Advertisements
Chapter 3 Reading MACIJINE SHI Asirai Masu Tarwatsa Zuciya by Aunty Mameey BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MACIJINE SHI Asirai Masu Tarwatsa Zuciya by Aunty Mameey

Author :  Aunty Mameey Category :  Complete Novels

Chapter   3 / 30

6K to 9K   out of 88K words

tana karanta addu'ar Allah ya tsareta.
Ga mamakinta kawai saitaji macijin ya hau kan cinyarta ya kanannaɗe jikinsa ya dora kansa a saman gammon da yayi da jikinsa.

Ahankali ta buɗe idanunta tana kallonsa,shima ita yake kallo saidai idanunsa na zubar da hawaye kuma na jini .

Jikinta kawai rawa yake cike take da tsantsar tsoron abinda zai faru .juyawa tayi tana kallon haroji dake ta faman ihu yana yaɗuwa kasa.sannan ta kalli jauro wanda yake kwance ba alamun numfashi atare dashi,ga jauronsa nan tayi wani irin kumbura na ban mamaki sai jini ke zuba .

Tsorone ya ƙara kamata cikin azama ta yunƙura tare da mikewa tsaye, ture macijin tayi daga jikinta ta kwasa da gudu tayi gida tana kuka .
Koda taje gidan, da sanɗa tayi saurin shiga ɗakinta tana kuka,zama tayi akan tabarmarta tare da kife kanta a tsakanin cinyoyinta tana kuka.damuwace fal cikin ranta,wai meke shirin faruwa ne da rayuwarta?wacece mahaifiyarta?waye wannan macijin da yake ɗaukan hukunci akan duk wanda yayi nufin cutar da ita?tanasan sanin wannan macijin waye shi,kokuma waye ya aikoshi gareta.tana cikin kukanta ne kawai taji abu yana hawa jikinta silililili!!! Afirgice ta ɗago kanta tana kallon macijin daya gama hawa jikin nata. kansa ya ɗora akan wuyanta yana fidda wani irin huci ,shiru tayi tana sauraron yadda macijin ke huci,sanan jikinsa yayi wani irin zafi sosai.duk yadda akayi bashi da lafiya ,kuma dukan da haroji yayi masane solar hakan.
Tausayinsane taji yayi mugun kamata,ahankali cikin tsoro ta miƙa hannunta tare da riƙo saitin wuyansa ahankali ta janyoshi, ko motsi baiyi ba bare ya hanata abinda yake yi ɗin.

Akan tabarmar ta ɗorashi tare da ci gaba da kallonsa,cikin muryar kuka tace "bawan Allah kai waye?meke tafe dakai?waya aikoka zuwa gareni?meyasa kake ƙoƙarin daukar mataki akan duk wanda ya zalumceni?dan Allah karka cutar dani, bani da kowa sai baffana,dan Allah kayi tafiyarki ,idan mutanen garin na suka farga da kai zasu kasheka ,bazan so hakan ba dan Allah na roƙeka ka tafi"ta ƙarasa maganar tana haɗa hannunta cikin kuka.

Shidai macijin nan ko motsi baiyi ba sai huci da yake yi sosai,
Ahankali ta kalli gurin da yaji ciwo dazu sai taga gurin yana turiri kuma yayi wani fari fat.shiru tayi tana kallonshi ,yanzu ya zata yi masa ne?dan da alama fa yana jin jikine, data rasa abinyi kawai saita lulluba zanin sallarta ta fara karatun Alqur'ani mai girma.cikin abinda bai wuce sakwan biyar da fara karatunta ba kawai macijin nan ya fara wata irin murmurɗewa yana sauya kala, da farko yayi jajur dashi,sai kuma yazo yayi baƙiƙirin sosai ,wani irin hayaƙi na fita daga jikinsa .
Duk abinda yake sam fattu bata kulaba ,dan ta ɗaga kanta sama ne tana karatun ,kuma idanunta na zubda kwalla.

Shikuwa macijin nan burburwa ya ci gaba dayi yana murɗewa jikinsa na turiri tare da sauya kala.can kuma ya fara wani irin ƙara mai kama da gurnanin zaki.cikin tsoro fattu ta dawo da kanta ƙasa tana kallon macijin , sakamakon wannan sautin ƙara da taji yanayi.sai lokacin hankalinta ya kai kanshi taga abinda ke faruwa.
Tsorone ya kamata ƙarara "innalillahi wa'inna ilaihir raji'un"shikenan ta tabbata wannan ba maciji bane tabbas aljanine ,ko kuma aljanine ya shiga jiki sa,na shiga uku ni fattu ya zanyi da rayuwata?meke shirin faruwa dani" ta faɗa cikin muryar tsoro da shiga ruɗu.
Shikuwa macijin nan tana daina karatun saiya daina burburwar da wanann gurnanin,ahankali kuma jikinsa ya dawo yadda yake . Ya jima kwance lamo kafin ya fara motsi,kansa ya ɗago tare da fasa kan yana kallon fattu,gaba ɗaya idanunsa sun koma baƙiƙirin dasu sannan wasu irin ƙananan layoyi suka bayyana kusan guda uku aƙasan kanshi, sai wani irin motsi suke kamar ya'yan tsutsa.

Karkarwa jikin fattu keyi kamar an saka mata shokin, lamarin ya matukar bata tsoro ,meye wannan ɗin haka suka bayyana jikin macijin nan? Me yasa daga fara karatun Alqur'ani gaba daya ya sauya kama?tabbas akwai wani boyayyen al'amari game da wannan halittar dake gabanta,kuma zata ci gaba da bibiyar macijin nan sannu kan hankali har saita gano menene tattare dashi.

Tana nan maƙale jikin katangar karanta kamar ƙadangaruwa dan tsabar tsoro da shiga shock ,idanunta ƙuri akan macijin ,wanda shima ita yake kallo ,kusan minti biyar suna haka ,taga macijin ya sulale ya bar ɗakin ta wannan hanyar tashi.

Rarraba idanu ta farayi tana dafe da ƙirjinta ,yau kam tana ganin ikon Allah kala kala ,anya kuwa bata janyowa kanta masifa ba?waima meye alaƙarta da wannan halittar ne?ko dai baffanta zata sanarwa halin da ake ciki ne?kai a'a ba yanzu ba tukunna ,ya kamata ta zama jaruma tayi wanann aikin koba komai zata taimaki rayuwar macijin,dan ta fahimci akwai boyayyen al'amari atareda shi.

Su haroji kuwa gaba ɗaya ya fice daga hayyacinsa sai ihu yake yana faɗuwa ƙasa ,ahaka ya nufi gidan lamiɗon garin ,wanda shine mahaifin jauro ,yana ihu yana tumami, har yaje gaban lamiɗo ya faɗi yana "wayyo idanuna ,wayyo fuskata lamiɗo ka taimaka min.

Ruɗewa lamiɗo yayi wanda yake tsaye jikin wata sanuwa yana bata ciyawa, lamiɗo bashi da imani ,azalumine sosai ,kuma mutanen garin suna matuƙar tsoronsa, dan haka yake mulki na zalumci agarina,ganin halinda haroji yake ciki"kai haroji menene hakan ?ina jauro?me yasameka?sune tambayoyin da lamiɗo ya jerowa haroji

Cikin azabar ciwo da fitar hankali haroji yace "jauro ya mutu maciji ya cinye masa jauronsa yana bakin rafi"
Ai dajin wannan batu hankalin lamiɗo ya tashi ,nan da nan yayi kan haroji yana faɗin wane macijin ?me kake cewa ?jauro ya mutu?ƙaryane badai agarina ba ,ba wanda ya isa ya zo garina ya kashe min ɗana."lamiɗo na gama faɗin haka ya kira mazan garin ,ya sanar dasu maza aje bakin rafi ataho da jauro.
Aikuwa cikin ƙanƙanin lokaci aka ɗauko shi kamar gawa .

Nan da nan lamiɗo ya nemi haroji ya sanar dasu abinda ya faru .
Nan ya sanar dasu iya abinda idanunsa suka gani,dan shima yana cikin mugun halin mutuwa ko rayuwa dan tuni gurin da jinin nan na macijin ya taɓa ajikinsa yayi wani irin kore shar yana zubar da wani yallow ɗin ruwa .

"Lamiɗo fattu ce ta Turo mana macijin nan ,shine ya kashe jauro"abinda haroji ya faɗa kenan ya sume.

Nan da nan mutanen gurin suka fara maganganu Suna faɗin da "da hansai ta faɗa tace mayyace yarinyar ,tunda har ta fara kashe mutane ba zasu yarda ba sai an hukunta itama.
Ran lamiɗo ya ɓaci sosai ,dan dama yana jin haushi yarinyar da ubanta,ya shirya neman aurenta amma sam taƙi yarda wai karatu take,yanzu kuwa dama tasameshi da zai hukunta su ita da tsohon nata.dan haka cikin bada umarni yace lallai lallai aje ataho da fattu da ubanta .

Nan da nan fusatattun maza suka nufi gidan malam bukar dan aiwatar da ƙudurin lamiɗo........


Masu karatu meke shirin faruwa ne ?

Wane hukuncin lamiɗo zai zartar akansu fattu?

Mai zai far nan gaba?
Muje zuwa yaki ce dai anty mammy

Mrs babi💘💘💘

Share and comments fisabilillah.

More comments
More typing.
29/08/2022, 10:45 am - Khadijah Salisu Fari: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄




MACIJINE 🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)




Elegant online writers📚📚


Page 9/10





__________________Nan da nan fusatattun rugar suka nufi gidan malam bukar ,dan aiwatar da ƙudirin lamiɗo.

Allah Sarki fattu kuwa a wanann lokacin tana ɗakinta cikin jimami da tunanin abinda ta gani yau ɗin nan,haka nan ta tsinci kanta da son sanin menene wannan abubuwan dake motsi aƙasan wuyan maciji? wanda tun daɗewa bata taɓa ganinsu ba sai yau,waya sani ma ko wani akayiwa asiri ajikin macijin ?tabbas zatayi iya ƙoƙarin ta dan ganin ta raba macijin nan da wannan abubuwan ,ta yadda koda wani aka yiwa asiri ta hanyar macijin, to asirin zai karye .sannan tana fargabar gwogwgo ta gano cewar tana gidan kuma bata ɗebo ruwan ba.kuma ahalin da ake ciki yanzu bazata iya komawa rafin nan ba ,.dan ta tsorata dasu jauro .

Hayaniyar mutane ce ta cika gidan nasu fattu ,wanda haka yasa gwogwgo hansai fitowa dole badan ta soba, Dan har lokacin nan ita da yaranta ba wanda yayi sallar asuba.

"Kai su waye haka suka zo suka cika mana gida da ihu kamar ana yaƙi?"cewar gwogwgo hansai tana gyara daurin ƙirjinta dake ƙoƙarin kuncewa bayan ta fito daga ɗakin.
"Aa meye hakan arɗo ?lafiya na Ganku da yawanku kun shigo?ta tambaya lokacin da idanunta ya sauka akan mutanen da suka cika gidan,kusan duk mazan garin ne.

Cikin masifa wanda aka kira da arɗo yace "wllh yau saimun ɗauki mataki akan bukar da fattu ,haka kawai yarinya ta fara kashe mutane ,kuma ta rasa ta kan wa zata fara sai ɗan gidan lamiɗo ?wllh yau sai mun kashe Shegiyar yarinyar nan"ya faɗa yana wani zazzaro idanu kamar zararre.

Eh wllh afito mana da ita kawai mukaita gurin lamiɗo ya bamu izini mu kashe mayya.gaba ɗayan mutanen gurin suka faɗi haka cikin nuna fusata da ƙosawa abasu fattun .

Wani irin farin ciki da jin daɗine ya kama gwogwgo hansai ,shikenan zata rabu da alaƙaƙai cikin sauƙi Allah yasa akasheta kowa ya huta ,dama su haɗa da bukar ɗin da yake ɗaurewa fattu gindi ,koba komai shanunsa sun zama nata.gwogwgo hansai ta faɗa cikin ranta.kafin ta kalli arɗo da sauran mutanen tace "aikuwa idan aka kasheta an kyauta ,dan nima nan wllh so take ta cinyeni nida yarana, jiya da kyar mukasha data maƙuremin wuya wai saita cinyeni, ku ɗan jira kaɗan yanzu zaku ganta shegiya gantalalliya,banma san inda ta tafiba, dama haka takeyi kullum inta fice yawon iskanci bata dawowa da wuri,tana can gurin maza"gwogwgo hansai ta ƙarasa maganarta tana mai buga hannu acinya.

"Aikuwa yanzu zamuje mu nemota ko ina ta shiga,wasu sutafi bakin rafin wasu sushiga jeji, mukuma zamu jira ana "cewar arɗo kenan yana kafe sandarsa akasa,sannan ya gyara tsayuwarsa.


Duk wannan abunda ke faruwa akan kunnen fattu, tana jin komai ,saidai tashin hankali,firgici tsoro da kuma ruɗewa sun hanata koda yin kwakwkwaran motsine .
Numfashinta ma da ƙyar yake fita tsabar ruɗewa.
Ta shiga uku !shikenan yanzu kasheta za'ayi?laifin me tayi da za'a kasheta?me baffanta yayi ake nemansa shima? Dama jauron mutuwa yayi ? innalillahi !!!yanzu ya zatayi.

Wani kukane ya kubce mata cikin sauri ta toshe bakinta tana kuka sosai kamar ranta zai fita,ji take dama tana da ikon ɓacewa, tabbas da ba abinda zai hanata ɓacewa ta bar duniyar ma gaba ɗaya.

Ahankali ta miƙe cikin sanɗa ta leƙo da kanta ,ba ƙaramin tsoro tajiba lokacin da taga mutanen da suka zo tafiya da ita.shikena kawai ta mutu,yanzu shikenan bazata cika burinta na ganin innarta ba?wayyo "Allah ka kawomin ɗauki "ta faɗa cikin raunananiyar muryarta mai cike da tsantsar tsoro.

Ahankali ta ƙara leƙo da kanta waje ,cikin rashin Sa'a kuwa sukayi ido huɗu da dan gidan gwogwgo hansai umaru.wanda hayaniyar mutane tasa suma suka farka.

"Laaaah aradu gwogwgo ga fattun can cikin ɗakinta tana leƙowa"ya faɗa yana nuna ɗakin da Fattu ke ciki
.cikin hanzari fattu ta koma cikin ɗakin tana mai runtse idonta ,tare da dafe ƙirjinta."shikenan sun ganni wayyo Allah na baffa,wayyo MACIJINA kana ina kazo ka taimakeni zasu kasheni wayyo ni fattu"fattu ta faɗa tana mai leƙa hanyar nan da macijin Kebi idan zai bar ɗakin nata inya zo kamar Zariya haka take bankada hanyar macijin da hannunta.

"Munafuka ,mayya dama kina ji ana neman ki shine kika ɓuya nan?to fito yau dubunki ta cika ,mutuwa zakiyi wllh saikin bar duniyar nan yau nima na huta da ganinki ,maza arɗo zoka tafi ta ita gata nan"gwogwgo hansai ke faɗin wannan maganar tana daga bakin ƙofar dakin Fattu,dan tun lokacin nan da tasha matsa agurin maciji bata ƙara shiga ɗakin Fattun ba.
Aikuwa kafin ta rufe baki su arɗo sukayo kan Fattu suna janta.

"Wayyo Allah gwogwgo karki bari su tafi dani zasu kasheni ,wllh ban aikata komai ba wayyo Allah na gwogwgo ki taimaka min"abinda Fattu ke faɗi kenan tana miƙawa gwogwgo hannu cikin kuka mai tsanani.

"Ai wllh dana taimakeki gara hannuna ya karye Shegiyar yarinya ,kutafi da ita can ku kashe banza" gwogwgo ta faɗa tana kaɗa hannu irin yadda ake korar kaji ,cikin farin ciki take maganar.

Ihu Fattu keyi tana kuka,amma haka suke janta kamar akuya aƙasa, suna cikin tafiya ne ,saiga baffa aguje yazo gabansuu ya tsaya riƙe da sanda yana ta haki,dan yana can bayan gari ya sami labarin abinda ke faruwa acikin garin da gidansa,shine ya rugo yazo .


Aikuwa Fattu na ganin baffa ta ƙara fasa ihu tana cewa" wayyo baffana ka taimakeni zasu kasheni" ta faɗa tana miƙa masa hannu,abin tausayi dukta susuce tayi buju buju da jiƙaƙkiyar ƙasa.kallonta baffa yayi
Cikin bacin rai mai tsanani ya ce.
"Sakarmin yarinya arɗo, kona rotsa maka sandar nan akanka" baffa ya faɗa cikin hargowa da ƙaraji,


Kasancewar baffa kowa ya sanshi arugar mutumin kirki ne ,sam ba ruwansa da shiga harkar wani,sanan kuma shine ke ja musu jam'i ,hakan yasa suke ɗan ganin girma da mutuncinsa, dan haka cikin Turo baki da hura hanci arɗo yasaki hannun Fattu wanda ke mata azabar ciwo da raɗaɗi,yana mai cewa"ato lamiɗo ne dai yace mu taho daku,dan haka ya zama dole ayiwa lamiɗo biyayya"ya faɗa yana hararar gefensa, dan yaji haushin sakin wannan hannun na Fattu mai shegen laushi da daɗin taɓawa da baffa yasa yayi.lol

Fattu kuwa yana sakar mata hannu ,da rarrafe ta ƙara so gurin baffa ta rirriƙe shi tana kuka da faɗin"wllh baffa ba abinda na aikata,ban kashe jauro ba " ta faɗa cikin matsanancin kuka da tsoro, jikin ta sai rawa yake.

Riƙota baffa yayi cikin tausayawa yace "na sani Fattuna,baki kashe jauro ba ,kuma ba wanda zai kasheki, Allah na tare dake kinji"?ya faɗa cikin sigar rarashi,sannan ya kalli arɗo yace"kai arɗo ka kiyayeni ,karka ƙara ƙoƙarin sake aikata irin wannan dabbacin akan ƴata, saboda baka da hankali shine zaka rinƙa janta aƙasa. Kamar wata dabba ?jahilan banza jahilin hofi,muje gurin mai garin zanji idan shiyasaka wannan ɗanyen aikin"baffa ya faɗa cikin mugun bacin rai yana mai riƙe Fattu suka nufi faɗa.

Lamiɗo na hangosu ya fara lasar baki ya kure fattu da idanu kamar maye , yana kissima abubuwa da dama cikin ransa....

Manage please yau ina busy,Dan banyi niyar typing bama yau wllh.

Masu karatu me lamiɗo ke nufine shima?

Hmmmmmm kubiyoni mu hade bayan sallah danjin yadda zata kaya.

Kafin nan ina mana fatan yin salla lafiya,sannan aci Nama ahankali kar azo ana .......

Taku anty mammy
Mrs babi,💘💘💘
29/08/2022, 10:45 am - Khadijah Salisu Fari: 🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄🎄


MACIJINE 🪱🪱🪱

Na mammy kabeer
(Anty mammy)




Elegant online writers📚📚


Free book

Page 11/12


Ta ƙabbalallahu Minna waninkum.
Slm, ƴan uwa masoyan littafin MACIJINE, ina miƙo gaisuwa tare da Barka da Sallah ,Allah ya maimaita mana,yasa munyi karɓaɓɓiyar
Ibada.



________________Kai tsaye su baffa suka nufi gurin lamiɗo,hannunsa riƙe da na fattu ,wacce ke tafiya ahankali cikin azabar raɗaɗin da hannunta keyi,dakuma ciwon jiki.yayinda su arɗo ke mara musu baya burinsu kawai suga wane irin hukunci lamiɗo zai ɗauka akansu fattu ,cikin zuciyarsa arɗo yake fatan inama lamiɗo ya kori su fattu daga rugar ,inyaso su bisu hanya suyiwa fattun fyaɗe,dan su kashe ƙishirwarta dake cin ransu.

Shikuwa mai gari tun daga nesa ya hango su fattu,gaba ɗaya nutsuwarsa ta bar jikinsa,ƙureta yayi da ido guri!!yana haɗiyar yawu da lasar leɓe kamar tsohon maye.
Kallonta yake yana ji kamar yaje ya kamota yayi ɗaka da ita.

haba malam ,yarinya bul-bul da ita kamar nunannen tumatur,lallai yau zai sha shagali.lamiɗo ya faɗa cikin ransa yana mai kallon fattun.

Baffa kuwa suna ƙarasowa gaban mai gari ya nemi guri ya zauna tare da zaunar da fattu kusa dashi,wacce gaba ɗaya arikice take ,tsorone ƙarara shinfiɗe akan fuskarta.tayi luƙus ajikin baffanta jikinta sai rawa yake, ta kasa ɗaga kanta ta kalli kowa ,sai hawaye take sharewa.


Kowa yanemi guri ya zauna ,masu tsayuwa suka tsaya , da ƙyar lamiɗo ya iya saita kansa ya aro nutsuwa ya yaɓa akansa, tare da ɓata ransa ya kalli baffa yace "malam bukar kana sane da irin abinda ƴarka take aikatawa awannan garin ?lamiɗo ya faɗa cikin kakkausar murya .
Ahankali baffa ya gyara zama kafin yace ,naji anata wai wai agari cewar ƴata tayiwa su jauro turen maciji ,amma sam ban yarda da wannan magana ba,dan kuwa ƴata ba mai kashe mutane bace ,sannan ba mayya bace kamar yadda ake faɗa"baffa ya faɗa cikin ɗaure fuska .
Cike da ɓaci rai lamiɗo ya fara magana.
"To wllh malam bukar bazan ɗauki wannan abun agarina ba,yanzu ace abun nata ya wuce kan kowa sai kan ɗana ?sannan kuma kace wai baka
yarda da zancen ba ?kana nufin nayi maka ƙarya ne?to bari kaji dole ne saina ɗauki mataki mai ƙarfi akanka da ƴar taka ,dan ka nuna rashin ɗa'a a gaban fada.bayan kuma kowa yaga abinda ƴarka tayiwa yaranmu,
Dan haka bazan yanke hukunci yanzuba sai zuwa gobe ,idan yaranmu sun sami lafiya,dan haka yanzu za'a shiga da ita cikin gida anan zata zauna cikin wancan bukkar da ake ajiye masu laifi .
Dan haka kowa ya watse sai zuwa gobe da la'asar adawo nan dan jin hukuncin da zan yanke"mai gari yana gama faɗin haka ya jingina da jikin kujerar da yake zaune akai.
gaba ɗayan mutanen dake gurin sunyi na'am da wannan hukuncin nacewar fattu ta zauna a gidan mai gari ,dan karta gudu.

Kuka sosai fattu ta sanya tana riƙe hannun baffa "wayyo Allah na baffa ka taimakeni,dan Allah karka bari akulleni adakin hukunci ,wllh bani nayi musu haka ba ,kuma sunzone da nufin keta min haddi baffa ka kalli Yadda ya famamin targaɗe na wllh ba laifi na bane" fattu ta faɗa cikin matsanancin kuka kamar zata shiɗe.

Cikin tashin hankali baffa ya riƙe hannun Fattu ,ji yake kamar ya fasa ihu,aduniya ba abinda ya tsana irin yaga Fattu cikin damuwa,"kiyi haƙuri fattu ba abinda zai sameki,in Sha Allahu Allah zai saka mana dan wannan mugunta ce ake son yi mana ,kuma Allah yana bayan mai gaskiya"yana gama faɗin haka ya juya gurin mai gari yace "lamiɗo ina neman alfarmar abarmin fattu mu tafi gida ,zamu dawo da ita zuwa goben,dan bata da lafiya kuma barinta ita kaɗai akwai matsala" ya faɗa cikin damuwa da alhinin wannan rashin adalci da ake ƙoƙarin aiwatar musu.

Cike da mugunta lamiɗo yace "kai bukar ina ganin girmanka karkasa in daina gani ka iya bakinka a faɗa kake,kasan idan na riga yanke hukunci ba mai ja dani ,dan

3 / 30