Advertisements
Chapter 45 Reading Amatullmaeek Book 1 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Amatullmaeek Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Complete Novels

Chapter   45 / 53

132K to 135K   out of 156.3K words

tabbatarda ASH ya dawo kenan.

Nauyi idanuwanta da zuciyarta suke sake shiga sbd fara fahimtar abinda ya faru,
Anty Farha dole riqe hannuwanta tayi suka nufi ciki suna Saka Kai a palon qasa din akan gawar da aka gama shiryawa ta Madame abeeda idanuwan Amatu suka fara sauka
Cak ta tsaya anty Farha na sake riqeta da kyau sbd jirin Daya dibeta idanuwanta na kan gawar.
#MAMUH#

*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
[12/5, 6:34 PM] safiya yushau: YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#

AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar

71
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096

************
Cikin qarfin hali anty Farha ta sake riqeta da kyau tana Bata kariya daga jirin dayakeson dibanta tana Jin itama firgici Yana kamata sbd ganin gawa kwance gabansu.

Kama Amatu tayi suka qaraso cikin palon dakyau Wanda yasa wainda keda Dan sauran karfin hali juyowa suka kallesu Amma su maamah Kam da Husnah Babu me qarfi bare hankalin juyowa su kallesu.

Hawaye ne suka ciko idanuwan Amatun suna gangarowa rawar jikinta na bayyanuwa sosai sbd a take tasan Mum Abeeda ce ta rasu itace a kwance a shirye.

"Innalillahi wainna ilaihirrajiun" take furtawa daga bakinta Amma Sam kalman taqi fita sbd kasa tsayuwa da qafafunta datai sbd shock da tashin hankali Dan haka ta silale a gurin jikin anty Farha wadda itama ta bita qasa tana rungumota cikin tsoron kada Wani abun ya sameta sbd firgitan rasuwar.

Mum Aisha da tinda suka shigo ta zubawa Amatun idanuwanta tana kallan cikinta Da suna shigowa akansa Idonta ya fara sauka tini ta taso Dan tabbatarwa ta kamawa farha Amatun tana cewa

"Ciki ne ita??
Idan ciki ne Kam to kuyi sama dakinta ku zauna kada ya bare sbd tashin hankalin ganin gawa.

Anty Farha Bata iya amsa mum Aisha dinba kokarin bawa Amatu data rikice gaba Daya hakuri da kalaman da zasu dawo da ita daidai takeyi Amma gaba Daya Amatun ta rude sbd Daman kafin isowarsu a rude da tashin hankalin take sai gashi ta tadda abinda ya qarasa rikitata ga kukan Husnah Dana maamah dayake tashi cikin palon cikin Wani sauti me yanka zuciya Dan dukkaninsu ganin sukeyi sune silan rasuwar nata,
Maamah ganin takeyi da Bata biye tashin hankalinsu ba ta tsaya ta tare Abeeda da Kila Bata fado ba,
Husnah kuwa Kai tsaye tasan itace sanadin halakan mahaifiyartata hakama a lokacinda ya kamata ace ta tsaya ta gana sosai da mum dinta kafin lokacin rasuwar tata Amma gashi ta rasu batareda sun sake ganin juna ba.

Amatu Sam ta gagara taruwa gabaki daya ma Neman sumewa takeyi Dan haka dole mum Aisha din anty Farha ta Saka ta kama mata ita sukai sama zuwa bedroom dinta sauran mutane na binsu da kallo cikin tausayawa Amatun sbd ganin juna biyu a tareda ita duk da basu ganeta ba Basu San itace 'yar maamah din da ASH yake aure ba.

Suna wucewa sama aka shigo daukan gawar Abeedan Dan ficewa da ita sbd anriga anmata sitira,

ASH dinne da kansa Se Haydar da Abdulhameed Wanda isowarsu kenan ko zama beyiba suka fito da gawar.

Husnah Wani irin kuka takeyi da ko fitowa ya Dena yi sbd wahala da tsananin Wanda taita yi tinda suka iso,
Maamah ma kusan siqewa take Neman yi kafin kace me zuciyarta ta riqe sedai aka kwasheta daga gurin da sauri itama Akai dakinta da ita su khaltume suna mata firfita kafin agama jana'izan a kira mata likita ko kaita asibiti sbd abin yafara Basu tsoro ma.

Husnah ma birkicewan tayi a gurin take ta sake somewa Akai kanta itama ana Neman cetan ranta.

Haydar kuwa kuka ne yakeyi sosai da da sosai sbd bayan tashin mum dinsu baa sanar masa komaiba hakama ko dayaje ganinta Greece yaga alaman sauki a tattare da ita harya tafi yabarsu Husnah da maamah baiga alaman ciwonta zai tashi ba sai kawai rasuwarta kwatsam.

Shi kansa Abdul yayi kukan rasuwar sbd tausayin Haydar da Husnah wadda kusan itace ma tafi basa tausayi tinda yasan depression datake fama dashi.

Anyi jana'izan Madame Abeeda Talba ankaita an rufeta aka dawo Karban gaisuwa Wanda akeyi a mansion din din cikin babbar palon ASH din Dayake qasa Wanda yake ganin baqi.

Acan cikin gidan ma a palon qasa ake karban gaisuwan,
Maamah da Husnah dole aka kira musu likita ya dubasu sbd suna dakunansu a kwance jikin ba sauki.


Amatu kuwa tinda suka kwantar da ita a gadonta hankalin anty Farha ke sake tashi sbd yanda gaba Daya jikinta ya rikice ga Mum Aisha ma ta tsaya tana nuna damuwanta sbd a yanzu data tabbatarda tasu ta qare a gurin ASH so zata nunawa Amatun da cikinta ko zata samu sassauci a gurinsa.

Kokarin saukar mata da zazzabinta anty Farha ta ringa yi kafin a gama jana'izan ta kira likita itama sbd yanzu ko ta kira Likita ana kokarin jana'izan ne bazata samu shigowa ba.

Mum Aisha ma haka ta ringa kaida kawo tsakanin palon qasa gurin karban gaisuwa da bedroom din Amatun har anty Farha ta gaji ta rufe dakin Dan mum Aisha din ta isheta bayan damuwan datake ciki na Amatun.

Dr beeba ta kirawa Amatun Se data Dan jima kafin tazo sbd tana asibiti ko da aka kirata Dan haka Koda ta iso Amatun ta gama galabaita harda ciwon mara har tayi baccin wahala Dan har kusan yamma ma tayi.

Dayake ba mutane sosai Tinda gaisuwan duk Wanda yayi ba zama yakeyiba wucewa yakeyi sbd kowa bayason zaman gaisuwar daga masu karban har masu zuwan tinda Wani lokacin zaman baida Wani amfani gwara kayi ka wuce.

Mum Aisha ce tayiwa Dr beeba jagora zuwa sama har dakin Amatu sukai knocking anty Farha ta taso ta Bude tana ganin Dr beeba ta saki ajiyan zuciya sbd ta fara saddakarwa da kawai ta dauki Amatun su tafi asibiti,
Bata kira Mr Jameel ba ta sanar amsa sbd kada a sanar da ASH a daga hankalinsa ayau dayake buqatan a barsa yaji da abu Daya tukuna.

Qarasowa ciki sukai Dr beeba na musu gaisuwan rasuwar tana nufar Amatu Dake kwance tana bacci a wahalce.

Zaunawa tayi tareda kallan Amatun tana kamo hannunta Daya Dayan Kuma tana Dan yaye rufarta ta Kalli Dan qaramin cikin tana dawo da kallanta kan Farha tace

"Meyasa Baki fadamun tana da ciki ba da bazan Dade haka ba ai zanyi kokarin zuwa kan time gaskia."

Kasa cewa komai anty Farha tayi sai numfashi me dumi data sake jiki duk a mace sbd yunwa da damuwa dakuma ciwon Amatun.

Fara dubata Dr beeba tayi tana Ciro wayarta Dan Kiran asibiti akwai abinda zaa kawo mata.

Mum Aisha fita tayi Takoma qasa duk an watse sbd sallan magrib da Kai kusan duk Yan gidan ne suka rage Dan haka itama dakinta ta nufa ta shige qafafunta duk ciwo suke mata sbd Hawa da saukan benan data ringa yi,Ina dalili ta fada tana zubar da kayan data cire Dan wanka ko jikinta ya sake mata.

Dr beeba kuwa har bayan isha takai a gidan kusan after 9 ma Saida jikin Amatun ya Dan dawo daidai kafin ta fito ta tafi bayan ta sake duba Husnah da maamah wainda suka sai alokacin kowannensu ya samu baccin wuya ya daukesa.

Amatu kuwa wanka anty Farha ta Sakata tayi da ruwan zafi sosai jikinta ya Dan sake sakewa kafin ta fito ahankali ba qwarin jiki ta zauna ta Saka kayan sanyi kawai ko Mai Bata buqata.

Milk tea me kauri sosai da soyayyan indomie me kwai da veggies anty Farha ta kawo mata Wanda itace da kanta taje kitchen ta dafa Mata ta dawo.

Duk da cikinta Baya hakurin yunwa yau hakanan ta wuni Bataci abincinba Dan haka ta daure daqyar take cusa abincin tana Shan tea din harta shanye tea taci kusan fiyeda Rabin indomie din ta aje.

Magani anty Farha ta Bata Wanda ba komai bane face su folic acid da sauransu,
Tana Shan maganin ta kwanta sbd gidan yayi tsit alaman kowa ya shige.

Anty Farha kanta wanka tayi taci abinci ta kwanta tareda kashe wayarta sbd itama zuciyarta daci take mata.

Kwanan damuwa da sanyin jiki Akai a TALBAs din Kuma kusan ba kowa ne yayi bacci ba kwance kawai wasu suke Amma baccin Kam bazai iya zuwaba.

Tinda safe kusan kowa a dakinsa yayi breakfast suka fito sbd baqi masu zuwa.

AmatulMaleek ma hakanan ta daure duk da tanajin jikin sukai wanka shirya suka fito itada anty Farha suka zauna palon qasa bayan tayiwa duka dangin mum Abeedan gaisuwa tareda Husnah wadda ko iya Bude idanuwanta dakyau Bata yi sbd nauyi da kumburinsu.

Dakin maamah da Bata iya fitowa sbd jikinta suka tafi itada anty Farha.

Doguwar Riga ce a jikinta da hijab har qasa Wanda ya boye Dan cikinta, fuskarta tayi haske sosai tareda Dan fadawa kadan duk da ta sauya sosai zuwa matar da Hutu ya gama ratsawa.
Itace a gaba kafin anty Farha suka shigo palon maamah Bata qaraso tsakiyar palon ba Idanuwanta ya sauka akan Haydar Dake zaune tareda Abdulhameed abincin breakfast ne Jere a gabansu Amma tea kawai suke sha Se Dan banana bread din dayake hadawa dashi shi kuwa Abdulhameed ita yaketa kokarin kira sbd tinda suka iso Basu ganta ba gashi ba Daman shigowa har sama sbd mutane Dake gidan da dare Kuma anty Farha ce ta sanar musu tayi bacci.

Cak ta tsaya jajayen idanuwanta da suka Dan kumbura akansu tana kallansu jikinta na sanyi hakama tanajin hawaye na ciko idanuwanta sbd batai tsammanin ganinsu ba adaidai lokacin da take tsananin buqatansu duk da Shima Haydar Yana buqatansu.

Haydar Daya ji tsayuwarta dagowa yayi ya zuba mata idanuwansa dasukai ja Yana kallanta batareda ya motsa ba sbd gabaki daya Jin yayi duniyarsa ta tsaya sbd ganinta ya fama raunin jarumtarsa na rashin mahaifiya Dan haka hawaye masu radadi suka ciko idanuwansa batareda ya sani ba sai gasu suna gangaro masa har lokacin idanuwansa na kanta.

Itama hawayen cikin idanuwanta ne suka fara gangarowa tanajin tausayinsa Yana danne duk wata damuwarta da quncin datake ciki daban daban.

Abdulhameed Dayaga Hakan da sauri ya taso Shima cikin tsananin tausayin Haydar dayasan shine itama a ranta dakuma damuwar dayasan tana ciki tinda komai nasu basa boyewa juna.

Rungumeta yayi ahankali itama qanqamesa tayi tana fashewa da kukan damuwoyin Dake kwance a ranta suna cinta batada abokin kokawa bayan anty Farha wadda take danne qarfin damuwarta a gabanta sbd kada ta Sakata damuwa da rashin walwala duk kokarin datakeyi da ita.

Runguman da Abdulhameed yayi mata ya sanyashi Jin tudun cikinta
ahankali ya saketa tareda dagota daga jikinsa yana kallan cikinta Dayake cikin hijab,
Kan fuskarta ya dawo da kallansa cikin tsananin mamaki da kasa yadda da cikine a jikinta.
##MAMUH#


*_AMATULMALEEK_*
By Mamuhgee
And
*_YANCI DA RAYUWA_*
By Hafsat Rano
Na kudi ne
For more page ku biya
500 for littafi Daya
1k for duka books din biyu
at👇
0022419171 access bank Maryam sani
09033181070
[12/5, 6:34 PM] safiya yushau: Abokiyar Nishadi YouTube channel and Meerah Herbs present you the sweetest story#


AMATULMALEEK
Mamuhgee
#ZafafaBiyar



73
*INA MATA,MANYAN MATA,MATAN DASUKA SAN KANSU,MATA MASU DARAJA,MATA MASU BUQATAN GYARA DA KULAWA DA KANSU???*
*SHIN KUNSAN SHAHARARRIYAR ME MAGANIN KUSAN DUKA MATSALOLIN MATA DASUKE FAMA DASU HARMA DA WASU DAGA CIKIN NA MAZAN WATO MEERAH HERBS* 100% Natural herbs💯🔥👍
*Amarya,budurwa,uwargida,bazawara da duk ma macenda take buqtaan gyara da ingantattun kaya karki wuce kayan Meerah Herbs sbd mun tabbatarda ingancinsu kafin tallata muku💯👍*

MAGANIN SANYI
MAGANIN NONO
MAGANIN HIPS
MAGANIN SLIMMING
MAGANIN NANKARWA
GYARAN AMARE
SET MAIJEGO
MALLAKA
SUBULU DA MAYUKA NA GYARAN JIKI
TURAREN WUTA
MATSI
MAGANIN NI'IMA
BACK TO VIRGIN SET
INFECTION FLUSHER

08142800199
07068558096


*************
AmatulMaleek da sosai zuciyarta ke zafi itam da bacin Rai tsayawa tayi tana yiwa Husnah Dake ihu kallan takaici da mamaki me girma Dan Bata dauka da gaske Batada hankalin ba sai yau din.

Anty Farha na zuwa saurin janye Amatu Dake tsaye tana kallan Husnah tayi
mum Aisha kuwa Husnah din ta riqe tana daka mata tsawa cikin tashin hankalin abinda zata janyo musu ana zaune cikin fargaba.

Ihun kukan baqin ciki da zafin zuciya da tafasan jini Husnah ke saki tana kokawan qwacewa tana ambatar ciki ne a jikin Amatun Kuma Bata yarda na Dad dinta bane.

Anty Farha data kasa daukan kalaman Husnah din hannu ta daga zata fizgo Husnah din a saketa tayi abinda zatai su Gani hannunta Amatu da idanuwanta suka rufe ta riqe tared daga nata hannun ta saukewa Husnah lafiyayyar Marin Daya Sakata dauke wutan mamaki da tashin hankalin ita Amatu zata mara,

Ita kanta Amatun yau ranta yakai maqurar Baci sbd maganganun Husnah din da tamkar karuwa ne take kiranta dashi da kalamanta.

Husnah qwacewa tayi daga jikin mum Aisha da itama mamakin Marin ya kasheta Dan abu ne da Basu taba dauka ba ko tsammata daga Amatu.

Qwacewan da Husnah tayi a fusace tana sake maimaita kalamanta yayi daidai da qarasowan maamah sama din hankali tashe sbd girman da balain yayi har bangarenta ana jiyosa.

Isowanta yayi daidai da kalaman anty Farha Dake tare Husnah tana cewa

"Wallahi hauka ya dibeki kika taba Amatu bayan kinga cikin Dad din naki dayake jikinta nice zan fara Baki mamaki kafin me cikin da kansa tinda ke haukarki batajin bari......

Kalaman ne suka raqe saurin qafafuwan maamah data qaraso gabansu ta tsaya tana kallan cikin Amatun dayake kallanta tana kallansa.

Rawa qafafunta suka dauka tayi saurin dagowa ta kalli Amatu da gaba Daya Jin takeyi kaman ta mutu ta huta da abinda take ji Dan kuwa mutuwarta kawai Kila zata kashe rigimar aurenta da ASH dayake haukata kowa harma da ita da auren yake kanta.

Maamah kokarin fahimtar komai takeyi a tsanake Amma Hakan ya kasa yiyuwa Dan kuwa cikin datake Gani a gaban Amatu shine Mafi girman shock data samu a rayuwarta bayan na rasuwar Abeeda.

Rikicewa tayi bakinta na rawa itama tace

"Cikin ne kenan da gaske a jikinki Amatu?
Cikin ne dai kike dashi?
Ciki fa Amatu?
Cikin haihuwar mutum fa Amatu..

Maganar maamah ya Saka tashin hankalin Amatun qaruwa mum Aisha kuwa maimaita ciki yayi wata biyar Kam da alama take fada Wanda yake sake juyar da kan Husnah Yana gigita maamah data kasa fitowa daga shock din ciki a jikin Amatun har ya fito haka...

Amatu rawa dukkanin jikinta ya qara dauka idanuwanta na yin ja
Maamah a rikice batamasan lokacinda tafara cewa

"Daga ina cikin ya fito a jikinki Amatu?
Cikin waye wannan nake Gani a jikinki Amatu??.......

Husnah sabon kuka me Qarfin gaske ta saki tana maimaitawa kunnuwan Amatu kalaman maamah din.

Mum Aisha data ga abin ya qarasa rikicewa sakin Husnah tayi tana Neman zamewa daga rigimar sedai ko Taku biyu bataiba maamah Tayo kan Amatun koina nata Yana rawa zata shaqeta taji inda ciki ya fito jikinta anty Farha tayi kan Amatu hakama Husnah kan Amatun tayi tana qarawa kukan baqin cikinta karfi mum Aisha ma ihun ta saki tana yowa kansu tsoron su taba Amatun takeyi sbd cikin...

ASH ne ya bayyana gurin Haydar da Abdul suna bayansa cikin mamaki da tashin hankalin meyake faruwa suke kallansu Abdul na yowa kan Amatun da anty Farha ta tarewa maamah kamowa,
Abdulhameed mamaah ya riqe sa sauri Haydar kuwa Husnah ya kamo kafin su furta komai Amatu Dake bayan anty Farha ta Yanke jiki ta zube a jikin ASH da taku Daya yayi ya tarota jikinsa jajayen idanuwansa akan qaramin cikinta Daya tsayar da komai nasa.

Duk Wanda yake gurin tsit yayi jikin Husnah Dana mum Aisha harma da maamah din Yana Dan daukan rawa
Hakama Haydar da idanuwansa suka sauka akan cikin dayake jikin Amatun sakin Husnah yayi jikinsa na Dan rawa kansa na sarawa ta ko Ina.

Anty Farha ce idanuwanta suka sauka akan jinin Dayake gangarowa daga qasan Amatu ta fasa Wani irin ihun salati tana Kiran sunan Amatun a ajikin ASH.

Abdulhameed ma maamah ya saki da sauri Yayo kan Amatun Yana kokarin taba ta Amma tana jikin ASH ba Daman Hakan Dan haka suka tsaya cikin tashin hankali da tsoron kada cikin ya samu matsala.

Miqewa ASH yayi da ita a ajikinsa ya dauketa ya nufi kofa da ita da sauri anty Farha ta bi bayansa hakama Abdulhameed da Haydar Daya rikice gaba Daya ya Dena gane komai a take.

Mr Jameel dayake jiyo hayaniyar cikin gidan Yana tsaye cikin baqin takaici da mamakin hankali irin nasu da bayan kisar da sukai Basu dawo hankalinsu ba haryanxu kenan gashi su kawu bello isowarsu kenan daga kauye sunzo gaisuwa kusan su ukun duka se uzaifa,
Suna tsaye suna gaisawa Yana musu barka da zuwa sama sama Dan hankalinsa Daya rabu.

Yana ganin fitowar ASH da Amatu a jikinsa yayi saurin Isa mota cikin mamakin yauma kisan suka gwada kenan ya Bude motar ASH din ya shigar da Amatun ya rufe motar tareda juyowa ya karbi key ya shiga motar Babu abinda ya furta ya tada motar yaja
Securities dake tsaye cirko cirko sukai saurin Bude masa gate ya fita da Wani irin mugun speed.

Rabonsa Daya ja mota da kansa harya manta baimasan yaushe ne ranar Daya tuqa mota da kansa ba sai yau din Dan haka Mr Jameel ya fada dayar motar tareda anty Farha suka bi bayansa Abdul ma key din wata motar ya Karba a hannun drivern Dayan motar Dake aje Shida Haydar suka bi bayansu.

Ba Dan sunso ba kowannen dole ya qarawa motarsa gudu sbd su samu Isa da ASH din Dan gudun dayake yi zai Isa ne harma a shiga da Amatun batareda sun isoba.

Su kawu iKon Allah suka tsaya kallo da mamaki da tsoron ganin abinda yake faruwan duk basu gane waye ASH din ya fita da ita ba jini duk jikinsa.

Tsoro ma kawu ashiru yaji shi Yana Neman kamasa daga zuwansu sai cin karo da mugun Abu saikace wainda suka taho da baqar kafa.

Mum Aisha da baqin cikin Husnah da maamah ya danne zuciyarta Dake tafasa kaman zata babbake ta kallesu tana Jin inama Wani balain ne ya samesu su taru su halaka akan sabuwar masifar dasuka tado musu akan Wanda haryanxu basusan meye hukuncinsu ba gurin ASH din.

Maamah ta kalla zuciya na tafasa tace

"Na dauka Husnah haukarta ta tabin hankalin data samu ne Ashe harda qarin gadon haukar uwar riqonta,
Ke yanzu da Abeeda ta rasu Bata duniyar

45 / 53