Advertisements
Chapter 106 Reading A Duniyata Book 2 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

A Duniyata Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Huguma Category :  Complete Novels

Chapter   106 / 119

315K to 318K   out of 356.9K words

sauri.

"Qaniyarki huda.....kakarki ce ni?"

"Barta ta fadi fa......sister gaskiya ta fada,Allah na tuba waye yayi yaku?,har yanzu gani nake BB bai kamoku ba,in kuna wani abun sai inga tabbas mu dukka 'yan koyo ne" Cewar fannah tana dariya bayan ta gama duba bayanan asibitin da yadda zasu gudanar mata da aikin. Kai kawai sabreen ta girgiza,bata iya ce musu komai ba don bata da abun cewar. A fakaice take bin huda da kallo,ranta fari tas tana godewa Allah,tana tuna shekarun baya......tana tuna nasir,wanda tabbas inda yakai ga cimma gaci qila yanzun huda ba'a wannan matsayin take ba. Yadda ta mori miji haka tayi imani huda ta mora,ta lura da yadda hudan ke qara mulmulewa abinta,jikinta kuma ya bata juna biyu ne,fadi ne kawai basuyi ba saboda kunya,uwa uba kuma sai Allah yayi mata baiwar juna biyu maras laulayi sam sam sam,kawai dai ya sakata mugun cin da ya sanya taketa qiba. Amna ce tayi fama da laulayi,yanxunma dai daya girma sai a hankali,abinka da auta shagwaba ga quruciya,duk da shekarunsu kusan daya da huda amma rainon ma ba daya bane,amna bata saba da wahala ba,huda kuwa ta daku da wuya iya wuya,qilan ma shi yasa yazo mata ba'a wani kayan wahala ba,duk da cewa asali halitta halitta ne.

Aikam zancansu dutse,don sanda fu'ad yake shigowa dakin duka kasa zama suyi,kowa yaja matarsa,daga qarshe ma sallama sukayi musu akan gobe zasu dako sammako don ayi aikin a gabansu.

A hanya suke gulmarsa,fannah tace.

"Kasan Allah mine......nasha gulman dude dinka,nakance wadda ta aureshi zata wahala,miskilancinsa yayi yawa,duk yadda kuke dashi sau daya ya taba rakoka zance,koda yaxo ma sai naga magana wahala take masa,nace wannan ina za'ayi walwala a gidansa?,ashe expert ne......Shahrukhan ne" Dariya sukayi gaba dayansu. Huda ta karba itama.

"To ai har yanzu adda fannah....." Harara fanna ta aika mata.

"Nifa ba fulbe bace.....ki daina kirana da addan nin.....bayinmu fulani ke amfani dashi" Dariya ta sake sosai.

"Adda kin riga fa kin shigo cikinmu,kema kin zama bafulatana daga yau......" Jujjuya kai fannah tayi alamun ya zata iya?,anfi qarfinta.

"Ko yanzun ba boss yake,yanzu fitowarmu daya shigo yana taku yana shan qamshi in ke baquwa ce ba zakice haka yake ba.....amma yana isa gurin matarsa ya koma wani mutum na daban" Huda tace tana dariya abinta. Da irin wannan hirar ta qawatacciyar soyyarsu suka qarasa gida.


*WELCOME TO THE WORLD*

*_The jadda's triplet_*
*_a bundle of joy_*
*_three little miracles_*


Idanunta tsakiyar nashi,ta kasa banbance tsakanin ita dashi waye yafi wani fargaba,waye yafi wani tsoro?,waye yafi wani shiga yanayi na zaquwa da kuma shauqin ganin yaran da har a sannan basusan wanne jinsi bane?.

Cikin tsararren dakin aiwatar da tiyatar,kwance saman gadon wanda likitoci ke kewaye da ita. Aikinsu suke daga qasanta,sun saki koren labule daga saman cikin nata zuwa kanta bata tare dasu......amma muhamma fu'ad jadda.....rauninta kuma qarfinta yana tare da ita.

Yana zaune daga saman kan nata saman kujerar da tsahonta yakai daidai kanta,sanye yake da wasu kayan green color shima da irin hular dake kawunan likitocin. Hannunsa cikin nata hannun,ya sarqafe yatsunsu guri guda,idanun kowannensu cikin na dan uwansu.

Qur'ani yake karanta mata qasa qasa,cikin wani irin daddadan sauti daya sanya hatta da likitocin sauraronsa babu shiri,idan kaji sunyi magana ya kama ne. Sosai takejin wani nutsuwa yana saukar mata,idanunta kan labbansa dake motsawa cikin gwanancewa da qwarewa cikin karatun qur'ani me girma.

Daidai sanda yakai kan ayar qarshe ta cikin suratu yaseen

"Innama amruhu iza arada shai'an an yaqula lahu kun fayakun,fasubhanallazi bayadihi malakuti kulli shai'in wa'ilaihi turja'un". Sound din kukan baby na farko shine ya biyo bayan saukar nashi muryar.

Sake sarqewa idanuwansu sukayi cikin na juna,zukatansu na wani irin bugawa da wani irin madaukakin farinciki.

"Second baby" Muryar likitar ya baqunci kunnensu da kuma wani sabon kukan jaririn.

"Third one" Suka fadi sanda sabreen din ta sauke wani nishi saboda fitar yaron daga cikinta da ya sanya qirjinta fadawa sosai.(wannan wani irin yanayi ne da kowacce uwa da aka taba yiwa CS ta sanshi,wani yanayi ne da bakya taba mantashi,ya Allah ka taimaki duk wasu uwaye musulmi,wanda CS ya zame musu abu na ko yaushe yayin haihuwa ya rabbi ka basu da sauqi,ka tsallakar dasu dukka wani hadari da wata wahala dake cikinsa,masu haihuwa da kansu don isar annabin rahama ka basu naquda me sauqi,masu neman haihuwa ya Allah don hasken fuskar manzan Allah ka azurtasu da ita,ka basu masu albarka wanda zasu iya dasu ameen).

(A wannan gabar nima nake barar addu'arku da bakunanku masu albarka😄,Allah ya azurtani da twins ko triplet nima🙏🏽🙏🏽,the dream of my life,ina fatan zaku sani a addu'arku,akwai wadanda suke qasa me tsarki duka ina fatan zaku jefani a Addu'arku,na gode).

A lokacin fu'ad ji yake kaman bazai iya jira su zagayo da yaran su nuna musu su ba,duk da yasan definitely zasuyi hakan. Bai jima da sauke tunanin ba kuwa mutum uku suka daga musu yaran yadda mahaifiyarsu ta haifesu suna tambayar sabreen meye gender dinsu.

"Boys" Ta fada muryar ta na rawa da wani irin narkewar zuciya. Shikam kasa magana fu'ad yayi,sai sake damqe hannunta da yayi cikin nasa,ya maido idonsa cikin nata yana dubanta da wani kasantaccen shauqi.

"Thanks hamma......na gode sosai hamma......inama ummeena tana raye?,ka bata jikoki da jinsin da har ta mutu ake mata gorin bata haifa ba.......ka bani wata kyauta da bazan taba iya mancewa da ita ba". Hannu ya dora saman lips dinta yana fadin.

" Shshshsh.....ki huta my world......ki huta duniyata" Ya aza hannunsa saman kanta yana shafa mata a hankali. Bayaso taci gaba da magana,don ya tabbatar muddin zataci gaba din to tabbas zata karya masa zuciya ne,zuciyarsa a kusa take da sakin kukan farincikin da a yau bayajin yana da nutsuwa idan bai dangana da masallacin ma'aiki ya miqa godiyarsa ba.

Yana iya hangen yaran bayan an gama tsaftacesu an kuma shiryasu cikin kayan jarirai,kowannensu ya cika kayansa,kaman ba jiriri ba,abinda yake bashi mamaki yadda cikin duniyarshi ya dauki manyan yara kaman haka,yana hangensu suns wutsil wutsil,yana jin shauqinsu daga nan inda yake zaune,amma kuma bazai iya sakin hannunta ya barta yaje wajensu ba. Tana ankare da hakan,saita saki tattausan murmushi ta kuma matsa hannunsa,wanda hakan ya jawo da hankalinsa kanta

"Tashi kaje hamma....tashi kaje wajensu" Kai ya girgiza mata yana sakin murmushi,qwalla cike da qwayar idanunsa.

"Bazan iya motsawa daga inda duniyata take ba....until you feel okay"

"Am okay hamma.....am okay" Ta bashi assurance,amma sai ya maqale kafadarshi yaqi tashi.

Cikin minti arba'in gaba daya aka kammala gyarata tsaf ita da yaran,sannan aka tura gadonta zuwa dakin da zata huta.

Tsaiwa nurses din kawai sukayi da yaran suna dariyan ganin drama din da akeyi tsakaninsu BB farouq huda anni saddiq harda fannah ma. Shidai abba Alhaji hamza kibiya da isowarsa kenan asibitin baya yaja ya tsaya yana dariya,don baisan shi kansa ya zaiyi musu ba,kowa so yake shi za'a fara bawa,wannan ya sanya kawai suka zarce wajen Alhaji hamza suka miqa masa daya,sauran biyun wuka sanya masa su kan cinyarsa.

"Shikenan sun raba rigima ko?" Abba ya fada yana dariya gami da zube idanunsa akan yaran.159


"Ma sha Allah,tabarakarrahman.......alhamdulillah.....alhamdulillah" Abban ya maimaita yana jin wani qaunar yaran sabuwa fil tana taso masa. Har ransa yakejin alfahari da samun yaran,har cikin jininsa yake jinsu tamkar amna ko farouq ne ya haifesu,wani irin rahama yaji kaman ta sauka a family din nasa,samun qananun yara har qwaya uku a lokaci daya,a sanda suke kewan yara qananu din. Baisan wani abu da yakeso yake kuma matuqar alfahari dashi ba irin iyalin nasa......irin family din nasa ba,wani baiwa da kyautar ahali Allah yayi masa,badon yafi kowa wayo ko dabara ba.

Addu'a sosai abban ya dinga musu a sarari a bayyane,su anni suna amsa masa da ameen,duk kuwa da cewa kowa ya qagu abban ya gama ganin yaran ya basu su.

Na hannun nasa da suka ce masa shine babba ya juya,yayi masa kiran sallah a dama,sannan yayi kasa iqama a hagu,bai ambatar masa sunansa ba,don shi din ba mutum bane me yawan kutse ga al'amarin yaran sa ba,muddin basu sabawa al'ada ko addini ba yana barin kowa ya zabi abinda yakeso ne.

Anni ya fara miqawa sannan ya dauki na biyun ya maimaita masa abinda yayiwa na farko ya sake miqawa anni,wadda ita kuma ta miqawa huda na farkon. Tana ganin irin zaquwar da huda ke ciki,ta kasa zama ta kasa tsaiwa. Hannu biyu anni ya karbeshi shima,sai ga hawayen da taketa riqewa sun soma diga saman lallausan abun daukan jariran,sai sautin kukan huda itama ya soma tashi.

Murmushi abba ya saki yana tsokanar annin.

"Da alama wannan kukan za'a yimin tawaye kenan,banda haka nine ya cancanci nayi kuka ai,nida aka yiwa kishiyoyi?,har uku rigis a rana daya a lokaci daya?,to ki daure zuciyarki dai karsuce matar tasu raguwa ce" Ta tsakiyar hawayen nata murmushi ya subuce mata,daga ita sai Allahnta su kadai sukasan irin farincikin da yake dawainiya da ita,yaran wani baiwa ce da rahama daga ubangiji zuwa garesu,lallai bawa ya kamata ya zama me yawan imani da qara girmama zatin mahaliccinsa.

Duk wanda ya dauka kaman kada ya sauke a cikinsu,sun karade wajen har basa ganin wani bare a wajen,ganin yara uku ya janyo hankulan mutane,duk wanda zai wuce sai ya tsaya ya kalla ya musu addu'a kuma.

"Wai ina muhammadu ne?" Abba da baiga fu'ad ba tun zuwansa gurin ya tambaya.

"Yana can wajen matarsa......inajin ko yaran bai dauka ba" Anni ta fada tana nannade yaro daya da yake hannunta.

"An kaita dakin hutu ai,inaga ya kamata sukai masa yaran.......kai saddiqu" Ya kira saddiq da suka lafe shida hudarsa suna tattauna yadda nasu yaran zasu kasance kyawawa kamar haka,sun saka yaro daya dake hannunsu a tsakiya sunata murmushi kaman wasu shashashai. Kai anni ta dauke tana sakin murmushi gami da girgiza kai,daga hudan har saddiq din akwai wauta tamkar 'ya'yan fari. Saida zamansu ya miqa ta fahimci lallai halayyarsu ta dace da juna sosai,shi yasa har yau bata taba jin kansu ko cikinsu ba.

"Karbeshi kuje kukaiwa babbansu su"

"To abba" Ya fadi yana sanya hannu ya karbeshi daga hannun huda,ji tayi kaman kada ta bada shi,shima ya karanci haka,sai ya saki murmushi murya qasa qasa yace

"Namu yana hanya in sha Allah". Murmushi ta saka cikin tsananin jin kunyarsa ta kauda kanta,tana ganin kamar su anni zasuji abinda ya gaya mata.

Dashi da BB farouq suka isa dakin,farouq yara biyu ne saman kafadarsa,yayin da saddiq din yake dauke da guda daya.

Wani irin nutsatstsen yanayi dakin ke dashi,ba yawaitar haske kuma ba yawaiyar duhu,wataqila sun barshi a hakanne saboda cikakken bacci da sukeso sabreen din ta samu.

Yana zaune gaban gadon saman wata farar kujerar,hannunsa cikin tsakiyar nata hannun,ya tattara dukakanin hankalinsa a kanta cikin matsananciyar kulawar da ko cikakken motsi baya so tayi.

Da alama magana sukeyi qasa qasa,wanda a tsakaninsu ne,don kana dakin babu lallai ka iya jin komai. Motsin shigowarsu ya sanyashi daga kanshi,ya zube idanunsa akan yaran dake hannunsu yana jin wani irin abu me nauyi na sauka a qirjinsa.

Cakudadden farinciki ne daya gauraya da nutsuwa da godiya da rahamar Allah a kanshi.

"Wannan duniyar taka ba zata taba barin yarana suyi farinjini a gurinka ba da alama......kawai dadin abun......uba da yawa maganin kukan d'a" BB farouq ya fada yana isa gabanshi ya jeresu daga gefen sabreen din duka su ukun.

"Minti kadan na baka ka gama kallonsu zanzo na debe kayana" Farouq ya fada da wani irin cin serious harda duba agogon hannunsa. Murmushi kawai faud ya saki,zuciyarsa na karyewa,nauyi da kunyar ubangiji tana kamashi,yana jin kaman baiwa Allah komai ba daya cancanci irin wannan kyautar da baiwar ba.

Har yayi taku biyu farouq din ya dakata,ya waiwayo yana dubansa.

"Ko barka kayimin ba.....kuma duk wanda baimin barka ba yana cikin black book dina" Murmushi ya sake qwacewa fu'ad,ya motsa labbansa a nutse.

"Congratulations BB farouq......ina tayaka murna da samun 'ya'ya da kayi". Wani ni'imtaccen murmushi ya bayyana a fuskar farouq din,sai kawai ya dawo da dan sassarfa,kafin yakai ga qarasowa kuwa fu'ad ya rigashi miqewa suka rungume juna sosai.

"Barka da arziqi dude......ina maka fatan alkhairi,ina tayamu murna mu gaba daya.....Allah yasa mu da musulunci gaba daya muyi alfahari dasu"

"Ameen dude......ameen na gode" Fu'ad ya fada yana jin jinin 'yan uwantaka yana yawo a jikinsa. Zare jikinsa farouq yayi,yaja da baya yayi saluting sabreen da sai a sannan ya lura idanunta biyu.

"Well done addarmu......" Ya fada yana qamewa. Murmushi ta saki idanunta na lumshewa saboda nauyi da sukayi mata,ta girgiza kai murya can qasa ta furta.

"Na gode BB". Gira ya dagawa faud tare da babban dan yatsansa sannan ya juya yana fita.

Da fari idanu suka zubawa yaran su duka shida ita,dakin yayi tsit sai qarar na'urar kadan kadan. Gaba dayansu bacci sukeyi,sunyi wani irin matuqar tafiya da zukatansu da wani qaqqarfar soyayyarsu data fusgi zuciyarsu lokaci guda.

Tare suka kai hannuwansu kan yaran,sai suka kalli juna kuma kowannensu ya sakarwa dan uwansa murmushi. Tsam fu'ad ya miqe tsaye,ya gaji da bugawar da zuciyarsa keyi,ya dauki.yaron farko ya mannashi a qirjinsa sosai yana jin dumin jikin yaron da qamshin sabbin tufafinsa.

"My heart beat" Ya furta a sanyaye har na tsahon second sittin sannan ya daukeshi daga qirjin nasa ya maida dubansa kan fuskarsa.

"Wannan hamza ne.....hamza ne wannan,jarumin sadaukin nan,baffan manzan Allah......kuma ubana abbana daya bani sabon ruhi da sabuwar rayuwa" Yayi maganar daga qasan zuciyarsa yana jin soyayyar yaron.

Idanunsa ya cire ya maida kanta,tana daga kwnace tana kallonsu da wani azababben kallo me cike da qauna. Rayuwarta take gani a tattare dasu,ruhinta dama komai nata.......daga sabreen ita daya ya daga darajarta ya maidata me rassa har uku.

Kadan ya Matso gareta,ya manna mata yaron itama a qirjinta.

"Ki masa addu'a.....hassan shine hamza"

"Allah kasa ya biyo halin asalin me sunan"

"Ameen" Ya amsa yana lumshe ido.

Juyawa yayi tana nufar gadonsu,ya kwantar dashi sosai yana gyara masa lullubarsa sannan ya dawo kan yaro na biyu.

"My world......dukkansu kamarsu daya.....kama suke da juna ta sosai da sosai......kinga har wani digo dake fuskarsu ma iri daya ne" Ya furta yana dubanta. Ajiyar zuciya ta sauke,ta gani itama,ta gani fadi ne akwai batayi ba.

"Wannan babban aminina ne,dan uwana kuma masoyina.....umar alfarouq" A wannan karon ita kanta saida murmushi ya subuce mata

"Wai Allah hamma......zaka kawo rigima fa.....tabbas BB bazai boye soyayyar hussain a zuciyarsa ba".

"Na sani ameenatu" Ya amsa mata shima yana imagining fuskar farouq,don ba zata yayiwa kowa,shi kansa baisan gender na yaran ba sai bayan an haifesu bare wani yaji sunan da zai sanya musu.

Shima sai daya mannashi sosai a qirjinsa sannan itama ya saka mata su,ya kuma sanyata ta masa addu'a kaman dan uwansa sannan yaje ya hadashi da dan uwansa ya dawo kan na ukun.

"Gamboliya gambo" Ya furta da wani irin nishadi a muryarsa daya sake saka sabreen din ita kanta a nishadi,duniyar duka sai take jinta kamar tasu ce su biyar dinnan suda yaransu.

"Shi wannan......abbana ne......sanadi na.......masoyina almustapha muhammad jadda" Ya qarasa fada yana kissing nasa sannan ya maidashi qirjinsa yayi masa kyakkyawar runguma. Tana iya hangen hawaye qasan idanunsa,wanda ta tabbatar na rauni ne. Wani tsohon miki ko rauni dake danqare qasan zuciyarsa.

Tanaso ta sassauta masa don haka tagi gyaran murya kadan,sai ya ware idanunsa da suka canza launi akan fuskarta.

"Amma hamma.....anya ba za'a samu jam'iyyu ba.....zakaso abba da yawa fa....." Murmushi ya qwace masa,ya dauke almustapha daga qirjinsa yana cewa.

"Wadannan dukkaninsu masoyana ne......idan kika cire daya daya daga cikinsu to tabbas babu fu'ad......tarihin muhammad jadda bai kammala ba,bazai kuma taba zama kammalalle ba". Ta aminta da maganarsa dari bisa dari,ya matso ya aza mata almustapha din saman qirjinta,shima ta bishi da addu'a.

Dawowa yayi saman kanta,yana shafa doguwar sassalkar sumarta a hankali.

"Kiyi bacci my world.....yi bacci duniyata.....kin cancanci ki huta,kiyi bacci me dadin gaske,mijinki yana daga bakin qofa yan gadinki,ko yatsarki kika motsa zan jiki......ki raya a ranki duk duniya ba wata mace me gatanki......ke 'yar gatan mijinki ce......mata tabbas rakiya sukayo miki zuwa duniya". Wani sassanyan ruwan nutsuwa maganarsa ta sakar mata a tsakiyar zuciyarta,ta lumshe ido tana sakin murmushi bar batasan sanda baccin yayi

106 / 119