashinta. A hankali yace Allah Sarki Cutie yasan ba karamar gajiya tayi ba. Tissue ya samo ya goge mata hannun, ya sauke plate din ya gyara mata kwanciya ya fita. Tausayi ta bashi sosai yadda ta dage tana saka ga girki tana yi akan lokaci. Kusan minti talatin da fitarsa yaji kamar ihu daga dakin Zuhra. Lokacin bai dade da kwanciya ba. Da sauri ya fito ya ganta a tsaye ta rike hannunta na dama tana kuka sosai. Saurin matsowa yayi kusa da ita Cutie me ya same ki? Kara matsawa tayi baya tana kuka tace kada ka matso Ya Hamza ni tawa ta kare. Bai fahimci inda zancen nata ya dosa ba yace taki ta kare kamar yaya? Ki dena kukan kiyi min bayani. Murya a shake tace abinci naci a wurin nan, ta nuna kujerar...sai bacci ya daukeni amma na tabbatar ban wanke hannu ba. Ina farkawa yanzu naga alamun an lashe hannun amma dai da saura kadan. Hannun damanta ta daga ta nuna masa. Yayi murmushi zai fada mata shi ya goge mata da tissue ta cigaba da magana. Ashe ni kuma a haka zan tafi Ya Hamza, Allah ma Ya sa mutuwa a dalilin annoba ana sakata cikin shahada. Ta sake barkewa da kuka, bera ya lashe min hannu Ya Hamza, ya saka min zazzabin lassa. Yadda Zuhra take kuka da gaske ya bashi dariya sosai. Yace banda sharrinki Cutie kin taba ganin bera a gidan nan. Tace shi bera ina ne baya shiga. A yadda naji a rediyo mutum ba wani dadewa yake ba idan ya kamu da ita. Dariya Hamza yake son yi amma ya gimtse. Zuhra bata da dama ya fada a ransa. Hannu ya mika mata zo kinji Cutie dina, babu wani bera ki kwantar da hankalinki. Can karshen dakin ta koma kada ka tabani ka kwasa kaima. Ka barni kawai anan har lokacina ya cika. Kodayake naji ance gwamnati na bayar da magani ka sanar dasu akwai mara lafiya a nan sai suzo su daukeni. Ta sunkuyar da kai, nasan ma dakyar zan kai labari. Shi dai Hamza dramar Zuhra nishadi ma ta saka shi ya zauna akan kujerar da ta tashi tace tashi kada ka dauka anan na kwanta. Yana kallo tasa hannun hagunta ta dan tattaba wuyanta. Kaga har na fara jin zazzabin kuwa. Yace Allah ko Dr Zuhra yana murmushi. Sake taban wuyan tayi tace inajin ba zazzabin bane amma shima nasan yana kusa. Hamza ya taso ya taho wurin da take tsaye ni zan zauna dake ko wane irin ciwo kike dashi kinji. Hannu ta daga masa alamun kada ya matso fuska duk hawaye tace Allah Sarki Ya Hamza shiyasa nake SON ka wallahi saboda kana da kirki da tausayi. Cak Hamza ya tsaya maganarta ta sauka a zuciyarsa. A hankali ya daga kai ya kalleta. Da gaske kina sona Cutie? Kunya taji har ta soma girgiza kai sai ta dena ta dago tana kallonsa. Ya Hamza idan mutum zai mutu ai babu zancen kunya da karya ko? Gara ma na fadi gaskiya na sami lada. Hamza yace wannan gaskiya ne. Zuhra harda gyaran murya tace nasan munyi daku zaka sakeni bayan wata shida to Allah Ya gani wallahi ni bansan ya akayi ba sai naji ina sonka. Ba a matsayin Yayana ba fa. Dadi Hamza yake ji sosai sai ya dan basar to a matsayin me? Sunkuyar da kanta tayi tana magana a hankali. Wallahi Ya Hamza irin na soyayya nake maka jiya har mafarki nayi ka kaini asibiti zan haihu. Amma kada kace min mara kunya wallahi ina zaman zamana tunanin yake zuwa. Kuma in fada maka wata gaskiyar ma duk sallah a sujjada sai nayi addua'a idan da alkhairi Allah Yasa kada ka sake ni. Tamkar ya zuba ruwa a kasa yasha haka Hamza yake ji a wannan lokacin. Ashe ba shi kadai yake sonta ba suka yi shiru da zasu kwari kawunansu. Ya dan bata rai dazu kika ce bakya sona kuma har kin tsayar da mijin aure. Tace wallahi karya nake, irin abin nan ne na mata zan maka ashe ma bani da rabon dadewa a gidan aure. Ko kanta ta kasa dagawa saboda yadda take jin kunya gashi zata mutu ko soyayyar basu fara ba. Takun Hamza taji ya matso gabanta yasa hannu ya bude bargon da ta rufe kanta dashi. Kuka take tana rokonsa zai kamu da zazzabin lassa. Hamza yayi mata kyakkyawan murmushi sannan ya dauketa tamkar ya dauki karamar yarinya. Da wata bakuwar murya mai dadi yace Cutie ni na goge miki hannun da tissue, ta ware masa idanunta da yake son kallo tace da gaske? Ya gyada kai. A take kunya mai tsanani ta lullube Zuhra. Hamza yayi murmushi yace bari na karasa lada na nayi miki wanka, sai na fara koya miki lesson din soyayya. Irin soyayyar da zata sa mafarkinki na jiya ya tabbata nan da wata tara. Kanta ta tura a kirjinsa don kunya ta kankameshi. Zuciyarsa cike take da son Zuhra yace kinsan wani abu? Girgiza kai tayi batare da ta dago ba...I love you too Cutie. Nima bansan yadda akayi ba sai kawai naji ina matukar sonki. Dadi ne ya mamaye zuciyarta wai ita Hamza mijin Izzatu yake furtawa so. Tafiya taji ya fara yi da ita hanyar toilet ta soma kokarin zillewa. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #63 Batul Mamman(Mrs)# A kofa toilet ya ajiyeta ya fara juyata a gabansa yana karewa kayan jikinta kallo. Kokarin rufe jikinta ta soma yi yace wai ni ta ina kika saka rigar nan? Duk na duba na rasa maballi ko zip. Ajiyar zuciya tayi mai karfi tana murna da bai gani ba. A tsorace take da Ya Hamza. Janyota yayi jikinsa ya zagayeta da hannuwansa. Daga gefen kafadarta ta dama taji ya kama zip din wanda yake boye a jikin riga ya soma sauke mata shi kasa. Duk yadda tayi ta gudu abu ya gagara. Jiki na rawa tace Ya Hamza don Allah banda wanka. Yace kin manta sunnah ne? A'a amma akwai wasu dayawa. Idan nayi wankan da kaina duk abinda kake so zanyi maka. Wani murmushi yayi mata wanda shi kadai yasan ma'anarsa yace to amaryata. Zan jiraki a daki. Sai da ya manna mata kiss a goshi sannan ya tafi. Sai yanzu take jin tsoron Ya Hamza kuma. Wanka zatayi kawai tayi kwanciyarta. Ta dade tana kalkale jiki ta fito aka bata lokaci a gaban mudubi ana ta shafe shafe. Turaruka ta saka masu kamshi sosai da daukar hankali sannan ta daura zani ta tayar da sallar isha da bata yi ba. Tana idarwa ta cire hijab ta fara neman rigar da zata saka. Daga ita sai daurin kirji Hamza ya turo kofar. Cikinta har kullewa yaso yi don kaduwar da tayi. Yana lura da yadda ta kidime ya matso daf da ita. Zuhra idanu kamar su fado kasa don tsoro tace dama riga zan saka na fito. Yace Cutie ba na hanaki daurin kirji ba. Da sauri tace yanzu zan kwance nasa kayan bacci. Don Allah ka tafi zan zo. Bai kulata ba sai ma hugging dinta da yayi yana murmushi. Kamshi kike yi maidadi Cutie. Ita dai kasa magana tayi jin yadda yake shafa kanta. A hankali ya saketa ya bude inda kayan baccinta suke. Wata riga ya dauko ruwan madara wadda da alama sabuwa ce ya warwareta. Bazata wuce mata gwiwa ba amma tamkar net haka take tasha ado sosai. Tana kallo ya karasa gaban mirror ya fesheta da turaruka sannan ya ajiye a kan gado. Wani irin kallo yake bin Zuhra dashi yace saka hijab muyi sallah. Idan baka kalli bakinta ba bazaka ji yadda tace nayi sallah ba can a kasan makoshi. Yace wannan nafila ce da zamuyi kafin mu kwanta. Abin sallah ya shimfida a gaban nata ya jasu sallah raka'a biyu. Bayan sun idar ya dade yana musu addua sannan yayi mata alama da hannu. Dan matsawa tayi kusa dashi ya dora hannunsa a kanta ya karanto addu'a kamar yadda yazo a sunnah. Rigar da ya ajiye ya dauko sannan ya kama hannunta ya kashe fitila suka tafi dakinsa. Kamar wani sabon mutum haka take ganinsa. Sonsa ne yake karuwa a zuciyarta amma ta kasa sakin jiki. Sai da ya kaita har bakin gado sannan ya kama hijab din ya cire mata. Duk abinda yake yi idanunsa a kanta yana yi mata murmushi. Rigar hannunsa ya saka mata sannan a hankali ya zare zanin ta kasa. Bin jikinta yiya da kallo ita kuwa kamar walkiya don sauri ta haye gado ta kudundune jikinta. Dariya yake yi yana kallonta ke da kika ce zaki min duk abinda nake so, ai ban fara ba ma. Zuhra ta turo baki cikin shagwaba Ya Hamza haka ake soyayyar,ka sa sai kunyarka nake ji. Sai da ya kashe fitila ya zauna kusa da ita yace wannan sunansa sharar fage yanzu za'a fara karatun sosai. Tana ji ya kwantar da ita rub da ciki, tashi take sonyi domin bata san abinda zaiyi mata ba. Ga mamakinta hannuwansa yasa a bayanta ya fara yi mata tausa tun daga kafada har karshen bayanta. Nasan kin gaji sosai just relax ki huta. Yau karatun bazaiyi nisa ba naga duk kin tsorata. A hankali ta saki jikinta tana dan murmushi. Bata taba kawowa a ranta rana irin wannan zata taba zuwa tsakaninsu ba. Ya kusa minti goma yana yi mata tausa yaji tayi shiru. Cutie, ya kira sunanta a hankali. Itama a hankalin tace Ya Hamza. Gyara mata kwanciya yayi ya dora kansa a kirjinta tare da kankameta a jikinsa. Tace Ya Hamza kunyarka nake ji sosai. Hannuwansu ya hada wuri daya yace zan rage miki ita a hankali ne Cutie. Yanzu bacci nake so kiyi saboda kin yini kina aiki. Kansa ta shafa a hankali tace a haka zanyi baccin da kanka a kirjina kamar wani baby? Dagowa yayi duk da duhun dakin ya saita fuskarsa da tata. Cutie na fada miki miji tamkar baby ake son matarsa ta rinka bashi kulawa. Gyada kanta tayi tace to sai da safe. Yace babu goodnight kiss? Rufe ido tayi ita kam yau Ya Hamza ya hanata sakewa. Idonta a rufe taji lips dinsa akan nata. A hankali yasa ta saki jikinta har suka dade a haka. Daga baya ya kwantar da ita a jikinsa a kunnenta yace love you Cutie, yanzu da nasan wace ce ke bana fata Allah Ya kawo abinda zai raba mu . Kanta na kirjinsa tace love you too Ya Hamza tana mai jindadin abinda ya fada . A haka bacci maidadi ya daukesu. Hamza yana tunanin ranar da zai mayar da ita cikakkiyar amarya. A hankali yake so ta gama sakin jiki dashi sannan su gina soyayyarsu cikin aminci. Ita ta fara tashi da asuba Hamza na rike da ita kamar zai mayar da ita ciki. Murmushi tayi cike da farincikin Allah Ya amsa adduarta Ya daidaita tsakaninta da mijinta. Kwantawa ta sakeyi kusa dashi ta kama gashinta ta soma zirawa a cikin kunnensa. Sau biyu yana kawo hannu idonsa a rufe sai tayi saurin matsawa. A na ukun janyota yayi ta fado jikinsa. Ya dan bude idanu, Cutie tsokana ko? Dariya tayi ka tashi asuba tayi. Ya sake rufe ido ba fa haka ake tashin miji daga bacci ba. Ina koya miki karatu kin kasa....bakinta ta hada da nasa tayi kissing yaji wani abu na masa yawo a jiki. Kafin ya ankara ta tashi ta fice daga dakin da gudu. Shi kam ya dace da mata ya fada a ransa sannan ya tafi yayi alwala. Yana dawowa daga masallaci suka hadu da ita tana saukowa zata kitchen. Kada ma ki karasa saukowa ya fada yana hawa benen. Ta dan bata fuska Ya Hamza ina da aiki da yawa fa. Ya kwaikwayi muryarta Cutie baki da aikin da ya wuce nawa, ni kuma bacci nake so mu koma. Daukarta yayi tana dariya ya koma da ita. Tala dake makale a bakin bene basu ganta ba tace Allah Yasa Hajiya Izzatu sai badi zata dawo gidan nan. ***** Karfe takwas na safe jirgin su Izzatu ya sauka a filin jirgi na Mal Aminu Kano. Ta kira wayar Hamza yafi sau ashirin bai sani ba. Wayar tana falonsa tun dare yasa ta a chaji. Ranta a bace domin tayi zaton zai zo tararta a airport din. Gajiya tayi ta nemi taxi ta daukota har gida. Koda maigadi ya bude mata kofa sai da jinin nasa ya dan haura. Shikenan zasu dena jindadi yadda suka saba. Tala ma tsoro ne ya bayyana a fuskarta da suka hada ido da ita. Ta wayance tana tambayarta lafiya ta dawo da sassafe? Izzatu tace Babyna bai fada miki kiyi min girki ba zan dawo yau da safe? Anyway ki kai min jakata daki tana bakin kofa. Tana magana tana hawa sama. Tala tace yau mun shiga uku..... Dakinta ta fara zuwa tayi wanka aka sha turare da kwalliya sannan tasa wata doguwar riga iya gwiwa. Surprising din Hamza zata yi. Tasan kila makara yayi shiyasa baije daukanta a airport ba. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #64 Batul Mamman(Mrs)# Tunda Hamza ya kai Zuhra daki akan gado ya ajiyeta ya soma bubbuga hannu, wai yarinyar nan haka kike da nauyi dama. Zuhra ta turo baki ni bani da nauyi. Yadda bakinta yayi ya bashi sha'awa ya zauna kusa da ita yasa dan yatsansa yana shafa bakin. Ina son dan bakin nan naki na rashin kunya Cutie mai nauyin buhun shinkafa biyu. Zuhra ta hade fuska kamar zata yi kuka ta sauke kafafunta daga kan gadon. Ni dakina zan tafi, dama dauko ni kayi don ka tsokaneni. Kuma yau da daurin kirji zan wuni a gidan nan. Yayi murmushi Allah Ya baki sa'a da yin daurin kirjin nan. Idan suka koma suka kwanta kamar na wata tsohuwa aure zan kara yi. Zuhra tace suwaye zasu kwanta? Abinda kike daurewa da zani mana ko na nuna miki su? Sunkunyar da kanta tayi tana murmushi don ta gane abinda yake nufi. Shima murmushi yayi ya tashi ya cire rigarsa saboda tun asuba yasa ake kashe inji yanzu. Garin sai yayi zafi kamar za'ayi ruwa dama wasu garuruwan na kusa da Kano sun fara samun ruwa. Tana ji tana gani ya kwance mata zanin da ta daura akan 'yar rigar jikinta tare da cire mata mayafi. Yace to mu kwanta da gaske bacci nake ji. Jiyan nan....sai yayi shiru yana gyara kwanciya a kusa da ita. Ya Hamza me ya faru jiyan? Babu komai Cutie kawai dai ki shirya yau ba irin jiya bane. Danyi min bayani meye bambancin jiya da kuma yau da kace na shirya. Bai bata amsa ba sai kallo da yake binta dashi. Zuhra tayi masa kyau sosai ga rigar jikinta..... Kula tayi da abinda yake kallo taji kunya. Rufe jikinta tayi tana cewa Ya Hamza zan dena zuwa dakinka indai haka zaka rinka kallo na. Yace to na dena amma dan cire bargon kinga ai babu laifi idan na kalli matata. Dariya tayi ta sake kankame jikinta. Tashi yayi ya koma can inda kafafunta suke ya daga bargon ya turo kansa. Dariya Zuhra takeyi tana cewa yayi hakuri. Bakiga komai ba yarinya ya fada lokacin da ya fito da kansa a daidai kirjinta da yake dukan uku uku. Runtse idonta tayi saboda yadda take jin kunyarsa. Gabadaya ya danneta sannan ya zubawa fuskarta idanu. A hankali ya fara kissing ko'ina a fuskar har ya kai bakinta. Jira kawai take yayi mata abinda ta fara sabawa dashi sai taji ya tsaya tana jin saukar numfashinsa a fuskarta. Cutie kice kin yafe min duk abinda nayi miki a baya. Ido a rufe tace Ya Hamza na yafe nima ka yafe min. Ya sake matso da fuskarsa, kin yafe har da na kusa cutar kaina nace zanyiwa Inuwa tayinki? Hakan ya bata dariya ta bude ido a hankali. Har shi na yafe Ya Hamza. Ya lumshe ido to tabbatar min da hakan. Bata san a inda ta sami kwarin gwiwar daga hannuwanta ta sauko da fuskarsa sosai ta hada bakinta da nasa. Shiru bata kara komai akan hakan ba yace naga alama karatun nan bai gama shiga kanki ba. Kinga yadda ake yi.....daga nan ya fara nuna mata sabon salon da bata san akwai shi ba. ****** Da wata irin tafiyar jan hankali Izzatu ta shigo falon Hamza. Da tayi niyar kiran sunansa sai ta fasa kada ta bata surprise dinta. A hankali ta bude kofar dakin ko bacci yake yi kada ya tashi sai ta kwanta a kusa dashi. Labulen ta daga ta dan tura kai......tamkar wadda taga wani mugun dodo haka tayi saurin sakin labulen ta koma da baya a hankali. Dakinta ta tafi kai tsaye ta wuce bandaki ta wanke fuskarta da sabulu. Ta fito ta tsaya a gaban mudubi tana mayar da numfashi a wahale. Lallai Izzatu, yau da abinda kika gani gaske ne kila sai kin shiga coma. Shine abinda ta fada a zuciyarta sannan ta sake sabuwar kwalliya ta fita. Tasan ba wani abu bane dama ance abinda kafi so ko kafi tsana wani lokacin sai kaga yana maka gizo. In ba haka ba me zaisa taga hannuwan mace sun rungume mijinta Hamza suna kissing juna irin haka. ******* Zuhra ke kokawa da Hamza ya dage sai ta cire rigarta tasha iska. Kamar tayi kuka tace Ya Hamza, bama Yaya ba, Baba Hamza kayi hakuri mana. Yace ni gaskiya Inna Fatima bazan hakura ba. A haka kike son nan da wata taran na kaiki asibiti haihuwa. Yana jan rigarta itama tana ja suna ta dariya. ***** Sake komawa dakin nasa Izzatu tayi sai dai wannan karon tun daga falon take jin dariyar Hamza da wata mace. Zuciyarta ce tayi wani mugun bugu kamar zata ballo kirjinta. A fusace ta banka kofar dakin ta ga wace karuwar Hamza ya kawo gidansa. Karar kofar ya mayar da hankalin Hamza da Zuhra kofar dakin. Izzatu ce ta shigo tamkar wata zakanya idanunta sun kankance babu abinda ake gani sai tsantsan bacin rai. Shima Hamzan a fusace ya tashi da ya ganta. Shaf ya manta tace yau zata dawo amma duk da haka hakan bai zama dalilin da zata shigo masa daki babu sallama ba. Ita kuwa Zuhra bargo taja ta suturta jikinta saboda rigarta ba mai kauri bace. Cikin masifa Izzatu tace Hamza me zan gani haka? Karuwa har cikin gidan aure, har kan matrimonial bed(gadon aure)din mu. Daurw fuska yayi shima yana fadan...Izzy a wane dalili zaki shigo min daki babu sallama. Heyyyy! aa'a! maza har abada bakwa rabo da abin mamaki. Na kamaka da karuwar kace zaka min wa'azin sallama. To ban karba ba sai ka kama wata hanyar borin kunyar ba wannan ba. Kallonta ta mayar ga Zuhra ta daka mata tsawa ke kuma tsohuwar 'yar bariki wallahi ni da kike gani bani da mutumci akan mijina. Sai kinyi nadamar hada jiki dashi. Zaki sakko daga kan gadon nan ko sai nazo na babballaki? A gigice Zuhra tayi yunkurin sauka daga gadon tana lullube da bargo hakan ya jawo ta bige gwiwarta da gefen gadon, tana tashi ta soma dingisa kafa. Hamza yayi saurin tareta, Cutie koma kiyi zamanki let me handle this issue. Ya nuna kofa Izzy wuce muje dakinki we need to talk. Ko sauraronsa bata yi ba ta taho gaban gadon ta kwaye bargon da Zuhra ke ta rufe jikinta dashi. Idonta cike da hawaye tace Hamza buduwar ka samo shiyasa naga har wani jan kafa take yi. Zuhra ta rasa inda zata saka kanta saboda wannan tozarci da Izzatu tayi mata. Bayan Hamza taje ta tsaya saboda tasan ko kadan bai kamata Izzatu ta ganta da wannan shigar ba. Gadon Izzatu ta rinka dubawa Hamza yana mata fada ko daga kai bata yi ba. Ka barni na duba shaidar cin amanar da kayi min da wannan 'yar isakar da take son nuna min ita budurwa ce. Hamza yace Izzy idan baki nutsu kin fita daga dakin nan ba wallahi zaki ga baccin rai. Jajayen idanunta ta dago tana kallonsa, bacin rai har ya wuce wannan munafukar karuwar da ka dauko daga bakin titi. Hannu ta kai zata janyo Zuhra dake zubar da hawaye a bayan Hamza ya rike hannun tare da zagba mata mari. Shima nasa idon bacin rai yasa sunyi ja yace kada ki sake kira min mata karuwa wallahi. Izzatu ta dafe kunci ni ka mara Hamza??? To na fada din karuwa matsiyaci....wani wawan marin ya bata wanda yafi na farko. I am warning you Izzy ki kiyaye bakinki. Zuhra matata ce ba karuwa ba. Magana Izzatu taso yi sai dai kalmarsa ta karshe tasa ta hadiye maganar tare da kukan da take yi. Kunnenta ta dan buga sannan tace me kace Hamza, Zuhra matarka ce? Wannan karuwar ce Zuhra? Ta fada tana nuna ta. Hamza yace idan ba ita ba ina da wata matar ne bayan ke? Haka kawai kin shigo kina ta bala'i kamar wata mahaukaciya. Ki fice daga dakin nan kafin na saba miki. Sai a lokacin Izzatu ta karewa Zuhra kallo. Ko da wasa bata ganeta ba da farko saboda ba haka tasan Zuhra ba. Jikinta a sanyaye tayi zaman 'yan bori akan gadon. Ta dago kai a hankali tana kallon Zuhra dake labe a bayan Hamza. Tsakanina da kai Hamza bazan taba yafe maka ba. Ni Izzatu Sunusi zaka yiwa irin wannan cin fuskar? Ka kasheni kuma bazan yafe maka ba. Har gara ace sophisticated prostitute( hadaddiyar karuwa) ka dauko sai nasan cewa gazawa nayi shiyasa ka nemi wadda ta fini amma ZUHRA, HAMZA KWANA DA ZUHRA yana nufin mummunan kaskanci gareni a matsayin mace. Maganar Izzy ta batawa Hamza rai sosai yace kinga for the last time ki fita daga dakin nan. Kina iya daukan tarayyata da Zuhra duk abinda yazo ranki amma ki sani matata ce ta sunnah wadda all thanks to your stupidity na aureta, kuma nake alfahari da auren. Now GET OUT. Cikin sanyin jiki Izzatu ta tashi jiri na dibarta ta kalli Zuhra da gabanta ke faduwa. Nayi miki alkawarin barin gidan nan kamar yadda nayi sanadin shigowarki cikinsa. Sai kinyi dana sanin cin amanata kika kawo kanka ga mijina. Nasan ba laifinsa bane Hamza baya iya dadewa babu mace shine kika yi amfani da wannan kika bashi kanki. Bakiyi nasara ba Zuhra sai kin koma inda kika fito domin ni ban daukeki a matsayin mace ba ma. Hannun Izzatu Hamza ya kama zai fitar da ita ta doke hannun, kada kayi tunanin zan sake bari ka tabani bayan ka taba waccan kazantar. Fita tayi daga dakin babu ko digon hawaye a idonta. Bakin cikin da take ji yafi karfin kuka. Hamza ya juyo ga Zuhra ya rungumeta, sai a lokacin ta soma kuka da sauti. Bayanta yake shafawa kiyi hakuri Cutie. Duk laifina ne da sakaci har ya janyo haka. In sha Allah Izzatu sai ta koyi mutuntaki a matsayin matata. I love you so much. Rabon Zuhra da ganin wulakanci tun ranar da aka mata April fool. Tayi kusan minti goma tana kuka Hamza na aikin rarrashi. Daga baya ta sake shi ta nemi zaninta ta daura. Hannunta ya riko Cutie ina zaki kuma. Muryarta a dashe tace dakina. Zama yayi ya dorata a cinyarsa. Ki zauna anan kema kinsan bazan iya barinki ki fita a haka ba. Tashi nayi miki wanka....murmushi tayi ta dora kanta a kafadarsa ni bazan yarda kayi min wanka ba. Shima murmushi yayi zaki zo da kanki ne kuma lokacin nima yanga zanyi miki. Rungumeta yayi a jikinsa yana ji tana ajiyar zuciya. A hankali ta tashi bari naje nayi wanka. Ya dan ja hancinta please Cutie na kada kisa komai a ranki kinji ko. Komai zai daidaita in sha Allah zanyiwa Izzy magana. Murmushin yake kawai Zuhra tayi ta fita. Tana zuwa falo Hamza ya tashi shima wankan yake shirin yi ya jiyo ihunta da salati. A guje ya fito ya ganta a tsaye jiki na bari. Ya Hamza kaga jini.....jini ne digo digo a falon har bakin kofa. Da hanzari suka bi jinin har kofar dakin Izzatu. A kulle Hamza yaji kofar ya soma bugawa yana kiranta amma shiru. Duk ya rude ga Zuhra tana kuka. Sai da ya gaji da bugun ga kofar da karfin tsiya ya tuna yana da spare key. Daukowa yaje yayi ya bude kofar dakin nata. Kwance suka tarar da ita a sume ga jini yana bin kafarta. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #65 Batul Mamman(Mrs)# Gabadayansu ba karamin tashin hankali suka shiga ba. Da sauri Hamza ya koma dakinsa ya dauko wata doguwar riga ya sakata gaba a baya ya dauko Izzatu. Zuhra ma hijab ta burma ta bi bayanshi da gudu da wani mayafi da ta gani a dakin Izzatun domin a suturta mata jiki. A kasa suka tarar da Tala da Nana zata hada mata tea. Idanunta ne suka bi Hamza dauke da Izzatu ga jini a jikinta. Zuhra tace mata ta kula da gidan da yara zasu je asibiti. Gudu Hamza ya rinka yi cikin dan lokaci suka isa asibitin. Maaikatan asibitin suka yi masa jagora zuwa emergency inda aka bukaci su tsaya a waje shi da Zuhra. Haka suka rinka kai kawo a wurin sai gashi an turo Izzatu akan gado an wuce dakin operation da ita. Hamza ya tambayi wani cikin likitocin menene ya sameta. Likitan yace bari mu fito zamu yi maka bayani. Ku dai kuci gaba da addu'a. Sun kusa awa biyu a corridor din babu wanda yake iya yiwa wani magana. Kowa da abinda yake sakawa da warwarewa a zuciyarsa. Zuhra ce tayi karfin halin cewa Hamza ko zai yi waya gida ya sanar dasu Hajiya, jikinsa duk a sanyaye yace ya barota a gida. Itama Zuhra tace bata dauko tata wayar ba. Suna magana likitan ya fito yace Hamza ya biyoshi office. Ga mamakin Zuhra sai taji ya kamo hannunta suka tafi tare. Ko zama basu yi ba Hamza yace don Allah ka fada min halin da take ciki. Likitan yace to ka zauna mana, Zuhra ya zaunar tare da rike mata hannu gam. Likita yace kaine mijinta ko? Hamza ya gyada kai. Ya cigaba da cewa to sai dai kuyi hakuri bamu iya saving din abinda ke cikinta ba. Bangane ba doctor? Kana nufin tana da ciki ne. Kwarai kuwa don har ya kusa wata biyu. To matsalar da aka samu shine mahaifar bata da kwari kwata kwata. Don ita da abinda ke cikin tare suka fara fitowa. A gigice Hamza yace fitowa kamar yaya? Ina nufin bari tayi wanda har mahaifarta ta fara fitowa saboda rashin kwarinta. Shiyasa muka ga dole muyi mata virginal hysterectomy saboda ceto rayuwarta. Kokari Hamza yake kada ya rasa nutsuwarsa yace kayi min bayani a yaren da zan gane. A wane hali Izzatu take? Likita yace yanzu tana bacci saboda anyi mata allurar anasiziya. In sha Allah nan da kamar awa daya zata farfado. Abinda nake nufi da hysterectomy shine mun cire mata mahaifa saboda ba karamin lalacewa tayi ba. Wata muguwar faduwar gaba Hamza yaji wanda hakan yasa shima ya zauna. Zuhra ta sake kankame hannunsa saboda firgici. Yace doctor kana nufin yanzu bazata sake haihuwa ba. Haka nake nufi amma don Allah kayi hakuri bamu fara sanar da kai ba kafin mu aiwatar da nufinmu. Yanayin da take ciki ne baya bukatar bata lokaci. Idan ta tashi ita tafi cancanta da ta fadi maganin da tasha ya illata mahaifar haka. Bazamu iya yanke komai ba sai munji daga gareta. Tashi likitan yayi ya barsu a office din bayan ya gama yi musu bayani. Yana fita Zuhra ta rungume Hamza tana kuka. Kayi hakuri Ya Hamza duk laifina ne. Ganina ne ya bata mata rai har hakan ta faru. Da hannunsa ya share mata hawaye...ki dena fadin haka Cutie kaddara ce da bata wuce kowa. Amma shima a kasan zuciyarsa gani yake kamar laifinsa ne tunda Izzatu ta fada masa ranar zata dawo, sai abin ya zama kamar cin fuska ma. Sabon dakin da aka kai Izzatu suka je. A nan ya bar Zuhra yace zaije gida ya fada musu tunda baizo da waya ba. ****** Daga Hajiya har Mama babu wanda labarin yayi masa dadi. Duk sun tausayawa Izzatu. Mama tace watan cikin nawa? Ni ban san dashi ba Hamza ya bata amsa. Sai a lokacin ta kula da rigarsa tace ya gyara ta. Kunu da kayan tea suka hada ya daukesu ita da Hajiya da Adabiyya ya kaisu asibitin sannan ya dauko Zuhra suka tafi gida. Har lokacin Izzatu bata farfado ba. Saboda yanayin da suka fita maigadi da Tala suna ganinsu suka fara tambayar ya mai jiki. Zuhra ce take iya basu amsa tana cewa da sauki. Wanka duk suka yi sannan Zuhra ta sauko ta hada masa abinci. Da kyar ta samu yasha tea yace zai koma asibitin. Damuwa ce tayi masa yawa yana tambayar kansa ta ina zai samo kudin asibitin Izzatu? Bashi da sauran kadarar da zai sayar sai wani fili da ya siya a Kumo wanda yanzu kafin a samu mai siya ma aikine guda. Shi ko irin budewa yara account dinnan bai taba tunanin yi ba saboda basu hango rana irin wannan da zasu fuskanci matsin rayuwa ba. Zuhra na kallon yadda ya zurfafa a tunani ta dan dafa kafadarsa. Ya Hamza kaine fa kake cewa kaddara ce abinda ya faru. Don Allah kayi hakuri. Idan ka bari damuwa tayi maka yawa waye zai rarrasheta idan ta farfado? Murya a sanyaye yace babbar damuwata yanzu inda zan samo kudin asibitin Izzy. Kinsan halin da nake ciki bansan inda zan samo kudin ba indai ba kudin kamfani zan dauka ba. Zuhra tace idan ka dauka aikinku zai sami rauni. Kuma kace har kun kusa kammala daya. Ta mike tsaye ina zuwa.... Bata dade ba ta dawo da wata karamar leda mai kyau a hannunta. A tafin hannun Hamza ta ajiye ledar yace koma meye ki rike kayanki zansan yadda nayi na sami kudin. Ko bashi ne sai na nema. Idonta fal hawaye tace yanzu ka gwammace ka nemi bashi akan ka karbi abinda kake da iko dashi? Wannan abin da na baka kai ka siya fa? Idan ka karba ai ba yana nuna gazawarka a matsayin namiji bane. Jarabawace Allah Ya dora maka. A hankali ya bude ledar ya ciro wata yar roba mai murfi. Sarka ce da dankunne da zobe na gwal a ciki. Saurin rufewa yayi ya dora mata a cinyarta. Cutie ki dauke kayanki bazan sayar miki da sarkarki ba....abinda ya kasa fada shine ko pant bai siya mata ba a lefenta. Komai Alhaji ne yayi. Hannuwanta biyu tasa ta rike kumatunsa tana kallon fuskarsa mai dauke da tsantsar rashin kwanciyar hankali. Tunda nake ban taba saka gwal ba a rayuwata don an sayar da wanan bazanji komai ba. Duk irin wadannan abubuwan dama ai saboda rana irin yau ake tanadin su. Ni a abinda su Baba suka koya min wannan shine aure. Taimakon juna a lokacin bukata batare da mun fita waje mun tonawa kanmu asiri ba. Su Alhaji ne baka son sanarwa halin da kake ciki to ni din da na sani ka bani damar taimakonka mana. Sarkar da hannunta ya hada ya rike sosai sai kawai taga hawaye ya fito daga idonsa. Lallai rayuwa bata da tabbas, babu wani yanayi da bawa zai tsinci kansa yace wannan yanayin zai tabbata a ciki har ranar busa kaho. Yau kana da arziki gobe waninka ne. Wa zai taba tunanin akwai ranar da Architect Hamza Nasir Hamza zai karbi taimako a hannun Fatima Bashir? Yarinyar da ko certificate din shaidar tayi secondary school bata dashi,ga kazanta ga rashin wayewa. Ikon Allah kenan, kada ka taba raina bawa domin baka san abinda Allah yayi masa na arziki ba. Arziki kuwa ko da ba na kudi bane. Hawayen da Hamza yake yi ya karyar mata da zuciya ta soma kuka. Haka suka rungume juna na tsawon lokaci. Daga baya Hamza yace ta tashi su koma asibiti tace a'a yaje kasuwa ba'a rasa masu bude shago ranar lahadi ya sayar. Ita kuma zata kara yin saka zuwa la'asar ko bai dawo ba zata yi girki ta tafi asibitin da kanta. Sai da ya kwashe kusan minti biyar yana kissing dinta sannan ya fita. Bai san da yaya zai gode mata ba. Tunda ya shiga mota har ya isa kasuwar ALHAMDULILLAH yake ta nanatawa saboda godiya ga Allah da Ya azurta shi da mace tagari a lokacin da rayuwarsa take tsaka da rushewa. A dalilin mugun tashin da dollar tayi wanda muke ta addu'a Allah Ya yafe mana Ya kawo mana sassauci sai da Hamza ya sami dubu dari uku da tamanin da hudu a matsayin kudin sarka, dankunne da zobe. A haka ma don mutanen sun kula kamar a matse yake da ya sayar. A hanyarsa ta tsallaka titi ya koma motarsa yaga wata tsohuwa tukuf itama ta rasa yadda zatayi ta tsallaka. Da a lokacin da yake Hamzansa ne mijin Izzatu ita kadai baya jin zai iya yadda hannunsa ya taba matar. Amma yanzu ya koyi darasin zaman duniya. Hannun matar ya riko tana tafiya da kyar har ya tsallakar da ita titi. Godiya ta rinka yi masa tare da addua. Harda dan kukanta tace ba don kai ba sai nayi kusan minti shabiyar ina kokarin tsallaka titin nan. Magani na karbowa dana yana fama da lalurar asma. Ta dauki wata leda da magani ta nuna masa. Hamza ya tausaya mata yace baki da wasu yaran ko jikoki da zasu je miki? Tayi murmushi, shi kadai ne dani. Bayan shekaru shabakwai sai yanzu matarsa take da tsohon ciki. Idan abin ya tashi ita take zuwa amma yanzu bazata iya doguwar tafiya ba. Yana ganin kansa a wani yanayi ga wadanda suka fishi. Kudin aljihunsa ya shafa ya sa hannu ya kirga dubu goma ya bawa matar. Hannu na rawa ta karba tana ta kuka...Allah Ya albarkaci rayuwarka data iyalinka, Allah Ya rabaka da masifun zamani, Allah Ya baka arziki na halali daga inda baka taba tsammani ba. Yaro nagode, nagode. Hamza na tsaye har ta shiga adaidaita sahu sannan shima ya tafi zuciyarsa kamar an cire masa wani nauyi. Hakika sadaka maganin masifa ce kuma waraka daga bacin rai. Asibitin ya koma ya tarar Izzatu ta farfado. Raliya ya kira a waya ya sanar da ita halin da Izzatu ke ciki. Cikin kidima tace gobe zata taho in sha Allah. Tana ajiye wayar ta kira kanwarta Larai ta fada mata asibitin da suke. Tsananin bacin rai da kishi yasa Izzatu kuka tunda ta farfado. Yanayin da taga Zuhra da Hamzanta shi kadai yake mata yawo a ka tunda ta bude ido. Su Mama kuwa sai tausayinta suke yi a nasu tunanin bakincikin bari da cire mata mahaifa da akayi take yi. Cike da tausayi Hamza yake mata sannu amma ko kallonsa taki yi. Su Mama sai suka dauke kai kamar basu kula da abinda suke yi ba. Adabiyya tace Yaya ina Anti Zuhra? Yace zata taho girki yasa bamu fito tare ba. Basu dade ba kuwa sai gata da kwandon abinci. Bata tashi daga kan sakarta ba sai da tayi mai yawa ta yadda abin da ya rage mata saura kadan. Itama ko kallo bata ishe Izzatu ba duk da halin ciwon da take ciki. Sauran 'yan uwan Hamza suma duk sun zo. Zuhra ma ta kira Baba ta fada masa Izzatu na asibiti yace zasu zo washegari tare da Umma. Anti Larai kanwar Raliya tazo tare suka karasa yinin sai dai ta baro maigidanta babu lafiya saboda haka bazata iya kwana a asibitin ba. Dole aka yanke shawarar Adabiyya da Zuhra su kwana da Izzatu. Ranta inyayi dubu ya baci amma ko tashi bazata iya yi ba shiyasa dole ta hakura. Shabiyu saura na dare su Zuhra suka fita suka bashi wuri ya dan zauna wurinta. Sai lallabata yake tana kuka ita bazata zauna da wadda tayi sanadiyar zubar mata da ciki ba. Da kyar ya lallabata yace gobe shi zai kwana. Haka suka rabu ranta a bace. Itama Zuhra yayi mata sallama sannan ya tafi gida. ******** Wasu matasa ne su uku duk da bakaken kaya harda abin rufe fuska suka shigo cikin kauyen da gudu da cikon na hudun a kafadar wanda yafi sauran girma. A kofar wani katon family house suka ajiye na kafadar wanda yake ta zubar da jini sakamakon harbinsa da aka yi a cinya suka gudu. Da yake tsakar dare ne babu wanda ya kula dasu. Sai can wasu maza biyu suka zo wucewa a buge suka ga mutum a kwance a kasa. Da har zasu gudu sai daya ya haska shi da touchlight, da sauri ya karaso giyar da yasha ta fara barinsa yace sa dayan kazo mu taimaka masa Felix ne kanin Mr Oscar miloniya. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: AL'ADUN WASU #67 Batul Mamman(Mrs)# Cikin hanzari suka burkito fuskarshi suna ganinshi duk suka razana "mr.oscar yau kaine ahaka? Afili hakkin hamza yafito,mr.oscar yana kuka yanacewa kutaimakeni na cuci hamza mutuwa zanyi wayyo Allah na. Nidai nawa tunanin kenan,kekuma wannene naki Gabadayansu ba karamin tashin hankali suka shiga ba. Da sauri Hamza ya koma dakinsa ya dauko wata doguwar riga ya sakata gaba a baya ya dauko Izzatu. Zuhra ma hijab ta burma ta bi bayanshi da gudu da wani mayafi da ta gani a dakin Izzatun domin a suturta mata jiki. A kasa suka tarar da Tala da Nana zata hada mata tea. Idanunta ne suka bi Hamza dauke da Izzatu ga jini a jikinta. Zuhra tace mata ta kula da gidan da yara zasu je asibiti. Gudu Hamza ya rinka yi cikin dan lokaci suka isa asibitin. Maaikatan asibitin suka yi masa jagora zuwa emergency inda aka bukaci su tsaya a waje shi da Zuhra. Haka suka rinka kai kawo a wurin sai gashi an turo Izzatu akan gado an wuce dakin operation da ita. Hamza ya tambayi wani cikin likitocin menene ya sameta. Likitan yace bari mu fito zamu yi maka bayani. Ku dai kuci gaba da addu'a. Sun kusa awa biyu a corridor din babu wanda yake iya yiwa wani magana. Kowa da abinda yake sakawa da warwarewa a zuciyarsa. Zuhra ce tayi karfin halin cewa Hamza ko zai yi waya gida ya sanar dasu Hajiya, jikinsa duk a sanyaye yace ya barota a gida. Itama Zuhra tace bata dauko tata wayar ba. Suna magana likitan ya fito yace Hamza ya biyoshi office. Ga mamakin Zuhra sai taji ya kamo hannunta suka tafi tare. Ko zama basu yi ba Hamza yace don Allah ka fada min halin da take ciki. Likitan yace to ka zauna mana, Zuhra ya zaunar tare da rike mata hannu gam. Likita yace kaine mijinta ko? Hamza ya gyada kai. Ya cigaba da cewa to sai dai kuyi hakuri bamu iya saving din abinda ke cikinta ba. Bangane ba doctor? Kana nufin tana da ciki ne. Kwarai kuwa don har ya kusa wata biyu. To matsalar da aka samu shine mahaifar bata da kwari kwata kwata. Don ita da abinda ke cikin tare suka fara fitowa. A gigice Hamza yace fitowa kamar yaya? Ina nufin bari tayi wanda har mahaifarta ta fara fitowa saboda rashin kwarinta. Shiyasa muka ga dole muyi mata virginal hysterectomy saboda ceto rayuwarta. Kokari Hamza yake kada ya rasa nutsuwarsa yace kayi min bayani a yaren da zan gane. A wane hali Izzatu take? Likita yace yanzu tana bacci saboda anyi mata allurar anasiziya. In sha Allah nan da kamar awa daya zata farfado. Abinda nake nufi da hysterectomy shine mun cire mata mahaifa saboda ba karamin lalacewa tayi ba. Wata muguwar faduwar gaba Hamza yaji wanda hakan yasa shima ya zauna. Zuhra ta sake kankame hannunsa saboda firgici. Yace doctor kana nufin yanzu bazata sake haihuwa ba. Haka nake nufi amma don Allah kayi hakuri bamu fara sanar da kai ba kafin mu aiwatar da nufinmu. Yanayin da take ciki ne baya bukatar bata lokaci. Idan ta tashi ita tafi cancanta da ta fadi maganin da tasha ya illata mahaifar haka. Bazamu iya yanke komai ba sai munji daga gareta. Tashi likitan yayi ya barsu a office din bayan ya gama yi musu bayani. Yana fita Zuhra ta rungume Hamza tana kuka. Kayi hakuri Ya Hamza duk laifina ne. Ganina ne ya bata mata rai har hakan ta faru. Da hannunsa ya share mata hawaye...ki dena fadin haka Cutie kaddara ce da bata wuce kowa. Amma shima a kasan zuciyarsa gani yake kamar laifinsa ne tunda Izzatu ta fada masa ranar zata dawo, sai abin ya zama kamar cin fuska ma. Sabon dakin da aka kai Izzatu suka je. A nan ya bar Zuhra yace zaije gida ya fada musu tunda baizo da waya ba. ****** Daga Hajiya har Mama babu wanda labarin yayi masa dadi. Duk sun tausayawa Izzatu. Mama tace watan cikin nawa? Ni ban san dashi ba Hamza ya bata amsa. Sai a lokacin ta kula da rigarsa tace ya gyara ta. Kunu da kayan tea suka hada ya daukesu ita da Hajiya da Adabiyya ya kaisu asibitin sannan ya dauko Zuhra suka tafi gida. Har lokacin Izzatu bata farfado ba. Saboda yanayin da suka fita maigadi da Tala suna ganinsu suka fara tambayar ya mai jiki. Zuhra ce take iya basu amsa tana cewa da sauki. Wanka duk suka yi sannan Zuhra ta sauko ta hada masa abinci. Da kyar ta samu yasha tea yace zai koma asibitin. Damuwa ce tayi masa yawa yana tambayar kansa ta ina zai samo kudin asibitin Izzatu? Bashi da sauran kadarar da zai sayar sai wani fili da ya siya a Kumo wanda yanzu kafin a samu mai siya ma aikine guda. Shi ko irin budewa yara account dinnan bai taba tunanin yi ba saboda basu hango rana irin wannan da zasu fuskanci matsin rayuwa ba. Zuhra na kallon yadda ya zurfafa a tunani ta dan dafa kafadarsa. Ya Hamza kaine fa kake cewa kaddara ce abinda ya faru. Don Allah kayi hakuri. Idan ka bari damuwa tayi maka yawa waye zai rarrasheta idan ta farfado? Murya a sanyaye yace babbar damuwata yanzu inda zan samo kudin asibitin Izzy. Kinsan halin da nake ciki bansan inda zan samo kudin ba indai ba kudin kamfani zan dauka ba. Zuhra tace idan ka dauka aikinku zai sami rauni. Kuma kace har kun kusa kammala daya. Ta mike tsaye ina zuwa.... Bata dade ba ta dawo da wata karamar leda mai kyau a hannunta. A tafin hannun Hamza ta ajiye ledar yace koma meye ki rike kayanki zansan yadda nayi na sami kudin. Ko bashi ne sai na nema. Idonta fal hawaye tace yanzu ka gwammace ka nemi bashi akan ka karbi abinda kake da iko dashi? Wannan abin da na baka kai ka siya fa? Idan ka karba ai ba yana nuna gazawarka a matsayin namiji bane. Jarabawace Allah Ya dora maka. A hankali ya bude ledar ya ciro wata yar roba mai murfi. Sarka ce da dankunne da zobe na gwal a ciki. Saurin rufewa yayi ya dora mata a cinyarta. Cutie ki dauke kayanki bazan sayar miki da sarkarki ba....abinda ya kasa fada shine ko pant bai siya mata ba a lefenta. Komai Alhaji ne yayi. Hannuwanta biyu tasa ta rike kumatunsa tana kallon fuskarsa mai dauke da tsantsar rashin kwanciyar hankali. Tunda nake ban taba saka gwal ba a rayuwata don an sayar da wanan bazanji komai ba. Duk irin wadannan abubuwan dama ai saboda rana irin yau ake tanadin su. Ni a abinda su Baba suka koya min wannan shine aure. Taimakon juna a lokacin bukata batare da mun fita waje mun tonawa kanmu asiri ba. Su Alhaji ne baka son sanarwa halin da kake ciki to ni din da na sani ka bani damar taimakonka mana. Sarkar da hannunta ya hada ya rike sosai sai kawai taga hawaye ya fito daga idonsa. Lallai rayuwa bata da tabbas, babu wani yanayi da bawa zai tsinci kansa yace wannan yanayin zai tabbata a ciki har ranar busa kaho. Yau kana da arziki gobe waninka ne. Wa zai taba tunanin akwai ranar da Architect Hamza Nasir Hamza zai karbi taimako a hannun Fatima Bashir? Yarinyar da ko certificate din shaidar tayi secondary school bata dashi,ga kazanta ga rashin wayewa. Ikon Allah kenan, kada ka taba raina bawa domin baka san abinda Allah yayi masa na arziki ba. Arziki kuwa ko da ba na kudi bane. Hawayen da Hamza yake yi ya karyar mata da zuciya ta soma kuka. Haka suka rungume juna na tsawon lokaci. Daga baya Hamza yace ta tashi su koma asibiti tace a'a yaje kasuwa ba'a rasa masu bude shago ranar lahadi ya sayar. Ita kuma zata kara yin saka zuwa la'asar ko bai dawo ba zata yi girki ta tafi asibitin da kanta. Sai da ya kwashe kusan minti biyar yana kissing dinta sannan ya fita. Bai san da yaya zai gode mata ba. Tunda ya shiga mota har ya isa kasuwar ALHAMDULILLAH yake ta nanatawa saboda godiya ga Allah da Ya azurta shi da mace tagari a lokacin da rayuwarsa take tsaka da rushewa. A dalilin mugun tashin da dollar tayi wanda muke ta addu'a Allah Ya yafe mana Ya kawo mana sassauci sai da Hamza ya sami dubu dari uku da tamanin da hudu a matsayin kudin sarka, dankunne da zobe. A haka ma don mutanen sun kula kamar a matse yake da ya sayar. A hanyarsa ta tsallaka titi ya koma motarsa yaga wata tsohuwa tukuf itama ta rasa yadda zatayi ta tsallaka. Da a lokacin da yake Hamzansa ne mijin Izzatu ita kadai baya jin zai iya yadda hannunsa ya taba matar. Amma yanzu ya koyi darasin zaman duniya. Hannun matar ya riko tana tafiya da kyar har ya tsallakar da ita titi. Godiya ta rinka yi masa tare da addua. Harda dan kukanta tace ba don kai ba sai nayi kusan minti shabiyar ina kokarin tsallaka titin nan. Magani na karbowa dana yana fama da lalurar asma. Ta dauki wata leda da magani ta nuna masa. Hamza ya tausaya mata yace baki da wasu yaran ko jikoki da zasu je miki? Tayi murmushi, shi kadai ne dani. Bayan shekaru shabakwai sai yanzu matarsa take da tsohon ciki. Idan abin ya tashi ita take zuwa amma yanzu bazata iya doguwar tafiya ba. Yana ganin kansa a wani yanayi ga wadanda suka fishi. Kudin aljihunsa ya shafa ya sa hannu ya kirga dubu goma ya bawa matar. Hannu na rawa ta karba tana ta kuka...Allah Ya albarkaci rayuwarka data iyalinka, Allah Ya rabaka da masifun zamani, Allah Ya baka arziki na halali daga inda baka taba tsammani ba. Yaro nagode, nagode. Hamza na tsaye har ta shiga adaidaita sahu sannan shima ya tafi zuciyarsa kamar an cire masa wani nauyi. Hakika sadaka maganin masifa ce kuma waraka daga bacin rai. Asibitin ya koma ya tarar Izzatu ta farfado. Raliya ya kira a waya ya sanar da ita halin da Izzatu ke ciki. Cikin kidima tace gobe zata taho in sha Allah. Tana ajiye wayar ta kira kanwarta Larai ta fada mata asibitin da suke. Tsananin bacin rai da kishi yasa Izzatu kuka tunda ta farfado. Yanayin da taga Zuhra da Hamzanta shi kadai yake mata yawo a ka tunda ta bude ido. Su Mama kuwa sai tausayinta suke yi a nasu tunanin bakincikin bari da cire mata mahaifa da akayi take yi. Cike da tausayi Hamza yake mata sannu amma ko kallonsa taki yi. Su Mama sai suka dauke kai kamar basu kula da abinda suke yi ba. Adabiyya tace Yaya ina Anti Zuhra? Yace zata taho girki yasa bamu fito tare ba. Basu dade ba kuwa sai gata da kwandon abinci. Bata tashi daga kan sakarta ba sai da tayi mai yawa ta yadda abin da ya rage mata saura kadan. Itama ko kallo bata ishe Izzatu ba duk da halin ciwon da take ciki. Sauran 'yan uwan Hamza suma duk sun zo. Zuhra ma ta kira Baba ta fada masa Izzatu na asibiti yace zasu zo washegari tare da Umma. Anti Larai kanwar Raliya tazo tare suka karasa yinin sai dai ta baro maigidanta babu lafiya saboda haka bazata iya kwana a asibitin ba. Dole aka yanke shawarar Adabiyya da Zuhra su kwana da Izzatu. Ranta inyayi dubu ya baci amma ko tashi bazata iya yi ba shiyasa dole ta hakura. Shabiyu saura na dare su Zuhra suka fita suka bashi wuri ya dan zauna wurinta. Sai lallabata yake tana kuka ita bazata zauna da wadda tayi sanadiyar zubar mata da ciki ba. Da kyar ya lallabata yace gobe shi zai kwana. Haka suka rabu ranta a bace. Itama Zuhra yayi mata sallama sannan ya tafi gida. ******** Wasu matasa ne su uku duk da bakaken kaya harda abin rufe fuska suka shigo cikin kauyen da gudu da cikon na hudun a kafadar wanda yafi sauran girma. A kofar wani katon family house suka ajiye na kafadar wanda yake ta zubar da jini sakamakon harbinsa da aka yi a cinya suka gudu. Da yake tsakar dare ne babu wanda ya kula dasu. Sai can wasu maza biyu suka zo wucewa a buge suka ga mutum a kwance a kasa. Da har zasu gudu sai daya ya haska shi da touchlight, da sauri ya karaso giyar da yasha ta fara barinsa yace sa dayan kazo mu taimaka masa Felix ne kanin Mr Oscar miloniya. [10/11, 2:27 PM] Mariya u madara: [10/10, 1:59 PM] #+234 809 156 9113#: AL'ADUN WASU #66 Batul Mamman(Mrs)# Daga Zuhran har Adabiyyan babu wanda Izzatu take son gani. Har gara Adabiyya tunda ita kanwar Hamza ce. Haka suka kwana jugum jugum ba abin suyi hira ba a junansu tace sun dame ta. Sau biyu Zuhra na fita kiran nurse a canjawa Izzatu drip idan ya kare. Ko baccin kirki bata samu ba amma banda sakon harara da tsaki babu abinda Izzatu ke aika mata. Wurin karfe bakwai Nura ya kawo Hamida da abinci yace Hajiya tace ya tafi da Adabiyya gida itama Zuhra ya kaita gida. Zuhra suka fara kaiwa. A falo ta hadu da su Khalifa duk suka rungumeta suna murnar ganinta. Khalifa yace wai Mummy bata da lafiya tana asibiti? Zuhra tace kuyi mata addua Allah Ya bata lafiya. Daddy ya tashi ne? Tala tace bai dade da fita ba kika shigo. Hanyar dakinta ta nufa tayi wanka Nana ta soma yi mata rigima wai sai ta goyata gata akwai jiki. Haka Zuhra ta sabata a baya ta hau sama. Kafin ta fito daga wanka ma Nanan tayi bacci, gefenta ta kwanta itama ko mai bata shafa ba, bata dade ba bacci ya dauketa. Sai shabiyu da rabi ta farka bata ga Nana ba, tasan kila tashi tayi ta sauka kasa. A gaggauce tayi alwala ta shirya ta sauko. Allah Yasa Tala ta riga tayi girki sai taci ta dauki na asibiti. Kafin ta fita Hamza ya kirata yace ta jira zaizo gida sai su tafi tare. Kamar ance Izzatu ta kalli kofa tana juyawa ta hada ido da Hamza da Zuhra. Wani karin takaicin ya isheta dama dakin daga su Mama sai Umman Zuhra. Tare suka zo da Baba shi ya tafi ya barta da Maman su Hajara. Zuhra murna an ga Umma sai washe baki take yi. Bayan ta gaishe da kowa kusa da ita ta zauna kamar zata shige ciki. Mama ta rinka tsokanarsu wai itama a bata sirrin shagwabar nan. Umma dai har kunya taji ita kuwa Zuhra ko a jikinta. Kamar jiya yau ma Zuhra tayiwa Izzatu sannu kin amsawa tayi tana wani yamutsa fuska. Suna haka Raliya da Larai suka shigo. Ganin mamanta nan da nan Izzatu ta soma kuka. Tausayinta suka rinka yi ana ganin kamar duk saboda ciwo ne ga rashin mahaifa. Haka su Zuhra suka zauna ana ta zuwa dubiya. Anti Faiza ma tazo tare dasu Mariya don sun zama kawaye. Ana sallar Isha su Hajiya zasu tafi Hamza yace Zuhra ta bisu Nura ya ajiyeta a gida. Babu musu ta tashi suka yi sallama da Raliya wadda ba kamar 'yarta ba ita tana dan sakar mata fuska suka tafi. Sai shabiyu saura Hamza ya dawo ya shiga dakin Zuhra. Bacci ya gansu suna yi ita da su Junior ga TV a kunne. Murmushi yayi cikin jindadin yadda take kula da komai da ya shafe shi ya kashe TV din ya rufe musu kofa. Da safe bayan su Khalifa sun tafi makaranta Zuhra ta koma ta dan kwanta. Kafin ta tashi Hamza ya tafi office daga can ya wuce asibiti. Yau saka ta zauna tayi sai da ya rage gabadaya saura biyar sannan ta tashi tayi jallof din couscous wadda tasha hanta da kayan lambu. Bata dade ba ta gama ta sake yin wanka. ******** Izzatu ke kuka tana fada ita dole sai Hamza ya saki Zuhra idan ba haka ba aurensu yazo karshe. Babu kowa a dakin daga shi sai Raliya da ta kwana a wurinta. Dukkanninsu sai rarrashinta sukeyi suna bata hakuri amma ta rufe ido tace bazata taba zama da Zuhra ba. Idan wata matar yake so ta amince yaje ya auri 'yar boko irinta amma bazata yi kishi da kazama kamar Zuhra ba. Duk da cewa maganganunta nayi masa zafi saboda ko kadan baya son abinda zai taba mutumcin Zuhra amma saboda tausayin yanayin da Izzatun ke ciki yasa yake bata hakuri. Idan ta warke dole asan me ake ciki don bazai dauki wannan wulakancin ba. Suna haka wayarsa tayi ringing. Yana ganin Cutie yayi murmushi ya dauka. Can kasakasa take magana tace Ya Hamza kana asibiti ko? Ina nan, ya akayi? Garin sauri na fito na manta jakata gashi mun kusa isowa asibitin. Ka fito ka bawa mai adaidaita sahu kudinsa kada ya tara min jama'a. Sai da yayi dariya sannan yace bazan zo ba, zan bari ya dan saita min bakin nan naki mai tsiwa. A shagwabe tace to shikenan zan ce ya saita shi irin yadda kake yi dinnan..... Ke, wallahi kada ki soma ina bakin gate din asibitin. Dariya tayi ...da ka koma kawai Ya Hamza ko na rabin minti sai..... Cutie bana son irin wannan maganar please. Na janye da nace ya saita miki baki. Ni kadai zan saita kayana. Sun dauki mintuna suna hira har suka karaso baki gate din ya biya mutumin ya tayata daukar kwandon abincin. Suna tafe suna hira abin sha'awa yace yau zaki san ni kika tsokana. Gwalo Zuhra tayi masa ai dai kai ka fara meye laifina don na taya ka? A haka suka iso kofar dakin. Hamza zai bude kofar kenan ya jiyo abinda Raliya ke fada wanda yayi matukar razana shi. Yanzu ke Izzatu har kina da bakin cewa Hamza ya saki matarsa? Me tayi miki da zaki tsaneta haka. Mum kinfi kowa sanin ni bazan iya sharing mijina da kowa ba talkless of kazama irin wannan yarinyar. Raliya tayi tsaki....ni bansan baki da hankali ba sai yanzu. Izzatu mahaifa aka cire miki fa. Kina tsammanin idan ya saki Zuhra bazai auri wata ta cigaba da haifar masa 'ya'ya bane? Muryar Izzatu suka ji tana kuka tace wallahi Mum idan ya dage sai ya zauna da yarinyar nan to zai ga tashin hankali. Sai na hana shi nutsuwa balle ya sami lokacin soyayya da ita. Bakinciki fal zuciyar Raliya saboda yadda Izzatu bata jin magana tace idan kika kuskura kika daga masa hankali nayi miki alkawarin sai na fada masa ke da kanki kika sha magani kika zubar da ciki. Kuma har asibiti kika je domin a cire miki mahaifa. Kin zauna mutane sai tausayinki suke ji basu san bukatarki bace ta biya. Izzatu ina jiye miki tsoro idan Hamza ya sakeki fa babu wanda zaiso ya auri macen da bazata haihu ba. Hannu Izzatu tasa a kan bakinta alamun Raliya tayi shiru. Sai dai aikin gama ya gama domin Hamza da Zuhra sunji komai. Cike da bacin rai Hamza ya sake kama hannun kofar zai bude Zuhra tayi saurin rike masa hannu saboda yadda taga fuskarsa gabadaya ta canja kamar bashi ba, jikinsa rawa yake sosai. Hannun nasa ya fizge daga rikon da tayi masa ya shiga cikin dakin. A take Izzatu da Raliya nasu idanun suka firfito waje saboda tsabar kidimewa. [10/10, 1:59 PM] #+234 809 156 9113#: AL'ADUN WASU #67 Batul Mamman(Mrs)# Yadda Hamza ya shiga dakin tamkar wani zaki. Zuhra ta biyo bayansa ta rabe a gefen kofa, bakinta a rufe da hannunta daya saboda zafin da lebenta yake sakamakon fizgar da Hamza yayiwa hannunsa ya bigeta. Kokarin tashi daga kan gadon Izzatu take yi domin yanayin Hamza ya bata tsoro. Murmushi yake mata wanda gara ace duka ya rufe ta dashi saboda duk wanda yaga yanayinsa dole ya tsorata. Sai da yaje kusa da gadon yace koma kiyi zamanki ranki ya dade. Nazo inyi miki godiya ne saboda irin abubuwan da kike yi min. Abu daya ya rage ki karasa ladanki shine ki kasheni ki huta. Raliya tace Hamza don Allah kayi hakuri ka tsaya muyi magana kada zancen nan ya fita. Wani shekeke ya kalleta abinda bai taba yi mata ba. Kinga ki dauki 'yarki ku koma gida idan an sallameta. Ke haihuwa ce kika gaji da ita. Ni kuwa da kika ganni ganinki ne gabadaya bana son yi. Ba don kina gadon asibiti bane babu abinda zai hana na nayi miki abinda zaisa a kawoki asibitin. Raliya ta hada hannuwanta biyu tana hawaye Hamza kayi hakuri kada ka saketa. Izzatu bata san meye rayuwa ba shiyasa take wannan haukan. Indai zata yi haihuwa uku amma ta kasa sanin meye rayuwa to ina ganin har abada bazata taba sani ba. Ya bata amsa rai a bace. Izzatu dai sai kuka take yi. Duk haukanta tasan Hamza yana son haihuwa bazai taba goyon bayanta a cire ciki ba balle mahaifa gabadaya. A hankali tace Sweetbaby am sorry. Bana son nayi ta haihuwa ka dena ganin kyau na har ka fara tunanin sake aure. Mamakin kansa yake yi da yadda ya iya zama da Izzatu duk tsawon shekarun nan. A kokarin kyautata mata ya rinka kuntatawa iyaye da 'yan uwansa. Kansa har wani irin ciwo yake masa, fadan ma ya kasa yi yadda ya kamata. Izzatu ta cigaba da magana, Baby a da indai nayi maka laifi fada kawai kake yi min. Amma yanzu duk ka canza saboda yarinyar nan da ko kadan bata waye ba. Har me ka gani a jikinta wanda bani dashi, me ya sami soyayyar da muke yiwa juna? Ai ta tabo wa kanta masifa tunda tasa Zuhra a ciki. Itama Raliya shiru tayi saboda irin fadan da Hamza yake yi yana gaggayawa Izzatu magana. Ke har kin isa ki hada kanki da Zuhra? To bari na fada miki wallahi ban taba son wata mace kamar yadda nake sonta ba, ciki kuwa harda ke Izzy. Zuhra tayi min abinda mata dayawa bazasu iya yiwa mazansu ba a lokacin da kike yawon gidan biki. Wannan yarinyar da kika raina ita ake kira matar rufin asiri. Kuma wallahi da ace wannan cikin da kika cire shine na farko bazaki kara komawa gidana ba daga nan sai kwasar kayanki. Hamza ni kake fadawa haka akan wannan yarinyar? To wallahi ko saki uku kayi min babu inda zani. Ni da kai mutu ka raba. Kuma zubewar cikin ba laifinka bane? Eyye nace ba laifinka bane??? Ai an tsayar da jinin tun a Abuja amma don wulakanci nazo na ganka da yarinyar nan a kan gado kana romancing dinta....ko kunyar Raliya bata ji ba take fadan wannan magana. Zuhra ta rasa me yake mata dadi. Shima Hamza ya manta da Raliyar a wurin yace shi kawai kika gani? Baki kula ko riga babu a jikina ba. Ki karasa bawa duniya labarin abinda kika gani a dakin mijinki sakamakon shigar masa daki da kika yi babu sallama. Raliya da Zuhra sai kallon kallo. Yau masoyan tamkar su cinye junansu don bacin rai. Sai da suka gaji don kansu Hamza ya finciko hannun Zuhra suka fita. Sauri yake kamar ya tashi sama. A motar ma babu wanda yace kala haka yaja suka tafi gida. Nana tana ta yi masa gwaranci ko kallonta baiyi ba ya haye sama. Yau ran Hamza ya baci fiye da yadda yaji lokacin da aka yi masa sata. Izzatu taci amanar soyayyar da yake mata. Duk abinda take yi yana kawar da kai, wannan karon ta kure hakurinsa. Tsoron binsa daki Zuhra tayi saboda yadda taga ya fusata. Lebenta ba kasa da ya bige har dan kumbura yayi sannan wurin yayi ja sosai alamun jini ya taru. Rufawa kanta asiri tayi ta dauki Al'Qurani ta shige wurin sakarta. Ta dade tana karatu tare da addu'ar nemawa mijinta sauki daga kuncin da ya shiga. ******** Mama Agnes na tsaye akan autanta Felix tana ta zubar da hawaye. Irin matan nan ne masu tsananin riko da addini ko takalmi bata sawa. Kwance yake akan gadon asibiti ga yayyensa maza biyu da mace daya sai 'yan sanda biyu. Dansanda daya yace a iya binciken da muka yi da kuma abinda abokan nasa da muka kama suka sanar damu sata suka je yi akan high way lokacin wasu 'yan uwanmu suna patrol shine aka harbe shi. Mama Agnes tace officer idan ya warke zaku tafi dashi ne? Yace kwarai kuwa tunda an samu bullet din ya fita. Share hawayenta tayi tace shikenan, ku zama shaida ta fada tana kallon sauran 'ya'yanta. Ko mutuwa nayi kada ku bari Felix yazo kan gawata. Na yafe shi daga cikin 'ya'yana kuma na tsinewa ranar da nayi cikinsa da ranar da na haifeshi. Cikinku idan akwai wanda yasan yayi sata to ya mayar da hakki ga maishi domin daga nan zanje Church ne. Zamuyi addua ga duk wani barawo a garin nan yayi mutuwar wulakanci da kaskanci. Duk cikin zuri'armu babu abinda muka fi kyama kamar sata. Felix na jin maganar da babarsa keyi ya soma kuka yana bata hakuri. Tace idan ma hukuncin kisa aka yi maka to kasani sarai gawarka bazata sami bikin burial ba. Zamu binneka tare da sauran masu abin ku yar kauyen nan..barayi 'yan uwanka. Mama Agnes na gama magana ta fice ko waige babu. Kauyensu Mr Oscar gara mutum yayiwa yarinya fyade akan yayi sata. Sata tafi kowane laifi girma a wajensu. Dayake Mr Oscar ya yarda sosai da adduar Church dinsu shiyasa ya tsorata da abinda mamansa ta fada. Kudin Hamza wanda har ya fara gini dashi su suka fado masa. ****** Bacci ne mai nauyi ya dauke Hamza sai karfe bakwai da rabi ya farka. Salati ya rinka yi da mamakin dadewarsa a kwance. Da sauri ya fada bandaki yayi alwala yazo ya gabatar da sallar magriba, kafin ya idar yaji ana isha a masallaci dole itama yayita a gida. Har lokacin zuciyarsa babu dadi sosai shiyasa shima ya zaune karatun Qur'ani. Ya dade yana addu'o'i tare da istigfar saboda neman sauki a wurin Allah. Haka yayi ta zama a daki har shadaya da rabi babu motsin Zuhra. Murmushi yayi da ya tuna karshenta tana can tana fushi saboda shareta da yayi. Dakinta ya fara dubawa babu kowa a ciki. Da ya sauka kasa ma tsit yaji sai karar injin saka. Da saurinsa ya bude kofar dakin da take sakar ya ganta tana yi. Zuhra na jin ya bude kofar gabanta ya fadi. Kusa da ita yaje ya zauna yana kokarin cire hannunta daga jikin wani karfe da take turawa. Kin saki tayi sannan ta sunkuyar da kanta kasa. Ka kyale ni yanzu zan gama ita ce ta karshe. Kin sakin hannun nata yayi ya cire shi sannan ya kira sunanta cikin sanyin murya Cutie....kamar wadda aka kunawa famfo sai kawai ta saka masa kuka hawaye na ambaliya a kumatunta. Rungumeta yayi yana shafa kanta...Cutie me ya sameki? Ki bar sakar haka muje ki kwanta. Iya karfinta ta soma kokarin ture shi tana tura baki....ni ka kyale ni idan nagama zan tafi na kwanta. Sake riketa yayi haba Fadimatu fada min waye ya saka min ke kuka, waye yake son yau na hana shi bacci tunda ya taba min Cutie. Marairaicewa ta sake yi tace ba kaine ba....Ya dan ware ido, ni da kaina Cutie? To fada min me nayi. Da yatsanta ta nuna masa lebenta da yayi ja amma yanzu babu kumburin. Ya Salam Cutie am so sorry, dazu ne a asibiti ko? Kai ta gyada yace kuma ka dena kulani duk da ina son baka hakuri akan abinda ya faru. Shhhhhh ya fada tare da dora yatsansa a bakinta. Kiyi shiru Cutie babu laifinki a dukkan abinda ya faru. Raina ne ya baci lokacin amma hakan bai zama dalilin da zan share matata ba. Kice kin hakura. Murmushi tayi tare da noke kafada. Yace please, please, please. Sake noke kafadar tayi yace to tashi muje mu kwanta kinga shabiyu ta kusa. Abin sakar ta kama ka bari wannan ce karshe saura kadan na gama. Kusa da ita ya zauna har ta karasa tace gobe sai ya kai musu. Godiya yayi mata da addu'a sannan ya kama hannunta suka tashi. Jikinta duk yayi tsami saboda zaman wuri daya. Sai da suka fito falo yace kince abinci kuwa. Tace a'a zata sha tea yanzu. Dariya yayi duk kaunarki da abinci ki kare a shan tea lallai nayi laifi. To muje na soya miki kwai kici da bread. Zuhra tayi dariya kaji ka Ya Hamza ka iya girki ne? Hannunta ya rike muje kiyi kallo yarinya. Kujera ya tura mata ta zauna sannan ya hada mata tea. Bayan ya gama ya dauko kwai guda uku a fridge Zuhra tace biyu zata ci. Yace shima zai ci. Tana kallo ya dora mai ya dauko maggi da cokali. Tana jira ya dauko roba ya fasa a ciki sai kawai taga ya fasa a cikin frying pan din. Da sauri ta taso Ya Hamza wace irin suya ce wannan? Bai kula ta ba ya barbada maggi kadan a saman ya dauko plate. Zuhra sai girgiza kai take yi taga ya juya kwan daya barin ma ya soyu sannan ya juye a plate. Kinga suya ba irin taki ba, muje falo kici ki ji. Bata yarda zata ji dadin suyar tasa ba sai da ya tura mata a baki. Sai da cinye na bakinta tayi murmushi tace da dadi....Hamza ya dauke plate din to kinci rabonki. Rokonsa ta fara yi taga yaki kawo mata, wuri ya samu ya zauna yana ci. Ta zauna ta soma kukan karya sai ya kawo mata. Tare suka karasa ci suna hira. Suna gamawa ya kulle gidan yace to sai bacci. A kofar dakinta tace masa zata je tayi wanka. Yace ke da kika gaji, muje ki dauko kayanki a dakina zaki kwana. Duk abinda zata bukata shi ya dauko mata sannan suka tafi dakinsa. Kai tsaye ta shige toilet zata yi wanka. Ta gama tara ruwa mai zafi saboda hannuwant da kafada duk sunyi tsami tana son gasa su taji an bude kofar. Wani irin ihu ta saka ganin Hamza a tsaye daga shi sai dogon wando. Da sauri yaje ya toshe mata baki da nasa. A haka ya karasa cire mata riga. Kuka take masa kamar wadda zai yanka yayi murmushi kin fiye tsoro Cutie. Ni taimakonki nazo yi kike min kuka. Hannunta ya kama tana ta harararsa ya sakata a cikin bahon sannan ya dauko karami tawul ya saka a ruwan zafin ya danna mata a kafada. Wani ihun tayi ta mike zata gudu ya riketa sosai. Kinga idan baki zauna ba matseki zanyi. Ki cigaba da hararata sai idanunki sun fado. Kunya taji ta dena harararsa. Kamar mai rada tace Ya Hamza ka dan rufe ido mana. Ki dena magana ba'a son surutu a toilet. Daga nan duk kauce kaucenta haka ya gasa mata jiki sosai sannan yayi mata wanka. A katon tawul ya nadota ido duk sunyi ja saboda kuka. Da kansa ya shiryata sannan ya dauko wata katuwar shirt dinsa ya saka mata. A bakin gado ya zaunar da ita shima yaje yayi wankan ya fito. Har ya gama shiryawa Zuhra na tura baki. Cak ya dauketa suka kwanta ta janye jikinta can gefe. Haka kawai kayi min wanka kamar wata yarinya karama. Ni bazan sake wanka a dakinka ba. Yana ji tana mita yayi dariya...zo na baki hakuri kinji my cute baby. Matsawa tayi gefe yasa hannu ya janyota ta fado jikinsa. Fuskarta yake shafawa da hannunsa daya yace duk abinda nayi miki kiyi hakuri harda wanda zanyi miki ma. Tace wanne kuma.....bai barta ta karasa maganar ba ya katseta ta hanyar kissing dinta da nuna mata soyayya irin wadda ya jima yana fatan zuwan ranar da zai nuna mata. AL'ADUN WASU #68 Batul Mamman(Mrs)# Babu irin yadda Hamza baiyi ba domin ya tashi Zuhra da asuba taki tashi. Ganin yana neman rasa sallah yasa ya rabu da ita yaje yayi wanka ya tafi masallaci. Niyarsa idan ya dawo sai ya sake tashinta. Tana jin sautin rufe kofar ta yaye bargon jikinta ta tashi jiki babu kwari. Abinda Ya Hamza yayi mata ne yasa ta tashi da wata irin kunyarsa, da wane ido zata sake kallonsa ma. Shiyasa tayi shiru tamkar bata jinsa lokacin da yake ta kokarin tashinta. Dama ita bata iya jin ciwo ba ta rinka raki da koke koke kenan to yau an sami maidalili. Da kyar ta iya zama cikin ruwan zafi sannan daga baya tayi wanka ta fito. Don kokari harda dan fesa turare tunda an zama 'yan gayu sannan tayi sallah. Zama ta cigaba tana azkar bayan ta idar taji har taji alamun antaba kofa. Jiki na rawa ta tashi ta jefar da hijab dinta ta haye gado. Har kanta ta rufe ta koma ta kwanta ko numfashin kirki bata yi. Dariya ta bawa Hamza da ya kula tabbas tayi sallah bayan fitarsa. A gefenta ya zauna yana mata magana a hankali. Cutie bazaki tashi mu gaisa ba? Shiru tayi babu amsa sai alamun tana kuka da yaji. Da kyar ya iya budeta ya kwantar da ita a jikinsa. Yace dama matsalar irinku kenan wadanda suke tashi babu wa babu kani. Kunfi kowa iya shagwaba. Yanzu duk kukan da kika yi jiya bai isheki ba shine zaki tashi da wani sabon. Tashi tayi suka hada ido tayi saurin juyar da kanta, to ba kai bane ina ta...... Yace na fa baki hakuri tunda wuri kuma me ya rage? Hmmm ko baki gane lesson din bane da kyau. Ya fada yana kashe mata ido. Murguda baki tayi ni bance ka koya min irin wannan ba. Eyye, Cutie ashe baki dena tsiwa ba. Lallai ya kamata a maimaita karatun ko zaki fi dauka. Irin wannan juya baki kamar idan na fara kissing kada na saki. Ido ta rufe ta kwanta a jikinsa...ai nasan Ya Hamza yana da kirki bazai kara sani kuka ba ko. Don Allah kayi hakuri na dena yi maka tsiwa. A hankali yace gaskiya banyi miki alkawari ba. Ke ko irin addu'ar da maza ke yiwa matansu da safe irin haka baki bari nayi miki ba sai korafi. Tashi zaune kiji wannan kwanciyar da kike yi a jikina sake kashe min jiki kike yi. Yadda yake magana yasa da saurinta ta tashi harda matsawa gefe. Hamza ya rinka dariya...matsoraciya kawai. Sannan ya kama hannunta...nagode miki Allah Yayi miki albarka Ya bamu zuri'a dayyiba. In sha Allah Zuhra zan rike ki amana kuma zan so ki fisabilillah. Idan har nayi miki wani abu ba daidai ba ina so ki rinka fada ba ki barshi a ranki ba muzo muna samun rashin fahimtar juna. Naso ace kinyi wanka a gabana dazu domin nasani ko akwai gyara duk da nasan matar tawa tana da ilimi. Amma kamar yadda naji wata malama Ummi Aisha tana fada yana da kyau duk miji ya san ko matarsa ta iya tsarki. Zuhra dai kunya duk ta isheta ta sunkuyar da kanta kasa. Hamza yace ina jinki fada min yadda kika yi ko muje nayi miki da kaina. Sanin ba karamin aikinsa bane yin hakan yasa ta soma yi masa bayani a hankali kamar wadda aka kamawa baki. Ya gamsu sosai da amsar da ta bashi yace to yanzu me ya rage? Zuhra tace naje kitchen nayi girki ko don asibiti...tana magana ta tashi da sauri saboda su Junior da ta tuna.. .Ya Hamza su Khalifa yau bazasu school ba? Tashi ka kaisu gashi har bakwai da kwata. Murmushi yayi...kinsa miji a daki kina masa dadin baki ba dole ki manta da yaranki ba. Ta tura baki ta fara jan hannunsa, don Allah ka tashi kada su makara yau. Yace to laifin waye? Ko kadan bai damu ba harda kishingida akan pillow Zuhra tana ta kokarin tayar dashi. Gajiya tayi ta hakura bari naje kasa nasan Tala tayi musu wanka. Don Allah ka taso kaji Ya Hamzana. Har wani fari take masa da ido duk don ya tashi. Sai da ya bari taje kofa sannan ya kirata. Da sauri ta dawo amma hankalinta yana kan yaran da tasan tun waccan alhamis din bayan dawowarsu daga Kaduna suka fara jarabawa. A gabansa ta dan durkusa tana jiran taji dalilin kiran. Bakinsa ya nuna mata...yau bamu gaisa ba. Idan kina so na tashi kizo mu gaisa. Kuma ki dena tafiya da sauri sauri kafin kizo kina min raki anjima. Kallonsa kawai take yi yadda yayi kwanciyarsa kamar bai damu da zuwan nasu makaranta ba. Bakinsa ya sake nuna mata tace jiya fa kaji min ciwo har ya kumbura ko ka manta? Dariya yayi ....you are not serious, duk abinda kika yi da bakin nan jiya sai yanzu zaki tuna da ciwo. Ko dai kiyi abinda nake so ko yaranki su zauna a gida yau. Da sauri ta fada jikinsa saboda tana hangowa su Khalifa makara sannan ta hada bakinta da nasa. A hankali Hamza ya rinka janta har ta saki jiki. Da kyar ta iya tuna masa su Khalifa...yace don't worry sun gama exams jiya so bazasu school ba sai ranar friday da zasuyi class party. Ta dan daki kirjinsa amma shine....bata sami damar karasa maganar ba ya katseta da wani salon soyayyar tasa. **** Sai shadaya saura ta samu Hamza ya kyaleta ta fito. Wanka ta sake yi ta saka wani lace dinta mara nauyi. Dinkin yayi mata kyau riga da zani tayi kwalliya sai kamshi take yi. Dakinsa ta fara shiga ta same shi zaune akan gado da laptop bashi da niyyar tashi. Ya dago mata hannu alamun ta je wurinsa...Cutie kinyi kyau. Har nan nake jin kamshink mai dadi. Murmushi tayi a kunyace tace ina daga nan Ya Hamza. Ni yanzu ko hannunka tsoron tabawa nake yi. Yana daga zaune ya rinka dariyar maganarta. Ka fada min me zaka ci ni yunwa nake ji. Kansa ya kada irin ya zama abin tausayi tunda taki zuwa. Zaki kawo kanki ne yarinya. Yanzu dai ki hada min tea kuma idan akwai sauran tuwon jiya ki dumama min. Bata jima ba ta kawo tea din falonsa da tuwon suka ci sannan tace zata dora abincin rana. Rabin cin abincin duk Hamza ke tsokanarta tana ta sunkuyar da kai. Can tace ni har kunya nake ji ba'a kai abincin safe ba asibiti kuma duk laifinka ne. Ya dauke kai su Mama sun aika shiyasa kika ga ban damu ba. Abincin ranan ma kiyi wake da shinkafa amma da manja shi nake sha'awa yau. Zuhra tace to abincin asibitin fa. Ya dan sha kunu, suma shi zasu ci ko akwai matsala ne? Zuhra tace babu, sannan ta kwashe kwanukan ta sauka kasa. Amma a zuciyarta tana tunanin yadda mara lafiya zata ci wake da shinkafa da mai duk da Izzatun ta fara cin abinci. Kafin azahar ta gama komai na abincinta ta hada salad da kunun aya yasha kankara. Su Junior duniya sabuwa sunji dadin abinci sai karawa suke yi. Bayan sun gama ta shiryasu saboda Hamza yace tare dasu zasu je asibitin. Sai da yayi sallah ya gama nuko nukonsa sannan ya fito suka tafi. Duk motsin Zuhra akan idonsa jin kansa yake kamar sabon shiga a aure saboda irin son da yake yi mata. Makarantun da suka bada aikin saka suka fara zuwa ya kai musu duk suka biya suna yaba kyan aikin da saurin da akayi aka gama. Sai gashi ya tashi da dubu dari uku da arba'in da hudu kudin da duka makarantun suka biya. A mota ya rinka yiwa Zuhra addua yasa su Nana suce Amin. Bakinta kamar gonar auduga don farinciki saboda yadda taga Hamza yayi murna. Har cewa yayi washegari zai karbo mata form ta cike zai bude mata account. Dubu dari biyu da hamsin zai saka mata a cikin kudin sauran suyi amfani dashi a gida. Tun a wurin tace bata yarda ba yace to abar magabar sai sun koma gida. ***** Duk magiyar da Raliya tayiwa Izzatu sam taki yarda taci abincin da aka kawo daga gidansu Hamza da kuma na gidan Anti Larai tace tana jiran Hamza tasan duk tsiya bazai barta da yunwa ba. Anti Larai dai ko kulata bata yi ba dama ba shiri take yi da Izzatu ba. Tun su Hajiya na asibitin ake cewa taci taki cin komai har suka tafi. Raliya tace ke yanzu banda baki da kunya yaushe zaki jira Hamza mutumin da kika batawa rai. Kina kallo yau tun safe bai zo ba shi da yana kai yara makaranta yake tahowa. Izzatu dai ta kafe bazata ci abincin ba dole Raliya ta kyaleta. Sai wurin karfe uku suka iso asibitin. Su Khalifa ne suka fara shiga dakin da gudu Hamza da Zuhra na bayansu. Shi ya dauko kwandon abincin ma sannan suka shiga dakin yana rike da hannunta yana tsokanarta tana dariya. Kiris ya rage Izzatu ta hadiyi zuciya sai dai ta hakura. Tunda yazo tasan baya iya dogon fushi da ita. Wannan 'yar banzar yarinyar kuwa sai tayi maganinta. Zuhra da Hamza suka gaisa da Raliya sannan Zuhra tayiwa Izzatu ya jiki. Kamar tayi magana da dutse haka ta shareta. Khalifa yace Mummy baki ji Maama tana yi miki ya jiki ba? Izzatu ta dan matse banji ba Khalifana. Junior ya dora hannuwansa biyu a baki yace Daddy kaji Mummy tayi karya ko? To mai karya dai dan wuta. Mu duka a dakinnan munji sai ke kadai. Hmmm, Maama fadawa Mummy idan jirgin aljannah yazo a nan zamu barta. Hamza ya kwashe da dariyar mugunta yace haka ne Junior Allah Ya shiryi masu karya. Yara suka ce amin. Ran Izzatu ya gama baci tace zuwa kayi ku wulakantani kai da matarka? Shine zaku saka 'ya'yana ma su tsaneni ko. Zuhra ce tayi karfin halin bata hakuri, shi kuwa Hamza dariya ya sake yi ya cigaba da wasa da yaransa. Raliya ta bude abincin zata zubawa Izzatu. Tana daga kan gado amma idanunta na ga abinda mamanta ke yi. Kamar tayi kuka tace Mum me nake gani kamar wake da shinkafa. Raliya tace shine kinji kamshin kayan salad ko? Tana bude man Izzatu ta sa ihu, Mum manja ne fa. Raliya tace to sai me kike yamutsa fuska kamar kinga abin kyama. A raunane Izzatu ta kalli Hamza,Baby wane irin abinci ne wannan kuka kawo min? Yace irin abincin da muke ci ni da iyalina. Sai nanatawa take yi a ranta wake da shinkafa. Basu taba yi ba tunda suka yi aure. Kamar tayi kuka tace ko dai ka sami karayar arziki ne, shi kadai ne dalilin da zaisa a fara cin irin wannan a gidanka. Junior ya dubi abincin da Raliya ta gama hadawa yayi kyau yace Mum ki bani inci, Maama ta iya girki. Izzatu tace haba ko da naji,ashe Zuhra ce ta dafa. Kaga irin abinda nake fada maka ko. Yarinyar nan bazata ta taba wayewa ba. Kamar kai Baby aci wake da shinkafa a gidanka sai kace wani talaka. Jikin Zuhra duk yayi sanyi. Hamza yace Cutie ga key ku tafi mota da yaran ina zuwa. Tana fita ya zauna a gaban Izzatu ya warware mata halin da yake ciki da irin gudummawar da ta bayar wurin fadawarsa wanda yasa ta mugun mamaki. Ya mike tsaye...saboda haka Izzy ki kiyayeni domin ko banyi aure ba ina gab da sakinki wallahi saboda kin jefani cikin tashin hankali sannan dayake kinfi amara son biki kika tsallake kika barni. Izzatu tace don ka sami matsala sai kayi min sharri? A take ya tuna mata duk abubuwan da tayi wadanda sukayi sanadiyarsa fadawa wannan halin. Baki bude haka ya fita ya bar Izzatu da Raliya don ma bai fada musu yadda Zuhra ta taimaka masa ba. AL'ADUN WASU #69 Batul Mamman(Mrs)# Daga asibitin gidan 'yan uwansa mata suka wuce. Dukkaninsu sunyi farincikin ganin Zuhra kowacce tana janta a jiki. Daga nan suka je gidan Anti Faiza wadda ta rasa inda zata sa kanta don murnar ganin Zuhra da Hamza tare. Dabarun kula da miji ta sake karanta mata da kyau sannan na karshe suka je gidan Ibrahim. A nan suka ci abincin dare sannan suka taho bayan Hamza da Ibrahim sun dawo daga sallar isha. Kafin suje gida su Khalifa duk sunyi bacci sai Hamza da Zuhra ke ta hira. Kayan da suka biya suka siyo Zuhra ta iya dauka yaran kuwa Hamza ne ya dauko su. Dama sauri take su iso gida gabadaya bata jindadin jikinta tun yamma daurewa kawai take yi tana tafiya. A dakinsu ya kwantar dasu Zuhra ta fadawa Tala taje ta kwana dasu sannan ta hau sama. Tana tafiya Hamza na binta da ido, jan kafa kawai takeyi tana tafiya da kyar. Tun yamma ya kula da yadda tafiyarta ta canja amma idan taga mutane sai ta daure ta rinka tafiya daidai tana bata rai. Girgiza kai yayi saboda yasan meye matsalarta. A dakinta ya sameta tana daura tawul zata yi wanka yace ta jira shi yana zuwa. Turo baki tayi ...Ya Hamza don Allah kada kace zaka yi min wanka yau ni bama ni da lafiya. Yace to Allah Ya sauwake, maganin ciwon naki zan baki. Idonta har ya fara kwalla tace kasan me ya sameni ne? Cike da tausayawa yace na sani Cutie, bari ki gani ina zuwa. Toilet dinta ya shiga ya tara ruwa mai zafi sosai a katuwar roba ya sirka shi kadan sannan ya fito ya cire rigarsa ya bar singlet yace muje. Duk ta gama tsorata ta fara ja da baya. Bai tsaya sauraronta ba ya dagata tanata dukansa. Tawul din kawai ya zare ya sakata a cikin ruwan zafin. Ihun da tayi yana tsammanin har maigadi sai yaji domin ba wutar inji bace bare ya rage sautin karar. Zuhra kuka take yi sosai tana kokarin tashi Hamza ya tsaya daga bayanta ya danna kafadunta. Ya Hamza akwai zafi sosai. Na sani kiyi hakuri, son jiki irin naki yasa baki shiga ruwan zafin tun da safe ba. Yayi 'yar dariya... Yau duk mai hankali kin gama tona min asiri a wurinsa da wannan tafiyar taki. Sharkaf haka fuskarta ta jike da hawaye tace na shiga ruwan zafin da asuba. Hannuwanta ya rike da take neman tashi tsaye yace nasan kin shiga ruwan da kika gama sirkawa ba. Wannan idan kika haihu da kaina zan miki wankan jego don kada ki cuce ni. Muryarta har ta soma dashewa tace cuta har ta wuce gasa ni da kake yi. Ta kai masa cizo a kirji ya kauce yana dariya. Zumbura baki tayi kuma na dena sonka. Yana dariya yace babu komai Cutie son da nake miki ya ishemu ai. Bata kula ba ya sake kara ruwan zafin saboda na robar ya fara hucewa. Kuka kala kala Hamza ya gani. Da kyar take magana don bakin ya mutu. A hankali tace to ka dawo ta gabana na rungumeka naji dadi. Yadda tayi ya bashi tausayi amma yasan abinda yayi mata zaisa taji dadin jikinta. Zagayowa yayi ta rungumeshi tana kuka yana shafa bayanta. Bai kyaleta ba sai da tayi kusan minti talatin a cikin ruwan zafin sannan kamar jiya yayi mata wanka. Sai da ya shiryata sannan ya shiga wankan shima. Kafin ya fito tayi baccin wahala. Gyara mata kwanciya yayi ya rumgumeta cike da tausayawa. A haka suka yi bacci tana kwance a jikinsa. Yau dai bata ji kunyar tashi da asuba ba har Hamza na tsokanarta. Da wuri ta kammala ayyukanta na gida saboda jiki yayi kwari ta dena tafiya da kyar. Da tayi zancen zuwa asibiti Hamza yace bazashi ba office zai tafi. Itama baiyi mata izinin taje ba. Ganin ya dauki zafi yasa bata matsa masa ba. Bata damuwa da bin kwaf akan matsalarsa da Izzatu. Tare ta gansu tasan idan fushin ya kare zasu daidaita. Kullum Tala ke kai abincin asibitin. Cikin 'yan kwanakin nan Zuhra da Hamza sun kara shakuwa sosai. Soyayya yake nuna mata tamkar wata 'yar yarinya haka yake lallabata. Itama dai ta fara sakewa dashi amma har yanzu tana jin kunyarsa. Ko kayan bacci tasa sai yayi da gaske yake cire mata hijab. Ana tashi daga office gida yake tahowa su sha soyayyarsu. Ana haka Hajiya ta kirashi tana masa fadan kwana biyu bata ganinsa a asibiti meye dalili. Dama yasan ba son Izzatu suke yi ba, idan ya fadi abinda tayi kuma kara wutar abin zaiyi sai kawai ya bata hakuri yace ayyuka ne suka saka shi a gaba. Kwanan Izzatu tara a asibitin sannan aka sallameta. Duk irin nasiha tagari Raliya tayi kokarin yi mata domin ta samu ta rike igiyar aurenta dake lilo a iska. Itama ta danyi karatun ta nutsu saboda bata taba tsammanin zai iya shareta haka ko waya babu ba. Tun safe akayi sallamar ta kira shi a waya yana can jikin Zuhra bai bi ta kai ba. Sai daga baya yaga missed call ya kira tace an sallameta ne tun safe. Hamza yace to sai ki tari adaidaita sahu ki taho gida ni motata jiya da kyar ta kawoni gida. Anjima kadan makanike zai zo ya dauka. Kamar ya kwada mata guduma haka taji maganar tasa. Adaidaita sahu kuma??? Ita ba don kada tayi karya ba sai ta iya cewa bata taba shigarsa ba. Motoci uku ne a gidansu kuma duk inda zata indai ba aiki ne yayi masa yawa ba Hamza da kansa yake kaita. Gashi ko zancen motarta da ta bari a Kaduna baya yi. A sanyaye tace Baby ko daga gidanku kasa azo a daukeni mana. Saboda yadda ta bashi haushi ko amsa bai bata ba ya ajiye wayar. Zuhra na falo tana biyewa yara suna shirmensu Hamza ya fada mata an sallami Izzatu tayi abinci da ita. Tace Mamanta fa? Gidan kanwarta zata wuce, kisa Tala ta gyara mata daki kafin ta karaso. Yana gama magana ya shige falonsa. Sakonsa ta fadawa Tala sannan tabi bayansa dama ta riga tayi girkinta kuma zai isa indai cikin Izzatu ne ita kadai. Kwance ta same shi akan doguwar kujera ya dafe kansa da hannu daya idonsa a rufe. A hankali ta rinka tafiya har tazo gabansa ta durkusa. Gashinta ta janyo daga cikin dankwali ta matso kusa dashi sosai sannan ta zira masa gashin a kunne tana wasa dashi. Da sauri ya bude ido ya dagota ta fado jikinsa. Kinci bashi Cutie ya fada yana karkade kunnensa. Tayi dariya kai dai kaji tsoro kawai zaka wayance. Hancinsa ya goga a jikin nata yana murmushi...Cutie I love you so much. Ganinki yana sa na manta damuwata. Mayar masa da murmushin tayi tace I love you too. Amma yanzu ka tashi muyi magana kaji. Ba haka yaso ba a yadda ta kwanta a jikinsa so yayi su zauna a haka. Yace idan na tashi kin min alkawarin zan sami duk abinda nake so. A kunyace tayi hada bakinta da nasa tace harma da kari. Zama ya gyara ya dorata akan cinyarsa. Ina jinki Cutie. Har wani dan gyaran murya tayi sannan tace Ya Hamza nasan bani da wani iko akan duk matsalarka da mamansu Khalifa. To amma abinda yake faruwa yanzu yana iya shafarsu. Idan har iyaye na fushi da juna yara su kan gane idan sun fara wayo. Jiya Khalifa cewa yayi yanzu baka zuwa wurin Mummy dinsu saboda tayi maka laifi. Nayi kokarin yi masa wayo nace kana zuwa. Daga baya yazo yace yanzu nice mamansu ko, ita kuma zata koma Abuja su dena ganinta. Bansan ya akayi yake irin wannan tunanin ba amma ya kamata ka nuna masa ba haka bane. Yanzu yaro ne bazai kawo komai ba, amma nan gaba idan ya kara wayo zai ga kamar baka sonta ne. Daga nan ko kai ko ita zai goyi bayan daya ya bar dayan wanda hakan bai dace ba. Hamza kallonta kawai yake yi har ta gama bayaninta. Fuskarsa dauke da murmushin jindadi, shi kam yaga ranar biyayya ga iyaye. Iska ta busa masa a ido da taga baya kiftawa. Ya shafa fuskarta, Zuhra ke dabance a mata. Lokacin da ya dace kiyi farinciki hankalin miji ya dawo gareki gabadaya sai kike tunanin kyautatawa wadda tayi sanadiyar jefaki cikin kunci. Zuhra tayi saurin dora yatsanta a bakinsa...Ya Hamza ni bana cikin kunci. Na aureka ba don ina so ba amma yanzu bana fatan ganin ranar da zamu rabu. Yayi murmushi Allah Cutie? Kice karatun da na koya miki yayi aiki kenan. Kunya taji ta sunkuyar da kai, ni ba haka nake nufi ba. Yayi murmushi ni haka nake nufi. In Sha Allah zanyi kokarin gyarawa kuma. Sai dai sai kinyi min hakuri da kunnenki kika ji abinda tayi. Zuhra tace babu komai indai zaka gyara itama zatayi da yardar Allah. Hamza ya jinjina kai, Cutie fada min gaskiya ke bakya jin haushin duk abinda tayu miki? Zuhra tace tabdi, ya za'ayi naji haushi ta hadani da mijin da babu kamarsa. Tana fadar haka ta tashi ta gudu tana masa dariya. ****** Mai adaidaita sahu ga gaji da ihun da Izzatu take yi ko yaya suka shiga gargada. Dama da ganinsa ko ba'a buge yake ba to yana dan tabawa ya kallota ta mudubi idanunta wuri wuri. Ke Hajiya ya zaki rinka min ihu kamar yau kika fara shiga adaidaita? Izzatu ta kankame karfen gefen da take tana mai nadamar kin bin mamanta a wanda ta tafi...ban taba shiga ba wannan ne shigata ta farko. Dan matashin yayi dariya yace shegiyar karya kice daga turai jirginki ya sauka kawai. Kallon yadda yake kurdawa tsakanin motoci take yi baki na rawa tace wallahi ba karya nake yi ba a Canada na girma. Dreban ya kwashe da dariya yace bari na dan shillaki kiji kamar a jirgin Canadan kike. Ai bata kara samun nutsuwa ba sai da ya tsaya a bakin gate din gidanta. Gudu yake yi da ita sosai har wani abokinsa na tambayarsa ina zuwa haka da suka tsaya a danja yace yau Canada ya nufa. Izzatu taga tashin hankali duk jikinta ya bugu. Kafarta kamar bazata dauketa ba da suka tsaya a kofar gida. Maigadi ne ya kwaso mata kayanta ta shiga ciki tana jan kafa. Tana shiga falon idonta ya dire akan Zuhra zaune a kan ledar cin abinci ta dora Nana a cinyarta ga Junior da Khalifa duk sun zagaye tray suna cin abinci. Zuhra ta dago kanta a dan tsorace tace mata sannu da zuwa. Ko bi ta kanta bata yi ba tace where are your table manners kids? Yaushe kuka fara cin abinci a kasa kuma a tray? Khalifa yace zumunci yake karawa. Izzatu ta dakawa Tala tsawa, daukesu ki zubawa kowa plate dinsa su koma dinning table. Tala ta ruga kitchen a ranta tana cewa shikenan mun shiga uku. Sai a lokacin Izzatu ta karewa abincin kallo tace meye wannan kuke ci a wulakance. Zuhra taji babu dadi. Farar shinkafa ta dafa sannan tayi miyar alaiyahu. Jajjagen attaru da albasa tayi sai tumatir kadan ta soya da manja ta zuba alaiyahu wanda ya tsane ruwansa sannan ta dafa kwai ta sakawa kowa. Tala na zuwa da plate din Hamza ya fito yace ta mayar ko kallon Izzatu baiyi ba ya koma falonsa rai a bace. Zamansa kenan wayarsa tayi kara ya dauka. Mutumin yace shine sakataren ministan tsara birane. An turowa Hamza sakon email ana bukatar ya karanta ya turo reply kafin gobe. AL'ADUN WASU #70 Batul Mamman(Mrs)# Hamza. Hamza.. Hamza.... Shigowar Izzatu falon nasa tana kwala masa kira yayi daidai da faduwar wayarsa daga hannunsa saboda yadda kiran nata ya dan razana shi. Ya fuskanci kamar da gayya Izzy ke zuwa a lokacin wani abu mai mahimmanci ta wargaza komai. Sunkuyawa yayi ya dauki wayar ya mayar da batir zai kunna tazo ta tsaya rai a bace. Yanzu Baby don kayi aure shikenan ni ban isa ba a gidan nan? Menene dalilin da zaisa ka hana Tala rabawa yara plates kamar yadda na saka ta? Hamza ya fasa kunna wayar kada ya bude email din Izzatu tayi abinda zai kasa fahimta ya bayarda amsar da bata dace ba. Sai da ya zauna sannan yace...daga yanzu da kika shigo gidannan zaki ga changes wadanda suka sha bamban da abinda kika saba dasu. Duk wanda baiyi miki ba ki fara magana dani kafin kice zaki gyara shi. Maganar yara na cin abinci a tray nima jiya haka muka yi dasu duka. Once in a while dai family suyi sharing plate yana kara saka shakuwa a tsakaninsu. Yanzu ki taimaka ki tafi daki kiyi wanka ko abinda ranki yake so kafin nazo na sameki. Yana kaiwa nan ya fita ya wuce dakinsa. Wayarsa ya kunna ya duba email din. Gayyatarsa akeyi zuwa workshop da za'ayi a Lagos na kwana hudu. Daga litinin zuwa alhamis, a ranar juma'a kuma za'ayi musu gwaji a fitar da mutum biyar da suka yi nasara a turasu Korea course na wata biyu. Jin abin yayi kamar a mafarki ya sake karantawa. Su goma aka zaba su halarci workshop din. Idan ya amince zashi akwai inda zai danna alamar ya amince sai su turo masa da kudin jirgi. Hatta hotel din da za'a sauke su a kwanakin da zasuyi duk an tanada. Hamza dai ya rasa bakin magana sai cewa yaje IKON ALLAH. Shi bazai iya tuna lokacin da ya tura application na halartar workshop din ba. Inuwa sakatare ne ya fado masa yayi saurin kiransa. Bayan sun gaisa yake sanar dashi abinda ke faruwa. Inuwa yace Alhamdulillah, ranka ya dade ai kusan wata biyu kenan da naga tallan abin a labaran NTA sai kawai na bude website dinsu na cike maka tunda naga abin na architects ne. Banyi tsammanin zamu sami nasara ba shiyasa nayi shiru da zancen. Hamza yace Allah Mai iko da daukaka ni bansan me zance maka ba Inuwa. Allah Ya saka maka da mafificin alkhairi. Inuwa yayi dariya ranka ya dade ai bazan taba biyanka alkhairin da kayi min ba a rayuwata. Ban gama karatu ba ka bani aiki kuma ka cigaba da biya min kudin makaranta har na kammala. Allah dai Ya sanya mana alkhairi a wannan aikin Ya bamu sa'a. Amin Hamza yace sannan ya ajiye wayar. Addu'ar tsohuwar nan da suka hadu a kasuwa ya tuna yayi murmushi. Lallai Allah shine mai bayarwa ga wanda Yaso a lokacin da Yaso. Duk wannan abu a dalilin canjin ra'ayi da ya samu ne ya kyautatawa Zuhra. Hakika Allah Yayi gaskiya da Yace a suratul Rahman " Hal Jaza'ul Ihsani Illal Ihsan"...babu wani sakamako ga kyautatawa sai kyautatawa. Hamza ya gyara alakarsa da matarsa wadda ya aura domin ya wulakanta. Ya bata damar zama wata jigo a rayuwarsa gashi tun ba'aje ko'ina ba yaga sakamako mai kyau a lokacin da yake cikin halin matsi da takura. Sai gashi komai yazo masa da sauki tunda ba'a taba rasa abinci a gidansa ba. Da duka mutane zasu zama masu kokarin kyautata alaka da sauran mutane da hakika zamu ga taimakon Allah a cikin dukkan al'amuranmu. Ya Allah Ka taimaki Nigeria da shuwagabaninta da dukkan kasashen da musulmi ke ciki. Amin Sallah Hamza yayi raka'a biyu yayi godiya ga Allah SWT sannan yayi addu'ar samun nasara. Baiyi saurin fadawa kowa ba yana jira sai dare ya fara sanar da Zuhra amma kafin nan ya fita zuwa gidansu. A nan ya fadawa su Alhaji wayar da ya samu. Alh Nasiru yayi murna sosai tare da yi masa fatan alkhairi. Su Hajiya ma duk sunyi farinciki suka yi masa addua. Yana fitowa bai biya ko'ina ba sai gida. ***** Izzatu ta sauko falo tana tafiya tana rangwada jiki. Tun daga sama take jin hirar Zuhra dasu Khalifa. Tana saukowa ta zauna daga can gefe ta fara kiran yaranta daya bayan daya. Abinka da da da uwa duk sai suka koma wurinta suna bata labaran abubuwan da suka yi lokacin da bata nan. Ko kadan Zuhra bata nuna damuwa ko bacin rai ba sai da ta tashi suka hada ido da Izzatu ta jefa mata muguwar harara. Bata tanka mata ba ta tashi ta shige kitchen zuciyarta babu dadi. Ita dai tana tsoron zaman da zatayi da Izzatu. Da ta gama abinci ta zubawa su Junior a plates daban daban yadda taga Izzatu tana so sai dai bata same su a falo ba. Tala ta tura ta kirasu suzo suci abinci. Ko da taje dakin Izzatu ta fadi sakon Izzatu cewa tayi taje ta dafa musu indomie guda uku ita da yaran. Khalifa ya tashi Mummy ni dai abincin Maama zanci. Indomie uku bazamu koshi ba. Junior ya tashi nima haka Mummy kizo muje tare akwai dadi ya fada yana jan hannunta. Izzatu ta fizge hannu tace Zuhra ba mamanku bace nice mamanku. Ita bata sonku, so take Daddy ya koremu mu bar mata gidan ita kadai. Khalifa yayi shiru alamar tunani...ni dai Maama tana sona da gaske. Amma bari naje na tambayeta dama tace duk wanda yake fadar abu ba mai kyau ba akan wani idan baya nan jirgin aljannah a Kano zai barshi. Ran Izzatu ya baci tace idan ka sake min zancen jirgin aljannah sai jikinka ya gaya maka. Kuma duk ku sami wuri ku zauna ko na zane ku. Babu musu suka zauna suna mata kuka. Juyawa tayi taga me Nana take yi a gaban dressing mirror taga bata nan. Da sauri ta tashi ta fita, ta sama ta hangota Zuhra na bata abinci. Ta girgiza kai wannan yarinya da shegen cin abinci take, bata san lokacin da ta fice daga dakin ba. Dole ta kula da abinda Nanan take ci saboda kada tayi kiba sosai. Tala ta kawo indomie haka su Khalifa suka ci ba don rai yana so ba. A dakin nata suka yi bacci Izzatu tasa Tala ta kaisu dakinsu. Zuhra dai tasan duk neman rigima ne yasa Izzatu ta hana su Khalifa cin abincinta. Babu ruwanta tunda 'ya'yanta ne fatanta Allah Yasa sun koshi da indomie din da aka dafa musu. Wurin karfe tara ta tashi daga falon ta koma dakinta. Dama bata yi gangancin zuwa dakin Hamza ba don tasan ko ba'a fada ba Izzatu ya kamata taje ta kwana dashi. Abincinsa ta ajiye a dinning table sannan ta tafi. **** Da murnarsa ya shigo gidan yau zaiyiwa Zuhra kyakkyawan albishir. Ganin bata falo yasa ya zauna ya ci abincinsa sannan ya tafi yayi wanka. Idan yayi tunanin Cutie dinsa sai yayi wani shu'umin murmushi. Yasan tana daki ana gyara jiki bata yarda tazo dakinsa ba wanka saboda sai ya yi mata fin karfi yayi mata da kansa. Air freshner ya fesa a dakin yana mamakin yadda akayi yau har ya dawo bata fesa ba. Shi da kullum idan ya dawo dakin sai sanyi da kamshi. Wata hadaddiyar rigar bacci Izzatu ta saka mai kyau. Ta gyara jikinta tana zuba kamshi ta fito ta rufe daki. A ranta ta kudurce idan har Zuhra na dakin to sai dai su kwana su uku don bazata fita ba. Duk abubuwan da yake kafin ya kwanta ya gama ya koma falonsa yana duba karin bayani game da workshop din da aka gayyace shi. Ba karamin project gwamnatin tarayya zata bawa wadanda suka yi nasara ba. Hankalinsa na kan aikinsa yaji an rufe masa idanu ta baya. Shiru yayi ya shaki kamshin wanda a take ya gane mai shi. Da sauri ya cire hannuwanta daga idonsa ya kalleta fuskarsa babu fara'a. Lafiya, kika shigo min daki a daren nan? Murmushi tayi don tasan har yanzu Hamza na fushi da ita. A hankali zata karkato da hankalinsa gareta har ya gane abinda tayi domin inganta rayuwarsu ne ba don ta kuntata masa ba. Ta sunkuyo zata yi kissing dinsa yayi saurin kawar da kansa gefe. Yanzu Izzatu bata burgeshi ko me zata yi abubuwan da tayi masa kawai yake tunawa. Fuskarta kamar zata yi kuka tace Sweety ya kamata ka manta da dukkan abinda ya faru mu sake gina rayuwarmu kamar da. Nasan nayi maka laifi ina rokonka ka yafe min. Wani irin kallo yake mata na rashin gamsuwa da abinda take fada....zancen na yafe miki kema kinsan ba abu bane da zai iya faruwa lokaci daya. Mu bar wannan zancen ma, na fada miki duk irin asarar da kika janyo min amma baki ce komai ba. Duk wata kadara da kika san ina da ita na sayar. Motata ce kawai ta rage da taki. Wace gudummawa zaki iya bani domin ganin mun cigaba da running din gidan nan kamar yadda muka saba? Izzatu tayi saroro tana kallonsa. Ita bata dauki abin serious ba lokacin da ya fada mata. Tayi ajiyar zuciya...nima bani da wani kudi yanzu duk nayi amfani dasu a wurin biki. Amma zanyi kokarin taimaka maka da gyaran tawa motar. Sun kira maigyara yace zata ci kamar sixty thousand. Hamza yayi murmushi tare da girgiza kai. Izzatu kenan, ita nata taimakon a kanta zai kare kenan. Yace to babu komai a hakan ma nagode. Taji dadi ta sami wuri kusa dashi ta zauna...nasan wannan problem din is not permanent amma zanyi kokarin ganin mun rage kashe kudi sosai. Abinci da kake siyo mana every thursday sai ka rinka siyowa a wurin da bai kai na da tsada ba, sannan... Bai bari ta karasa magana ba ya tashi..bari naje na rufe gidan ina zuwa. Ko sake kallonta baiyi ba ya fice ya barta zaune. Gani yayi idan ya cigaba da zama ransa ne zaiyi ta kuna a banza. Ita a irin nata hankalin duk abinda ta lissafa gani take yi ba karamin taimako tayi masa ba kenan. Babu wani rufe gida da zaiyi domin ya rufe tunda ya dawo. Dakin Zuhra ya nufa yaji dalilinta na kin zuwa dakinsa yau. ***** Kwance take a kan gado amma sam bacci yaki zuwa. Tunanin Ya Hamza take yi, yana can yau tare da Izzatu. Hawaye taji ya cika mata ido zuciyarta na zafi. Yanzu duk irin yadda yake bata kulawa haka zaiyiwa Izzatu? Gaskiya taga kokarin Izzatu sosai da ta bari Hamza ya aurota. Bata fatan ranar da Hamza zai nemi karin aure, gani take ciwon zuciya ne kawai zai kamata. Da wannan tunanin Zuhra ta rinka kuka wanda ta kasa gane dalilin yinsa. A hankali Hamza ya bude kofar dakin ya shigo. Fitilar a kashe take amma yana iya jin sautin kukanta a hankali. Cikin sauri ya kunna fitilar ya karasa gefen gadon ya zauna. Zuhra na jinsa taki kulawa sai wani hawayen da yafi na da. Muryarsa a sanyaye yace to bari na tafi tunda baki so zuwan nawa ba. Yana rufe baki ta tashi zumbur ta rungume kam tana kuka mai sauti. Shima rungumetan yayi tare da sauke ajiyar zuciya. Ashe dai ba shi kadai yake sonta sosai ba. Sun jima yana rarrashinta har ya samu tayi shiru tana mayar da numfashi. Dago kanta tayi ya shafa fuskar yana goge mata hawaye...Cutie haka kike da kishi? Ina da aiki a gabana kenan. Ni da nake so idan an tashi rabon kwana ya zama sati bibbiyu. Kyakkyawan mintsini yaji a hannunsa sakamakon maganar da yayi ya daga hannun yana yarfewa....banda kishi harda mugunta a lamarinki. Zuhra ta harare shi...ni ka tashi ka tafi tunda abinda kazo fada min kenan. Dan bakin da take turowa ya kama da nashi yana kissing. Bata dade ba ta manta ta fushin ta biye masa. Bayan dan lokaci ta ture shi ya tambayeta dalili...ance babu kyau satar kwana. Dariya yayi kafin yace wa ya fada miki satar kwana nazo yi? Sai gobe ya kamata muyi maganar rabon kwanan amma kawai sai naji ki shiru. Zuhra tace naga ta dade bata gida ita ya kamata ta kwana. Nima bazan so ayi min haka ba. Ka tashi ka tafi. Ya shafa lips dinta...sai da kika gama cinye min baki zaki ce na tafi. Sunkuyar da kanta tayi tana murmushi. Ya dago fuskata suka hada ido tayi saurin kawar da kanta....gobe akwai albishir da zanyi miki maidadi Cutie. Ki tanadi tukwicin da zaki bani. Ba a son ransa ya tashi zai barta ba. Yana cikin tafiya yaji Zuhra tace..Ya Hamza I love you. Iyakar karfin zuciyarsa ya tattaro ya fasa komawa wurinta. I love you more Cutie. Goodnight. **** Izzatu ta cika fam kiris ya rage ta fashe. Hamza daga rufe kofa ina ya tsaya sama da minti goma. Zuciyarta tafi zargin yana dakin yarinyar da a yanzu ta tabbatar asirce mata miji tayi. Da sannu zata kama ta a hannu. Alkawari ne sai ta bar mata gidanta. Da ya shigo dakin ko kallonsa bata yi ba ta tafi ta kwanta. Dama haka yake so, kwanciyarsa yayi ya juya mata baya yana tunanin Zuhransa. A haka bacci ya soma daukar shi. Hannun Izzatu yaji ta rungume shi...Baby ko goodnight kiss bazan samu ba? A goshinta yayi mata peck..goodnight Izzy. AL'ADUN WASU #71 Batul Mamman(Mrs)# A yadda Zuhra ta sani idan akace yau girkin mace ne to ita ke da alhakin ciyar da jama'ar gidanta. Sai gashi har tara da rabi Izzatu bata fito ba balle ta fadi me Tala zata dafa idan bazata yi da kanta ba. Su Nana tun wurin takwas suka tashi suka tafi dakin Zuhra. Dole ta farka daga bacci suka sauko kasa tare. Zaman jiran Izzatu suke yi amma shiru, karshe Zuhra ta tashi dama gudun rigima yasa bata dora komai ba tun farko. Kitchen ta shiga ta hada tea a wani jug din roba ta dauko bread guda da butter. A falo ta zauna tana ci tana bawa yaran ko kopi bata dauko ba. Suna haka Izzatu da Hamza suka sauko tare duk sunyi wanka. Tana ganin abinda Zuhra keyi ta soma fada don me zata hada breakfast bayan ba ita ke da girki ba. Zuhra ta dan ware ido ni fa ba girki nayi ba. Yunwa nake ji na hada tea shine naga suna so na basu a nawa. Izzatu ta harareta, tea din cikinki ke kadai shine kika hada a jug? Zuhra tace to ni haka na saba ki tambayi kowa a gidan nan. Tana gama magana ta tashi da jug din da suka shanye da ledar bread ita kuma kadan suka rage. Sama ta wuce ko kallon wurin da Hamza yake bata yi ba saboda tsabar kishin da taji ganin sun sauko tare da Izzatu. Shima baiyi mata magana ba sai dariya da ta bashi. Zuhra daru, ita kuma irin nata kishin kenan. Dole ya koya mata ba'a kyale miji saboda kishi kada hankalinsa ya koma kan kishiya gabadaya. Sannan yadda ta ciyar masa da yara yaji dadi. Duk abin Izzatu bazata ce anyi mata karambani ba. Ya dade yana tashinta daga bacci amma taki tashi. Shi da su Tala ranar sun gasu don sai shadaya da rabi ta gama suyar pancake ta hada custard. Gudu biyu aka sakawa maigadi da custard a dan karamin kofin roba. Yana gani yasan cewa lokacin gashin kuma ya dawo. ***** Sai bayan la'asar Hamza ya taso daga wurin aiki. Yana zuwa gida yayi wanka ya bukaci ganin Izzatu da Zuhra a falonsa. A jikinsa Izzatu ta zauna tana ta wani shige masa. A haka Zuhra ta shigo ta same su. Tamkar tasa ihu haka taji. Hamza yayi ta kokarin ture Izzatu tana kara manne masa. Karshe da yace ta dan matsa sai da tayi masa kiss a kumatu ta matsa gefe. Yana kallon sanda hawaye ya zubo daga idon Zuhra tayi saurin gogewa. A take yaji tausayinta ya kama shi kamar yaje ya dauketa. Gyaran murya yayi sannan ya fara da ambaton Allah kafin ya sanar dasu dalilin kiran. Duk su biyun yake kallo yace...kamar yadda kuka sani duk wani magidanci yakan tara iyalinsa a lokacin da ya kara aure domin ya sanar dasu abinda yake bukata daga garesu na dangane da zaman lafiya a gidansa. Kowacce a cikinki sadaki na biya na aureta saboda haka babu wadda zan wulakanta kuma bazan yarda wata cikinku ta wulakanta ta ba. Abubuwa da dama sun faru tun kafin auren nan har zuwa yanzu amma ina fata mu manta da komai mu gina rayuwarmu bisa doron addini. Zaman lafiya da kwanciyar hankali nake bukata daga gareku ni kuma in sha Allah zanyi kokarin yin adalci a tsakaninku. Sai maganar rabon kwana.... Izzatu tayi saurin katse shi...rabon kwana ai ba sai anja zance ba a rinka yin sati sati... Da sauri Zuhra ta dago suka hada ido da Hamza. Ko batayi magana ba yasan yadda ya hango shirme a shawarar Izzatu itama haka ta gani...Izzy sati daya yayi yawa,yadda muka saba ji anayi muma haka zamuyi wato kwana bibbiyu. Izzatu tace to naji amma sai an rama min kwanakin da nayi da bana nan. Ga sati biyun zuwa Kaduna da Abuja sannan ga kwanakin zaman asibiti tara. Hamza yace wannan sunansa lalura saboda haka ki manta dashi kawai. Gobe Cutie zata karbi girki and that is final. Sannan babu takura kowa zata yi girkinta. Wadda take da girki zata yi dani da su Khalifa da masu aiki. Abu na karshe dole mai girki tayi breakfast kafin tara ya zama ready, abin rana kada ya wuce azahar sannan na dare kada ya wuce magriba. Akwai mai tambaya? Zuhra tace babu, ina iya tafiya? Hamza yayi murmushi yana kallon rigima ta Zuhra. Ita da gaske fushi take yi dashi...to idan babu ni ina da abin fada. Nan ya sanar dasu sakon da ya samu daga wurin minister. Wani ihun murna Izzatu tayi sannan ta haye cinyarsa ko la'akari da Zuhra bata yi ba....ni nasan abinda yafi wannan ma zaka iya Baby. Am so proud of you. Tana ta kankame shi wani abin ma da gayya take yi Zuhra ta tashi don bazata juri kallon wannan kayan bacin ran ba. Tana fita Izzatu tayi dariya a ranta tace yarinya baki ga komai ba. Hamza dai tureta yayi yabi bayan Zuhra. ***** A kan kujerar dakinta ya sameta tana kuka. Ya rufe kofar harda saka key ya dawo kusa da ita ya zauna. Jikinsa ya janyota ta ture shi. Hannuwanta ya kama yace kalle ni nan Cutie. Bata iya masa musu ta dan daga kai amma bata kalli cikin idonsa ba. Yace idan kina irin wannan kishin to kishiya ta gama dake. Wa ya fada miki ana share miji saboda kishi? Baki san sai nayi fushi ba nima na dena kulaki. Wadda tafi kulawa dani sai na tare a wurinta ke kuma sai lokacin da naga dama zan nemeki. A dan tsorace Zuhra tace...Allah ko? To ya zanyi Ya Hamza? Cike da tausayinta ya dorata a cinyarsa tare da rungumeta a jikinsa...kinsan wani abin yi za'ayi kawai don kiji haushi saboda haka ko anyi kiyi kamar baki gani ba. Sannan ki yawaita addua Allah Ya rage miki kishin da zai cutar dake. Ranar da nake tare dake kuma kema sai ki dage wurin kyautata kin yadda zanyi ta tunaninki koda bama tare. Murmushin jindadi tayi...nagode Ya Hamzana..dazun ma kune kuke ta wasu abubuwa a gabana. Don Allah ai kaga dole naji babu dadi. Fuskarta ta rike a tsakanin tafukan hannunsa...nasan fushin duk na meye bari kema na baki rabonki. Matsowa taga yayi yana neman hade bakinsa da nata tayi saurin sa hannu ta tare. Ya Hamza babu kyau irin wannan fa. Yanzu idan gobe kayi min haka bansan irin kukan da zanyi ba...ta tashi tsaye ka koma wurinta amma gobe..sai ta kasa karasawa. Dan bakinta ya shafa yace gobe zaki fanshe kwana biyun nan ko yana daga mata gira. Ita dai bata ce komai ba ya fita. Tsalle tayi ta dire akan gado tana hango zuwan gobe. Tana juyinta cikin murna text din Hamza ya shigo wayarta. Sanar da ita yake ta fara shiri da ita zai tafi Lagos ranar litinin. Kasa boye murnarta tayi wanda duk abinda Izzatu tayi mata ya dena tsaya mata a rai. Washegari da ta karbi girki kuwa banda sauran mutan gidan da suka san anyi canji Hamza yaga soyayya daga Zuhra irin wadda bata taba nuna masa ba. 'Yar kunyar nan da take hanata sakewa gefe ta ajiyeta na wannan lokacin. A wannan kwana biyun ko sabuwar amarya taga su Zuhra sai ta kara kallo. An turowa Hamza kudin jirgi shiyasa da kudin hannunsa ya biyawa Zuhra. Tunda a hotel zasu zauna yasan dai zata sha kadaici idan ya fita amma duk yamma zuwa dare zasu kasance tare. Ana gobe zasu tafi ya bata kudi yace taje tayi kitso da kunshi. Unguwarsu tace zata je shiyasa ya kaita gida da kansa. Bakin Umma ranar kamar gonar auduga. Zuhra tayi fes da ita kamar ba ita ba. Suna tare har Baba ya dawo. A tsakar gidansu aka kira mai kunshi tazo ta rangada mata mai kyau. Safara'u 'yar wan Baba da take zaune a gidan yanzu ita tayi mata kitso kanana mai kyau bayan ta wanke kan. Sai dare da Hamza yazo daukarta yake sanar da su Baba zancen tafiyar. Yasha addua da fatan alkhairi. Har gidansu Hajara sai da suka shiga dashi ya gaishe da su Mama sannan suka wuce gida. Izzatu ta gama yanke shawarar biyawa kanta kudin jirgi ta bi Hamza. Har kaya ta gama hadawa ta ajiye kusa da jakar kayansa wadda Zuhra ta hada ranar da zata fita girki. Surprise zata yiwa Hamza idan ya dawo yau. Tasan dole yaji dadi tunda ya sauko ya dena fushin da ita. Bata san kokarin ya kamanta adalci tsakaninta da Zuhra yasa taga saurin shiryawarsu ba. Da suka dawo kowa dakinsa ya nufa. Izzatu ta kawo masa abinci yaci sannan yake tambayarta game da jaka da ya gani kusa da kayansa. Da dan murmushinta tace kayana ne na tafiyarmu gobe. Ba shiri ya tashi yana kallonta. Wane irin kayan tafiyarmu gobe? Ni nace zan tafi dake ne ko me? Izzatu tace kwantar da hankalinka zan biyawa kaina kudin jirgi. Shiyasa ban fada maka ba saboda nasan zaka ji dadi idan na fada lokacin da baka tsammani. Hamza ya hade rai...to kinyi kuskure da Zuhra zani.... A fusace ta tashi itama...wallahi baka isa ba Hamza. Ni zaka rinka wulakantawa akan wannan yarinyar. Shekararta ashirin da daya fa har zaka hada ta da mace kamar ni. Kuma meyasa baka fada min ba da wuri? Girgiza kai yayi yana mamakin yadda take daga masa murya. Ban fada miki ba saboda gudun kada kizo ki tayar min da rigima kice sai kinje. Amma naga alama hakan ya zama kuskure. Ki zauna a gida ki karasa jinyar jikinki lafin mu dawo. Kuma bana son cigaba da maganar nan don banyi niya ba saboda haka idan wata tafiyarar tazo sai nayi dake idan naga dama. Ficewa tayi daga dakin ta tafi dakin Zuhra rai a bace ta buga kofar da karfi tana masifa....Zuhra ki kiyayeni wallahi. Ki bar ganin na kyaleki lokaci na baki kafin na koreki daga gidan nan. Hamza da yake bayanta yace tunda ki kike auranta ba. To kema ki kiyayeni wallahi ko gobe mu tafi airport tare ki koma gidanku. Kada ki kaini bango Izzy darajar 'ya'ya kawai kike ci kema kuma kin sani. Zuhra dai kallonsu take daya bayan daya ta kasa magana. Tana kallo Hamza yaja hannun Izzatu suka fita. Ranar basuyi baccin arziki ba saboda yadda take ta fada. Sai da Hamza yace idan ta saki bude baki a bakin igiyar aurenta. Cikin masifa tace guda nawa? Yace sai kinyi maganar zan sanar dake ko nawa kika tsinke. Ba arziki ta yi shiru amma ta gama sikewa da Zuhra. Dole tasan yadda zata yi da ita kafin tayi sanadiyar kashe mata aure. Tun bayan asuba Zuhra tayi wanka ta gama shiri saboda Hamza ya fada mata jirginsu karfe bakwai zai tashi. Shima da wuri ya shirya ya shiga dakinta. Sai kai kawo take yi a tsakar daki. Tana ganinshi ta gaishe shi yace wannan tafiyar ta meye? Kinci abinci kuwa? Zuhra tace wane irin abinci Ya Hamza? Cikina sai kullewa yake saboda fargaba. Anya zan iya shiga jirgin kuwa. Yayi dariya idan bazaki iya ba sai na tafi da yayarki. Jin haka Zuhra ta fita daga dakin da sauri har tana tuntube. Shi ya dauko mata akwatin kayanta yabi bayanta. Da kyar ya samu tasha tea duk hankalinta baya jikinta. A tsorace kawai take da maganar shiga jirgi. Basu dade ba Nura yazo daukarsu shi zai kai su airport din. Har suka fita Izzatu ko kofar daki bata fito ba. Ana shiga airport Zuhra na kara razana. Gabadaya a tsorace take. Hamza kuwa sai dariya yace yau ga 'yar kauye ga jirgi. Kamar tayi kuka tace Ya Hamza ko dai mu tafi tasha ne mu sami mota. Ya kama hannunta ya rike....Cutie kada ki damu babu inda zanje in barki kinji ko. A hankali ta gyada kai. Cikin dan lokaci ya karbar mata ticket suka fita inda jirgin yake. Layi suka bi tare da wasu masu tafiyar. Zuhra sai kallo wai ita ce yau zata shiga jirgin sama. Ga wasu manyan jiragen da suka fi wanda zasu shiga ma. Tana rike da hannun Hamza tace kuma yanzu a iska dreban jirgin yake gane hanya ko akwai alama da ake sakawa yadda bazasu bata ba? Yace wurin tukin nasu ne yake aiki da na'ura mai kwakwalwa tana nuna musu hanya sannan daga can airport dinma ana yi musu bayani... Suna shiga ciki har suka zauna ya daura mata seat belt yana mata bayanin yadda jirgi ke tafiya a sama. Kusa da taga ya zaunar da ita shi kuma yana gefe. Sai da ya gama bayaninsa tace ni dai duk bangane ba. Hamza ya ja mata kunne,amma shine kika barni ina ta surutu ko? A hankali jirgin ya fara tafiya a kasa cikin Zuhra ya murda don tsoro ta kankame Hamza. Ihu taso yi lokacin da ya fara tashi har ta bude baki yayi saurin rufe shi da nasa. Bai kyaleta ba sai da yaji sun daidaita a sama. Da sauri da sauri take fitar da numfashi ta dan bata fuska Ya Hamza muna cikin wannan yanayin wa yake ta soyayya? Sai da ya ja hancinta sannan yace ai magana ta kare tunda soyayyar ta hana ki cikawa mutane kunne da ihu. Harda wani kara lafewa a jikina,kai wannan yarinya kin zama abinda kika zama. Kunya taji da kawar da kanta tana kallon waje. Daga nan hirar ta koma ta abubuwan da take gani. Suna haka aka kawo abinci. Zuhra tace kaji fitina har mutum yana da nutsuwar cin abinci a nan. Hamza yayi dariya yau yaga shirme wurin Cutie kala kala. Har dan bacci tayi wanda ta farka lokacin da jirgin ya fara sauka kasa. Taxi suka samu zuwa hotel din da aka ce suje ana ya hadu da wasu mutum biyu da suma basu dade da zuwa ba suka gaisa. Mukullan dakunansu aka basu sannan mutumin da aka turo wurinsu ya sanar dasu karfe goma mota zata zo daukarsu saboda a yau zasu fara abinda ya kawosu. Sai da Hamza ya tabbatar Zuhra ta sami nutsuwa sannan yayi wanka ya shirya. Kashedi yayi mata kada ta bude kofar sai karfe daya lokacin da yayi magana da receptionist za'a kawo mata abincin rana. Kamar kada su rabu lokacin da zai fita. Tayi ta masa addua sannan suka yi sallama. Hajiya Izzatu har karfe uku bata fito daga daki ba. Tala ce tayi komai. Wayar kawarta wata baturiya Laura ta kira ta sanar da ita halin kuncin da Hamza ya sakata a ciki. AL'ADUN WASU #71 Batul Mamman(Mrs)# A yadda Zuhra ta sani idan akace yau girkin mace ne to ita ke da alhakin ciyar da jama'ar gidanta. Sai gashi har tara da rabi Izzatu bata fito ba balle ta fadi me Tala zata dafa idan bazata yi da kanta ba. Su Nana tun wurin takwas suka tashi suka tafi dakin Zuhra. Dole ta farka daga bacci suka sauko kasa tare. Zaman jiran Izzatu suke yi amma shiru, karshe Zuhra ta tashi dama gudun rigima yasa bata dora komai ba tun farko. Kitchen ta shiga ta hada tea a wani jug din roba ta dauko bread guda da butter. A falo ta zauna tana ci tana bawa yaran ko kopi bata dauko ba. Suna haka Izzatu da Hamza suka sauko tare duk sunyi wanka. Tana ganin abinda Zuhra keyi ta soma fada don me zata hada breakfast bayan ba ita ke da girki ba. Zuhra ta dan ware ido ni fa ba girki nayi ba. Yunwa nake ji na hada tea shine naga suna so na basu a nawa. Izzatu ta harareta, tea din cikinki ke kadai shine kika hada a jug? Zuhra tace to ni haka na saba ki tambayi kowa a gidan nan. Tana gama magana ta tashi da jug din da suka shanye da ledar bread ita kuma kadan suka rage. Sama ta wuce ko kallon wurin da Hamza yake bata yi ba saboda tsabar kishin da taji ganin sun sauko tare da Izzatu. Shima baiyi mata magana ba sai dariya da ta bashi. Zuhra daru, ita kuma irin nata kishin kenan. Dole ya koya mata ba'a kyale miji saboda kishi kada hankalinsa ya koma kan kishiya gabadaya. Sannan yadda ta ciyar masa da yara yaji dadi. Duk abin Izzatu bazata ce anyi mata karambani ba. Ya dade yana tashinta daga bacci amma taki tashi. Shi da su Tala ranar sun gasu don sai shadaya da rabi ta gama suyar pancake ta hada custard. Gudu biyu aka sakawa maigadi da custard a dan karamin kofin roba. Yana gani yasan cewa lokacin gashin kuma ya dawo. ***** Sai bayan la'asar Hamza ya taso daga wurin aiki. Yana zuwa gida yayi wanka ya bukaci ganin Izzatu da Zuhra a falonsa. A jikinsa Izzatu ta zauna tana ta wani shige masa. A haka Zuhra ta shigo ta same su. Tamkar tasa ihu haka taji. Hamza yayi ta kokarin ture Izzatu tana kara manne masa. Karshe da yace ta dan matsa sai da tayi masa kiss a kumatu ta matsa gefe. Yana kallon sanda hawaye ya zubo daga idon Zuhra tayi saurin gogewa. A take yaji tausayinta ya kama shi kamar yaje ya dauketa. Gyaran murya yayi sannan ya fara da ambaton Allah kafin ya sanar dasu dalilin kiran. Duk su biyun yake kallo yace...kamar yadda kuka sani duk wani magidanci yakan tara iyalinsa a lokacin da ya kara aure domin ya sanar dasu abinda yake bukata daga garesu na dangane da zaman lafiya a gidansa. Kowacce a cikinki sadaki na biya na aureta saboda haka babu wadda zan wulakanta kuma bazan yarda wata cikinku ta wulakanta ta ba. Abubuwa da dama sun faru tun kafin auren nan har zuwa yanzu amma ina fata mu manta da komai mu gina rayuwarmu bisa doron addini. Zaman lafiya da kwanciyar hankali nake bukata daga gareku ni kuma in sha Allah zanyi kokarin yin adalci a tsakaninku. Sai maganar rabon kwana.... Izzatu tayi saurin katse shi...rabon kwana ai ba sai anja zance ba a rinka yin sati sati... Da sauri Zuhra ta dago suka hada ido da Hamza. Ko batayi magana ba yasan yadda ya hango shirme a shawarar Izzatu itama haka ta gani...Izzy sati daya yayi yawa,yadda muka saba ji anayi muma haka zamuyi wato kwana bibbiyu. Izzatu tace to naji amma sai an rama min kwanakin da nayi da bana nan. Ga sati biyun zuwa Kaduna da Abuja sannan ga kwanakin zaman asibiti tara. Hamza yace wannan sunansa lalura saboda haka ki manta dashi kawai. Gobe Cutie zata karbi girki and that is final. Sannan babu takura kowa zata yi girkinta. Wadda take da girki zata yi dani da su Khalifa da masu aiki. Abu na karshe dole mai girki tayi breakfast kafin tara ya zama ready, abin rana kada ya wuce azahar sannan na dare kada ya wuce magriba. Akwai mai tambaya? Zuhra tace babu, ina iya tafiya? Hamza yayi murmushi yana kallon rigima ta Zuhra. Ita da gaske fushi take yi dashi...to idan babu ni ina da abin fada. Nan ya sanar dasu sakon da ya samu daga wurin minister. Wani ihun murna Izzatu tayi sannan ta haye cinyarsa ko la'akari da Zuhra bata yi ba....ni nasan abinda yafi wannan ma zaka iya Baby. Am so proud of you. Tana ta kankame shi wani abin ma da gayya take yi Zuhra ta tashi don bazata juri kallon wannan kayan bacin ran ba. Tana fita Izzatu tayi dariya a ranta tace yarinya baki ga komai ba. Hamza dai tureta yayi yabi bayan Zuhra. ***** A kan kujerar dakinta ya sameta tana kuka. Ya rufe kofar harda saka key ya dawo kusa da ita ya zauna. Jikinsa ya janyota ta ture shi. Hannuwanta ya kama yace kalle ni nan Cutie. Bata iya masa musu ta dan daga kai amma bata kalli cikin idonsa ba. Yace idan kina irin wannan kishin to kishiya ta gama dake. Wa ya fada miki ana share miji saboda kishi? Baki san sai nayi fushi ba nima na dena kulaki. Wadda tafi kulawa dani sai na tare a wurinta ke kuma sai lokacin da naga dama zan nemeki. A dan tsorace Zuhra tace...Allah ko? To ya zanyi Ya Hamza? Cike da tausayinta ya dorata a cinyarsa tare da rungumeta a jikinsa...kinsan wani abin yi za'ayi kawai don kiji haushi saboda haka ko anyi kiyi kamar baki gani ba. Sannan ki yawaita addua Allah Ya rage miki kishin da zai cutar dake. Ranar da nake tare dake kuma kema sai ki dage wurin kyautata kin yadda zanyi ta tunaninki koda bama tare. Murmushin jindadi tayi...nagode Ya Hamzana..dazun ma kune kuke ta wasu abubuwa a gabana. Don Allah ai kaga dole naji babu dadi. Fuskarta ta rike a tsakanin tafukan hannunsa...nasan fushin duk na meye bari kema na baki rabonki. Matsowa taga yayi yana neman hade bakinsa da nata tayi saurin sa hannu ta tare. Ya Hamza babu kyau irin wannan fa. Yanzu idan gobe kayi min haka bansan irin kukan da zanyi ba...ta tashi tsaye ka koma wurinta amma gobe..sai ta kasa karasawa. Dan bakinta ya shafa yace gobe zaki fanshe kwana biyun nan ko yana daga mata gira. Ita dai bata ce komai ba ya fita. Tsalle tayi ta dire akan gado tana hango zuwan gobe. Tana juyinta cikin murna text din Hamza ya shigo wayarta. Sanar da ita yake ta fara shiri da ita zai tafi Lagos ranar litinin. Kasa boye murnarta tayi wanda duk abinda Izzatu tayi mata ya dena tsaya mata a rai. Washegari da ta karbi girki kuwa banda sauran mutan gidan da suka san anyi canji Hamza yaga soyayya daga Zuhra irin wadda bata taba nuna masa ba. 'Yar kunyar nan da take hanata sakewa gefe ta ajiyeta na wannan lokacin. A wannan kwana biyun ko sabuwar amarya taga su Zuhra sai ta kara kallo. An turowa Hamza kudin jirgi shiyasa da kudin hannunsa ya biyawa Zuhra. Tunda a hotel zasu zauna yasan dai zata sha kadaici idan ya fita amma duk yamma zuwa dare zasu kasance tare. Ana gobe zasu tafi ya bata kudi yace taje tayi kitso da kunshi. Unguwarsu tace zata je shiyasa ya kaita gida da kansa. Bakin Umma ranar kamar gonar auduga. Zuhra tayi fes da ita kamar ba ita ba. Suna tare har Baba ya dawo. A tsakar gidansu aka kira mai kunshi tazo ta rangada mata mai kyau. Safara'u 'yar wan Baba da take zaune a gidan yanzu ita tayi mata kitso kanana mai kyau bayan ta wanke kan. Sai dare da Hamza yazo daukarta yake sanar da su Baba zancen tafiyar. Yasha addua da fatan alkhairi. Har gidansu Hajara sai da suka shiga dashi ya gaishe da su Mama sannan suka wuce gida. Izzatu ta gama yanke shawarar biyawa kanta kudin jirgi ta bi Hamza. Har kaya ta gama hadawa ta ajiye kusa da jakar kayansa wadda Zuhra ta hada ranar da zata fita girki. Surprise zata yiwa Hamza idan ya dawo yau. Tasan dole yaji dadi tunda ya sauko ya dena fushin da ita. Bata san kokarin ya kamanta adalci tsakaninta da Zuhra yasa taga saurin shiryawarsu ba. Da suka dawo kowa dakinsa ya nufa. Izzatu ta kawo masa abinci yaci sannan yake tambayarta game da jaka da ya gani kusa da kayansa. Da dan murmushinta tace kayana ne na tafiyarmu gobe. Ba shiri ya tashi yana kallonta. Wane irin kayan tafiyarmu gobe? Ni nace zan tafi dake ne ko me? Izzatu tace kwantar da hankalinka zan biyawa kaina kudin jirgi. Shiyasa ban fada maka ba saboda nasan zaka ji dadi idan na fada lokacin da baka tsammani. Hamza ya hade rai...to kinyi kuskure da Zuhra zani.... A fusace ta tashi itama...wallahi baka isa ba Hamza. Ni zaka rinka wulakantawa akan wannan yarinyar. Shekararta ashirin da daya fa har zaka hada ta da mace kamar ni. Kuma meyasa baka fada min ba da wuri? Girgiza kai yayi yana mamakin yadda take daga masa murya. Ban fada miki ba saboda gudun kada kizo ki tayar min da rigima kice sai kinje. Amma naga alama hakan ya zama kuskure. Ki zauna a gida ki karasa jinyar jikinki lafin mu dawo. Kuma bana son cigaba da maganar nan don banyi niya ba saboda haka idan wata tafiyarar tazo sai nayi dake idan naga dama. Ficewa tayi daga dakin ta tafi dakin Zuhra rai a bace ta buga kofar da karfi tana masifa....Zuhra ki kiyayeni wallahi. Ki bar ganin na kyaleki lokaci na baki kafin na koreki daga gidan nan. Hamza da yake bayanta yace tunda ki kike auranta ba. To kema ki kiyayeni wallahi ko gobe mu tafi airport tare ki koma gidanku. Kada ki kaini bango Izzy darajar 'ya'ya kawai kike ci kema kuma kin sani. Zuhra dai kallonsu take daya bayan daya ta kasa magana. Tana kallo Hamza yaja hannun Izzatu suka fita. Ranar basuyi baccin arziki ba saboda yadda take ta fada. Sai da Hamza yace idan ta saki bude baki a bakin igiyar aurenta. Cikin masifa tace guda nawa? Yace sai kinyi maganar zan sanar dake ko nawa kika tsinke. Ba arziki ta yi shiru amma ta gama sikewa da Zuhra. Dole tasan yadda zata yi da ita kafin tayi sanadiyar kashe mata aure. Tun bayan asuba Zuhra tayi wanka ta gama shiri saboda Hamza ya fada mata jirginsu karfe bakwai zai tashi. Shima da wuri ya shirya ya shiga dakinta. Sai kai kawo take yi a tsakar daki. Tana ganinshi ta gaishe shi yace wannan tafiyar ta meye? Kinci abinci kuwa? Zuhra tace wane irin abinci Ya Hamza? Cikina sai kullewa yake saboda fargaba. Anya zan iya shiga jirgin kuwa. Yayi dariya idan bazaki iya ba sai na tafi da yayarki. Jin haka Zuhra ta fita daga dakin da sauri har tana tuntube. Shi ya dauko mata akwatin kayanta yabi bayanta. Da kyar ya samu tasha tea duk hankalinta baya jikinta. A tsorace kawai take da maganar shiga jirgi. Basu dade ba Nura yazo daukarsu shi zai kai su airport din. Har suka fita Izzatu ko kofar daki bata fito ba. Ana shiga airport Zuhra na kara razana. Gabadaya a tsorace take. Hamza kuwa sai dariya yace yau ga 'yar kauye ga jirgi. Kamar tayi kuka tace Ya Hamza ko dai mu tafi tasha ne mu sami mota. Ya kama hannunta ya rike....Cutie kada ki damu babu inda zanje in barki kinji ko. A hankali ta gyada kai. Cikin dan lokaci ya karbar mata ticket suka fita inda jirgin yake. Layi suka bi tare da wasu masu tafiyar. Zuhra sai kallo wai ita ce yau zata shiga jirgin sama. Ga wasu manyan jiragen da suka fi wanda zasu shiga ma. Tana rike da hannun Hamza tace kuma yanzu a iska dreban jirgin yake gane hanya ko akwai alama da ake sakawa yadda bazasu bata ba? Yace wurin tukin nasu ne yake aiki da na'ura mai kwakwalwa tana nuna musu hanya sannan daga can airport dinma ana yi musu bayani... Suna shiga ciki har suka zauna ya daura mata seat belt yana mata bayanin yadda jirgi ke tafiya a sama. Kusa da taga ya zaunar da ita shi kuma yana gefe. Sai da ya gama bayaninsa tace ni dai duk bangane ba. Hamza ya ja mata kunne,amma shine kika barni ina ta surutu ko? A hankali jirgin ya fara tafiya a kasa cikin Zuhra ya murda don tsoro ta kankame Hamza. Ihu taso yi lokacin da ya fara tashi har ta bude baki yayi saurin rufe shi da nasa. Bai kyaleta ba sai da yaji sun daidaita a sama. Da sauri da sauri take fitar da numfashi ta dan bata fuska Ya Hamza muna cikin wannan yanayin wa yake ta soyayya? Sai da ya ja hancinta sannan yace ai magana ta kare tunda soyayyar ta hana ki cikawa mutane kunne da ihu. Harda wani kara lafewa a jikina,kai wannan yarinya kin zama abinda kika zama. Kunya taji da kawar da kanta tana kallon waje. Daga nan hirar ta koma ta abubuwan da take gani. Suna haka aka kawo abinci. Zuhra tace kaji fitina har mutum yana da nutsuwar cin abinci a nan. Hamza yayi dariya yau yaga shirme wurin Cutie kala kala. Har dan bacci tayi wanda ta farka lokacin da jirgin ya fara sauka kasa. Taxi suka samu zuwa hotel din da aka ce suje ana ya hadu da wasu mutum biyu da suma basu dade da zuwa ba suka gaisa. Mukullan dakunansu aka basu sannan mutumin da aka turo wurinsu ya sanar dasu karfe goma mota zata zo daukarsu saboda a yau zasu fara abinda ya kawosu. Sai da Hamza ya tabbatar Zuhra ta sami nutsuwa sannan yayi wanka ya shirya. Kashedi yayi mata kada ta bude kofar sai karfe daya lokacin da yayi magana da receptionist za'a kawo mata abincin rana. Kamar kada su rabu lokacin da zai fita. Tayi ta masa addua sannan suka yi sallama. Hajiya Izzatu har karfe uku bata fito daga daki ba. Tala ce tayi komai. Wayar kawarta wata baturiya Laura ta kira ta sanar da ita halin kuncin da Hamza ya sakata a ciki. AL'ADUN WASU #72 Batul Mamman(Mrs)# Laura ta gama jin korafin Izzatu tayi tsaki tace.... Duk laifinku ne 'yan Nigeria. Kuna bawa iyayenku mahimmanci fiye da yadda ya kamata. Na tabbata duk abinda mijinki yake miki yanzu don ya faranta musu ne. Izzatu tace hakane amma kinsan mu addininmu da al'ada duk basu yarda da rashin biyayya ga iyaye ba. To ai kuwa bazaki dena ganin bacin rai ba Izzy...Laura ta fada tana kara jin haushin al'ada irin ta hausawa....idan baki manta ba sai da nace kada ki yarda kuyi aure. Ku zauna tare ku haihu kamar yadda nayi. Duk lokacin da kika gaji dashi ki tattara ki bar masa gidan amma kika ki. Shawara daya zan baki shine kice ya zaba ko ke ko iyayensa da wannan matar da ya auro. Ni kinga mahaifiyata ce bata son Phil kinga tuni na yakiceta. Sai karshen shekara muke haduwa a wurin anniversary din mutuwar babana. Izzatu tayi kasake tana jin gurguwar shawarar Laura. A ranta tace duk ranar da ta bawa Hamza wannan zabin to ko minti biyar tasan bazata kara a gidan ba. Su turawa basu san al'adunmu akwai bambanci ba. A gurguje tayi sallama da Laura domin ta fuskanci shawararta tamkar ta kama kafar wala ne. Dole ta sake sabuwar shawara amma zaman Zuhra a gidan nan bazarana yake ga igiyar aurenta. ****** Kullum karfe goma Hamza yake fita sai takwas na dare yake dawowa. Kafin ya dawo Zuhra zata wuni bacci amma yana dawowa to fa sai a bude soyayya. Zamansu suke lafiya cike da kwanciyar hankali. Basu da wata damuwa sai ta junansu. Kullum dai zai kira Izzatu kuma zai gaisa da 'ya'yansa. Rashin lokaci yasa bai sami damar kai Zuhra ko'ina ba. Amma ita kasancewarsu tare ya isheta shiyasa bata damunsa da su fita. Ranar da zasuyi jarabawa Zuhra tayi ta masa addua. Karfe uku ya dawo ranar ya dauketa suka sami taxi suka fita gari. Shine har bakin ruwa(beach)ya kaita. Suka dan zagaya kasuwa ya siyawa Zuhra kananan kaya masu kyau don yaga bata dasu sosai. Wata rigar idan ya dauko sai taji kunya. Asabar da lahadi ma duk yawo ya kaita sai ranar litinin suka biyo jirgin safe suka koma Kano. Wannan karon kauyancin Zuhra ya ragu. Nura ne ya sake zuwa daukarsu amma sai da ya biya gida ya gaisa da iyayensa sannan suka wuce nasu gidan. Tun asuba Izzatu tasa Tala guaran gida ita kuma aka shige kitchen girkin tarar maigida. Tana jin tsayuwar mota tun daga bakin kofa ta taresu ta kankame Hamza tana murna. Kiss take zuba masa ko ta ina a fuska ga Nura a bayansa dauke da jaka sai kawar da kai yake sannan ga Zuhra da ta hade rai. Izzatu tayi dariyar keta, ko babu komai tasan Zuhra bazata iya yin abinda tayi ba. Shi kanshi Hamzan yanzu sai da yaji kunya sabanin da da suke abinsu hankali kwance. Ko zama baiyi ba taja hannunsa suka tafi daki tana fada masa yadda tayi missing dinsa. Zancen yaya aikin da ya kaishi kuwa ko a waya bata yi. Bata da zance sai na korafin ya tafi ya barta. Haka rayuwa ta kasance musu kowacce ranar girkinta tana kokarin farantawa mijinta rai. Kwanansu biyar da dawowa Hamza ya sami sako cewa yayi na uku a jarabawarsu ana bukatar ya kai passport dinsa Abuja ofishin minister domin neman visa. Da farincikinsa ya sanar da Izzatu saboda ranar girkinta ne. Tana jin haka ta tashi ta nufi dakinta. Hamza ya bi bayanta da sauri don ya zata wani abin ne ya faru...Izzy saurin me kike yi haka ko gama sauraron abinda nace bakiyi ba? Wardrobe ta bude ta janyo wata jaka sannan ta fuskance shi...naji abinda kace mana. Sai dai Sweety nasan ba abin mamaki bane idan kayi nasara saboda I believe in you my darling. Kayana zan hada na tafiyarmu Abujan....ta daga jakar sama, kana ganin wannan zata isa ko tayi kankanta? Rasa bakin magana yayi sai binta yake da ido kamar lokacin ya fara ganinta. Babu godewa Allah, babu taya shi murna sai jaka da ta dauko zata hada kaya bayan shi kanshi bai sami cikakken bayani game da tafiyar ba. A kalla jakar zata dauki kaya bakwai zuwa goma idan an cusa su sosai. Ko ya fada mata a Abuja zasu yi course din ne bai sani ba. Haka ya fita ya barta ba tare da ya bata amsa ba ya tafi dakin Zuhra. Kulu ne tumuli guda a gabanta tana warewa saboda ya samar mata wata makarantar sun bada kwangilar sakar rigunan sanyin makaranta. Da murmushi ta tarbe shi tace Ya Hamza ba na hanaka satar kwana ba? Shima murmushin yayi ai kece satar kwanan. Ace mutum bashi da ikon ganin matarsa sai ranar girkinta. Kusa da ita yaje ya zauna ya kama hannunta ya rike. Cutie albishirinki? Idonta a kan fuskarsa tace goro Ya Hamzana. Me zaki bani idan na fada miki? Duk abinda kake so indai baifi karfina ba. Ya shafa lebenta da yake kyallin lip gloss da ta saka mai kyau...so nake ki soni har abada kuma kada ki taba rabuwa dani. Maganarsa tasa jikinta yayi sanyi saboda ta lura kamar yana cikin damuwa. A hankali tace Ya Hamza har a aljanna ni matarka ce in sha Allah. Amma nan...ta nuna lebenta...kai dashi sai jibi. Tana magana tana masa dariya. A hankali ya rinka sakewa. Dama bacin ran abinda Izzy tayi masa ne. Cutie nayi nasarar cin wannan jarabawar har ana bukatar ganina a Abuja. Da murna Zuhra ta rungumeshi tana cewa Alhamdulillah. Can sai ta sake shi ta durkusa tayi sujjadar godiya ga Allah SWT. Tayi kusan minti biyu tana hamdala da takbir. Ko da ta dago kanta wasu zafafan hawaye ne suka sauko daga idanun Hamza. Kullum Zuhra daban yake ganinta. A tsorace ta tashi yana daga zaune ta rungumeshi a kirjinta. Murya a raunane tace Ya Hamza me yasa ka hawaye? Muryarsa a can kasa yace Cutie ina sonki. Ina sonki. Ina sonki. Kuma nagode miki for being who you are. Sake kankameshi tayi tace nima ina sonka Ya Hamza. Uhmm sai dai dan turancin nan na karshe kace who you are ko.. Toh, I am Fatima Bashir. Mai Hamza zaiyi in ba dariya ba. Zuhra tayi kicin kicin da fuska ita tayi fushi. Hamza ya rike habarta haba my darling Zuhra? Kada kiyi fushi dani. In sha Allah idan komai ya daidaita na wannan course din da za'a turani zamu fara English lessons dake. Dole na ware lokaci na koya miki da kaina. Zuhra ta turo baki ni bazan koya ba kuma ka tashi ka koma dakinka ni munyi fada. Cakulculi Hamza ya rinka yi mata har ta soma dariya sannan ya fita zuciyarsa fari kal. Washegari da safe ya sami cikakken bayani game da zuwansa Abuja. Da yake abin na gwamnatin tarayya ne kuma da izininsu kwana biyu aka ce zasu yi a tantance su. Babu wani zancen masauki alamun kowa yayi ta kansa kenan. Harda dariyar mugunta ya fadawa Izzatu basu da masauki saboda haka bazai tafi da ita ba. Kila yaje gidan abokinsa ya kwana. Itama dariyar tayi tace ta riga ta sanar da iyayenta batun zuwansu har an gyara musu wurin kwana a gidansu. Baiji dadin wannan karambanin ba shiyasa yace mata baza shi ba. Ko minti ashirin basuyi da maganar ba Alh Sunusi mahaifin Izzatu ya kirashi da kansa yace lallai yazo gidan anyi masa masauki ko da shi kadai ne. To ta yaya zaije gidan shi kadai dole ya tafi da Izzatu. A haka suka rabu yayi shirin tafiya office. Da rana da ya dawo a kitchen yaji motsin Zuhra. Yana shiga ya tarar da ita tana rabon abinci a cikin irin abin take away dinnan. Jallop din shinkafa tayi sai kwai da ta dafa ta yanka shi bibbiyu take sakawa a abincin. Hamza ya dan dauki lokaci yana kallonta bata kula ba saboda ta juyawa kofa baya. A hankali yaje ya rufe mata ido tayi murmushi tace Ya Hamza ka dawo? Cikin wasa ya bata rai, ya akayi kika gane nine? Tace da kamshin turarenka mana. Jera abincin yaga tana yi a wasu manyan robobi yace abincin meye wannan Cutie? Ta dan kalle shi tayi murmushi...ni banso ka dawo ka tarar ban gama ba. Abincin sadaka ne zan bawa maigadi yace akwai makarantar allo a nan baya. Nayi da niyyar Allah Ya baka sa'a kuma Yasa kayi karatun ka gama lafiya. Tana kaiwa nan idonta ya ciko da kwalla, tunanin rabuwarsu da Hamza na wata biyu ke damunta. Shi kuwa kasa magana yayi kamar kodayaushe idan tayi wani abin da yafi karfin tunaninsa. Har abincin sadaka take yi wanda yasan akan yi lokaci lokaci a gidan iyayensa. A take yayi wa kansa alkawari indai ya sami sarari da yardar Allah Hajji zai kai Zuhransa. A duniya dai shine kawai abinda zaiyi mata na karshen jindadi a matsayinta na musulma. Amma a nan kanta ya dafa ya rinka saka mata albarka. Sonta kuwa kullum karuwa yake a zuciyarsa saboda kyawun halayenta. Kwanaki biyu a tsakani su shirya tafiya Abuja. Izzatu sai rawar kafa take kamar farin shiga a zuwa Abuja. A motar Hamza suka tafi da aka gyaro. Zuhra tasha kukanta a daki Hamza na rarrashi sannan ta fito ta rakasu. Kwanansu uku suka dawo aka fara shirye shiryen tafiyar Hamza zuwa kasar South Korea. Kwanaki uku suka rage ya tafi idan kaga Zuhra duk tayi wani iri. Har rama ta danyi saboda zulumin tafiyar Ya Hamza. Dambun nama ta roki Umma tayi mata saboda ita idan tayi duk sai rabi ya kone. Ai kuwa Umma tayi mai dadi musamman da tasan na tafiyar Hamza ne. Da aka kawo yayi ta murna. Izzatu ma a nata bangaren cake tayi masa kanana mai dadi ta jera a wata roba sannan ta liketa saboda kada ya bushe. Itama Hamza yayi mata godiya. Da asuba ana saura kwana biyu ya tafi kuma ranar Zuhra zata fita girki. Tunda ta idar da sallah take masa kuka. Duk abinda zaiyi mata tayi shiru yayi amma minti kadan sai ta cigaba. Ya zuba mata ido kawai yana kallonta. Cutie wai kukan nan na meye? Ba fa yau zan tafi ba. Ta dago jajayen idanunta...to meye maraba Ya Hamza daga yau kai da ka sake kwana...sai tayi shiru kanta a kasa Ya share mata hawaye kina tunanin zanyi wata biyu bamy hada shimfida ba ko? Gashi ke kuma kina son kwanciya a jikin mijinki. Rufe ido tayi a kunyace...ni ba haka nake nufi ba. Hamza yayi dariya yace ai ba sai kin fada ba na sani. Addua kawai nake bukata daga gareki. Kinga jiya munfi awa daya ina nuna miki yadda ake whatsap saboda haka zamuyi ta hira kullum kinji ko. Idan kika yi kwalliya kullum ki turo min hotonki na gani. Ta gyada kai wani hawayen na taruwa a idonta...Ya Hamza yau kada kaje ko'ina har sai lokacin da zan fita girki. Don Allah ka zauna dani. Hannunta ya kama ya tasheta daga kan gadon. Muje har breakfast tare yau zamuyi. Manne jikin juna suka sauko saboda asabar ce su Khalifa basu da makaranta. Sai karfe goma zasu je islamiyyar safe. Kayan kwabin fanke Zuhra ta debo ta fara kwabawa. Hamza taji ya tsaya a bayanta ya zira hannu a robar da take kwabin yana wasa da hannunta sannan yana bin wuyanta yana kissing. Gabadaya aikin gagararta yayi cikin kankanuwar murya tace Ya Hamza don Allah ka bari na gama. Koma can gefen ka tsaya. Yi yayi kamar yayi fushi yace ba ke kika ce kada na barki ba yau. Ni babu inda zani ya fada yana sake rumgumarta ta baya. Muryar Junior ce tasa ya saketa ba shiri da ya shigo kitchen din yana murza ido. Maama fanken zaki yi min don Allah? Zuhra tayi murmushi tace kaga har na gama kwabawa sai mu dan jira ya tashi ko. Rungumeta yayi daidai kafarta yace Maama kinfi sona akan Daddy shiyasa kike dafa abinda nake so.. nima idan na girma ke zan fara siyawa mota da jirgi kafin Mummy da Daddy. Hamza ya bude baki yana kallonsa. Lallai yaran zamani kun iya sa ido. Kai yanzu har kasan so? Ya fada yana daga Junior sama suna dariya. *********** Wannan shafin naki ne Maman twins. Gaisuwarki ta riskeni ina fata nima tawa ta iso gareki. Godiya mai tarin yawa tare da fatan alkhairi. Allah Ya albarkaci zuria.# AL'ADUN WASU ##73 Batul Mamman(Mrs)## Jirginsu Hamza shabiyu da rabi na dare zai tashi shiyasa ya yanke shawarar barin gidan karfe goma domin ya sami damar zuwa gidan iyayensa yayi musu sallama. Sai da ya dawo daga masallaci bayan sallar isha sannan yaci abinci kadan yaje yayi wanka. Gidan duk yayi wani iri saboda kowa na tunanin tafiyar Hamza. Ya shirya cikin kananan kaya yayi kyau sannan ya dauki rigar sanyi a hannu saboda banda sanyin jirgi ya bincika ana sanyi sosai a South Korea. Ya gama shirinsa tsaf suka sake wata sallamar da Izzatu sannan ya fito zaije dakin Zuhra. Gabansa Izzatu tayi saurin tarewa ta daure fuska....Baby ina zaka je kuma? Shima tasa fuskar a daure saboda bata masa lokaci da yake ganin zata yi yace zanje sallama da Zuhra mana. Yana soma tafiya ta rike masa hannu....bafa zan yarda ba. Yau girkina ne saboda haka bai kamata kace zaka wata sallama da Zuhra ba. Ba tare zamu airport din ba? Sai kuyi sallamar a can. Dan rufe idonsa yayi sannan ya bude a hankali....Izzy kada kisa mu rabu da bacin ran juna. Zanyi tafiyar wata biyu har zancen wani girki zai taso? Kije ki fito min da jakar kayana, idan bazaki iya ba ki jirani a kasa ina fitowa zamu tafi. Bai kara saurararta ba ya tafi dakin Zuhra. Zaune ya ganta akan kujera tana sharar hawaye. Ta gama shiryawa ta saka wani katon hijab tana jira Hamza ya fito su tafi. Tana ganin ya shigo tayi saurin goge hawayenta ta mike tsaye...Ya Hamza har ka fito? Murmushi yake yi yana kallonta. Na fito Cutie, wato baki dena kukan ba ko? Kamar yace yi wani kukan ta soma wani sabo. Ya dauki lokaci yana bata hakuri da rarrashi duk ta hanyar da yasan zai dauke mata hankali. Da kyar tayi shiru tana fada masa irin yadda zata yi kewarsa idan ya tafi. Wayarsa ya dauko yana daukarta hoto tana ta rufe fuska wai bata yi kyau ba. Yace gara na dauki fuskar a haka nasan cewa idan na tafi kullum zaki tuna dani kamar yadda zan tuna dake. Jin haka yasa ta dauke shi itama sannan suka yi wani tare. Suna cikin haka suka ji wani mahaukacin bugun kofa. Yasan aikin Izzatu ne dama yana sane ya kulle kofar dakin don ba karamin aikinta bane ta bude su. Sai da ya sake yiwa Zuhra kyakkyawar sallama sannan suka fito tare fuskokinsu dauke da murmushin da ya kona ran Izzatu. A gida aka bar yaran wurin Tala saboda dare ne. Kowa yana fadar me Daddy zai siyo masa na tsaraba. Suna zuwa gaban mota Izzatu tayi saurin shiga gaba. Dama Zuhra bata yi tunanin shiga ba saboda tasan ba ita ke da girki ba. Kafin su je gidansu Hamza taga kayan takaici kala kala. Hannun Izzatu a cinyar Hamza yana tuki. Ko ta sakala hannun a wuyansa ta wani kwanta a jikinsa. Yayi mata magana har ya gaji. Baya son abinda zai batawa Zuhra rai. Da suka je gidan Izzatu ta zauna kwam sai Hamza ya bude mata kofa. Hakan ya bashi damar tsayawa bawa Zuhra da ta fito hakuri. Don bata son ya tafi da baccin rai shiyasa ta nuna masa babu komai. Izzatu ta gaji da jiransa ta bude ta fito suka shiga ciki. Duk kannen Hamza sun zo yi masa sallama. Mota uku suka yi zuwa airport wasu a tasa wasu a ta Ibrahim da Nura. Sai da zai shiga ciki Izzatu ta soma kuka duk ana jinta ta rungume shi tana cewa zatayi missing dinsa. Tamkar ya tona kasa ya rufe kansa saboda kunyar kannensa dake wurin. Ibrahim barin wurin yayi saboda bacin rai. Sai da Hamzan yayi mata tsawa sannan ta kyale shi tana kallon yanayin Zuhra wadda ranta ya gama baci. Abinda yake gudu dai sai da ya faru sun rabo da Cutie dinsa ranta babu dadi. Key din motarsa ya bawa Izzatu yace su tafi gida ita da Zuhra don yasan ta kware a tuki. Bayan ya shige ciki motocin su Nura da Ibrahim ne suka fara yin gaba sannan Zuhra da Izzatu suka tafi wurin motar Hamza. Da Izzatu ta bude ta shiga sai tayi saurin danna central lock ta rufe Zuhra a waje. A take hankalin Zuhra ya soma tashi ga dare ta fara buga glass tana yiwa Izzatu alama da ta bude mata. Glass din ta sauke kadan tace....naga babu abinda baki iya ba shiyasa kullum Hamza yake yabonki to wannan yabon ya kaiki gida. Daga nan ta fige mota tayi gaba ta bar Zuhra a tsaye. Wayarta ma Hamza ya jona mata chaji tana cikin motar. Zuciyarta ke wani irin bugu saboda tsananin bacin rai. A rayuwarta bazata taba mantawa da Izzatu da ire-iren wulakancin da take mata ba. Kukan ma ta kasa ita daga airport din ma bata san hanyar da zata bi taje gida ba gashi tasan ko ba'a fada ba shabiyun dare ta kusa. Wani irin tsoro ne ya ziyarci zuciyarta ta fara addu'o'i. Jiki a sanyaye ta fara tafiya hanyar da tasan zata kaita bakin gate ta fita. Motoci kadan ne suke wuceta tana tafiya a gefen titi. Ga irin yanayin da muke ciki na raunin tsaro babu wanda ya tsaya yayi yunkurin taimaka mata. Itama ko an tsaya bazata shiga ba saboda tsoro. Shabiyu saura minti uku Izzatu ta shiga gida. Maigadi ya tareta yana mata sannu da zuwa. Cike da nishadi ta shige ciki saboda ta gama tsara abinda zata fadawa Hamza idan Zuhra ta kai kararta. Rantsewa zata yi motar Ibrahim ta ga ta shiga shiyasa ta taho. Dama shima Ibrahim din ta tsane shi saboda tun farkon aurenta ta kula baya sonta. Kai tsaye dakinta ta wuce ta tafi ta kwanta hankali kwance. Shiru Tala bata ga shigowar Zuhra ba tana son bata canjin kudin kulu da ta aiketa saboda bayan asuba take son tafiya garinsu zata je tayi sati biyu kamar yadda Hamza ya bada umarnin ta je. Gajiya tayi da jira ta fita waje maigadi har ya kwanta ta buga masa kofa ya fito ta tambayeshi ko yaga shigar Zuhra ciki. Yace shima yayi mamaki amma Izzatu ita kadai ta dawo. Har Tala ta juya zata koma ciki sai dai hankalinta bai kwanta ba. Da yake da waya ta fito sai ta gwada kiran Zuhra. Karar wayar suka ji daga cikin mota saboda a gefen motar suke a tsaye. Nan da nan Tala da maigadi suka shiga tashin hankali. Tace bari naje na tambayi Maman Khalifa ko ba a gida zata kwana ba. Maigadi yace ashe baki da tunani ban sani ba? Tare ya kamata su dawo amma basu dawo ba kuma duk munsan ba da ita maigida zaiyi tafiya ba. Ni a tawa shawarar ki kira wani a gidansu Yallabai kiji ko a can zata kwana tunda ya fada min da bakinsa can zai fara zuwa kafin yaje iyafot din. Da yake a rude take a take tace bata da numbar kowa. Har ta soma kuka tana tunanin ko wani mugun abin ne ya sami Zuhra. Daga baya ta tuna jiya da safe Hamida ta kira wayarta saboda bata sami ta Zuhra ba. Sai da suka rinka bin nambobin da aka kira a wayar wajen shida gashi babu kudi sosai sannan suka yi sa'ar samun ta Hamida. **** Hamida da Adabiyya suna ta hira basu ji wayar da wuri ba. Tala har ta hakura sun kira wasu nambobin biyu sai ga kiran Hamida ya shigo. Ita duk ta tsorata ganin daga gidan Yaya aka kira da wannan daren. A tunaninta ko babu lafiya Zuhra ta kirata da numbar Tala. Jiki na rawa Tala ta dauka tace kiyi hakuri na kiraki a tsohon daren nan. Dama tambayarki zanyi ko a nan gidanku Maama zata kwana ko gidan iyayenta? Hamida tace bangane ba Tala. Kina nufin Anti Zuhra bata dawo gida ba? To ina Anti Izzatu? Tala tace tana dakinta munga ita kadai ta shigo kuma ga wayar Maaman a motar Yallabai an jona ta da wani abu. Sautin kukan Hamida Tala ta jiyo tasan lallai ba lafiya ba. Ko ajiye wayar bata yi ba ta tafi dakin Mama ta tarar bata nan. Dama tasan Hajiya na falon Alhaji tun da suka dawo daga airport a nan suka gansu suna hira. Falon ta nufa da gudu tana yiwa Adabiyya bayanin abinda Tala tace. Sallama tayi ko amsawa basu jira anyi ba suka daga labulen suka shiga falon. Alhaji ne da matansa suke ta hira yau basu kwanta da wuri ba. Hajiya ta daka musu tsawa tana son jin dalilinsu na shigowa a haka. Cikin kuka Hamida ta fada musu wayar da suka yi da Tala. Babu wanda hankalinsa bai tashi ba a wannan lokacin. Alh Nasiru ya dauki waya ya kira Ibrahim ya sanar dashi sannan ya tafi dakin Nura ya taso shi. Ko hula babu a kan Alhaji suka fita da Nura. Airport din zasu fara dubawa kafin suje gidan iyayenta. ***** Hadari ne yake hadowa garin yayi duhu sosai sai fitilun cikin airport na gefen titi. Iska da kura sai kada Zuhra suke tana tafiya idonta sharkaf da hawaye. Banda Izzatu hatta Hamzan haushinsa take ji. Don me bai tabbatar da ta tafi ba ya shige ciki. Kullum Umma na fada mata maza basa son macen da tafi kawo kara amma wannan karon suna yin waya da Hamza idan har ta isa gidanta lafiya kenan zata fada masa. Dole ayi mata iyaka da Izzatu idan ba haka ba kuma lallai zasu daku. Ko a unguwarsu babu mai takalar Zuhra dambe don da gaske karfi gareta. Ajiyar zuciya tayi da ta ga ta kusa isa bakin gate sai dai tun kafin ta isa ta fara jin ana daka mata tsawa. Nan take ta gigice ganin sojoji sunfi biyar a kanta da bindigogi. ***** Sanarwar karshe akeyi cewa jirgi zai tashi kowa yasa seat belt kuma a kashe waya. Ran Hamza a bace ya kira Zuhra yafi sau ashirin bata dauka. Izzatu kuma da suka sake sallama tace Zuhran na dakinta. Ya tabbatar idan yace ta kai mata tata wayar kuma bazata kai ba. Dole ya hakura ya kashe wayar. Sauran mutum hudu da zasu tafi tare duk ta Abuja suka tashi da kyar ya sami alfarmar tashi ta Kano saboda iyalinsa. Yayi yunkurin kashe wayar sai ga text ya shigo. Da sauri ya bude ya zata Zuhra ce. (Sir idan kana da lokaci gobe ka kirani. Mr. Oscar) Rasa abin yi yayi ba don yana cikin jirgi ba ai yanzu zai kirashi yaji abinda zai fada masa. Addu'ar abin hawa da ta tafiya Hamza yayi ya kashe wayarsa zuciyarsa tana tunanin me ya sami Cutie dinsa. **** Kneel down sojojin suka saka Zuhra suna ta turancin da pidgin ta kasa gane abinda suke fada. Kuka take yi kamar ranta zai fita saboda tsabar fargaba. Wani cikin sojojin ya harare katon hijab dinta yace ta cire shi da Hausa. Zuhra ta sake kankame jiki tace bazata cire ba. Saita ta suka yi da bindigogi suna fada...ki cire hijab mu tabbatar babu komai a jikinki idan ba haka ba a wurin nan zamu harbe ki. Wasu cikin sojojin har sun fara ja da baya saboda kin cirewa da tayi. Wani yace me ya kawoki nan? Bakinta har hardewa yake ta fada musu abinda tazo yi. Dariya suka yi suka karyata ta. Suka bata umarni na karshe ko ta cire hijab dinta ko a harbe ta. Can gefe wasu sojojin ke ta buga waya ga manyansu suna sanar dasu abinda ke faruwa. A haka Zuhra tana kuka tana rokonsu ta kama hijab din ta cire gashi kanta ko dankwali babu dadinta ma doguwar riga ce ta atampa a jikinta. Rigar duk ta matse ta sama rabin kirjinta a waje. Idon wasu ya kai nan tayi saurin rufewa tana kuka sosai. Ta saddakar mutuwarta tazo amma har abada bazata taba yafewa Izzatu ba. Shi kanshi Hamza idan har wani dalili yasa ta tsira to ta bar gidansa kenan. Motoci biyu ne suka iso kusan a tare sai ga motar 'yan sanda guda daya. Tun kafin su tsaya Alh Nasiru ya hango Zuhra a durkushe. Idanunsa suka kada suka yi ja saboda bacin rai. Wannan cin kashi da aka yi mata da me yayi kama, me zai fadawa Mal Bashir? Ibrahim ko kashe tasa motar baiyi ba ya fito da sauri amma da ya karaso sauke idonsa yayi saboda bazai iya kallon matar dan uwansa a wannan yanayin ba. Nura kuwa mai raunin zuciyar da tafi ta Hamza kuka yake yi kamar wani yaro. Duk fitowa suka yi sojoji na tsayar dasu 'yan sandan suka taho suka fara yi musu bayanin report din da Ibrahim ya kai musu. Shaida suka nema domin gaskata zancen 'yan sandan. Nura ya duba wayarsa yayi sa'a akwai hoton ranar yinin Zuhra da suka je daukota daga Ajingi shine ya nuna musu. Duk da haka sai da suka bukaci washegari a kawo wani na'uin shaidar ko wacece Zuhra. Alh Nasiru da kansa ya dauko hijab din da akayi wurgi dashi ya dora mata a kanta. Kasa tashi tayi ya dagata da kansa. Sai a lokacin ta kara sa kuka mai sauti. Ibrahim ya kalli sojojin yace mace mai hijab sunanta musulma ba 'yar ta'adda ba da zaku wulakanta ta haka. A baya Alhaji ya zaunar da ita ya shiga gaba. Ibrahim ma binsu yayi a baya suka tafi gida. Jugum jugum haka su Hajiya suka zauna a falo. Ana shigo da Zuhra Hajiya ta ajiye kunyarta taje ta rungumota. Zuhra ta kankameta tana kuka kamar mai ban tausayi. Cikin kuka tace Hajiya ai ba laifi bane idan ban yafewa Maman Khalifa ba ko? Kowa a wurin yaji tausayinta. Ga masu tayata kuka su Adabiyya suna yi. Da kyar falon ya sami nutsuwa har ta fada musu abinda ya faru. Alhaji ya bata hakuri sannan yace ta kwantar da hankalinta zuwa gobe zasu san abin yi. Ruwa mai zafi Mama ta sa aka dafa mata tayi wanka amma taki cin komai. Dole suka kyaleta ta kwanta cike da tunani kala kala. [10/22, 4:49 PM] #+234 705 352 3457#: AL'ADUN WASU #74 Batul Mamman(Mrs)# Gudu take yi a wani daji kafarta ko takalma babu ga gumi da ya wanke mata jiki. Sautin harbi take ji amma ta rasa daga ina yake fitowa. Tana cikin gudun ta hango wani gida a tsakiyar dajin ta tafi da sauri ta shiga ta rufe kofar harda saka kwado. Juyawar da zatayi idonta ya sauka akan sojoji da bata san iya adadinsu ba. Dariya suka fara yi mata kafin su saita ta da bindiga su fara harbi. Hajiya tana idar da sallah ta juya gefen gado inda Zuhra ke kwance tana ta mutsu- mutsu duk ta hada gumi. Da sauri ta tashi ta tsaya a kanta ta fuskanci kowane irin mafarki take yi ba na lafiya bane. Kafadar Zuhra ta dafa da niyar tashinta Zuhran ta tashi a razane tare da kwalla kara. Ganin Hajiya yasa ta kankameta sai kuka ya kwace mata. Hajiyan tana rarrashinta tana kokarin mayar da hawayen da yake barazanar fitowa daga idonta. Tashin Zuhra na uku kenan tunda suka kwanta. Kamar ta sani ta hanata kwana dasu Hamida tace ta dawo dakinta. Sai da Zuhra tayi shiru sannan Hajiya tace...ki tashi kiyi sallah ba'a dade da kiran assalatu ba. Kuma ki yawaita addua nima zan cigaba da yi miki musamman na kwanciya saboda wannan mafarke mafarken da kike yi. Jiki a mace Zuhra tace to Hajiya sannan ta tashi ta shiga toilet. Tun faruwar wannan al'amari 'yan awanni da suka wuce Zuhra da Hajiya suka manta da kunyar juna irin na surukai. Bayan ta idar da sallah ne Mama ta shigo dakin da gani itama sallar tayi. Zuhra ta gaisheta ta amsa fuska a sake sannan ta tambayi Hajiya ya suka kwana...wallahi jiya Alhaji baiyi baccin kirki ba duk ya damu. Kusan a zaune muka kwana. Hajiya tace to ai nima bamuyi baccin ba. Sau uku bacci na daukarta ta tashi a firgice. Allah Kaltume da sakin Izzatu a hannuna yake sai da yaron nan ya dawo ya tarar ta dade a gidansu. Mama tayi murmushi, Hajiya Halima bata taba sanya kanta cikin lamuran 'ya'yanta musamman Hamza da ya kasance na fari. Wannan maganar tata ta kara tabbatar da cewa ba karamin bacin rai abinda Izzatu tayi ya sanyata ba. Haka suka zauna suna taba 'yar hira har gari ya karasa wayewa Mama ta tafi kitchen tare da Hamida wadda ita ce mai tayin abincin safe yau. **** Dayake jirgin Emirate Hamza ya hau sun tsaya a Abu Dhabi canjin jirgin da hutun awa biyu. Wayar Zuhra ya rinka kira yanzu ko shiga ma bata yi. Hankalinsa yayi matukar tashi. Da ya kira Izzatu bayan sun gaisa lokacin karfe takwas na safe tace masa Zuhra bata fito daga daki ba. Hankalinsa gabadaya a tashe yake. Yace taje ta kwankwasa mata kofa tace yace ta kunna wayarta. Izzatu tace ita bazata je ba ta kashe wayarta ma a cewarta kada ya dameta ita babu ruwanta da matarsa. Haka ya hakura ya kira iyayensa suka amsa wayarsa kamar babu abinda ya faru. A hira ne ya sanar da Mama ya kasa samun Zuhra tun daren jiya bayan ya shiga jirgi. Mayar da zancen nasa wasa tayi har tana cewa ko zai biyata ne taje ta gano masa lafiyar amarya. Shi dai jikinsa duk babu dadi har ya sake shiga jirgin da zai kaisu Thailand wanda daga shi zasu shiga mai kaisu South Korea. ***** Tunda Izzatu ta ajiye wayar Hamza jikinta yayi sanyi. Jiya dai lafiya kalau tayi bacci amma tunda ta fuskanci Zuhra bata dawo gida ba hankalinta ya kasa kwanciya. Ita fa a tata wautar ba niyarta wani mugun abin ya sami Zuhra ba. So tayi ta bata wahala karshe kila ta biyo motar haya a daren. Tunani tayi ko an saceta a hanya taji wani mugun tsoro ya shigeta. Sai yanzu take danasanin abinda tayi domin batan Zuhra ba karamin abu bane. Daga baya tayi tunanin ko gidansu Zuhran ta wuce sai tayi dariya. Karshen abin kenan kila ta koma gida ne tana son ta hadata da Hamza. Indai hakane kuwa ko a jikinta don tana da bakin kubutar da kanta. Tun daga wannan lokacin hankalinta ya kwanta. Mama ce da kanta ta kira Tala wadda take ta hada kaya cikin kwanciyar hankali saboda Hamida ta tabbatar mata da anga Zuhra amma Alhaji yace kada ta kuskura ta fadawa kowa. Mama tace tasan yadda zatayi ta dauko wayar Zuhra a motar Hamza ta kawo mata gida. Wurin maigadi taje ta fada masa. Sai da rana ta fito yace Tala ta fada mata yace zai wanke mata motar yaga datti a ciki. Babu musu Izzatu ta leko ta tagar dakinta ta danna remote ta bude masa motar. Dama tana son zuwa shopping anjima. Motar ya bude ya dauko wayar ya bawa Tala. Ita kuma bata dade ba tayi sallama da Izzatu ta dauki kayanta da sunan ta tafi kauye. Gidansu Hamza ta fara zuwa inda su Adabiyya suka labarta mata abinda ya sami Zuhra. Tala tayi kuka sosai sannan ta kawo wayar ta bawa Mama. Da aka kira Zuhra ta fito suka gaisa dukkansu sai da suka yi kuka. Tala tasan uwargidan nasu sai a hankali amma bata taba tsammanin abin nata yakai ta aikata wannan rashin imanin ba. Tayi musu sallama kuma su Hajiya suka kara mata guzuri ta tafi. Wurin shabiyun rana Alhaji ya tara iyalinsa harda na gidan miji su Jidda da Mariya aka sake sanar dasu halin da ake ciki. A nan ya fada musu cewa bai yarda wata ta nuna tasan inda Zuhra take ba har Hamza ya dawo. Daga masu hawaye suna tausayin Zuhra sai masu zagin Izzatu da yi mata muguwar addua. Bayan sun tashi Alhaji ya wakilta Mama taje tasan da yadda zata yi ta daukowa Zuhra kayan sawa kafin ya dinka mata wasu. Bayan sun fita yace da Hajiya ta shirya ita da Zuhra zasu je unguwa. Ibrahim ke jan motar har iya inda mota ke shiga a layin gidansu Zuhra. Yana tsayar da motar Zuhra ta fita da gudu ta shige gida. Umma da Baba na zaune a falo suna jiran Safara'u ta gama girkin rana zasu je Ajingi barka maman Safara'un ta haihu. Kamar an jehota Zuhra ta fada kan Baba tana kuka. Daga shi har Umma hankalinsu ya tashi suna tambayarta abinda ke faruwa ta kasa magana. Sallamar Hajiya ce ta katsesu Umma ta tashi ta tarota. Bayan sun gaisa ta fadawa Baba tare da Alhaji suke. Da kyar ya daga Zuhra daga jikinsa ya fita ya shigo dasu shi da Ibrahim. Bayan sun zazzauna Hajiya ta kalli Zuhra da ta lafe jikin Umma, ita kuma Umman tana shafa mata baya tace...lallai Zuhra ke 'yar shagwaba ce ajin karshe. Umma taji kunya ta soma ture Zuhra. Baba yace dawo daga nan uwata nima ina da jikin da zaki tumurmusa. Kasa karasawa tayi ta sunkuyar da kanta saboda kunya. Ita ta manta ma da surukanta a wurin. Umma da Baba kuwa indai Zuhra zata yi kuka to basu da kwanciyar hankali. Alh Nasiru yace nasan zakuyi mamakin zuwanmu a wannan lokacin kuma a irin wannan yanayin. Dole ce ta kawo haka domin bahaushe yace ranar wanka ba'a boyon cibi. Daga nan Alhaji ya warware musu gaskiyar lamari game da auren Hamza da Zuhra. Baba da Umma duk mamaki ya ishesu yadda Zuhra bata taba nuna musu ba auren soyayya tayi ba. Alhaji ya cigaba da cewa a yadda na fahimta Yaya da Zuhra suna son junansu yanzu duk da irin abinda ya faru kafin auren. Baba ya rike hannun Zuhra yace kada ki cuci kanki kinfi karfin wulakanci muddin ina raye. Ki fada min gaskiya idan ba kya son auren sai a waraware. Kana ganin Baba kasan ba karamin bacin rai yaji ba game da labarin April fool da aka yiwa 'yarsa. Kanta a kasa Zuhra ta kasa magana sai kara rike hannun Baba da take yi. Hakan da tayi ya bashi tabbacin tana son mijinta. Da akasin haka ne kiri kiri zata masa da ido yadda tayi da ya taba cewa yaron shagonsa yana sonta. Ya dago kai ya kalli Alhaji...to yanzu menene yake faruwa kuka dawo da ita gida daga tafiyar Hamzan jiya? Alh Nasiru bai damu da yadda Mal Bashir ya canja ba. Abinda yafi haka ma yana da ikon yi akan 'yarsa. Babu uban da zai zuba ido yaga ana wulakanta masa 'ya'ya komai talaucinsa. Alhaji ya sake fada musu abinda Izzatu tayiwa Zuhra a daren jiya. Kuka ne ya kwacewa Umma sosai ta rungumo Zuhra jikinta har rawa yake. Da da ajali a kusa babu abinda zai hana sojojin nan harbe Zuhra. Hajiya ma wani kukan take tayata. Hakika duk da rashin wadata sosai amma gidansu Zuhra gida ne mai cike da soyayya a tsakanin iyayen da tilon 'yarsu. Baba ma idanunsa ja suka yi sosai. Alhaji yace na zabi fada muku gaskiya saboda halin rayuwa. Ba don mai aikin gidansu ba da tayi tunanin sanar damu da karshenta yau labari yasha bamban. Mal Bashir ina mai baku hakuri da neman afuwarku. Wallahi idan Yaya ya dawo zan dauki mataki akan shegiyar yarinyar nan. Mal Bashir ya kalli Zuhra yace babu wani abu da ya sameki ko? Tayi masa murmushi Allah babu komai. Yace to Alhamdulillahi sai mu jira Hamza ya dawo lafiya ya baki takardarki. Yau ko akuyar gidan nan kike bazan yarda ki koma inda akayi miki wannan diban albarkar ba, bare 'yata. Alhaji kuyi hakuri amma bazan bari ku koma da ita ba. Ita kadai Allah Ya bani idan ka duba da wuya idan bamuyi sa'anni da kai ba amma sai a kanta haihuwa ta tsaya tsaya mana. Wallahi duk kawaici irin na mutumin kauye bazan iya dauke kai ba idan abu ya shafi uwata. Gara na aurar da ita a kauye da ta fuskanci rayuwa irin wannan. Umma ta nuna ta goyi bayan mijinta. Alhaji da Hajiya suka shiga bawa su Baba baki amma kememe Baba yace shi fa bazai yarda ba. Ibrahim yace Baba idan bazaka damu ba ka bani damar magana. Baba yace ina jinka amma bazan canja kudirina ba. Murmushi Ibrahim yayi sannan ya sanar dasu irin canje canjen da ya gani tattare da dan uwansa bayan aurensa da Zuhra. A takaice abinda iyayensu basu sani ba dangane da irin taimakon da tayi masa bayan durkushewar kamfaninsa a dalilin Izzatu duk sai da ya fada musu. Mamaki sosai suka yi Zuhra ta sake samun masauki a zuciyar surukanta. Ibrahim yace shekaranjiya yazo har office ya sameni ya sanar dani komai yace wasiyyace ya barmin saboda yanayin tafiya idan har bai dawo ba kada na taba bari ta wulakanta a duniya. Wannan jawabi na Ibrahim ya sanyaya zuciyar iyayen Zuhra ita kumq yasata kuka sosai tare da dagewa wurin yin addua Allah Ya bashi sa'a kuma ya dawo dashi lafiya. Alhaji Nasiru yace bukatarsa daya a wurinsu kada su taba cewa sunsan inda Zuhra take domin Izzatu da hannunta zata girbe abinda ta shuka. **** Mama da su Hamida ta tafi gidan Hamza. Ihun su Khalifa Izzatu ta ji suna murnar ganinsu ta fito daga kitchen a tsorace. Ba dai can Zuhra ta tafi ba. Ai kuwa tasan Alhaji sai ya bata mata rai. Ga Mama itama wata mara son nata. Gashi uwa uba bata san takaimaimai inda Zuhra ta tafi ba. Har wayarta ta gwada kira bata samu ba. Da dan cokalin miya Izzatu ta fito tana murmushin da bai kai zuci ba tayi musu sannu da zuwa. Mama ta amsa fuskarta a sake tana tambayar ya suka kwana. Izzatu tace lafiya kalau Junior yace amma yau tun safe bamu ga Maama ba. Inata kiranta bata amsa ba. Izzatu ta make shi sannan tace tana dakinta kila bacci take yi. Mama tayi 'yar dariya tace su Hamida su duba mata. Dama da wata jaka mai dan girma da Adabiyya ta sako cikin hijab. A gaggauce suka debo mata kayan sawa, 'yan ciki da na bacci suka sauko. Hamida tace Mama da gaskiyar Junior Anti Zuhra fa bata dakinta.. Cokalin hannun Izzatu ya fadi don tsoro tace au na tuna tun safe ta tafi gidansu tace a can zata yini. Adabiyya da Hamida suka kalli juna suna dariya kasakasa. Mama ta dauke kai kamar bata gansu ba tace to ga wannan dama Alhaji ne yace na duba ku. ..dubu biyar ta bawa Izzatu...idan Zuhran ta dawo ki gaidata. Daga nan suka fita suna mamakin karyar da Izzatu tayi musu. Suna fita tayi ajiyar zuciya hankalinta ya kai karshen tashi. Yanzu idan Zuhra bata dawo ba ina zata fara nemanta? Dole ta kai cigiya wurin 'yan sanda tun kafin a kara dawowa nemanta. **** A gidan Zuhra ta yini sai dare Nura ya dawo ya dauketa saboda washegari zasu tafi Ajingin da suka fasa zuwa a yau. Tana zuwa gidan wayarta tayi chaji. Sakonnin text goma ta gani na Hamza masu nuna damuwarsa da rashin samunta a waya. Wurin shadayan dare ya sake kira lokacin suna masaukinsu a wani hotel. Ba karamin dadi yaji ba da ya sameta. Tayi ta bashi hakuri akan cewa wayar ce ta fada kasan kujera a motar bata ganta ba. Hirarsu suke ta masoya har Hamida da Adabiyya suka bar mata dakin suna tsokanarta don ta dage ita wurinsu zata rinka kwana. Alhaji yace kada ta nunawa Hamza komai yanzu saboda kada ya kasa yin abinda ya kaishi. Ta nuna masa tana gida kamar yadda yake tunani. **** Haka rayuwa ta kasancewa Zuhra a gidan Alhaji babu irin gatan da su Hajiya basa nuna mata. Haka sauran 'yan uwan Hamza ma. Umma da Baba kullum sai sun kirata a waya. Lokacin da ta cika sati biyu ne suna kitchen ita da su Hamida suna aiki Zuhra tana wankin nama taji zuciyarta na tashi. Abu kamar wasa ta fara cewa naman yayi karni da yawa Adabiyya tace ai kuwa yana da kyau. Bata kara magana ba ta soma amai kamar kayan hanjinta zasu fita. Kofar kitchen din ta baya ta fita tayi aman tana yi tana kuka. Hajiya da Mama aka kirawo suka shigo kichen din. Ita dai Hajiya tana ganin aman da Zuhra take yi murmushi kawai tayi ta ja da baya, Mama ta wuceta ta taimakawa Zuhra. Yadda take aman har kirjinta na amsawa yasa take kuka. Mama tace oh ni Kaltume haka kike yiwa Yaya wannan kukan shagwabar? Gaskiya Umma Atine ta shagwaba mana 'ya. Hajiya na daga gefe tace don ba tare muka je gidan dake ba da kinsha kallo. Yadda kika san ta shige ciki. Zuhra duk kunya ta kamata ta tashi da gudu. Mama tabi bayanta da sauri tana dakatar da ita...haba Zuhra yanzu kuma ai lokacin tattalin jikinki ya kama sai kinbi a hankali. Bari na kira Nura a waya yazo ya kaimu asibiti don a tabbatar mana da abin alkhairi. Kan Zuhra a kasa ta kasa cewa komai. Itama tana zargin abinda Mama take fada saboda 'yan alamun da ta gani daga irin hirar 'yan mata da kawayensu. Da yamma suka je asibiti aka tabbatar tana da ciki wanda ke cikin watansa na biyu. Tun a hanya Mama ta kira Hajiya harda Alhaji tayi musu kyakkyawan albishir. Siyayyar 'yan kayan kwadayi tayiwa Zuhra wadda don kunya ta rufe fuskarta da mayafi. Shima wannan labarin bata sanar da Hamza ba a lokacin da sukayi waya. Tafi son ya gani da idonsa. Sai dai suyi ta hira yana tambayarta me tayi yau. Kulawa kuwa a wurin 'yan gidansu sai godiyar Allah. **** Izzatu sam bata da kwanciyar hankali a gidanta. Ga Tala ta tafi gida ga yara su dameta. Junior da Nana sunki yarda ta saka musu pampers ko ta saka musu sai sun cire. Dakinta har zarni yake saboda fitsarin da suke mata a kwance. Kafin ta gama girki kullum sai Nana tayi kuka saboda ta riga ta saba da kin dorawa da wuri. Idan ta zuba musu anjima kadan suce yunwa tunda bata zubawa da yawa. Duk wannan bai dameta ba kamar rashin sannin inda Zuhra take. Hamza dai ya dena tambayarta Zuhra shiyasa take mamaki. 'Yan kwanakin nan har mafarkinta take yi. Don tsananin tashin hankali ko shara bata yi a gidan ga uba wanke wanke ta tara. Tunani ne ya isheta wata rana bayan ta dauko su Khalifa daga makaranta ta wuce airport. Ya zama dole ta fara neman Zuhra tun kafin Hamza ya dawo kashinta ya bushe. Daga bakin gate tayi parking ta fito ta tafi wajen masu karbar kudin shiga ta tambayesu ko sun ga wata mata da bata wuce shekara ashirin da daya ba sati biyu da suka wuce da daddare. Wanda ta tambaya yace ranar bashi bane da aiki amma bari a tambayi sojojin saboda yawanci a nan suke. Da tafiyarta ta 'yan gayu ga takalmi mai tsini Izzatu tabi bayansa zuwa wurin sojojin. kafin su karaso yawanci duk sun taho wurinsu. Mutumin ne ya tambayesu abinda Izzatu tace ai kuwa wani gabjeje a cikinsu ya daka mata tsawa yace tayi kneel down a nan. Kamar ta saki fitsari don tsoro tayi abinda yace tana rarraba idanu. Ya kalleta sama da kasa yace...chege kaine ka bar kishiya a nan ko? Izzatu tayi saurin girgiza kai alamun ba ita bace. Wasu mutum biyu suka nunata da bindiga tayi saurin cewa nice, wallahi nice. Katon yace dama kaine kawai zaka ki zuwa nemanta sai bayan two weeks. Mugu yau sai munci ubankaaaa. Ya fada yana wata irin dariya mai ban tsoro. A take Izzatu taji saukowar fitsari daga mararta saboda tsabar kidima. [10/23, 5:48 PM] #+234 806 611 3313#: AL'ADUN WASU #75 Batul Mamman(Mrs)# Wani soja musulmi wanda baiji dadin lokacin da suka sa Zuhra cire hijab ba, don babu yadda zaiyi ne saboda yadda ake amfani da hijabi ana cutar mana da addini da sauran musulmi. Muguwar harara ya dankarawa Izzatu sannan yace banda kneel down ta daga hannu sama. A dole tabi umarninsa babu inda baya rawa a jikinta. Tana daga hannu mayafinta yayi sama sai ga shatin fitsari a jikin zanin shaddarta. Kafin ta ankara ta rufe wurin sun gani suka rinka dariya. Sauran mazan dake gefe ma dariyar suke yi. Izzatu yau taga wulakanci irin wanda bata taba gani ba. Daga nan suka rinka yi mata fada akan me zata bar yarinyar mutane a airport da tsakar dare. Ita dai Izzatu babu bakin magana bare ta tambayesu ina suka ga yarinyar tayi. Su Khalifa ne suka hango mamansu daga cikin mota a wannan yanayi suka soma kuka. Wani soja da yaso sata tsallen kwado ya kula da yaran ya fadawa ogansu. Ogan yace to albarkacin yaran nan ta koma motarta da rarrafe sannan sun bata sati daya ta nemo kishiyarta ko su zo har gida su tafi da ita. Abin tausayi haka Izzatu ta rinka rarrafe akan gwiwarta duk tsadar shaddar jikinta haka ta rinka jan jiki zuwa motarta. Khalifa da Junior sun sha kuka. Itama da kukan ta karasa wani soja yana binta a baya yana zungurinta da kasan bindiga. Tana shiga motar Khalifa yace Mummy laifi kika yiwa Uncle dinku ya saka ki kneel down? Idonta ta share tace a'a Khalifa takalmi na ya tsinke shine na gwada yadda muke yi da muna yara. Motar ta tayar sai dai ga mamakinta sojoji biyu ne suka shiga wata motar a bayansu suka bi bayanta. Zuciyar Izzatu har bugawa take don tsoro tace yau na shiga uku. Maimakon ta tafi gida haka tayi ta yawo a titi. Tun su Nana na kukan yunwa har duk suka yi bacci don wahala. Man motar har kusan karewa yayi ta shiga gidan mai. Motoci wurin goma ne a gabanta amma bata damu ba. Burinta kawai wadannan sojojin su gaji su dena binta. Lokacin da ta fito daga gidan man tayi sa'a bata gansu ba. Sai biyar na yamma ta isa gida jikinta ya gama tsami. Har kusan faduwa tayi da ta fito daga mota ga yara sunyi bacci. Dole ta dauke su daya bayan daya ta shigar dasu gida. Wannan rana ta kafa tarihi mai girma a rayuwar Izzatu. **** Bayan kwana hudu Zuhra na kwance a daki taji wayarta na ringing. Hamza ne ya kirata ta dauka tana murmushi. Har yanzu bai san halin da ake ciki ba. Idan ya kira hirarsu suke yi sosai. Wani lokacin suyi ta turawa juna hotuna. Gaishe shi tayi yace ni dai na gaji da gaisuwar nan Cutie. I miss you so much. Dan bakin nan na tsiwa yayi min nisa. Tana jindadin kalaman Ya Hamzanta ta gyara kwanciya...saura wata daya da 'yan kwanaki kazo ka hadu da dan bakin. Ji nake kamar na jawo su Ya Hamza. Har rashin lafiya nake yi saboda rashinka. Hamza yayi dariya yace ashe dai na siye zuciyarki...wayarsa ya dan cire ya kalla. Karo na uku kenan da Izzatu take kiransa tun bayan sunyi waya dazu. Ya rasa dalilin kiran ya danyi tsaki yace Cutie bani minti biyu zan sake kiranki. Ba jimawa ya kira Izzatu yana tambayarta ko lafiya. Murya cike da kissa tace Baby dama ina son fita ne anjima to Zuhra ta fita dazu tace gidansu zata je. Ka kwatanta min gidan nasu idan na dawo sai na biya na daukota. Har cire wayar yayi daga kunnensa ya sake kallo don ya tabbatar da Izzatu yake waya. Wai zata biya daukar Zuhra??? To ko sun fara zaman lafiya ne bai sani ba. Sake magana Izzatu tayi sai yayi mata kwatancen. Sai da yayi kuma ya fara tunanin ko wani abin zata je yi. Yace yaushe ta fita ban sani ba? Izzatu tace to ai tunda ka tafi tana yawan fita nima bansan inda take zuwa ba. Matar taka gwanar yawo ce. Shi dai hankalinsa bai kwanta ba har ya ajiye wayar. Zuhra ya sake kira ya tambayeta yaushe ta fita bai sani ba. Gabanta ne ya fadi da farko sannan ta dake tace ita tana gida. Yasan bazata masa karya ba shiyasa bai daga zancen ba. Amma sai da ya sake kiran Izzatu yace bai yarda taje dauko Zuhra ba. Idan har ta fita ta dawo da kafarta. Tuni zancensa yabi iska. Lokacin da ya sake kira ma ta kusa fita daga unguwarsu. **** Umma na kwashe kayan wanki Izzatu ta shigo da sallama tare da yaranta. Tarba mai kyau Umma tayi mata sannan tace sai dai banganeki ba. Izzatu sai yatsina fuska take. Gaskiya gidansu Zuhra basu da wani arzikin azo a gani. Tace sunana Izzatu matar Hamza. Umma ta hade fuska tana dana sanin irin tarbar da tayiwa matar dake son kashe mata 'ya. Har zata fara fada ta tuna Alhaji yace kada su nuna sunsan abinda ya faru. A dole Umma ta kirkiri fara'a ta fara kiran su Khalifa tana tambayarsu sunayensu. Izzatu ta harare su suka koma suka zauna. Umma ta dan waiga tace tare kuke da Zuhran? Ina fata dai lafiya. Toh fa...Izzatu tayi tunanin samun Zuhra a nan gashi ga dukkan alamu iyayenta basu san abinda ke faruwa ba. Murmushi tayi ta mike dama hanya ce ta biyo damu shine nace bari nazo mu gaisa. Umma tace Allah Sarki, kin kyauta. Nagode sosai zan fadawa Baban Zuhra idan ya dawo. Kamar wadda ake kora haka Izzatu ta fita daga gidan tana tunanin daga nan kuma ina ta nufa. Kwanaki sai gaba suke yi, me zata fadawa Hamza idan ya dawo? A bangaren Umma kuwa Izzatu na fita tayi dariya sannan ta kira Zuhra ta fada mata. **** Bayan sayi biyu su Zuhra na cin abinci a falo ana dan taba hira. Hankalinsu yana ga labarin da Nura ke basu na sabuwar buduwarsa mai son kudi tunda iyayen nasu basa falo suka ji horn din mota. Dariyar da suke yi duk suka dena Adabiyya ta fita waje da sauri. Murya suka ji ta daga da karfi tana cewa oyoyo Nana. Hamida ki fito ga su Junior da Khalifa. Jin haka Zuhra ta tashi ta shige ciki da gudu. Dakin Hajiya ta shige ta rufe kanta a toilet. Izzatu ta shigo tare da su Khalifa. Ita da yaran duk sun rame. Ita damuwa da fargaba ke damunta su kuma rashin kula da basa samu daga gareta. A falon ta zaune jiki a sabule tana tararrabin abinda zai faru. Police station yafi goma taje duk ba'a tsinci Zuhra ba. Tayi zurfi a tunani bata ji sallamar su Mama ba sun dawo daga makota jaje. Sai da Hamida ta taba ta tayi firgigit ta gyara zama. Har kasa ta durkusa ta gaishesu. Suma basu nuna komai ba suka amsa mata. Hajiya tace ina 'yar uwar taki? Mama tace nima tambayar da zan mata kenan. Kwana biyu su Hamida sunce basa samunta ko a waya. Cikin Izzatu har 'yar kara yayi sai kuma ga Alhaji ya shigo yace wayar waye ba'a samu? Hamida ta amsa masa...wayar Anti Zuhra ce bama samu. A ranta Izzatu tace munafukai wato har waya sukeyi da ita amma ita basa ko yi mata text. Junior ya tafi wurin kakansa ya rungume shi sannan yace nima bana ganin Maama tunda Daddy ya tafi. Izzatu ce tayi saurin katse shi tace kai Junior ba tana bacci ba lokacin da muka fito. Har ka manta? Su Izzy an fara kwarewa a karya. Khalifa yace nima dai bana ganinta maybe da Daddy suka shiga aeroplane. Ji take inama bata zo gidan ba. Sai murmushi take kamar sabuwar shashasha tace Alhaji don't mind them. Tana gida. Bari mu tafi dama zuwa nayi mu gaisa. Mama tace da sauri haka ko ruwa baku sha ba? Izzatu tace babu komai ta tattara yaranta suka yi waje. Tun kafin ta fita su Adabiyya ke dariya Hajiya tace bata son rashin hankali. Daki suka bi Zuhra suna bata labarin karyar Izzatu. Washegari Tala ta dawo daga kauye. Izzatu kamar ta cinyeta da fada. Duk bakincikinta na wata daya da kwanaki akan Tala ta saukeshi banda tulin aikin gidan da ta tara mata. A haka har akayi azumi da sallah. **** Sati daya ya rage Hamza ya dawo wanda yayi daidai da kwana sha daya azo kawo kudin auren Hamida da Adabiyya. Kannen Mama mata biyu ne suka zo daga Maiduguri. Mai binta Falmata sai autarsu a mata Yagana. Sun zo da wuri saboda akwai siyayyar da suke son yi na bikin sauran namijin gidansu da baiyi aure ba. Kwanansu daya da zuwa Mama ta kira Zuhra ta hadata da Yagana...ga 'yata nan Yagana so nake kafin ku nan da ranar da za'a kawo kudin nan ni kaina kada na ganeta. Ki hada min ita ciki da waje amma ayi min hankali da dan jikalle a cikin. Duk abinda kike bukata zan baki kudi kuje kasuwa a siyo. Zuhra ta sunkuyar da kanta kasa cike da kunya. Yagana tace kwantar da hankalinki Ya Kaltume. Irin gyaran da zan mata ko Adabiyya da Hamida sai kin saki kudi zan musu irinsa. Tun jiya da kika bani labarinta na kudiri niyar sai na banbanta ta da wannan karan sigarin Izzatu. Mata tana tafe kamar an sawa taliya riga da zani. Falmata ta kwashe da dariya. Yagana baki da dama wallahi. Kiyi aikin da aka saka ki kawai ki fito mana da 'ya. Kafin sati aikin Yagana ya fara nunawa a jikin Zuhra. Dama ga hasken da ciki ya kara mata. Ita kanta tana jindadin gyaran don ma laulayi yasa ba komai ake yi mata ba. Hamza ya koma kirgen kwanaki kuma a lissafinsa zai dawo lokacin da Zuhra ke da girki. Don murna har fada mata yayi yana sanar da ita irin tarbar da yake so da irin abincin da zata dafa masa. Har tausayi ya bata saboda tasan zai dawo ya tarar da sabanin abinda yake tsammani. Izzatu dake gidan ta kasa nutsuwa tayi wani abu na murnar dawowar mijinta. Kwatakwata bata da nutsuwa. Kwanakin dawowarsa na matsowa tana kara firgicewa. **** Karfe biyu da rabi jirgin su Hamza ya sauka a filin jirgi na Malam Aminu Kano. Da kansa yace kada Zuhra tazo saboda yasan da kyar idan zai iya hakuri da tabata indai ya ganta ko da a gaban mutane ne. Ibrahim ne yazo ya dauko shi. Ya kara haske yayi kyau kamar ba wanda yaje karatu ba. Farincikinsa baya misaltuwa. Gidansa yace Ibrahim ya kaishi idan yayi wanka zuwa anjima zaije gidansu. Nan kuwa son ganin 'ya'yansa da Zuhra ne a ransa. Motar Ibrahim na tsayawa maigadi ya soma kiransu Khalifa ga babansu ya dawo. Da gudu yaran suka fito suka dafe jikin babansu. Yadda cikin Izzatu ya tsirga saboda tsabar tsoro da gudu ta shiga toilet. Gudawarta ta tara kenan tunda gari ya waye ko wanka bata yi ba. Hamza ya shiga gidansa da murna ya ajiye Nana ya hau sama har yana tsallake bene uku uku don sauri. Dakin Izzatu ya fara shiga yaji alamun tana bandaki ya fita. Dama dai ba nan yafi damuwa da zuwa ba. Cike da murna ya bude kofar dakin Zuhra yana tunanin me ya hanata fitowa tarbarsa a waje. Turus ya tsaya tun bai gama shiga ba, dakin yayi kura tamkar ya shekara babu shara. Da sauri ya fito ya koma dakin Izzatu wadda ke labe a jikin kofa. Zuciyarsa sai raya masa abubuwa take tun kafin ya tambayi ina Zuhra take. Muryar Izzatu da kyar take fita saboda tsoro tace tun ranar da ka tafi ta bar gidan nan. Wani irin kallo ya bita dashi sannan ya dauki waya ya kira Zuhra. A kashe yaji wayar bayan ko da suka tsaya canjin jirgi sunyi waya. Nan take gaban [truncated by WhatsApp] [10/24, 3:43 PM] #+234 705 352 3457#: AL'ADUN WASU #76 Batul Mamman(Mrs)# A yadda ya dago kai dole Izzatu ta kara tsorata ta shige daki ta kulle kofar da mukulli. Hamza bai kulata ba ya sauka ya tambayi Tala ina Zuhra take. Tala tace ita tun washegarin tafiyarsa rabon da ta ganta. Da ta dawo daga kauye ma bata gidan. Wannan abu da daure kai yake. Maigadi ma irin amsar da ya bayar kenan. Murna da dokin dawowarsa gida duk suka bace a lokacin sai zulumin abinda ke faruwa. Kofar dakin Izzatu ya koma yana bugawa iya karfinsa....Izzy ki bude kofar nan idan kina son kanki da arziki. Daga ciki tace bazan bude ba Hamza. So kake ka taba lafiyar jikina akan abinda bani da masaniya akan sa. Daurewa yayi yace ni ba dukanki zanyi ba. We need to talk. Ko kina da amsar da zaki bawa iyayenta ne? Duk da haka Izzatu bata bude kofar ba sai da ya tabbatar mata babu abinda zaiyi mata. Dakin nata duk a hargitse yake kamar ana wasan dambe aciki. Ko a mafarki bai taba tunanin akwai ranar da Izzy zata yi kazanta ba saboda ba halinta bane. Kujerar gaban mudubi ya jawo ya zauna. Iyakar dauriya yake yi kada ya tsorata Izzatu taki bashi amsar da yake nema. A nutse ya fara magana.....Izzy kin tuna lokacin da muka fara haduwa?kunzo school dinmu ke da yayarki Zeenatu a Canada ko. Idan kin tuna ours was love at first sight. Daga haduwar farko bamu rabu ba sai da nasan gidanku da numbar wayarki. Kuma sanin kanki ne ko bayan aurenmu duk wata suka da ake kawo min game dake ban taba saurare ba saboda son da nake miki. Hatta iyayena basa son irin zaman da muke yi amma kullum ina supporting dinki. Haka ne??? A dan tsorace ta gyada kai. Hamza yace good, ashe kenan duk ranar da kika ga na juya miki baya bai kamata kiga laifina ba. Kinfi kowa sanin da yadda na auri Zuhra. Kafin ba aureta na soma ganin sauyi a rayuwata wanda yasa dole na sake tunani akan yadda muke gudanar da rayuwarmu a matsayinmu na musulmi. Na rokeki da mu canja kika ki. Sai Allah Ya kawo matar da sanadiyarki ta shigo gidana amma sai ta dace da irin dabi'un da duk mai hankali yasan sune dabi'un da suka dace da al'adun mu. Bin al'adun wasu da muke yi tamkar mun saka mask(fuska)ne. Duk yadda muka so da nuna mu turawa ne hakan bazai taba tabbata ba saboda a karkashin fuskar nan mu na ainihin muna nan. Da ace kin dauki shawarata babu wani abu da Zuhra zata yi da zai dauke min hankali. Ke kika yi sake har yarinya kamarta ta zame min abin alfahari. Duk da haka kinsan a irin abubuwan da kike min kuma har yanzu kike gidan nan akwai sonki a zuciyata. Duk tsarin zancen nan na Hamza hankalin Izzatu ba a kwance yake ba. Babu abinda take tsoro kamar yasan gaskiya ya saketa. Idan Hamza ya saketa tabbas zata iya rasa rayuwarta. Babu wani mutum da take so kamarsa. A hankali yaje gabanta ya rike kafadunta. Idanunsa sunyi ja sosai...Izzy ki taimakeni ki fada min inda Zuhra take. Hannunsa ta ture dama nasan duk wannan tsarin zancen kana yi ne don kawai kaji inda matarka take. To ni ban sani ba. Da zaka tafi ai ba ajiyarta ka bani ba. Tunda ka tafi bata sake kwana a gidan nan ba. Kan Hamza ya daure...ranakun da kika ce tana dakinta ko ta fita duk karya ne kenan? Izzatu tace karya ne. Nima nemanta nake yi saboda gudun rana irin wannan. Ka dawo ka fara blaming dina. Shekaru sama da goma Hamza ya gama sanin Izzatu ya kuma san lokacin da zancenta yake karya...kisa mayafi ki fito ina jiranki, ki taho min da key din mota. Yana fadin haka ya fita daga dakin. Ji yake kamar ya shake Izzatu amma bazaiyi haka ba. Gara ya daure kila ta fadi gaskiya. Sai da ya bita ciki har sau biyu tana kin fitowa karshe kusan janta yayi ya turata a mota. Gudu yake kamar motar zata tashi bai tsaya ko'ina ba sai gidansu. Dama su Alhaji sun san hakan zai faru shiyasa aka hana Zuhra zaman falo. A dakin su Hamida ta zauna tayi tagumi. Ta rasa gane dalilin su Hajiya na kin sanar da Hamza inda take. Tana wannan zaman taji muryarsa a falo...gabanta ne ya fadi taji kamar ta fita. Ba karamin kewarsa takeyi ba. Domin ya dan wuce wata biyun kafin ya dawo. ***** Hamida ya gani a falo tana masa sannu da zuwa ko amsawa baiyi ba yace ina Alhaji? Hanyar dakinsa ta nuna ya wuce yana jan hannun Izzatu. Sallama ya rinka yi Mama ta fito da sauri. Itama Hajiya ta fito daga dakinta. Kana ganinsa kasan hankalinsa a tashe yake Mama tace Yaya lafiya? Mama ina Alhaji? Tace yana falonsa. Itama tausayi Hamza ya bata. Zata so a barshi yaga matarsa. Ta tabbatar ko zama baiyi ba ya fito. Suna zazzaune a falon Alhajin Hamza ya gaishesu. Batare da ya jira sun amsa ba bare a tambayeshi ya hanya yace Zuhra ta bata. Kamar gaske suka nuna mamakinsu. Alhaji yace wace irin magana ce wannan? Hamza yace tunda na dawo banganta ba. Kuma kafin na taho kullum muna waya da ita amma yanzu na kasa samu. Na tambaya a gidan duk sunce tunda na tafi basu kara ganinta ba. Nayi tunanin zuwa gidansu amma ina tsoron ko bata can kada na tadawa su Baba hankali. Alhaji ya kalli Izzatu yace ke kalle ni nan. Ai kuwa ta daga kai ta masa kiri da ido. Yayi murmushi irin na manya...tunda mijinku yayi tafiya kin fada mana baki ga Zuhra ba? Sai yau zaku zo nan kuna nemanta? Da kika zo gidan nan kwanaki ba cewa kika yi tana gida ba? Hamza yace Alhaji duk karya take. Don Allah ku taimakeni.... Hajiya ta tashi zata bar falon. Tausayin danta take ji. Maganar Izzatu ta dakatar da ita...Baby ina jin fa kauyensu ta koma. Kasan tun farko munyi shawarar zaka saketa bayan wata shida... Ba kunya Hamza yasa hannu ya toshewa Izzatu baki a gaban iyayensa. Idan ya kyaleta zata baro masa matsala ne. Alhaji yace sakar mata baki tayi magana. Sakinta yayi yana harararta. Izzatu tace tunda aka yi auren ba sonta yake ba muka yanke shawarar bayan wata shida zai saketa. Ina jin saukaka masa tayi ta tafi kauye wurin 'yan uwansu. Hamza ya dafe kai Izzatu kuwa tayi murmushi..ko ba komai yanzu ta fitar da kanta daga zargi. Ran Alhaji a bace yace Yaya da gaske da girmanka da hankalinka ka taba fadar magana irin wannan? Kai a kasa Hamza yace eh Alhaji, amma tuntuni maganar ta wuce. Alhaji ya mike to ni babu ruwana. Tunda har yanzu bakayi hankali ba Allah Yasa a dace ka ganta. Kwana uku na baka ka nemo 'yar mutane ka bata takardarta. Na zata auren da nayi maka gata ne ashe kai tunanin mafita kawai kake yi. Hamza ya fara bawa Alhaji hakuri. Wannan magana ta dade Alhaji. Don Allah kada kace na saketa wallahi ina sonta. Idan ka iya nemota nan da kwana uku shikenan idan ba haka ba kuwa duk inda aka ganta zaka saketa ne. Ka tashi ka bani wuri. Jiki ba kwari Hamza ya fita Izzatu na bin bayansa hankali ya dan kwanta ance zai saki Zuhra. Suna fita Hajiya ta koma ta zauna. Alhaji yace kinga shirme irin na babana ko? Ni so nayi wannan mara kunyar ta fada da bakinta abinda tayiwa Zuhra yaji sai gashi ashe shima akwai nasa laifin. Ni kam da gaske idan auren nan bazai yiwu ba gara su rabu kada watarana su kashe 'yar mutane. Mama tace anya Alhaji batun rabuwa bai taso ba. Yaran nan suna son junansu. Kayi hakuri ta koma dakinta. Tunda kace zaka hukunta Izzatu ai shikenan. Shima Yayan sai na hukunta shi. Niyata a yau dinnan ya dauki matarsa. Amma tunda naji wannan zancen hukuncinsa shine ya tafi nemanta. Yadda suka kuntata mata a gidan nan suma su dandana. **** Kwanaki biyu sun wuce a lokacin da Alhaji ya bawa Hamza. Police station din da yaje shi kanshi bai san adadinsu ba. Maganar bacci dama sai dai ya sace shi. Abinci ma rabonsa da abin kirki tun a jirgi. Lokaci guda duk ya zabge. Yana son bada cigiya a gidan rediyo da talabijin amma yana gudun kada su Umma su gani. Da daddare ya bude jakar kayansa ya dauko tasu tsarabar. Babu wanda ya bawa komai sai a lokacin ya dauka ya tafi gidansu Zuhra. Su Baba suna ta tambayarsa ya hanya amma hankalinsa na ga ta ina zai ga bullowar Zuhra. Sai da Umma tace tana fatan Zuhra lafiya kwana biyu basa samunta a waya ya tabbatar bata gidan. To shi yanzu ina zai duba kuma??? Da ya tafi Umma har kuka tayi tace ita wallahi zata fada masa inda Zuhra take....Haba Baban Zuhra ka duba kaga yadda ya rame duk ya fita hayyacinsa. Baba yace nima ina tausayinsa amma ki bari muga iya gudun ruwan Alhaji. Mu bashi dama kamar yadda ya nemi alfarma. **** Daga gidansu Zuhra gidan Ibrahim ya wuce ko Allah Yasa sun san inda take. Nan ma babu wani abun arziki da ya samu. Haka ya tafi gida jiki a sanyaye. Izzatu ya tarar ta gyara jikinta sannan tayi masa girki mai kyau. Ita tunda laifin ya tashi daga kanta to babu matsala. Tana ji a ranta dai duk inda Zuhra take tana lafiya tunda har suna waya da Hamza kafin ya dawo. Idan taki bayyana kanta wannan matsalarta ce. Ko kallon abincin baiyi ba ya shige daki. Yana kwanciya Anti Faiza ta fado masa a rai ya sake daukar mukulli ya tafi gidanta. Har falo ta kaishi wurin mijinta suka gaisa itama ta nuna kamar bata san komai ba. A haka ya koma gida duk yadda Izzatu taso ya saurareta ko abinci ya ci abu ya gagara. Washegari da safe ya bawa Tala umarnin ta gyara dakin Zuhra kafin ya dawo. Da murnarta tace an ganta ne? Hamza yayi murmushi mai ciwo...a'a amma bana so ta dawo ta rasa wurin kwana. Yadda yayi magana yasa Tala hawaye. Me yasa iyayensa suka ki sanar dashi inda matarsa take. Sajensa duk yayi wani iri saboda rashin gyara wani gashin yafi wani tsaho. Ruwan tea kawai yasha ya fita zuwa office din 'yan sanda da suka kirashi an tsinci wata mata. Yaje ya tarar ba Zuhra bace kafin ya fito Alhaji ya kirashi yana masa tuni gobe ne za'a kawo kudin Adabiyya da Hamida kuma za'a saka ranar aure. Shiru yayi na dan lokaci sannan yace yanzu Alhaji ni baza'a yafe min zuwa ba? Duk su Kawu basu isa ba sai nazo? Alhaji yace kaine babba a gidan nan Yaya rashin zuwanka bazai nuna abu mai kyau ba. Kuma ina maganar Zuhra ta kwana? Har yanzu baka ce komai ba. Ina kan dubawa Alhaji yanzu ma ina police station. Tausayin dan nasa yaji yace ka koma gida haka gobe kuzo kai da matarka. Na sami labari ina tunanin an kusa ganinta. Bai jira amsar Hamza ba ya kashe wayar. Cikin minti talatin Hamza ya iso gidan ya dami Alhaji sai ya fada masa labarin da yaji. Alhaji yace ya bari sai gobe idan ya tabbatar amma yazo tare da Izzatu idan an gama karbar kudin zasuyi magana. *** Zuhra na daki tun shigowar Hamza tana kuka. A haka Mama ta shigo ta sameta sai tace abu ne ya fada mata a ido. Idanun Mama suka ciko da hawaye na tausayi. Wurin Alhaji taje tana rokonsa ya bar Hamza yaga matarsa haka. Musamman Zuhra da take da ciki ga damuwa. Alhaji yace zuwa gobe in sha Allah zasu ga juna. Mutumci yake son siya mata. Hamza bai taba ganin dare mai nisa kamar na yau ba. Zuciyarsa ta gama bashi Alhaji ya san inda matarsa take. Tunda ya koma gida ya fadawa Izzatu zasu je gidan za'a kawo kudin auren kannensa. Baki ta turo tana mita. Tasan aiki kawai zasu sakata. Tun karfe takwas Hamza yayi wanka ya kuma dami Izzatu sai da tayi. Batun office dama tunda ya dawo bai waiwayesu ba. Suma sun masa uzuri saboda ya dade baya tare da iyalinsa. Tara na safe suka isa gidansu. Lokacin mutan gidan basu gama tashi daga bacci ba. Ita dai Izzatu ranta ya gama baci amma yadda Hamza ya zama masifaffe tunda ya dawo baiga Zuhra ba dole tayi hakuri. Kowa ya fito sai yayi mamakin ganinsu. Adabiyya ta fadawa Zuhra yazo dadi ya isheta saboda Mama ta fada mata yau zata koma gidanta. Duk wani shiri da ya kamata mace tayi anyiwa Zuhra. Hatta salon taje an gyara mata gashinta ga lalle baki da ja irin wanda Hamza yake so. Kana ganinta kaga amarya da dan karamin cikinta da yake fitowa idan kaya suka kama ta. Ana aikin soye soyen da za'a kaiwa baki idan sun zo Mama ta kira Zuhra kitchen ta tambayeta ko zata iya girki. Zuhra tace eh saboda yanzu bata wannan tashin zuciyar. Mama tayi murmushi to maza ki dafawa mijinki abinda kika san zai masa dadi zansa ayi gadin kitchen har ki gama. Allah Yayi muku albarka. Murmushi kawai Zuhra tayi. A yadda su Hamida suka ce mata Hamza ya rame sosai kwana uku kawai sai tayi masa tuwon shinkafa da miyar taushe. Nutsuwa tayi tayi girkin yadda zaiyi dadi sosai. Ta dai sha tsiya wurinsu Mariya amma yau ko a jikinta. **** Hamza ya gaji da jan lokacin da Alhaji yake masa amma haka ya hakura don babu yadda zaiyi. Izzatu duk aikin da akeyi tana zaune a wurinsa a falo. Su Hajiya kawai taje ta gaisar a dakunansu ta sake komawa wurin mijinta. Suna nan zaune har su Ibrahim suka zo sannan 'yan uwansu da suka kwana a gidan maza suka fito zuwa falon Alhaji. A nan aka hadu da dangin mazan suka yi abinda ya kawosu aka saka biki bayan sallah babba. Da kyar Hamza ya iya bari suka gama tafiya ya matsa kusa da Alhaji. Alh Nasiru yayi dariya babana ban sanka da zumudi ba. Yau ance a kusan a gidan nan ka kwana. Hamza dai babu amsa sai jiran bayanin da Alhaji yake dashi. Alhaji ya tura Nura ya kirawo su Hajiya da Izzatu. Hankalinta kwance tana tunanin kwanakin da aka bawa Hamza sun kare Alhaji zaisa ya saketa. Duk sun zauna harda su Ibrahim. Alhaji ya kalli Izzatu yace... Izzatu ina so ki dubi girman Allah ki fada mana inda kika kai Zuhra. Daga ke sai ita ne a gidanku saboda haka ko zata bar gidan na tabbatar akwai sa hannunki a ciki. Izzatu ta firgita ta daga kai suka hada ido da Hamza. Shima kallonta yake yi ya kasa gane dalilin Alhaji na yi mata wannan tambayar. Idanun kowa a kanta suke tace ni fa bansan inda take ba. Tashi nayi da safe kawai naga bata nan. Har nemanta naje yi banganta ba. Wallahi Baby ka da ka yarda da duk abinda za'a fada maka sharri ake son kulla min. Ba tun yau ba nasan babu mai kaunata a gidan nan. Hakuri kawai kuke yi.... Tsawar da Hamza ya daka mata ce tasa tayi saurin yin shiru. Izzy idan kina da masaniya akan batan Zuhra ki fada min tun wuri. Sama da wata biyu Allah kadai Yasan halin da take ciki. Alhaji ya dubi iyalinsa yace ya isa haka Yaya. Kunga dai na bata dama ta wanke kanta wurin mijinta sai ta zabi tayi karya. To ni nasan inda Zuhra take amma tunda bazaki fadi gaskiya ba ku tashi ku tafi kawai. Hamza duk ya gigice yace Izzy zan saba miki wallahi. Ki fadi abinda Alhaji ke tambayarki. Me kika sani game da batan ta? Izzatu ta dage bata san komai ba. Alhaji yace to ni na sami labari kin hada bako da wasu sunzo har gida sun saceta ko ba haka bane Ibrahim? Ibrahim yace haka ne don akwai shaidu. So suke ta fadi gaskiya da bakinta. Tana jin haka ta fara zare ido saboda yadda taga Hamza yayo kanta... wallahi karya ake min. Duk wanda ya fada karya yake yi. A airport kawai na barta a daren da ka tafi na koma gida ni kadai. A ransa Hamza yaji maganar....a sanyaye yace me kike nufi Izzy? Ibrahim yace bari nayi maka bayani kamar yadda idanunmu suka gane mana. Hamza dai har kuka yayi da yaji a irin halin da suka ga Zuhra a gaban sojoji. Shiyasa babu wanda yayi yunkurin dakatar dashi a lokacin da ya kwadawa Izzatu mari har uku. Zaiyi na hudun Alhaji ya hana shi. Hamza ya nunata da yatsa...nasan baki da hankali wani lokacin amma bansan ke mahaukaciya bace sai yau. Yanzu da sun harbeta kina tunanin zaki cigaba da rayuwa ne? Duk abinda kike yi ina kawar da kai sai da kika kureni. Izzy har mahaifa kika cire da ciki da gangan na cigaba da zama dake. Me kike so ne a rayuwarki? Yana hawaye su Hajiya suna yi saboda jin irin abinda tayi. Alhaji yace nayi hakuri da halinki Izzatu amma wannan karon zan nuna miki matsayina a wurin mijinki. Kai Hamza yi mata saki daya.... Gaban Alhaji taje ta durkusa tana kuka tana rokonsa yayi hakuri. Fuskarsa a hade yace ko baka ji bane? Hamza yace na sakeki saki daya. Alhaji yace nagode kara mata daya... Wannan karon gabansu Hajiya ta koma tana kuka tana rokon su rufa mata asiri. Bata bawa kowa tausayi ba duk da basu taba tsammanin haka daga Alhaji ba. Hamza ya kara cewa na sakeki Izzatu. Alhaji yace to saura igiya daya tsakaninku. Idan kina da hankali sai kiyi tattalinta har karshen rayuwarki domin na bashi dama ranar da kika sake kwatanta irin haka ya cika miki na ukun. Allah ne yayi Zuhra na da sauran kwana a yadda sojoji ke harbi idan suna zargin mutum. Ki koma gidanki kiyi idda wannan kuma umarni ne na addini ba nawa ba. Hamza ka fada mata idan ta kuskura taki zama a gidan to sauran igiyar ma zaka karasata. Kamar mutum mutumi haka Hamza ya zama ya maimaita abinda Alhaji yace. Zuciyarsa na can tana saka masa abinda zai faru ba don Tala tayi tunani ba. Kukan Izzatu duk ya cika falon Alhaji yace ko tana da sauran magana tayi saurin girgiza kai. Kada yayi sanadin rabata da farincikin rayuwarta. Yace Nura tashi ka kaita gida. Nura ya fara kunkuni, yaushe zai manta yadda yaga Zuhra babu ko dankwali sojoji sun zagayeta da bindiga. Don babu yadda zaiyi ne suka fita tare tana kuka. Suna fita Alhaji yace Yaya ka mayar da matarka yanzun nan. Hamza ya dago jajayen idanu yace Alhaji bazan iya ba. Da kanka kace na saketa. Ni bani da burin rabata da 'ya'yanta. Ka mayar da ita amma kada ta sani sai tayi wata uku a tunaninta idda take. Kila idan anyi sa'a ta canja hali a dan lokacin. Nayi haka ne don tasan cewa ba'a wasa da ran dan Adam. Idan bazaka iya ba kuma zan mayar da Zuhra ga iyayenta. Ba shiri Hamza yace na mayar da ita. Mama don Allah ina Zuhran take? Muryarta yaji daga bakin kofa tana sallama. Dama a tsaye Hamza yake tana shigowa yayi saurin rungumeta ita kuma tana kokarin ture shi. Su Hajiya kowa sai kawar da kai yake yi. Alhaji da yaso tarasu yayi musu nasiha yace kai Yaya ku bar wurin nan. Sam Hamza bai ji ba ya fara neman bakin Zuhra. Alhaji ya daga murya yace kai Hamza zan saba maka. Nace ku bar wurin nan. Wani murmushi yayi ya juya ya kalli iyayensa. Sai a lokacin yaji kunya yaja hannun Zuhra wadda take jin kamar ta nutse a kasa suka fita. Mama ta kwashe da dariya. Alhaji ni bazan ce komai ba sai Allah Ya kara. Dama rabon kaga rashin kunya yasa kaki bashi matarsa da wuri. Dariya suka soma yi harda Hajiya sai suka kula da Ibrahim da ya rufe fuska da hula. Alhaji yace bana son gulma kaima tashi ka tafi wurin matarka. Da gudu ya fice yana dariya. **** Rasa dakin da zai shiga da ita yayi ya ja hannunta zuwa dakin Nura. Yana rufe kofar ya juyo yana kallonta. Sai da ya juyata a gabansa yace Cutie babu inda yake miki ciwo? Dariya take yi tace Ya Hamzana babu. Ya rungumeta sosai yana suna ajiyar zuciya. Ya dago kai yana shafa bakinta...I miss you Cutie. Kiyi hakuri don Allah ban kula dake yadda ya kamata ba. Duk abinda ya faru laifina ne. Yakamata ace naga tafiyarku kafin na koma ciki. Hawaye fal idonta tace duk ya wuce. Zai sake magana ta rufe masa baki da nata. Sun jima a haka sannan yace Cutie duk kin canja kin kara kyau. Hannunsa ta kama ta zira a karkashin rigarta. Ya ware ido sosai yana kallonta...tauri fa nake ji Cutie. Sai kuma taji kunya ta sunkuyar da kanta kasa tana murmushi. Ya sa hannuwansa biyu ya dago kan nata....are you pregnant? Maimakon ta bashi amsa sai kawai ta rungumeshi. A hankali tace wata hudu kenan. Sakinta yayi ya durkusa a gabanta yana shafa cikin cike da kulawa...baby your daddy is back. Yayi kissing cikin sannan ya tashi ya kura mata ido. I love you so much Fatima. Tace nima haka.. Hamza yace ban karba ba. Tayi dariya I love you Ya Hamza. Wani kallo yake binta dashi ya kama hannunta muje ki dauko mayafinki mu tafi gida. Tace har girki nayi maka kuma su Hajiya basu ce na tafi ba. Kinga na baki minti goma ki dauko abinda zaki dauko mu tafi idan ba haka ba kuma na maimaita irin abin dazu a gabansu. Fita tayi cikin farinciki ta dauko dan kwandon da ta saka flask din abincin. Dakinsu Adabiyya ta shiga daukar mayafi su Jidda suka fara tsokanarta. Mariya tace kinga wuce ki tafi Mama tace sun yafe sallamar wai wadda kuka yi dazu ta wadatar. Zuhra taji kunya sosai ta fita suka rakata har bakin mota suna ta shakiyanci. Ganin Hamza ya hade fuska yasa suka koma ciki. Shi kuma ya tada mota sai gida. [11/3, 6:36 PM] Angel Teema: AL'ADUN WASU #78 Batul Mamman(Mrs)# Saida suka gama wanka sannan Hamza ya dauko Zuhra. Bai ajeta ko'ina ba sai kan gado ya dauko vasseline dake kan dress mirror ya mikawa Zuhra gami da lakutar hancinta yace Cutie sai ki qarasa aikinki. Murmushi tayi gami da rufe fuskarta da tafin hannunta alamar kunya janyota yayi jikinsa sannan ya fara magana a kunnenta chan qasa yace Cutie tunda bazaki qarasa aikinki ba bare naje Izzy ta min. Dagowa tayi da sauri suka hada ido sannan ta dauki vasseline din dake gefensu ta shiga shafa masa cikin shagwaba tace nifa ba haka nake nufi ba Yaya Hamza, yace to yayane Cutie ya qarasa maganar cikin dariya. Zumburo baki tayi, kissing dinta yayi sannan yace to kiyi haquri My Cutie. Haka suka gama shiryawa cike da nishadi suka sakko qasa. Izzatu dake zaune a palo ganin Zuhra na sakkowa tare da Hamza ta miqe da sauri ta nufi inda suke da murmushi gami da rungumeshi tana fadin Baby ga abincinka yana jiranka a dinning, a hankali ya saci kallon Zuhra data hade rai sannan ya ture Izzatu yana fadin bana son shirme Izzy. Wait for Batul Mamman lol. Da kuka Izzatu ta fito daga motar Nura. Maigadi ya biyota yana tambayar ko lafiya. Bata bashi amsa ba sai kallon banza. Murya a sama tana kuka ta shige ciki. Nura dai tsaki yayi ya ja motarsa. Tala ma da yaran duka babu wanda ta kula ta wuce ta tafi dakinta. Wai ita Hamza zaiyiwa saki har biyu? Lallai dan Adam ba'a ci masa laya. Irin soyayyar da suka yi tun kafin suyi aure ta zauna tana tunawa. Bakincikinta ya karu ne saboda a ganinta ba karamin kaskanci bane ace an saketa saboda wata Zuhra. Yarinyar da bata jin ko brush din kirki ta iya lokacin da Hamza ya aureta. Rasa mafita tayi ta dauki waya ta kira Raliya. Babu abinda ta ragewa mahaifiyar tata na dangane da abinda tayiwa Zuhra zuwa halin da take ciki yanzu. Raliya ma kukan ta soma yi tace Izzatu kinga abinda nake ta ji miki tsoro sai da ya faru. Ban ga ranar bin al'adun wasu don ka burge wasu tsiraran mutane ba. Kwalin tissue din da ta kusa kararwa daga shigarta daki ta kuma janyo wata ta goge hawaye....Mum ya zaki ce ina bin al'adun wasu. Duk abinda muke yi da ai tare dashi mukeyi. 'Yan wadanda nayi da baya so sosai kadan ne. Kuma naga shima dan zaman da yayi a Canada ya isa ace ya waye da dabi'unsu. Ace mu kullum 'yan Nigeria babu wani canji a rayuwarmu. Ni a ganina kawai gajiya yayi dani amma babu wasu al'adun wasu da nake yi. Ta yaro kyau take Raliya ta fada tana tuna irin sakacin da ya samo asali daga wurin Alh Sunusi a fannin tarbiyar 'ya'yansu. Shine ya dage sai su barsu su sake bayan sun bar kasarsu. Tun Raliya bata jindadin yadda 'ya'yansu ke sajewa da na turawa ta fannin dabi'a har ta fara so musamman idan suka zo gida Nigeria suka shiga cikin 'yan uwa. Dan turancin da sukeyi da 'yar fitsara shi yake burge mutanenmu. Sai kaga kowa na kokarin kyautata musu tamkar anga 'ya'yan wani shugaban kasa. Kuma irin haka dama halinmu ne musamman Hausawa. Da 'yan uwanmu sun tafi kasar waje mun rinka shela kenan sai kowa ya sani. Idan suka zo ganin gida kuwa ba'a magana. Kowa jiki na rawa yana tasa bajintar. Raliya tayi ajiyar zuciya....yanzu duk bazaki gane abinda nake nufi ba kila sai nan gaba. Amma ina so ki sani namiji duk inda yake indai akwai sauran mutumci a tare dashi to yana son a kyautatawa iyayensa. Sai kika yi rashin sa'a gidan Alh Nasiru tsarin rayuwarki bai burgesu ba. A zatonki sonki ne basa yi shiyasa kuka yi ta samun sabani da Hamza da farko har sonki ya rufe masa ido ya koma yana biye miki. To kada ki manta dama tun da fari ga irin tarbiyar da ya tashi da ita yake hakuri da irin taki tunda ke kinki canjawa don ki faranta masa. Sai Allah Ya kawo wadda zata yi masa yadda yake so kafin yace yana so. Ai wallahi dole ra'ayinsa ya juya can. Gashi ke kuma sai shirmenki ya karu ninki akan na baya. Izzatu dai kuka take tana sauraron mahaifiyarta. Raliya tace kina jina kuwa? A hankali tace eh. Duk abinda kika yi masa kinga ai ya hakura musamman cire mahaifa. Amma yau da yarinyar nan ta mutu wallahi banda saki uku nasan sai yasa an kulleki. Kinyi sake tauraronki ya dishe a zuciyarsa. Abinda Larai take ta korafin zai iya faruwa kenan duk muka banzatar da ita. Yanzu ki bari zan kira Ustaz dan gidan Kawu mai zare na tambayeshi game da dalilin cewa sai kinyi idda a gidan. Kafin nan don Allah Izzatu ki kama kanki kinji ko. Zan kiraki idan munyi magana. Yau daya a rayuwarta da take ganin ta rasa abu mai matukar mahimmanci ta nutsu ta saurari mahaifiyarta. Idan har akwai yadda zatayi ta sake mallakar Hamza to zata yi. Abu daya ne bata yarda dashi ba saboda tashin turai da tayi shine bin malaman tsibbu da bokaye. Kyankyaminsu take ji kuma gata da tsoron zuwa irin wuraren nan. Ta taba kawa da ta kaita wai a basu maganin mallaka. Tunda taji ana zancen tayi masa lemo da jinin al'adarta na ranar karshe a wata bata koma ba. Bokan na fada tana amai ma. **** Babu wata hira tsakanin Hamza da Zuhra a motar sai kallon juna da murmushi. Karshe ma hannunta ya hada da giyar motar ya rike. Dukkaninsu farincikin da suke ciki bazai misaltu ba. Maigadi na bude gate da ya hangota kamar yayi tsalle don murna. Tabbas yasan inda take a bakin Tala amma dole yayi kewarta. Abinci da kyautawar da take musu ai bazasu manta ba. Hatta jakar hannunta mika hannu yayi zai karba Hamza ya karbe yana dariya...Mal Talle anya kayi farincikin ganina ranar da na dawo kuwa. Irin wannan murna haka? Zuhra tayi murmushi kawai ta shige ta barsu. Maigadi yace Yallabai ka rike matarka da kyau. Wallahi tana da kirki sosai. Hamza yace nagode. Ga wannan gobe kaje gida kayi sati biyu....Kudi ne maigadi ya karba da murna. Lallai an sami canji. A da Hamza don kansa baya barinsu zuwa ganin gida sai sunyi ta roko amma yanzu ya san hakkin mutane sosai. A cikin gidan ma tamkar an kawo wutar nepa bayan shekara daya haka suka yi ta murna. Tala ta kwashi 'yan kayan da Zuhra ta sami daukowa ta kai sama. Su Khalifa kuwa suka dane jikinta. Nana sarkin rigima tace Maama goyani.. Zuhra na durkusawa Hamza ya shigo yace ke rufa min asiri. Nana zo na goyaki kinji. Maama da kayana a jikinta. Nana ta sa kuka ita bayan Maama. Tun yana lallabata har ya soma fada. Zuhra ta dage zaya iya goyata yace sam bai yarda ba. Izzatu ce taji kukan ya isheta ta fito. Ganin Hamza yasa zata koma sai kuma ta kula da Zuhra. Ba karamin kyau tayi ba idan aka hadata da Zuhran da ta sani da farko. Kamar ta sauko tayi mata magana taji dalilin da yasa ta boya ta jawo mata saki. Sai ta tuna da shawarar da Raliya ta bata ta koma dakinta tare da bugo kofa da karfi. Da kyar Hamza ya lallaba Nana ta yadda ya goyata. Amma ta dage sai ya saka zani. Zuhra dasu Junior suna ta yi musu dariya yace bazai saka ba. Zuhra ya kalla yace zaki san ni kika yiwa dariya idan na kamaki. Tana jin haka ta haye sama tasan zata sha aiki. Sai dai ga mamakinta dakin fes ta same shi. Komai a gyare, hatta zanin gado Hamza ya dauko sabo Tala ta shimfida a kan gadon. Tare dasu Junior ta tafi dakin suna ta bata labarin abubuwan da sukayi lokacin da bata nan. Hamza ya shigo da Nana a hannu tun yana saka baki a hirar har ransa ya soma baci. Yau da yake son kasancewa da Zuhra bayan lokacin da suka dauka basa tare shine ta biyewa yara hira. Gajiya yayi ya fita dakinsa ya bude jakar kayan tsarabar da bai sami damar budewa ba tunda ya dawo. Kayayakin da ya siyowa yaran ya debo harda wasu riguna da ya siyowa Tala da maigadi. Bawa kowa nasa yayi sannan ya basu nasu Tala. Harda kashedi idan kun kai musu kuje ku nunawa Mummy. Yara an sami abinda ake so suka fita suna ta murna. Suna tafiya ya rufe kofar harda murda mukulli. Zuhra ta dawo kusa dashi ta tsaya yana ta kallonta musamman dan cikinta da ya tasa kadan. Hannuwanta ta sakala a wuyansa ta rungumeshi. Yace da kinsan abinda kike so kenan kika biyewa yara kina hira kawai don ki ja min aji....ya kama hannuwan nata ya cire...nima yanzu zan ja nawa sai ki bisu kuyi hira ni bacci nake ji. Zuhra tayi dariya ta sake rungumarsa. Haba Ya Hamza kaga suma nayi kewarsu ne shiyasa. Dan zo kaji irin yadda nayi kewarka duk tafi ta kowa. Matsawa ya kara yi naki din. An fada miki mata ne kadai suka iya yanga. Sai nan da sati daya zamu fara kwana a daki daya ma. Kinga tafiyata. Yana tafiya Zuhra ta sake binshi ta rungumeshi ta baya tana masa dariya....idan ka fita abinda na kawo maka na murnar dawowarka zan fasa baka....yadda take magana tana jan kowane harafi yasa shi saurin juyowa suna kallon juna. Kafin ya daga hannu ya tabata an soma kiran sallar magriba. Ya cije lebe Zuhra ta kwashe da dariya. Ai kaga yanzu sai kayi yanga da hujja. Ni bari naje nayi alwala sai bayan sati idan mun hadu. Hannunta ya rike suna bin kiran sallar har aka gama suka yi addua sannan yace yau idan kika shigo hannuna Cutie...hmmmm sai na dawo dai. Love you. Itama tace masa Love you too sannan ya fara shiga toilet dinta yayi alwala ya fito ya tafi masallaci. Da Zuhra ta idar da sallah kasa ta sauka wurinsu Tala. Abincin da tayiwa Hamza bashi da yawan da zasu ci duka gidan shiyasa ta dora jallof din taliya. Ba jimawa ta gama ta zubawa kowa. Tala sai kallonta take tana murmushi. Ba karamin kewa ta barsu dashi ba. Bare da ta kula kamar Zuhran ciki gareta shikenan komai sai tace kawo na karasa. Haka suka gama girkin ta koma dakinta tayi sallar Isha. Bayan Ishar Hamza ya dawo. Yau fa anga Cutie bashi da wurin zama sai inda take. Hijab din da tayi sallah ya samu tana ninkewa ya karba ya karasa mata sannan yace ta zauna zasu yi magana. Zancen abinda Izzatu tayi yayi mata sannan yace nasan kina sane da hukuncin da Alhaji ya yanke na cewa na saketa ko? Sunkuyar da kai Zuhra tayi bata ce komai ba sai hawaye dake barazanar saukowa daga idonta. Sauran abubuwan da Izzatu tayi mata duk da bata ji dadi ba amma tana iya danne bacin ranta ta hakura. Wannan karon kuwa idan har tace ta hakura babu komai ita kanta tasan dole a jerata sahun farko a makaryata. Babu macen da zata fuskanci abu makamancin wannan tace ta hakura lokaci daya. Duk tunanin da Zuhra take yi Hamza na kallonta. Abu ne mai wuya ace Zuhra ta yafewa Izzatu....sake matsowa yayi jikinta sosai yace..babu wanda zai iya kwatanta halin da kika shiga sai wanda ya tsinci kansa a ciki. Abinda Izzy tayi miki ba abu bane da zamu iya mantawa da wuri. Sai dai ina rokonki alfarma yadda kike kokarin kiyaye dukkan abinda kika san ya sabawa shari'a ko zaman aure don Allah Cutie kada ki fara shi saboda bacin rai, kinji. Bata iya magana ba sai kai da ta gyada a hankali. Hawayen da take boyewa suka fara sintiri a fuskarta lokacin da yace mata a gidan Izzatu zata yi Idda. Ga kishi ga bakincinkin abinda ya faru. Hamza bai hanata kuka ba sai ma rungumarta da yayi. A hankali ya sake magana saboda yasan ranta a bace yake... Cutie nasan abinda zan fada yanzu zai kara bata miki rai sai dai ina son kada kiyi hukunci da son zuciya. Kiyi tunani a matsayinki na musulma wadda take fatan itama idan tayi kuskure a yafe mata. Rikon da tayi masa ya tabbatar masa tana jinsa.... Alhaji yasa na mayar da Izzy bayan fitarta dazu saboda haka a matsayin matata take har yanzu duk da bata san hakan ba. Na fada miki ne saboda kada kiga wani dalili yasa naje inda take tana da hakki a kaina har yanzu. Zan bari sai tayi tunanin ta gama idda sannan na sanar da ita. Hakan muna fata ya zama sanadiyar nutsuwarta. Batun girki kuma zata dafa iya na cikinta banda su Nana. Zancen Hamza har zuci ya daki Zuhra sai dai kuma tana da tabbacin son zuciya bazai taba zama alkhairi gareta ba. Shi Izzatu tayi sai gashi ita da take raina kanta da kanta ta mallaki zuciyar mutum kamar Hamza. Dago fuska tayi suka hada ido tayi saurin rufe nata....Ya Hamza in sha Allahu bazan taba shiga tsakaninka da matarka ba. Tare na ganku kuma nasan duk matsalolin nan saboda ni suke faruwa. Idan a da ban fahimceta ba yanzu nasan ya mace take ji idan taga mijinta da wata. Allah Yasa a samu abinda ake nema...ta mike tsaye tana jan hannunsa.... ka tashi muje muci abinci sai ayi wanka a kwanta. Dawo da ita yayi kan cinyarsa...dan fada min ya mace take ji idan taga mijinta da wata. Zuhra tace tabdi ai rai ne yake baci sosai. Nifa ranar da ta dawo da kyar nayi bacci. Hamza yayi dariya yace kina ta tunanin ko muna can muna.... Bakinsa ta toshe da hannunta ta tashi tana jin kunya. Kafin ya tashi ta fice daga dakin. **** Abin duniya ya ishi Izzatu sai juyi take akan gado ga wata uwar yunwa na cinta. Bata son fita ta hadu da Zuhra ko Hamza. Da wane ido zasu kalli juna? Kila Zuhra ta rinka mata dariya ma saboda yanzu an saketa. Tana wannan tunanin Raliya ta kirata. Da sauri ta dauki wayar tana son jin jawabin Ustaz. Raliya tace to ki saurare ni da kyau Izzatu. Idan kika bari wannan damar ta wuceki babu ruwana. Ustaz yace ba karamin kokari suka yi ba suka ce kiyi idda a gidan. Mutanenmu da yawa basu san cewa yana da kyau idan anyi saki daya ko biyu mace tayi idda a gidanta ba. Hakan zai sa a wannan lokacin tayi kokarin jan hankalin mijinta har ta mantar dashi dalilin sakin ya yafe mata ya dawo da ita . Sai ayi saki daya ace na baki minti biyar ki kwashe kayanki. Izzatu tace to Mum hakan dole ne ko mutum nada zabi? Raliya tace mace na da zabi amma zaman shi yafi. Kinfi kowa sanin Hamza saboda shekarun da kuka yi tare. Kinsan me kike yi ki janyo hankalinsa. Sai ki dage da ladabi da biyayya. Girki ma ko bazaici ba kiyi maidadi kiyi masa tayi. Banda saurin fushi kuma babu ruwanki da Zuhra. Idan kika yi ganganci da sauran igiyar nan zaki yi kuka da idanunki don yanzu 'yan mata ma neman miji suke ido rufe bare bazawara mara mahaifa. Haba mana Mum ya zaki fadi haka? Izzatu ta fada kamar tayi kuka. Ya bazan fada ba Izzatu. Ai mahaifar nan da kika cire wallahi ko yau ko gobe sai kin cije yatsa. Naga har yau baki fara damuwa bane. Allah Ya kyauta . Izzatu tace Amin ta tashi da kwarin gwiwa. Wanka tayi ta bata lokaci wurin gyara jikinta sosai tayi kwalliya. Wata rigar bacci ta saka shara shara ta feshe jikinta da turare ta fito ta sauka kasa. Tala har bari tayi saboda shigar da Izzatu tayi. Tayi saurin rufe ido tana tunanin yaushe Hajiyarsu zata dena irin wannan abubuwan. Ita bata taba ganinta da riga irin wannan ba duk da ta saba yawo a gidan da kayan bacci amma masu mutumci ne. Hayaniyar su Khalifa ta jiyo a falon Hamza tayi murmushi tasan yana ciki. Canja tafiya tayi ta shiga falon. Zuhra da Hamza ke cin tuwon da tayi masa da Nana wadda idonta idon tuwo. Junior da Khalifa suna ta wasa da bindigar roba. Kamshin turarenta ne ya fara sanar dasu ta iso. Junior ya kalleta baki bude yace Mummy yau kuma baki saka kaya ba kika fito daga daki? Khalifa yace kai ta saka amma irin rigar da Malam yace idan mace ta saka ta fita za'a sakata a wuta ne. Mummy wallahi babu kyau yawo a haka. Zuhra dai kawar da kanta tayi gefe don tsiraicin yayi yawa. Hamza yasa su Khalifa suka daukarwa Nana plate din tuwon yace su tafi wurin Tala. Suna fita ya juyo kan Izzatu ransa a bace. Yanzu don Allah Izzy baki ji kunyar saukowa haka 'ya'yan cikinki su ganki ba. Kila Tala ma ta ganki ko? Izzatu tayi murmushi...Babyna bansanka da zafin kishi ba. Kuma harda su Khalifa. Ni yunwa nake ji me zamu ci ne? Zuhra yake kallo ido ya cika da hawaye. Yasan dole taji babu dadi musamman da tasan ya mayar da Izzatu. Uwa uba yadda ta kunyata kanta batare da ta damu ba. Ya tashi ya tsaya a gabanta. Kinga Izzy ki bar wurin nan kafin ranki ya baci. Idan har kina so mu shirya to wallahi kada ki sake fitowa da irin wannan kayan. Sai kinyi kamar hankali ya shigeki sai ki fara wani shirmen. Meye amfanin yaro kamar Khalifa yana fada miki babu kyau irin wannan dressing din. Izzatu dai bata damu ba ko kadan. A ranta taji dadin yanayin da Zuhra ta shiga. Dole ta dage ta karkato da hankalinsa ta dawo matsayin matarsa. Karshen takaici Zuhra taji sai ta daure ta tashi ta kama hannun Hamza... Ya Hamza muje nayi maka wanka kaga dare yana kara yi. Daga shi har Izzatu baki suka bude don ko su kadai ne yasan tana jin kunyarsa. Yadda suka yi yasa sauran kadan ta karaya sai ta daure tace...muje mana Ya Hamzana. Bin bayanta yayi suka fita suka bar Izzatu a tsaye rai a bace. Ita bata ga laifin shigarta ba. Tala dai mace ce 'yar uwarta sai kuma 'ya'yanta. To cikinsu waye bai kamata yaganta a haka ba. Tabe baki tayi ta fita ta tafi kitchen ta dafa indomie kwaya daya. Indai haka ake zaman iddar ai bazata dade ba komai zai daidaita. Dakinsa ya ja Zuhra ya bude mata nata tsarabar. Kananan kaya ne da kayan bacci masu kyau. Bakin nan nata ta turo shi gaba ita a dole tana fushi tace ni a dakina zan kwana. Tana magana tana tattare kayan da ya bata. Hamza yace ai baki isa ba sai kinyi min wankan nan. Da bakinki ki fadi abu kuma yanzu ki canja. Zuhra tace ka rufa min asiri Ya Hamza ai sai ace min mara kunya. Daya bayan daya ya sauke kayan hannunta ya shafa cikinta....kinga karshen rashin kunya kuma kin riga kinyi to me kuma ya rage. Sosai taji kunyar maganarsa ta fara sunne kai a kirjinsa....ai kawai fada nayi amma ba gaske bane. Yace to ni da gaske na dauka bari ki gani...bata ankara ba ya dauketa yana cewa kin kara nauyi fa yarinyar nan. Bai ajiyeya ko'ina ba sai cikin toilet ya rufe musu kofa. [11/3, 6:36 PM] Angel Teema: AL'ADUN WASU #78 Batul Mamman(Mrs)# Saman ta bisu yau zata ga karyar soyayya. Sai tayi abinda zai hanasu kwanan farinciki kamar yadda itama bazata yi ba. Dadi taji Hamza bai rufe kofar falon da mukulli ba ta shiga da sanda. Tana zuwa kofar dakin ta jiyo dariyarsu shi da Zuhra. Kunne ta saka jikin kofar har ta gane fadan waye zai fara shafawa dan uwansa mai ake yi. Mutuwar tsaye tayi har wani daci take ji a bakinta saboda bakinciki. Bata taba kawowa a ranta akwai ranar da Hamza zai kasance a cikin dakinsa da wata matar ba ita kuma a waje a matsayin sakakkiya. Hawaye ne mai zafi ya fara sakko mata har tayi nadamar labewa a bakin kofar. Hirar soyayya suke abinsu hankali kwance basu san Izzatu na bakin kofar ba. Jikinta duk yayi sanyi ta fasa abinda tayi niyya ta koma dakinta. Kwana tayi tana kuka don a yanzu ta tabbatar Zuhra ta gama da ita indai ta maganar zuciyar Hamza ne, sai dai bazata bari ta rabata da yaranta ba saboda su ma kirikiri suke nuna sunfi son Zuhran a kanta. Da sassafe ta tashi ta hadawa su Khalifa breakfast. A wadace tayi abincin tunda yanzu Zuhra ta bude musu ciki da shegen cin tsiya a ganinta. Ita dama saboda tana gudar musu kiba ne take basu dan kadan. Kafin karfe takwas tayi musu wanka da kanta duk da babu makaranta ta basu abinci sunci. Zama tayi a dakinsu ta biye musu suna ta wasa. Sunji dadin hakan tunda basu saba ba. Kafin ta bar gidan sai tasa sun kara sonta yadda bazasu yarda ta tafi ta barsu ba. Dole Hamza ya zaba ko ya mayar da ita ko ya bata 'ya'yanta. **** A gaggauce Zuhra ta tashi tayi wanka. Zata tafi dakinta Hamza ya bude ido ya ganta tana yafa mayafi akan tawul din jikinta. Murmushi yayi na jin dadin ganinta...Ina zaki je da sanyin safiyar nan? Ke da kika kusa wata uku baki ganni ba ki dawo yau a nan zamu wuni...ya fada yana nuna mata kusa dashi akan gadon. Itama murmshin tayi masa...Ya Hamza su kila su Nana sun tashi kaga har tara saura basu ci komai ba. Tala ta nan fa please Cutie ki dawo ki kwanta. Kinsan irin yadda nayi missing dinki kuwa? Kusa dashi ta koma ta zauna har ya fara murna tace...ka bari na je na hada abinci ina gamawa namu anan zamu ci ma babu inda zan sake zuwa sai zan dora na rana. Ba'a son ransa ta fita ba. Ganinta yake kamar wata sabuwar amarya. Tayi masa kyau sosai ga dan cikinta da yake kalla yaji dadi. Kofunan tea ta gani a falo da plates da sauran dankali da kwai a cikin wasu. Tala ce ta fito zata kwashe ta tambaya ko ita ta bawa su Khalifa. Tala tace Izzatu ce tayi girki itama da ta fito sun riga sun ci abinci. Ko kadan bata ji bacin rai ba ta wuce nata kitchen din ta hada musu nasu abincin. Ba jimawa ta koma ta samu har lokacin Hamza yana nan kan gado amma yana aiki da laptop a gabansa. Yana ganin Zuhra ta shigo ya tura laptop din gefe...taho my Cute baby nayi miki tausa nasan kin gaji. Nan da lokaci kadan zaki dena girkin nan bana so ki wahalar min da baby. Zuhra ta turo baki...ba tani kake yi ba sai baby din da baka sani ba. Nagode bari na koma wurinsu Khalifa muyi hira. Yi hakuri wasa nake miki. Ai babu dan da zaki haifa ya kai rabin matsayinki a wurina. Ke ai daban kike da kowa. Ta shafa cikinta...to kai kaji babanka yace baya sonka. Har ka bani tausayi, amma babu komai ni ina sonka kaji. Hamza ya bude baki yana kallon Zuhra tana ta surutu da ciki....haka kika zama kanwa uwar hadi?...kansa ya kai daidai cikin yace kada ka bari ta hadamu. Mata rikicinsu da yawa. Rigima zata min na dan yi mata dadin baki shine zata juya zancen ta hadamu fada. Idan kuma ke mace ce to tun wuri kada ki koyi rigimar mamanki don bata jin magana. Haka suka zauna suna ta hirarsu ana soyayya. Zuhra bata sami saukowa ba sai karfe daya lokacin Hamza ya gama shiryawa zai je masallaci daga nan ya wuce office. Abinci suka samu su Khalifa na ci Izzatu tana bawa Nana a baki. Wani material ta saka dinkin yayi mata kyau sosai tasha kwalliya. Tana ganin sun sauko muryoyinsu na jiya taji suna mata yawo a kunne. Gaskiya labe masifa ne musamman idan miji da kishiya aka yiwa, wata har ta mutu abinda taji bazai taba gogewa daga zuciyarta ba. Shiyasa gara kawai mace ta nesanta kanta daga irin wannan dabi'ar. Ba karamin dauriya tayi ba ta gaishe da Hamza wanda shima haushinsa take ji yanzu. Amsa mata yayi fuskarsa babu yabo babu fallasa. Zuhra ma tayi tata dauriyar tace mata an tashi lafiya? Da kyar Izzatu ta amsa. Riga da skirt ne na atampa a jikin Zuhra itama tayi kwalliyarta. Rigar ta fito da dan cikin wanda idon Izzatu ya kai gareshi. A take taji kamar an sara mata guduma a ka. Ciki kuma??? Gara ta fitar da rai da samun Hamza. Yana kallon yadda fuskarta ta canja da ta kula da cikin yayi murmushi. Irin wannan lokacin yake jiye mata da tayi gangancin cire mahaifa. Rai a dan bace yace Izzy ina son ganinki a falona. Zuhra ta kawar da kai ganin Izzatu tana rangwada jiki ta bi bayansa. Zama tayi suka suma hira da su Junior. **** Ko zama Hamza baiyi ba yace har kin manta matsayinki a yanzu? A wane dalili zaki yiwa yarana abinci? Iya abinda zaki ci nace ki dafa idan ba haka ba kuma idan Zuhra tayi ta zuba miki. Izzatu tace dama shine dalilin kiran? to gaskiya idan kayi min haka baka yi min adalci ba. Dan zaman da zanyi a gidan nan takaitacce ne. A iya abinda yayi saura ka bari na kara shakuwa da 'ya'yana. Yayi murmushin takaici...yanzu da can baki gama shakuwa dasu ba. Na riga na fada miki kiji da kanki kafin lokacin tafiyarki. Ganin ya kafe yasa ta soma kuka. Tasan baya kaunar kukanta tana yi tana rokonsa ya bari ita ta rinka yin abinci dasu har zuwa lokacin da zata tafi. Burinta ya amince ta yadda zata ce idan suna ci suka ganshi su matsa masa shima sai yaci. Tasan yadda yake son yaransa kila yaci din. Dagewa zata yi da dafa irin abincin da tasan yana burgeshi. Ai duk sonsa da abincin gargajiya dole wata rana yaso na zamani wanda tasan tafi Zuhra iyawa. Yadda take ta magiya da hawaye yasa Hamza amincewa amma da sharadin ta rinka basu su koshi baya son wannan abincin kamar an roka. Ta nuna masa farincikinta sosai harda rungumeshi. Yana kokarin tureta ta rike shi kam. A hankali ta soma bashi hakuri tana rokonsa ya yafe mata. Ita ko bazai mayarda ita ba yace ya yafe mata. Tana magana tana bin fuskarsa da kiss yana kawar da kansa. Izzy kada kisa na makara sallah naji na yafe please ki sakar min riga. Kanta a sunkuye ta sake shi tana murmushi. *** Lokacin da suka fito Zuhra tana kitchen. Izzatu baki har kunne ganin Hamza ya nufi hanyar kitchen din. Durkushe ya sameta zata dauko tukunya ya karasa ya dauko mata. Zan tafi Cutie ina jin bazan dawo da wuri ba saboda na tara ayyuka da yawa. Adawo lafiya kawai tace amma taki kallonsa. Murmushi yayi don yasan fushi take yi. Mata iyayen rigima ya fada a zuci. Hannu yasa ya dago fuskarta har ta fara kuka...kishin ne ya motsa ko kallona bazaki yi ba. Ko kina so na kasa yin aikin ne yau? Dago idon da tayi ta ga kayan bacin rai. Goshinsa da kumatu har da gefen bakinsa duk ga shatin janbakin Izzatu don tasan dai ba ita tayi ba. Sannan wuyan rigarsa da kafada ma duk akwai. Wani kukan ta fashe dashi Hamza ya rasa ya zaiyi da ita. Izzatu dake bakin kofa tayi kwafa tana dariya kasa kasa tace... Yarinya an fada miki zama da kishiya kamar cin tuwo ne. Sake lekawa tayi fa taji shiru idonta ya sauka akan Hamza da Zuhra kamar zasu shige cikin juna. Rungume suke da juna bakinsu wuri guda. Da sauri ta bar wurin zuciya na dukan uku uku. Wannan Zuhran ko mayya sai haka. Minti daya tana kuka cikin dan lokaci har ta manta. Ajiyar zuciya Zuhra tayi da ta hango Izzatu na barin wurin. Tana cikin kuka ta hango inuwarta shine ta rungume Hamza. Ko ba'a fada ba tasan abinda ya faru anyi ne da gayya shiyasa ta biyo bayansa taga yadda zasu kare. Shi kuwa Hamza bai san me ake yiwa ba yace ashe abinda kike so kenan kika tada min hankali. Ohhh yarinyar nan kinfi karfina...ya fada yana rike baki. Dariya kawai tayi masa tace adawo lafiya amma ka fara zuwa ka canja kayan nan kuma ka goge fuskarka. Yace kayan ne bakya so? Zuhra tace eh ka canja su wannan sunyi wani jirwaye daga wuyan. Bai fahimceta ba amma dai don a zauna lafiya ya koma sama ya cire kayan. Mamaki ne karara a fuskarsa da yaga janbakin Izzatu. Da sauri ya tafi gaban mudubi yaga na fuskar ma. Allah Sarki Zuhra dole tayi kuka. Shi har kunya yaji ma da ya sakko ko kitchen din bai koma ba ya fita. A haka suka yi wata daya har da kwanaki. Duk yadda Izzatu zata bi ta janyo hankalin Hamza tana yi. Waya da text idan ya fita ko yana daki shi da Zuhra kala kala. Abin yana batawa Zuhra rai amma dai tunda tasan da aurensu sannan kuma ba shari'a ake takewa ba dole take sawa zuciyarta hakuri. Wata alhamis da safe Hamza ya gama shirin fita wurin aiki ya duba turarensa ya kare. Shi kuma yafi son fesa akalla biyu a lokaci daya. Tunawa yayi da wani da ya siyo a tafiyar da yayi ya dauko ya fesa. Yana gama fesawa Zuhra ta shigo dakin ko magana bata yi masa ba ta ruga toilet tana ta amai. Bayanta yabi yaje ya na shafa mata baya har ta gama sannan ya bata ruwa ta dauraye bakinta. Suna fitowa dakin ya rungumota jikinsa ta sake shakar kamshin turaren ta zame jikinta ta kuma komawa yin wani aman. Sai da tayi haka sau hudu yana ta yi mata sannu. Muryarta can kasa tace zata koma dakinta tana jin warin turarensa ne bata so. Hamza yace wari kuma Cutie? Turare ai baya wari. Ko dai kinci wani abin ne yaki zama. Hancinta ta toshe ta ce fita daga dakin. Shi dai abin ya bashi mamaki ya bita daki. Yana shiga ta soma amai a inda take zaune. Ko tabata baiyi ba ya koma dakinsa ya cire kayan. Hatta vest sai da ya cire ya saka wasu ya fito. A zaune ya sameta a kasa tana ta kakari ga hawaye. Shi kam yana jinjina ranar da zata shiga labour room. Dagata yayi ya kaita toilet ya gyara mata jiki sannan ya dawo dakin ya gyara. Jikinta duk babu kwari ya kwantar da ita akan gado...bari na turo Tala ta zauna min dake. Bazan dade ba in Allah Ya yarda. Kinsan na fada miki minista zai turo ayi inspecting kamfaninmu kafinsu bamu aiki. Kuma ina sa ran yau za'a biya kudin aikin ginin da muka gama. Da zarar mun kammala zan dawo kinji. Kai kawai ta gyada masa sannan tayi masa adduar fatan alkhairi. Ya dan ja hancinta...wannan baby din zai gamu dani ne. Baki ga tsadar turaren nan ba designer ne amma shine ya saki amai. Maganarsa ta bata dariya yaji dadin ganin ta dan sake ya sauka ya turo mata Tala. Da ya dan sami lokaci sai ya kirata a waya. Daga baya yaji shiru yasan kila tayi bacci ne. Bata tashi ba sai wurin biyu da kwata cikinta a rarake. Tala ta kirawo ta roketa ta soya mata fanke sannan taje tayi sallah. Kafin a kawo fanken su Khalifa sun dawo daga makaranta. Sai da suka je dakinta suka gaisheta sannan suka wuce wurin Izzatu suka ci abinci. Hamza ne ya kafa dokar idan sun dawo su gaishe da kowa. Izzatu dai tace so yake lallai sai yaga ana irin zaman da Hajiya da Mama suke yi. Ita kuwa tasan shisshigi ne kawai zai sa kishiyoyi su mayarda juna 'yan uwa. Wannan munafurcin ba da ita ba. Tala ta gama soyar fanken ta kaiwa Zuhra. Junior ta ce ta turo mata shine masoyin fanke. Da murnarsa ya zo ta zuba masa a wani plate tace yaje suci tare da su Khalifa. Kasa ya sauka yana kiransu. Ya dauki daya zai sa a baki Izzatu ta fizge tare da dauke plate din tana masa fadan ita bata son kwadayi. Jiya ma ta soya masa fanken nan kuma yanzu ba ta fada musu abincinta kawai zasu rinka ci ba. Junior yana ji yana gani Izzatu ta juye fanken a shara tace idan ya koma dakin Zuhra sai ta zane shi sannan tayi tafiyarta daki. Har ya manta da batun fanke suna wasan goyo da Khalifa yace bari yaje yasha ruwa. Kwandon sharan kitchen din ya kula dashi ya duba fanken suna ciki. Ukun sama ya dauko ya karkade sannan ya boye a cikin rigarsa yayi gaba. Tala ta shigo kitchen din Izzatu da tsintsiya da abin kwasar shara a hannu. Wata sharar ta zuba ta dauki kwandon ta fita waje. Wurin maigadi taje tace ya zubar da sharar a drum din waje saboda aikin store din Izzatu tayi. Leda ce a hannunta baka ta rufe hannunta sannan ta dauko kwandon. Maigadi yace wannan rufe hannu kamar kin dauko guba. Tala tace ai gubar ce, motsi Hajiya taji a store tasa na fesa fiya fiya tana tunani ko bera ne. Sharata ta uku kenan bamu ga komai ba. Gara ayi waje da sharar kasan f[truncated by WhatsApp] AL'ADUN WASU #79 Batul Mamman(Mrs)# Tun uku da ashirin Tala ta gama shirya Khalifa zasu tafi islamiyya amma shiru basu ga Junior ba. Tayi kiran da neman har ta gaji. Ga Khalifa ya soma rigima shi ta fara raka shi idan taga Junior ta kawo shi daban saboda kada malaminsu yayi masa bulalar makara. Sama ne bata duba ba ta hau lokacin ana sallar la'asar ta shiga dakin Zuhra. Sallah ta tarar tana yi ta dan jira har ta idar sannan ta tambayeta ko Junior ya shigo. Zuhra tace ai tunda na bashi fanke bai dawo ba. Bari na duba falon Daddyn su ko can ya tafi. Hanyar kasan tabi ita kuma Tala ta shiga dakin Izzatu. Itama fitowarta kenan daga toilet tayi alwala. Da Tala ta fadi me ya kawota tace ki duba falon Daddy dinsu ni sallah zanyi. Har karkashin table din da Hamza ke aiki Zuhra ta duba babu alamun Junior. Abu kamar wasa suka fita har bayan gidan. Gashi maigadi yayi ta rantsuwa baiga fitowarsa ba. Izzatu ma ta fito daga dakinta don taji a inda aka ga Junior ta tarar har lokacin nemansa akeyi. Hankalinsu duk ya tashi sai kiransa suke yi shiru. A gigice ta dauki waya ta kira Hamza lokacin yana tare da wasu baki bai sami damar daukan wayar ba. Shi a tunaninsa ma irin wayar da take masa ne yanzu kullum ta tambayeshi aiki. Murmushi yayi da yaga ita ke kiran da niyar idan bakin sun tafi zai kirata. A can gidan kuma daga Izzatu har Zuhra kuka suke yi. Tala sai basu hakuri take yi. Khalifa ne ya dami Izzatu akan ta barshi ya cire uniform dinsa tunda ya makara da yawa. Idan aka kaishi yanzu malam zai zane shi. Ko kula shi bata yi ba suka fara shirin fita waje nemansa. Sake tambayarta yayi ta daka masa tsawa...jeka ni kada ka dame ni. Da 'yar murnarsa ya shiga dakinsu. Ba'a dade ba ya fito da gudu su Izzatu har sun kai bakin gate yace ga Junior a cikin drawar kayansu. Da sauri suka dawo ciki Izzatu ta gama kulewa tana tunanin irin dukan da zata yi masa saboda yadda ya tayar musu da hankali. Zuhra kanta har ciwo yake saboda kukan da tayi gashi dama jikinta babu kwari. Wayar chaja ta ga Izzatu ta ciro tasan sarai Junior zata daka tabi bayanta da sauri. Suna shiga dakin ta fara bata hakuri Izzatu ta janyo hannun Junior da yake kwance cikin kaya kamar me bacci tace...tashi wato har bacci kake yi duk ka tayar min da hankali. Maimakon ya bude ido sai taga ya biyota gabadaya ya fadi a kasa. Tsorata tayi sai ta dan dake tace Junior tashi mana. Shiru ko motsi baya yi. Zuhra ce ta fara kula da yawon da ya fara fitowa daga bakinsa sakamakon motsa shi da aka yi ta durkusa a gabansa ta fara shafa fuskarsa tace ....Junior bude idonka. Sai a lokacin Izzatu ta kula da yawun ta kwala ihu...Junior bude idonka don Allah. Yawun meye wannan? Daga ita har Zuhran a gigice suke ta girgiza shi ko zai bude ido amma abu ya faskara. Tashi tsaye Izzatu tayi ta daga shi tana kuka sai fanke ya fado daga hannunsa na dama. Ta bi shi da ido har ya fadi sannan ta tura hannu a bakinsa sai ga wani gutsiren fanken ta ciro. Ajiye Junior tayi ta cakumi wuyan Zuhra idanunta a birkice. Yanzu don kina da ciki Zuhra sai ki kashe min da? Har me nayi miki haka da zaki huce akan innocent yara na? Sai da na kwace fanken nan na zuba a shara shine kika sake bashi wani saboda mugun nufinki. Zuhra sai kokarin cire hannun Izzatu take yi ta kasa sai da Tala ta shiga tsakaninsu. Da kyar ta iya raba hannun Izzatu da wuyan rigar Zuhra. Kasa magana tayi saboda yanayin da Junior yake ciki ga muguwar shakar da aka yi mata tana ta tari ido na fidda hawaye. Suna kallo Izzatu ta kwance dankwalin kanta ta goya Junior sannan ta fizge mayafin jikin Tala tayi hanyar waje tana kuka. Kafin ta fita tace...idan yaron nan ya mutu Zuhra dayanmu zata bi bayansa. Zuhra ta kalli Tala hankalinta yayi matukar tashi tace Tala wane irin plate kika dauko na zuba musu a ciki? Nima naci kuma babu abinda ya sameni. Ya Allah Kasa Junior ya tashi...tana magana tana kuka ta hau sama ta dauko wayarta. Itama dai Hamza bai dauka ba sai kawai ta dauko jaka ta sakko. Tala da maigadi ta gani sunyi jugum a waje sai Khalifa a gefensu. Zuhra tasan mota Izzatu ta fita ta nema don babu wata motar a gidan tace da Tala ina Nana take? Tana dakin Hajiya tana bacci. Dama bukatarta ace bata ci fanken ba. Tana jin haka ta fita tayi sa'ar hango Izzatu na shiga taxi. Adaidaita sahu ta samu tace yabi bayan taxi din gabansu. Suna tafiya tana ta kokarin kiran Hamza wayar taki shiga saboda a wannan lokacin Izzatu ma kiransa take yi shiyasa duk basu samu ba. Taxi din na tsayawa a bakin gate din wani asibitin kudi inda Izzatu ta taba kwanciya su Zuhra ma suka tsaya. Da gudu suka shiga asibitin Zuhra ta manta da tata rashin lafiyar. Emergency suka nufa nan da nan nurses biyu suka karbi Junior aka kirawo likita suka shige dashi aka bar Izzatu da Zuhra suna ta kai kawo kowacce da irin abinda zuciyarta take saka mata. Tsananan tashin hankali yasa Izzatu bata kula Zuhra ba. Jira take taji a wane hali Junior yake. Suna nan tsaye Hamza ya kira wayar Izzatu. Da kuka ta dauka...Hamza matarka ta kashe min da. Yanayin muryarta ya tabbatar masa ba wasa take yi ba yace...ban fahimceki ba Izzy. Tun dazu naga kuna ta kirana. Me ya faru? Waye ba lafiya? Muryarta a dashe don kuka tace poison Zuhra tasa a fanke ta bawa Junior. Muna asibiti yanzu. Dama ya riga ya shiga mota a rude ya tayar ya fita bayan ta fada masa wane asibitin suka je. ***** Sai bayan kusan awa daya likitan ya fito tare da nurses din. Fuskarsa kadai zaka kalla kasan cewa akwai matsala. Fitowarsu tayi daidai da shigowar Hamza. Duk kan likitan suka yi suna tambayarsa halin da Junior yake ciki. Office dinsa ya kirasu sannan yace...a gaskiya mata da yawa kuna sakaci da maganin kwari. Sai ku rinka ajiye shi a inda yara zasu gani su dauka su ci. Hamza da gumi ya gama wanke shi yace doctor ka fada min abinda ya sami yaron nan. Likita yace to a iya bincikenmu Sunusi ya ci maganin kwari ne possibly piya piya. Wanda yaci babu yawa sosai sai dai an bari tayi masa illa sosai a hanjinsa. Yanzu munyi stabilizing condition dinsa amma zuwa jibi idan babu cigaba ina ganin sai munyi masa aiki an yanke wurin da ya baci a jikin hanjin. Kafafun Izzatu nema suke su kasa daukarta don fargaba. Zuhra tasa bakin mayafinta ta toshe baki tana kuka. Hamzan ma dai idanunsa sunyi jazur ya dubi likitan...ni dai idan har kasan yana bukatar aikin nan kawai kayi masa doctor ba sai am jira kwana biyu ba. Izzatu suka gani ta durkusa akan gwiwoyinta tana kuka...ka rufa min asiri likita ka ceci rayuwar Junior. Dr Ghali yace kuyi hakuri ba haka kawai zamuyi aiki ba sai bukatarsa ta tashi. Idan jikinsa ya karbi medication din da ake masa muna fata ba sai anyi masa aikin ba. Yana kare magana ya tashi suma suka bi bayansa suka fita. Ran Hamza a bace yace su biyo shi waje. Kallon da yake musu yasa Zuhra kara tsorata kada ya yarda ita ta bawa Junior guba....ina saurarenku ku fada min abinda ya faru. Izzatu ce ta soma magana ta sanar dashi yadda suka yi da Junior da fanke. Itama Zuhra ta fadi abinda ta sani. Kansa ya daure Izzatu ta dage Zuhra ke neman kashe mata da. Kuka Izzatu take yi sosai tana tararrabin abinda zai faru. Hamza ya rungumeta yana bata hakuri. A wannan yanayin Zuhra ta koma ciki zuciyarta babu dadi. Tabbas fanke ne a bakin Junior kuma ita ma shi taci. To a ina ya sami maganin kwari shine tambayar da take yiwa kanta. Bata dade da shiga dakin ba su Hamza suka shigo sai ga Tala goye da Nana ta riko hannun Khalifa. Hankalinta ne ya kasa kwanciya ta biyo bayansu. Dakin babu mai magana sai sautin kuka har aka kira magariba. Jikinsu duk babu kwari suka yi sallar. Junior bai farka ba sai da aka yi isha. Lokacin har su Alhaji sun zo. Umma da Baba ma duk suna asibitin. Su Raliya ma sunyi alkawarin bin jirgi da sassafe su taho Kano. A hankali Junior ya bude idanunsa. Yini daya duk ya fada sai haske da yayi fayau. Da kyar ya iya motsa bakinsa yace ruwa. Ibrahim yace bari na tambayi likitan ko za'a iya bashi kada muyi garaje. Bayan fitarsa Junior ya soma kukan cikinsa na ciwo. Hamza ya dora kan Junior a cinyarsa yace bari Uncle Ibrahim ya kirawo likita sai ya duba maka cikin. Izzatu ta kama hannunsa na hagu wanda babu allurar karin ruwa ta rike gam tana fitar da hawaye mai zafi. Bakin Junior har tsagewa yayi yace Mummy kice kin yafe min. Maganarsa tasa dakin yayi tsit kowa na tausayinsa. Izzatu tace yi shiru babyn Mummy ka dena magana kaga baka da lafiya. Zuhra ta taso ta tsaya a gefen gadon Izzatu ta galla mata harara. Junior yace ni dai kice kin yafe. Maama tace babu kyau mutum ya dauki abinda ba'a bashi ba. Kin karbi fanken da ta bani kin zuba a dustbin dinki shine naje na dauka naci gashi yanzu cikina yana ciwo. Kin yafe min Mummy? Wani salati Tala ta soma yi da karfi tana kuka. Hajiya a cikin kwandon sharar kitchen dinki na zuba sharar store da kika ce na saka piya piya dazu. Dakin ya kaure da salati Izzatu kuwa kasa ta zauna tana kuka mai sauti. Ji take kamar zuciyarta zata faso mata kirji. Zuhra ta durkusa a gabanta tana kokarin dagata tace...Zuhra na kashe Junior ko? Da na sani na barshi yaci fanken. Zuhra na kuka tace baki kashe shi ba tsautsayi ne. Izzatu ta ki tashi duk da haka...barni kawai gara na mutu da naga mutuwar dan cikina. Ni ba kara haihuwa zanyi ba idan duk suka mutu wa zan kalla inji dadi. Tausayinta ne ya kama su Hajiya suka taimaka mata ta tashi tsaye. Duk abinda ake yi Hamza bai kula su ba. Hankalinsa yana kan Junior da idanunsa suke ta kafewa. Ibrahim ne ya shigo da likita aka sa kowa ya fita. Sun dan dauki lokaci kafin likitan ya fito yace yayi masa allurai su barshi yayi bacci. Haka kowa ya tafi jiki a mace ya rage Hamza da matansa don su Hajiya sun tafi dasu Tala. Daga kai Hamza yayi zai musu maganar tafiya gida saboda dare yayi sosai ya gansu kowacce tana kuka. Nasiha da ban hakuri ya kirkiro duk da yadda yake ji a ransa yayi ta basu baki sannan yace bari ya kai Zuhra gida ya dawo. Da farko kin yadda tayi ta tafi sai da yayi da gaske. Haka suka tafi babu mai cewa komai. A falo ta zauna yaje ya daukowa Izzatu da Junior kaya yace mata zai koma can amma zai sa a dawo dasu Tala. A hankali tace to Allah Ya kiyaye hanya. yace amin. Daren ranar babu wanda ya iya yin bacci. Da asuba Zuhra ta tashi ta dafa ruwan zafi ta soya dankali. Karfe bakwai Hamza ya shigo jikinta har rawa yake tace ya jikin Junior yace da sauki. Wanka kawai yayi suka koma asibitin. A gaban gadon ta zauna tana kallon yadda lokaci guda Junior ya fita daga hayyacinsa. Kafin shabiyun rana ranar Juma'a dakin ya cika da mutane harda Raliya wadda Izzatu na ganinta ta fada jikinta tana kuka. Tana rarrashinta Junior ya farka. Zuhra ya gani a tsaye a gefensa yayi dan murmushi....Maama a aljanna akwai fanken da baya sa ciwon ciki ko? Zuhra ta share hawaye tace sosai ma kuwa. Ai duk abinda ka sani na dadi akwai a aljanna. Yace Allah Yasa mu shiga jirgin aljanna tunda Mummy tace ta hakura naci abinda ta hanani. Maganganun Junior banda karyar musu da zuciya babu abinda suke yi. Daga masu kuka da sauti sai masu share kwalla. Izzatu ta kasa kukan ma. Ji take ina ma ciwon ya dawo jikinta akan taga danta a wannan yanayin. Hamza yana can wurin likita suna tattaunawa akan aikin da za'ayiwa Junior a daren ranar saboda yadda yake jin jiki babu amfani a jira sai washegari. Tare suka taho da likitan zai sake duba shi suka shiga dakin. Izzatu ke kallon Junior tana tambayarsa ko akwai abinda yake so. Sai yayi wani irin tari sannan yace Maama ki goyani irin yadda kike yiwa Nana. Izzatu tace bari ni na goyaka. Junior yace shi dai Zuhra yake so ta goya shi. Tuni ta cire mayafinta tana kokarin daukarsa su Mama suna hanata saboda cikin jikinta. Izzatu dai gefe ta matsa saboda duk abinda Junior yake so tana so ya samu. Likita yace ya haka ina za ku kaishi? Idanun Izzatu fal hawaye tace don Allah ku bari ta goya shi ko na minti daya ne. Hamza yace a'a ba'a so ana motsa shi da yawa. Jin haka Izzatu, Zuhra da Junior suka soma kuka. Likitan yace to ta goya shi amma yanzu zata sauke shi. Junior har da murmushin karfin hali. Izzatu ta daga shi ta dora a bayan Zuhra dake durkushe. Iyayensu na kallo amma ansan bazasu hanu ba ko ance su bari. Zuhra tasa mayafi ta daure shi kadan yayi ajiyar zuciya. Hamza da kowa yana kallon yadda ya lumshe ido a bayan Zuhra. Likita yace to ya isa haka zamu je wurin scanning a sauko shi. Zuhra suka ga tayi kasa gabadaya da durkusa kan gwiwoyinta. Jikinta yayi matukar sanyi tace Innalillahi....ko karasawa bata iya yi ba ta saki wani irin kuka. Dogon numfashin da Junior yaja taji bai sauke ba ne ya tsorata ta. Hamza yayi hanzarin sauko da Junior likitan ya fara duba shi. A raunane ya dago yace sai dai muyi hakuri.... Izzatu bata ji karshen maganar ba ta fadi kasa a sume. Lokaci guda dakin ya rude da koke koke. Suka taimakawa Izzatu ta farfado. Suna nan tsaye aka cire masa allurar hannunsa aka rufe shi da bedsheet. Innalillahi wa inna ilaihi rajiun. Hamza ya dauko dansa a kafadarsa suka fito. Zuhra ke kuka sosai amma Izzatu hawayenta ya kafe. Zuciyarta ke zafi kamar ta fashe. Sun zo wucewa idonta ya hango mata a zazzaune a bakin kofar family planinning unit. Kamar wadda aka aika ta tafi wurinsu harda yi musu sallama. Tace...kunzo a dakatar muku da haihuwa ko? To wallahi kuyi a hankali dai. Ni da nafi kowa mahaifa na cire daga haihuwa uku. Kunga ko shekara ba'ayi ba ga gawar dana can ana fita da ita daga asibitin. Haihuwa ai kyautar Allah ce. Kamar wata zautacciya haka take maganar Mama tazo taja hannunta. Matan wurin suka yi musu gaisuwa. Suna tafiya uku a cikin na layin suka tashi suka ce sun fasa. Wadda ta fito a lokacin ma ta fara kiran nurse azo a cire mata loop din da aka saka mata yanzu danta daya kacal. Tuni wurin ya hargitse ranar dai babu wadda tayi abinda ya kawota duk matan suka watse. **** 'Yan uwa da abokan arziki duk sun zo gidan lokacin su Hamza sun tafi kai Sunusi Hamza Nasir gidansa na gaskiya. Kuka kam Zuhra tayi sosai. Lokaci guda sai Allah Ya kawo wa bawa jarabawa domin gwada imaninsa. Izzatu ce dai idonta har yanzu a soye. Suna zaune ta gama waya da yayarta Zeenatu ta tashi tayi hanyar kitchen. Ana tambayarta ko akwai abinda take so bata kula kowa ba taje ta fere dankali cikin dan lokaci tayi faten dankali ta zuba a plate ta sako cokali ta dawo falon. Inda Zuhra ke kwance jingine da kujera tana kuka taje ta zauna a gabanta. Su Hajiya da Umma sai kallonsu suke yi. Izzatu tace Zuhra.. A hankali ta bude ido tace naam. Ga abinci kici nasan kila rabonki da abinci tun jiya. Idan baki kula da kanki a wannan lokacin ba matsala na iya tasowa nan gaba. Sake fashewa da kuka Zuhra tayi. Izzatu tace dazu kika gama cewa idan muka yi hakuri muna da lada. To kukan na meye. Jarabawa ce Allah Yayi mana hakurinmu shine ladanmu. Kici abinci ko don abinda ke cikinki. Idan bazaki ci ba kuma wallahi zan dura miki ta karfi. Bar ganina haka nima karfi ne dani. Dan murmushi Zuhra tayi mai ciwo sannan tasa cokalin a ciki ta debi kadan tasa a bakinta. Tana ajiye cokalin Izzatu ta dauka itama taci dashi ta sake mikawa Zuhra. Sunyi haka wurin sau uku matan wurin na kallonsu da tausayawa sai kawai suka kankame juna suka saka kuka wanda yasa duk wadda ke wurin zubar da hawaye. ************* Sadaukarwa ga duk wadda ta taba rasa da ko 'ya Allah Ya jikansu Yasa masu ceto ne a garemu Ya bamu hakurin jure rashin. Amin Mai turo sakon gaisuwa sakonki ya iso gareni kuma nagode ina miki fatan alkhairi. AL'ADUN WASU#80 Batul Mamman(Mrs)# Yau kwanan Junior uku da rasuwa amma kullum jinta suke kamar lokacin aka yita saboda yaro ne mai shiga rai. Zuhra bazata taba mantawa ba shi ya fara cewa zai zama abokinta a gidan. Ga Nana idan tayi wasa ta gaji sai ta fara neman shi ko Khalifa kamar yadda ta saba. Idan kaga Izzatu dole ka tausaya mata a wannan lokacin. Ta rame sosai duk da cewar da wuya ka ganta tana kuka. Mafiya yawan lokaci ita ke rarrashin Zuhra saboda ita akwai raguwar zuciya. Abin kuka baya mata kankanta. Yadda ta koma ya bawa duk wanda ya santa mamaki tare da zama abin burgewa saboda ta dauki qaddarar da tazo mata hannu bibbiyu. Suna zaune a falo Raliya tana kallon Zuhra da Izzatu suna karbar gaisuwa. Wata mata cikin 'yan gaisuwar tace wace mahaifiyar yaron ne a cikinku? Izzatu ta nuna Zuhra. Matar ta rinka bawa Zuhra hakuri akan ta rungumi qaddara ta sami lada. Batan san kukan Zuhra a wannan lokacin ba na rasuwa bane. Tana jinjina yadda Izzatu ta nunata a matsayin maman Junior ne. Wannan abu akan idon Hajiya akayi da Raliya. Sunji tausayinsu sosai. Raliya tace a ranta lallai kowane rashi daga Allah baya rasa alkhairi a tattare dashi sai dai ba kowa yake ganin wannan alkhairin ba bare ya amfana dashi. Misali mutane da yawa suna wa'azantuwa da mutuwar wani makusanci su daina akaita barna da sukeyi a da. Wasu kuma imaninsu ne yake karuwa idan suka yi rashi. Wasu kuma abinda idonsu ya rufe da basa gani sai su fara fuskantarshi a wannan lokacin. Ga mai hankali mutuwa ayah ce mai ishara ga barin mummuna da komawa ga kyakkyawa. Rasuwar Junior tayiwa kowa ciwo amma Raliya tasan shine ta zama sanadin shiriya ga 'yarta. Saboda irin tarbiyar da suka bawa 'ya'yansu Izzatu ta tashi da irin halin nan na bature daga ni sai iyalina makusanta wato miji da 'ya'ya. Duk wanda yazo a bayansu ana iya rayuwa batare dashi ba. Hakan yasa ta kasa fahimtar mijinta a lokacin da yaso ta gyara halayenta don su zauna lafiya da 'yan uwansa. Sannan kuma 'yan uwan nasa suma suka ki ta saboda ta kasa barin al'adun da ba nata ba ta shigo musu da bakin al'amura. Babbar matsalarta kuma shine bata daukar abubuwan da take da mahimmanci shiyasa ko sun nuna fushinsu sai ta ga kamar hakan ba komai bane. Ajiyar zuciya Raliya tayi tana addu'ar Allah Yasa ta dore a haka Ya yafe musu kuskurensu wurin bawa 'ya'yansu tarbiya. Dama haka Allah Yake hukuncinSa. Abinda ka raina baka dauke shi laifi ba sai yayi sanadiyar bata tsakaninka da mahaliccinka. Abinda kuma ka raina a matsayin aikin lada sai ya kaika ga rahmar Allah. Allah Yasa mu dace. Amin **** Da yake Junior yaro ne gidan baya cika sosai. Hamza yana waje inda yake karbar gaisuwa daga makota da abokan aikinsa. Cikin masu zuwan ne kawai yaga wani mutum ya shigo rabin fuskarsa duk a rufe yasa bakar jacket da bakin wando gashi kansa da hula. A gaban Hamza ya durkusa ya cire bakin glass din idonsa yace Sir I am very sorry about your loss. May his soul rest in peace. Ba Hamza ba sauran 'yan office dinsu da suke wurin tuni suka gano muryar Mr Oscar. Wurin mutum biyar suka yi kansa harda masu zagi. Hamza ya tashi da sauri ya hanasu. Inuwa sakatare ya harzuka yace haba yallabai Mr Oscar ne fa. Babu wanda zai ce ya manta halin da ya jefa mu sanadiyar satar da yayi maka. Shine har zai shigo gidan nan hankali kwance. Hamza yayi dan murmushi yana rike da hannun Oscar....idan har rashin da mukayi zai sa yazo gidan nan duk da cewa yasan nemansa nake yi to lallai dole ne nayi hakuri. Har kun manta abinda ya tara mu a nan? Mutuwa ce fa mai daukar babba da yaro talaka da mai kudi.... Ya mayar da dubansa ga Oscar....nagode sosai da nuna damuwarka gareni a wannan lokacin. Mr Oscar ya soma hawaye yace...Oga nasan nayi kuskure ina neman afuwarka. Ka yafe min domin nayi nadama. Tsoron abinda zai faru yasa na kasa zuwa na sameka. Inuwa yace abinda zai faru bai wuce na kira 'yan sanda suyi gaba da kai ba. Shege arnen banza. Bata rai Hamza yayi sosai yace haba Inuwa. Kada fushi yasa ka sakawa mai laifi da tsiya. Ko baka san maganganunka zasuyi tasiri a zuciyarsa ba ya sake tsanar Hausawa da musulmai....kaga Mr Oscar nasan naji ciwon abinda kayi min amma yau godiya nake da kazo min taaziya saboda haka kaje kawai. Cheque Mr Oscar ya dauko daga aljihunsa... Oga kayi hakuri nayi kokarin mayar da kudin kamar yadda suke amma na kasa. Na yi amfani da miliyan daya da duba dari takwas kuma bani da hanyar maido maka da kudin nan. Ka bani lokaci ko aiki idan na samu zan rinka biyanka a hankali. Godiya Hamza yayi ga Allah sannan yace babu komai kaje na yafe maka. Ba kowa bane zai iya abinda kayi. 'Yan office dinsu basu ji dadin yafe masan da Hamza yayi ba sai dai kuma Mr Oscar ya basu mamaki. Shima mamakin yayi yadda Hamza yayi saurin yafe masa yace..Oga haka duk musulmi suke da saurin yafe laifi? Hamza yace a'a amma haka musulunci yace mu rinka yafiya ga wadanda suka cutar damu. Mr Oscar yace indai kuwa haka ne to na yarda wannan addinin naku akwai adalci. Zan iya zama musulmi dan uwanku yanzu? Wani cikin mutanen wurin ya tuna lokacin da Umar Farouq Mukhtar ya musulunta a masallacin unguwarsu. Yaji ance yaron har ya auri wata yarinya Ruqayya wadda tayi sanadiyar musuluntarsa. Kabbara suka yi abin alkhairi ya samu aka musuluntar da Mr Oscar. **** Daga ranar aka gama zaman makokin duk 'yan uwa suka koma gidajensu. Wata Juma'ar na zagayowa Hajiya ta dawo gidan. Ita da bata zuwa gidan 'ya'yanta sai da dalili mai karfi shiyasa suka yi mamakin ganinta. Ibrahim ne ya kawota ya zauna a falo saboda Hamza baya nan. Izzatu da Zuhra basa kasa Tala tace mata suna sama Zuhra ce bata jindadi. Waya Izzatu ta saka a speaker tana magana ga kofin tea a hannunta Zuhra ta kwabe fuska kamar zatayi kuka. Izzatu tace...Baby har yanzu taki shan tea din fa. Ga idonta ya cika da hawaye. Ni tsorona kada ta haifa min baby mai kuka. Daga office dinsa Hamza yace kyaleta idan na dawo dura zamuyi mata irin na jiya. Zuhra tace don Allah kuyi hakuri. Zan sha da kaina. Hajiya tana tsaye a kofar dakin Zuhra tana jinsu. Zuciyarta cike take da farinciki mara misaltuwa. Sallamarta ce tasa Izzatu tayi saurin kashe wayar duk suka gaisheta suna yi mata sannu da zuwa. Hajiya da fara'arta ta amsa tace su zauna wurinsu tazo. Izzatu tace bari na kawo miki abinci Hajiya. A'a dawo ki zauna nagode. Zuhra Hajiya ta kalla tace ki shanye tea din sannan muyi magana ko. A yadda Hajiya ta tsareta da ido dole ta karbi kofin ta fara sha. Izzatu tayi dariya bari na dauko miki bread kada ruwan tea ya kulle miki ciki. Kamar tayi kuka haka ta rinka tura bread tana kurbar tea kamar magani. Sai da ta shanye tea din sannan Hajiya ta bukaci su bata hankulansu tana son yi musu magana ne. A nutse ta fara magana duk su biyun sun sunkuyar da kai kasa suna sauraronta.... Nasan zakuyi mamakin zuwana gidan nan a wannan lokacin duba da cewa ba abu bane da na saba yi. Yanzun ma dole ce tasa ni zuwa domin akwai shawara da nake son baku. Tun kafin rasuwar Sunusi nake kula daku a asibiti har zuwa kwanaki ukun da mukayi muna karbar ta'aziyya a gidannan. Tabbas canjin da nagani a wurinku ya sanyani matukar farinciki. Nagode Allah Yayi muku albarka. Sai dai akwai kalubale a gabanku. A lokacin da kishiyoyi basa zaman lafiya idanuwa basu fiye zama a kansu ba dama shaidanun mutane burinsu su ga ana tashin hankali. Amma daga yanzu da mutane suka kula yanayin zamanku ya canja to 'yan gulma da hada fada daga danginku ko na mijinku zasu kawo muku farmaki. Da sunan soyayya wata zata wargaza muku farincikin da kuke kokarin ginawa. Abubuwa da yawa sun faru a iya zamanku a gidan nan tun daga lokacin aurenki Izzatu har zuwa yanzu da kuka zama ku biyu. A da can ki sani mu ba kinki mukeyi ba sai dai halayen da kika zo dasu ne bama so. Munyi kokarin ganin kun canja tun a baya sai ya zamana shima maigidan naku ya biyewa irin wadannan bakin al'adun. To babbar matsalar da kika fuskanta shine duk inda ake aure to idanu sunfi yawa akan mata. Komai munin halin miji indai matarsa tana da kyawun hali sai kiga ba kasafai ake damuwa da halinsa saboda mace ita ce gida kuma da ita aka fi hulda. Haka komai kirkin namiji idan matarsa bata kyan hali to nan ma gabadaya gidan za'ace basu da hali saboda ita mace ita take nuna irin gidanta a waje. Alhamdulillah tunda har Allah Yasa idanuna sun gane min irin zaman da kuke yi yanzu ina so don Allah ku zauna lafiya. Ku yafewa juna abubuwan da suka gabata ku rike juna da zuciya daya. Idan ance ki zauna da kishiya da zuciya daya wata zata ji tsoron cutarwa daga kishiyar to ki sani duk abinda tayi miki na cuta kuma tayi nasara dama Allah Ya kaddara hakan sai ya faru. Kada tsoron muguntar kishiya yasa kema ki zama muguwa. Ni da Mama ba karamin toshe kunne da hakuri da juna yasa muke irin wannan zaman da kuke gani yanzu ba. Dole sai anyi hakuri sosai. Idan mace taki kwantar da hankalinta kina ji kina gani watarana miji zai sakeki kuma ya barwa kishiya 'ya'yanki ko ta rike ko ta cutar dasu idan baki da karfi dole kiyi hakuri daga inda kike kina jin labari mara dadi game da 'ya'yanki. Ko kuma rai yayi halinsa kishiyar nan dai da bakya so ki bar mata 'ya'ya da mijin baki daya. Kunga kenan har gara ki fahimceta ku zauna lafiya ko don gaba. Allah Ya kara rufa mana asiri Ya baku zaman lafiya. Shima zanyi masa nasa fadan na yin adalci tsakaninku. Tunda Hajiya ta fara magana Izzatu da Zuhra ke kuka. Izzatu tace Hajiya mungode kuma don Allah ku yafe min. Kema Zuhra ki yafe min duk abinda nayi miki. Tun daga april fool har bayan auren. Zuhra ta share hawaye na yafe miki nima ki yafe min. Banyi wani kokari na daidaita ku ba saboda ina jin haushin abinda kika yi min. Hajiya dai tana kallonsu tana jindadi. Addu'a ta sake yi musu sannan ta tafi duk yadda suka so taci abinci ta ki. ***** Hamza na tuki yana murmushi shi kadai. Yadda gidansa ya koma yasa shi jindadi. Tun kafin rasuwar Junior dama babu wadda ke kwana a dakinsa. Yau zai bukaci su daidaita yadda zasuyi. A son ransa dai Izzatu yake son ta fara karbar girki saboda wasu dalilai nasa. Tun ana zaman makokin ya fada mata ya mayar da ita. Siyayya ya tsaya yayi musu ta kayan kwadayi sannan ya wuce gida. Da sallama ya shigo falon Nana da Khalifa suna masa sannu da zuwa. Zuciyarsa ce tayi masa zafi da ya tuna da Junior. Allah sarki rayuwa. Zuhra da Izzatu suna hira suma suka yi masa barka da zuwa. Bakinsa ya kasa rufuwa don jindadi. Sai da yaci abinci ya basu tsarabar da ya kawo musu. Wurin goma da rabi na dare ya bukaci ganinsu a dakinsa. Kowacce tayi wanka tayi fes da ita. Kusan tare suka shigo yana zaune a tsakiyar doguwar kujera yayi murmushi to sai ku sakani kawai a tsakiya irib yadda matan Alhaji suke yi masa. Zuhra ta rike baki ...sai na fadawa su Hajiya. Yace ke kuma daga magana sai ki fassara mutum. Izzy ai ba haka nake nufi ba ko? Ya fada yana kallonta. Dariya tayi sannan tace zaka ga fassara mutum idan kaji mun maimaita abinda ka fada. Zama suka yi suka saka shi a tsakiya yace mata kun iya sharri. Dama wani albishir nazo muku dashi amma tunda abin naku yazo da haka na fasa. Magiya suka shiga yi masa har ya fada musu cewa ya sami kwangilar zane daga gwamnatin tarayya kuma an biya shi kudin aikinsu. Sannan Mr Oscar ma ya dawo masa da wani bangare na kudinsa. Sunji dadi sosai suka yi masa addua. Daga nan suka dan taba hira sannan Zuhra ta tashi ta tafi daki bayan sun amince Izzatu ce zata fara karbar girki. Tun daga wannan rana zaman lafiya ya kara samun wurin zama a gidan Hamza. Cikin kudin da ya samu ya nemi shawararsu akan ya sayi mota daya ya daukar musu dreba ko ya sayawa kowa daban tunda Izzatu ta amince ya sayar da tata. Guda daya suka nemi ya saya musu nan gaba idan ya sami hali kowa sai ya saya mata. **** Wata rana da daddare Zuhra na kwance Hamza na yi mata tausa saboda kafafunta duk sun kumbura. Tun bayan rasuwar ta zama yau da lafiya gobe babu. Hamza yana kallonta tana lumshe ido yace Cutie kin tuna sarkar da kika bani na sayar lokacin da Izzy bata da lafiya? A hankali ta gyada masa kai don har bacci ya fara daukarta. Wata karamar leda ya ciro daga aljihunsa ya saka mata a tafin hannu. Sai a lokacin ta bude ido tace menene wannan Ya Hamza? Murmushi kawai yayi ta tashi zaune ta bude. Sarka ce da dankunne da zobe na gwal mai matukar kyau. Dadi ya kamata ta rungume shi tana masa godiya. Wani kallo tayi masa tace ina fata ba biyana kayi ba? Ko kadan Cutie. Abinda kika yi min sakayyarki na ga Allah. Wannan kyauta ce kawai. Na bawa 'yar uwarki ita ma. Zuhra tace to Allah Ya saka da alkhairi Ya kara budi. **** Yau ta kama asabar sun tashi da sanitation din gida. Izzatu da Tala ke aikin harda Khalifa. Zuhra kuwa an hadata da zama da Nana, Izzatu tace kada ta tashi sun yafe mata aikin. Tana zaune taji mararta ta fara ciwo kadan kadan. Da yake tasan watan cikin bakwai sai bata damu ba. Yinin ranar haka tayi ta fama da dan ciwo amma bata fada ba. Sai dare har ta fara baccin ciwo ya tasheta. Tun tana daurewa har ta soma kuka. Da kyar ta iya zuwa dakin Hamza ta kwankwasa kofa. Cikin bacci Hamza yaji kamar ana kiransa. Juyawa yayi yaga Izzatu tana bacci. Sake kiran akayi da karfi wannan karon ya tabbatar Zuhra ce. Shi da Izzatu suka taso yana bude kofar ya sameta a tsaye ta kasa daga kafa. Daga shi har Izzatun sun rude ya daga Zuhra ya sauka kasa da ita Izzatu na bin bayansu. Koda suka isa asibitin likita ya tabbatar musu haihuwa ce Allah Yasa suna da dakin da aka ajiye yara bakwaini da dole sai dai su tafi Aminu Kano ko asibitin Murtala. Ga fargaba ga ciwo Zuhra ta rinka kuka. Dama Hamza yana ta tsoron ranar haihuwarta saboda ta iya kuka da raki. Shi da Izzatu suna waje kowa hankali a tashe. Zuhra na kuka a ciki Izzatu tana yi masa nata a waje. Ya rasa inda zaisa kansa. Sai da ya tafi sallar asuba sannan Zuhra ta haihu. Nurse ta fito ta kira Izzatu bayan sun gyarawa Zuhra jiki. Wani sabon kukan ta saka da taga Izzatu. Nurse din ta soma tsokanarta wai sun gama ganin rakinta. Izzatu ta rike mata hannu sannu Maama. Kukan kuma na meye ai an gama wannan saura na gaba kuma. Fuska a kwabe Zuhra tace wane irin na gaba. Don Allah dena fada. Duk kankantar yaron nan sai da yaja min dinki. Kunji salati na da anayi ko? Nurse tace salati ko kuka. Da kyar fa muka yi duk taki tsayawa. Ina ganin idan likita ta dawo daga inda suke duba baby din sabo zata bukaci yi miki. Shigowar Hamza yasa duk hankalinsu yayi bakin kofar. Bakinsa kamar gonar auduga duk da basu ga baby din ba. Izzatu ta dan wayance tabi bayan nurse don ta basu wuri. Tana fita kuwa Hamza ya karasa wurin gadon ya rungume Zuhra....'yar shagwaba yau ta shiga labour room. Ta turo baki...tsokanata ma kake yi ko? Baza'a sake ba daga wannan. Rufa min asiri Cutie ai an bude kofar kenan. Daga wannan sai munyi tara. Uhmm kai da wa? Ni dai na gama. Kaje ka duba mana baby din ko ganinsa banyi ba. Allah Yasa dai yayi kama dani don nasha wahala. Hamza yayi dariya kada ma kisa rai. Mu jininmu akwai karfi duk jikokin Alhaji dashi suke kama yadda muke kama dashi. Bari naje idan zasu barni na ganshi zanyi masa huduba da sunan babanmu Muhammad Bashir. Dadi ya mamaye zuciyar Zuhra tace Ya Hamza nagode ko baiyi kama dani ba babu komai. I love you. Kiss yayi mata a goshi yace I love you more. **** Tun daga ranar asibitin kullum a cike da 'yan uwa da abokan arziki. Gwaggo Hasiya yayar Umma ita ke kwana da Zuhra. Gabadaya Izzatu bata hutawa daga gida zuwa asibiti. Yadda take kulawa da Zuhra yana bawa kowa sha'awa. Raliya ma tazo barka da kanwar Izzatu. Duk da ba'a sallame su ba amma Hamza ya gama tanadin radin suna. Raguna biyu ya siyo manya aka daure a cikin gidan. Ana gobe suna da daddare Zuhra na cin tuwo kowa ya tafi suna hira da Gwaggo Hasiya tace kina nan da cin abincin nan naki ko Fati. Gashi kin haihu yanzu rumbun Hamza zai girgiza. Zuhra tace ni da labari yazo min cewa a wurinki na gada. Kaniyarki, Gwaggo Hasiya ta fada tana dariya ita ma. Dama shawara nake son baki ina fata kuma zaki dauka. Nasan kin riga kin fada mana sunan yaron nan har kina ce masa Babana to amma ni ina ganin me zai hana ki kara karfin zumunci tsakaninki da abokiyar zamanki? Wallahi na kula da gaske take kaunarki. Jiya da za'a gyara miki dinki ita da Atine har da hawaye saboda kin cikawa mutane kunne da ihu. Zuhra ta sunkuyar da kai kasa. Gara ta koyi dauriya dai kowa yace ta fiye raki. Gwaggo Hasiya ta cigaba shagwaba ce su Atine sun koya miki. Batun sunan yaron don Allah ki daure asa sunan marigayi yaron wajenku. Nasan Izzatu zata ji dadi kuma zumuncinku zai kara karfi. Idan da rabo sai ki haifi mai sunan Babanyara. Shawara ce fa kawai na baki bance dole ba. Kada ki dauke shi a matsayin sunan baban kishiya. Ki dauka yaro yaci sunan wansa ne. Zuhra tace Gwaggo nagode sosai. Naso saka masa sunan Baba amma shawararki tasa nafi son yaci sunan dan uwansa. Tana gama cin tuwon ta turawa Hamza text sai taji tsoron kila yayi bacci kada yazo bai gani ba sai da safe. Kira tayi kuma tayi sa'a ya dauka. Da yaji bukatarka ba karamin murna yayi ba yayi ta sa mata albarka. Bai fadawa Izzatu ba ya bari sai da safe taji. Yasan zatayi murna. Bayan asuba kuwa Izzatu ta sauko hada kayan abincin asibiti Tala ta shigo kitchen gaisheta harda dan hawaye tace Hajiya munji sunan jariri Allah Ya raya mana Muhammad Sunusi. Shikenan sai mu rinka kiransa Junior. Izzatu taji zancen wani iri tace Amin amma sunansa Bashir. Tala tace a'a yanzu babansu Khalifa ya fada min sunan kafin ki sauko. Da sauri sauri Izzatu ta hau sama. Hamza na jin motsinta ya tsaya yana dariya. Karasawa tayi ta rungumeshi tana kuka. Baby da gaske ne abinda Tala tace? Sai da ya share mata hawaye sannan yace jiya kina wanka Zuhra ta kirani tace ga sunan da take so. Izzatu ta sake kankame shi tana kuka tana dariya. Kafin taje asibitin sai da ta kira Raliya ta fada mata. Ita ma taji dadi sosai. Tana shiga dakin kuwa rungume Zuhra tayi tana ta yi mata godiya. Daga murna suka koma kukan rashin wancan Junior din. Gidansu Hamza ma duk sun yabawa Zuhra da wannan karamci da tayiwa Izzatu. Da aka sallamesu bayan sati biyu gidansu ta tafi wanka duk da ba haka Hamza da Izzatu suka so ba. Har kara'in suna sai da suka yi wanda mutane da dama suka halarta. Haka rayuwar gidan Hamza ta cigaba da kasancewa cikin zaman lafiya da kokarin koyi da addini da al'adunmu wadanda basu sabawa addini ba. Zuhra da Izzatu kuwa kullum suna kokarin kyautatawa mijinsu da junansu. Yanzu haka ma islamiya ya sama musu a nan unguwar tasu suke zuwa tare. Junior kuwa idan ka ganshi a wurin Zuhra to yunwa ce ta kawo shi. Komai Izzatu ke yi masa. Watansa takwas Zuhra ta fara wani laulayin. Hamza ba karamin dadi yaji ba. Saboda yadda take wahala aka yaye Junior. Cikin ikon Allah bayan wata tara ta haifi 'yan matanta guda biyu. Murna wurinsu ba'a magana su Nana an zama yaya. Yaran suka ci sunn Umma wato Fatima da Mama wato Ummukulthum ake kiransu Ummi da Ummu. Suma shekararsu biyu aka haifi Muhammad Bashir. Gidan Hamza ya soma cika da yara. Sai da muyi musu fatan zaman lafiya mai dorewa. ALHAMDULILLAH! Godiya ta musamman taku ce 'yan gidan Batul Mamman Novels. Ni da ku 'yan uwan taka yanzu ma muka fara. Allah Ya kara zumunci Ya albarkaci rayuwarmu. Marubuta Hakika naji dadin kwarin gwiwa da kuka rinka bani a wannan littafi Al'adun Wasu. Nagode sosai.. Ummu Abdoul Aisha Yau Kurah Ummu Nass Feenat Ja'far Maryama Mmn Afreen Baby Maryam Queen Mimi Ummi Aisha Mamu Ummu Hannan Groups Bazan manta daku ba yan... Feenat Ja'afar Novels Taskira Rufaida Omar Fan's duka biyun Allah Ya saka muku da alkhairi Ya kara mana zumunci. Sai kuma 'yan uwana na Fikrah Writers Association ina kara mika godiya tare da fatan alkhairi. Masu waya da text kuma bazan manta[truncated by WhatsApp]