Advertisements
Chapter 95 Reading A Duniyata Book 2 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

A Duniyata Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Huguma Category :  Complete Novels

Chapter   95 / 119

282K to 285K   out of 356.9K words

dake qafarsa,ya rage saura socks kawai wadda ita tayi masa jagoranci har zuwa bakin gadon da take zaune.

Hannuwanta dake lullube da kyakkyawan zanen lalle ya kalla,baisan sanda ya ajiye wayarsa da keys dinsa gefe ba,ya miqa hannu yana dora tafin hannunsa saman nata tafukan hannayenta ba ya riqesu sosai. Wata sheshsheqa ya saki gami da nannauyar ajiyar zuciya duka lokaci daya,wanda suka fito tare da kalmar

"Alhamdulillah". Karon farko a rayuwarsa da hannunsa ya soma taba na fannah bayan ta zama halalinsa......karon farko da sukayi kusaci da juna har irin haka,duk da yadda yake tsananin sonta,yake kuma shauqinta,itama kuma haka,amma dukkaninsu sun killace hakan,sun kuma boyeshi qasan ransu,ba wanda ya bari dan uwansa ya fuskanci hakan.(qalubale ga matasanmu)

"Babarbariya ta" Ya fada a tausashe da wani taushi da baisan yana dashi ba. Wani suna qwaya daya da ba soyayya ba da yake kiranta dashi,yake kuma mata tsananin dadi.

"Taimaki wannan dan bawan Allahn a bude masa wannan fuskar mutanen maidugurin ya kalla" Ya fada yana zamewa,sosai ya zauna a gabanta gami da komawa kalar tausayi,ya koma kaman wani dan almajiri,sai yakejin tun yanzun kaman zai fara sakin kukan da fu'ad ke cewa ya riqeshi tukunna. Kafada ta maqale ba tare datace komai ba,sarai ya gani,duk saita rudashi.

"Roqo nake badon halina ba" Ya fada yana riqe hannayenta da kyau cikin nasa.

Murmushi ya qwace mata,duk da fargabar da take ciki,sai ta zame hannunta daga nashi a hankali ta sanyasu tana janye lafayarta baya ba tare data daga kanta ba.

"Kan uba!....subhanallah" Ya fada yana wani wantsalawa cikin wani irin mamaki. Fannah ta shammaceshi,tunda suka fari soyayyarsu har suka qare bazaice ga wani shape nata daya taba gani ba,koda da wasa kuwa,a yanzun saiga wata ajiyayyar kyakkyawar halitta kuma dukka mallakinsa ce?,yayi yadda yakeso?. Hannu ya miqa zai zame lafayar daga kafadarta,yanason ya sake ganinta sosai sai ya janye hannun da sauri yana murmushi,yana jin kaman wani shock ke jansa.

"Dan sake budemin please fannah.....i wanted to see you all". Wuyanta ta langabe alamun aah,ai baibi ta kanta ba sai gashi ya dawo gabanta. Hannuwansa duka ya sanya ya dagata,ya miqa hannunsa gefan qugunta inda ta daure lafayar ya wareshi,ya kuma zarce da wareta gaba daya daga jikin nata.

Tsaf ya ware kayarsa,sai yakejin wani abu yana ratsa sassan jikinsa.

"Subhanallazi lam yattakiz waladan wala saheeba" Ya tsarkake girman zatin Allah a abinda idanuwansa suka gane masa karo na farko(qalubale gareku mata,wata sai ran bikinta ma take fidda shape din gaba daya mazan duniya dana media su tayashi kalla).

Ji yayi idan ya qara koda second daya bai sanyata a jikinsa ba kaman zai mutu,sai ya jawota gaba daya cikin jikinsa yana lullubeta da hannuwansa,qamshin jikkunansu suna cakuduwa guri guda.

"Alhamdulillah,first halal hug" Ya fadi a bayyane yana sake godewa Allah da yadda ya bashi iko ya tsare mutuncinsa.

Sai da yayi da gaske ya zame jikinsa,don ya fahimci wannan al'amarin bame sauqi bane,idanma har za'a biyewa ta zuciya da gangar jiki,tabbas dukka addu'o'innan da musulunci ya koyar da sallolin ba zasu samu ba.

"Ki shiga toilet ki daura alwala,ki rage wannan nauyin na jikinki kizo muyi sallah" Ya fada yana tattare mata lafayarta guri daya. Dama gurin tsira take nema,don haka da sauri da sauri ta wuce bandakin ta turo qofar.

Wani wawan tsalle ya buga bayan ya isa dakinsa.

"Alhamdulillah" Ya sake maimaitawa yana sauraren bugun da zuciyarsa keyi,sai ya miqe ya soma shima rage kayan nasa jikin sannan ya wuce bandaki.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862


𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 142

*_Domin qulla huldar kasuwanci damu,HUGUMA CLOSET.....siya ko siyowa wani,reposting ko sari akan farashin da babu irinsa_*


https://chat.whatsapp.com/FrqgC0YmUWP4FPmUzYuLJX



142


Sai da suka tabbatar an kai amarya,an kuma dawo,kowacce mota an ajiyeta a muhallinta sannan sukabar farfajiyar gidan shi da saddiq suna wucewa sassansu da tuni kowannensu shima ya kwashe komai nasa banda furniture din ciki,aka kuma shirya a tagwayen gidajensu masu tsananin kyau da fasali.

Saida musaddiq din yayi wanka don yaji dadin jikinsa,ya kuma canza kayansa zuwa sassauqar jallabiyya ta maza. Har zai tada sallah sai kuma ya fasa,ya koma da baya yana dauko wayarsa da tunda suka gama waya da amna ya sakata a charge ya kulle ya barta a dakin.

Yayi hakanne don kada ta matsa masa da kira da magiya,taje ta karya masa zuciya yayi abinda baiyi niyya ba. Sam bayajin zai barta fita a gidan,fita daya yakeso tayi,daga gidan sai gidanshi a gobe in sha Allah.

Ya tarar kuwa da miscal dinta har guda biyar.

"Rigimammiya" Ya fadi yana murmushi sannan ya koma ya zauna yana yunqurin kiranta.

Kiran farko aka gaya masa layin a kashe yake,mamaki yadan kamashi,don zai wahala ka kira amna wayarta a kashe,tunda dai su ba rashin wuta sukeyi ba,inverter ne 24/7 a gidan.

Sake gwadawa yayi aka sake gaya masa hakan,sai ya haqura ya kira saddiq zuciyarsa na raya masa tayi fushi ne dashi bai kaita ba,shi yasa ta kashe wayar don ta rama,shikam bazai iya jura ba,gwara ya lallaso abarsa,

"Huda zaka kiramin,kace tace da amna ta bude wayarta badon halina ba". Dariya saddiq ya bushe da ita.

"Man.....wannan karyar da kai haka?,'yan mazan anni na dab da zubewa"

"C'mon saddiq.....zaka taimakamin ko na shiga gidan da kaina na nemota?".

"Ni na isa?,bari na kira maka ita.....hold on kada ka kashe". Ya fada yana hada conference call .

"Hubby..." Ta furta da shagwabar data sanya musaddiq jin kunya ta kamashi.

"Love ya akayi?".

"Ina kewarka hubby"

"I know love......but mun kusa kasancewa da juna in sha Allah,awanni kadan suka rage.....kina ina?" Ya tambayeta calmly.

"Na boye a daki hubby.....kunyar anni nakeji".

"Anni love?....." Ya fada dariya na subuce masa.

"Anni ai bata da surukai sai 'ya'ya,tasha fadin hakan.....fell free please".

"I will tray hubby"

"Good girl....amna fa?"

"Tun dazun da muka karbi adda fannah ban sake ganinta ba,ina tunanin tana wajen anni".

"Thanks......bari nayi wanka.....get ready zan kiraki ki rage....." Bai qarasa jinsu ba ya yanke kiran,kada suje suyi masa baranbarama a kunne.

Still ya sake kiran saddiq.

"Ina kunyar tambayar anni please saddiq tambayar min ita"

"A nawa?" Ya sake zolayarsa

"Ka fadi price dinka" Ya fada yana jin zaquwa.

"Bari na kira maka din sai mu tsadance" Ya fada yana yanke kiran.

Minti daya kacal saiga kiran saddiq din.

"Anni tace suna tare da huda,gashi kuma huda tace tana wajen annin". Gaban musaddiq ne yayi wata irin mummunar faduwa,haka kawai yaji fargaba tana ratsashi.

"Ya akayi haka?....amma,ina zuwa" Musaddiq ya fadi yana yanke kiran,sai ya zura flip flops dinsa yana fita a dakin.

Kacibus sukayi da saddiq wanda ya fasa wankan shima ya zura tasa rigar.

"Ko wani dakin ta shiga bacci ya dauketa" Saddiq din ya fada shima yana jin haka siddan tsoro yana kamashi.

"Haka nake tunani"

"Muje cikin gidan" Saddiq ya fada yana yin gaba musaddiq da yakejin kaman an sabule masa gwiwoyinsa ya bishi a baya.

Harabar gidan ba kowa don kowa ya gaji ya wuce makwancinsa,baqi suna can shiyyarsu a bangaren baqi na gidan,a haka suka kutsa sassan anni.

"Kira anni kice ta sauko" Saddiq yace da badawiyya me aikinta,ta amsa da to. Harta fara haurawa saddiq ya dakatar da ita yace ta dawo sai ya haura da kansa.

Ya samu annin tana cire dankunnayenta da sarqa,saita juyo da mamakin ganinsa a irin wannan lokacin tana kallonsa.

"Ya akayi saddiq?"

"Amna fa bata wajen huda anni,kota gaya miki tana wani gurin?,dakunan wajen nan kuma mun duba kafin mu shigo,wayoyinta switched off". Yankewa gaban anni yayi ya fadi,hannuwanta data miqa kunne don cire dan kunnenta sai taji sun mata nauyi dole ta ajesu tana dubansa.

"Kun gama duba gidan nan gaba daya?". Kai ya girgiza.

"Kusan ko ina dai anni" Hannu kawai ta miqa ta dauki mayafinta ta yafa tana cewa.

"Muje". Tare suka sauko dashi,ta dubi musaddiq.

"Qarfe nawa ta kiraka kira na qarshe?".

"Takwas da rabi anni mukayi waya,tace zataje gidan BB nace ta bari if possible zan dauketa na kaita taga gida mu dawo....idan bai samu ba tayi haquri,na saka wayar charge saida muka gama komai na koma daki na samu miscal dinta me yawa,na kira kuma wayar a kashe take". Wani abune ya tsargawa anni,a jikinta kawai taji wani baqon abu yana shirin faruwa,don amna bata taba irin wannan ba. Koda garden na gidan zata shiga saita gaya ma anni ballanta ace ta fita ko tayi nisa da gida irin haka.

"Kiramin duk masu aikin gidannan" Anni ta buqata tana duban badawiyya. Da sassarfa ta juya,ba jimawa sai gasu kafataninsu,annin ta leqa daga qofar falon ta gaya musu,matan su bincike cikin gidan,mazan kuma wajen gidan dama kewayensa,saita koma cikin falon ta zauna kawai tana jin qafafuwanta suna dab da gagara daukarta.

Kimanin mintuna biyar matan suka dawo,saidai kowacce abinda take gaya mata shine.

"Bamu ganta ba"

"Ba kowa a dakunan"

"Bata nan". Shuru kawai annin tayi tana jan hasbunallahu wa ni'imal wakil tana dakon dawowar mazan.

Jimawa kadan suka kammala nasu duban suma,har zuwa qofar gidan. Kasa tashi annin tayi,don haka tace musu su shigo parlor din kawai.

" Mun duba duk inda ya dace ace mun duba din,tun daga cikin gidan nan har street din daga farkonsa har qarshe amma bamu sameta ba,bamu samu kuma komai nata ba"

"Innalillahi wa'inna ilaihi raji'un,hasbunallahu wa ni'imal wakil" Anni ta fada tana runtse idanunta,fargaba tana kamata.

Gaba daya rasa abun yi tayi,hakanan kuma ta rasa abun fada kwata kwata,kwanyarta ta daure tamau kamar bata tunani me kyau ba tunda take.

Fu'ad da farouq dukkaninsu suna gidajensu da matayensu,abba kuma baya nan,a yadda sukayi magana a safiyar gobe qarfe takwas zuwa tara jirginsu zai sauka. Kai ta girgiza,ba wanda zata bari ya sani a cikinsu,ba wanda zata dagawa hankali.

"Anni ko su yaa fu'ad za'a kira?" Saddiq da tuni hankalinsa yayi qololuwar tashi ya fada. Kai ta girgiza tana miqewa.

"Ban yarda ku gayawa kowa komai ba a darennan,don ba abinda hakan zai amfanar saidai ku daga musu hankali,bayan koda sunzo ba zasu yanke abun yanzu yanzu ba,sai wanda ya qaddara faruwar hakan ya qaddara warwarewar lamarin...." Ta fada cike da tauhidi da qarfafa imaninta,duk kuwa da cewa ita kadai tasan abinda takeji.

"Kuje kuci gaba da kula da aikinku....kuma ku wuce zuwa safiya ko asuba muga abinda Allah zaiyi" Annin ta fada tana duban kowa.

Kowa din ya juya ya fice,amma banda musaddiq dake qame a wajen,tamkar ma baisan abinda yake faruwa ba.

"Musaddiq" Anni ta kirashi cikin dakiya. Kansa kawai ya daga ya kalli annin,don yasan baida sautin da zai iya amsa mata.

"Kayi haquri kaje ka kwanta"

"Kwanciya anni?" Ya tambayeta kaman baya fahimtar hausa.

"Ta yaya zan iya kwanciya bansan halin da take ciki ba?,anni ina aka kaita?,waye ya dauketa?,me tayi musu?,me sukeso?,amna ce fa?.....kwata kwata shekararta nawa?,waye ta tsarewa wani abu?" A nutse anni ke karantarsa,ta fahimci kaman abun yanason fin qarfin kwanyarshi ne,don haka ta kira saddiq.

"Ko baka kwanta ba kaje kayi addu'a musaddiq mu barwa wayewar gari" Tsam.ya miqe ba tare daya kalli koda saddiq dake jiransa ya tashi su tafi ba.

"Ina zaka?" Saddiq ya zaburo yana tambayarsa gami da shan gabansa.

"Zan fita nemanta ne,tunda kai baka damu da ita ba" Ya fada da alamun tashin hankali muraran akan fuskar sa. Kai saddiq ya girgiza

"Akwai hadari a fitarka musaddiq,tunda ko su waye sukayi hakan bamu sansu ba,bamusan dalilin daya sanya suka aikata hakan ba,bamusan kuma meye manufarsu ko target dinsu ba".

"Ko report sai naje na shigar,ba zasu dauke mana mutum.sukutum da guda mu kulle qofofinmu mu kama bacci ba kaman kaza suka dauka" Anni ta fahimci da gaske abun ya soma haurawa tunaninsa ne,don haka ta tako gabansa tana kiran sunansa.

"Kanason jefa amna a hadari bayan wanda take ciki?" Kai ya girgiza da qarfi.

"Yayi....to kada ka soma wani motsi ko aikata komai har sai munji daga bakin yayyenku.....qila fitar da zancan shine zai zama namu kuskuren.....kayita karanta ya hayyu ya qayyumu birahmatika astagis". Kafin ta dire ya kama,a hankali sai yaji hankalinsa yana daidaita,ya miqa hannu ya kama hannun saddiq da kanshi yana cewa

"Muje".

A parlor dinsu ya zaunar da saddiq shima ya zauna yana matsowa dab dashi,ya kalli saddiq din sosai muryarsa tana Rawa

"Saddiq tsoro nakeji su waye?,tsoro nakeji karsu cutar da ita,saddiq munaji muna gani a hannunsu zata kwana?,wanne irin gurin kwanciya zasu bata?" Wanne kalan ruwa da abinci zasu bata?" Sosai saddiq ya riqe hannunsa yana fadin.

"Kayita maimaita fadin ha hayyu ya qayyumu din kamar yadda anni tace......bamu zalunci kowa ba in sha Allah ba wanda Allah zai dorashi a kanmu".

Sun jima yana riritar musaddiq kafin ya samo nutsuwarsa 'yar kadan,saidai ko cikakken zama ya kasa bare ayi maganan kwanciya,kai kawo.kawai yake tsakanin qofa window zuwa farfajiyar gidan,yana jin kamar ya zura da gudu ya tafi neman amanansa.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862



𝐃 𝐔 𝐍 𝐈 𝐘 𝐀 𝐓 𝐀
_Zafafabiyar_

ΜΆBΜΆOΜΆOΜΆK ΜΆ2

β±§Ι„β‚²Ι„β‚₯β‚³

π™‹π˜Όπ™‚π™€ 143


*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*


*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*


*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*

*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*

*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*

*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*

*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*

*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*

*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*

*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*

*_HAIHUWA KIKAYI?_*

*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*

*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*

_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_

08104553105
08127084190

*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*


*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*




143


β˜…A nutse ya shafa addu'a daga sallar asubar da suka idar shida fanna din tasa,koda bai kalli madubi ba yana iya jin yadda qwayar idanunsa suka tasa,wanda bana komai bane saina kukan farinciki daya dinga yi a daren jiya. Yaso yayi haquri ya kauda kai saboda walimar da za'a gudanar a yau,amma inaaaa.......ya gaza jurewar,har sai da yakai ga inda zuciya ruhi da gangar jiki suke muradi.

Juyowa yayi gaba daya gareta,tana zaune a takure,kanta a qasa tana duban yatsun hannuwanta.

Ita dinma fuskarta duk ta tasa,saboda kusan tare akayi kukan,tana yi yana tayata. Idanu ya lumshe ya budesu yana jin nishadi yana saukar masa. Kullum cikin zulumin yadda zai taddata yake,saboda ya sare da halayen 'yammatam yanzun duk da cewa yana da cikakken yarda da dabi'unta,to amma wani lokaci abun ba'a kama bane ko siffa.

"Taho nan flower" Ya fada da sassanyan muryarsa yana miqa mata hannunshi. Bata wani musa ba ta miqa masa nata,don tana buqatar inda zata jingina taji dadin zaman.

Jawota yayi zuwa jikinsa yana rungumeta tsam,yana jin wata shaquwa tana tsaga jikkunansu,yana jin kamar ta tabbata a rungume a jikinsa kaman haka.

Qoqarin gaidashi takeyi,ya amsa mata yana shafa kanta ya amsa cikin kulawa. Sosai ya dinga jero mata addu'o'i,kanta a qasa tana amsa masa da matuqar alkunya. Mintuna kusan goma sha biyar suka debe a haka kafin ya gyara mata zamanta,ya ciro alqur'ani guda biyu ya bata daya ya dauki daya.

"Ko na minti biyar ne flower,saboda mu bude wunin rayuwarmu na farko da neman albarka". Ya fadi yana miqa mata. Rainon anni ne wannan ta saba musu da farawa da qur'ani,kaman yadda yasan itama fannah din 'yar gado ce wajen iya sarrafa harshe a qur'ani.
(Ina kira a gareku iyaye,kiyi qoqari a mazauninki na uwa ki wadata kwanya da harshen 'ya'yanki da qur'ani,su zama gwanaye wajen karanceshi daga bango zuwa bango,idan da hali suna karantawa suna fahimtar ma'anar,saboda hakan yana taimakawa wajen zaunar dashi a kansu yana kuma taimakawa wajen sake jin asalin gard'insa da dadinsa. Allah ya sani ina mamaki naga babban mutum babbar mace ko sangamemiyar buduwa musulma,amma ba zata iya karance miki qur'ani daga bango zuwa bango ba,ko ba zata iya biya miki wani adadi me yawa ba,don kwanyar da aka horata da qur'ani zaka sameta da kaifin basira da fikira me tarin yawa,Allah ya bamu ikon tarbiyyantar da yaranmu akan hakan,ya shirya mana zuria kafatanin musulmi Allahumma ameen).

Suna kammalawa kira yana shigowa wayar tasa. Fannah ce ta miqo masa da hannu biyu ya karba yana murmushi

"Allah yayi miki albarka" Saidai sunan daya gani mamaki ya kamashi,baiyi zatonma zaa kirashi da safe

95 / 119