Author : Maryam Category : Complete Novels
faruwa tana tsaye tana gani, babu tsoro ko nadama a cikin idanunta hasalima wallahi taso abin yafi haka.
Baba lami a cell ta kwana ga dukan data sha gurin Asabe dilalliya, Kuluwa daga nan suka nufi gidan mai gari yana zaune da mutane ana fadanci.
Ta zube ta kwashi gaisuwa sannan ta fashe da kuka.
Mai ne Kuluwa zata yi gurin mai gari??
Yawan likes yawan typing, bana yin update ranar juma'a, amman idan kuka yi likes zaku samu ko babu yawa.*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaBJBOr8vd1H4qb9rd1a
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/EEiLcD9ZnpbFRLSjSOZozT
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
(Ta Batulu)
Chapter 7️⃣
Juyin duniya Kuluwa taƙi magana mai gari ya sallami ƴan fada akan su bashi guri, ta gyara zama ta ce.
"Ranka ya daɗe daman wani abu na gani wanda hankalina ya tashi, kuma naji ba zan iya shiru ba sai na faɗa maka."
Mai gari ya gyara zama Kuluwa ta harari Ummi data zuba mata ido.
"Munje hospital bani da lafiya, a can naga Sa'ida taje zubar da ciki." Kuluwa ta faɗa babu tsoro ko shakka a cikin idanunta.
Mai gari ya fara salati yana sallalami.
"Idan baka yarda ba zaka iya zuwa da ita hospital a duba ta." Kuluwa ta faɗa tana miƙewa.
"Idan kuma nayi binciken na gano ƙarya ne.?" Mai gari ya faɗa.
"Ka yanke mun hukuncin da kaga ya dace dani." Kuluwa ta faɗa tana yin gaba Ummi na take mata baya.
"Ummi zo muje kasuwa." Kuluwa ta faɗa tana sanja hanya, sun kusa kaiwa ta tsaya.
"Kakus bata nan kuma, ina jin cin kaza dan haka muje gida."
Suka nufa gida a hanya taga mai siyar da kayan miya, ta ce.
"Tattasai da albasa na ɗari biyu."
Ya bata sannan ta karɓa tayi gaba tana faɗin.
"Zan biyaka idan na samu kuɗin da ba zan yi amfani dasu ba."
Gab da za su shiga gida ta tsaya gurin mai shagon unguwarsu ta sai maggi na ɗari biyu, tayi gaba tana cewa.
"Zan rubuta sunan ka a cikin littafina koda na mutu, karka bari a fita da gawata sai an biyaka kuɗinka."
Gida ta shiga ta duba inda Kaka take ajiye makulli, ta buɗe ɗaki sannan ta kamo kaza babban ciki.
Ta kalli Ummi ta ce.
"Danne mun kanta." Ummi ta danne kan kaza.
"Yanzu sai ki faɗa mun addu'ar da ake yi idan za yanka kaza." Kuluwa ta faɗa tana ɗaura wuƙa a wuyan kazar.
"Nawaitu zabri yanka." Ummi ta faɗa Kuluwa ta yanka kaza har sai da kai ya kusa fita, bayan ta mutu suka ajiye a gefe aka kunna wuta.
An fige kaza an dafa sai tashin ƙamshi gidan yake yi, an gama Kuluwa ta ce.
"Babu mangyaɗar suya."
"Kaza a haka tafi daɗi." Ummi ta faɗa suka raba kaza biyu, Kuluwa ta ɓoye rabin ɗayan kuma suka ci.
Bayan sun gama suka gyara gurin suka zubar da gashin kazar, suka gyara gidan harda saka turaren wuta.
Suka zauna suna fira Ummi take bata labarin saurayinta Nazeer, ranar kam Kuluwa ba a ƙara fita ba ta kwaso kayan makaranta suka wanke, suka goge gobe Monday akwai zuwa school.
Kaka ta dawo tayi farin cikin ganinsu a natse, suka ta yata girki bayan an gama suka ci abinci suka ƙoshi, sannan Kuluwa ta raka Ummi gida.
Bayan sunje gidan Ummi ta rako Kuluwa gida, haka suk ringa yi idan Kuluwa ta raka Ummi sai itama ta rakota, Kaka ganin abin yaƙi ƙarewa ta kori Ummi gida.
Kuluwa da wuri ta kwanta bacci domin tana san tayi sammako, zuwa gidan Mallam tayi kallo daga nan sai ta wuce school.
A ranar mai nama yazo karɓan kuɗi sabon tashin hankali, Baba lami ta rufe ido ta zageshi tass kuma ta yi rantsuwa ba zata biya kuɗin ba.
Mallam ya tambayi mai nama abinda ya faru, ya bashi labarin yanda suka yi da Kuluwa Mama tayi saurin fitowa har zani yana neman faɗuwa ta ce.
"Tabbas ɗazun ta aiki Kuluwa siyo nama, wallahi nima shaidace."
I'm sorry uzri ya riƙeni yau kuma nayi alƙawarin update.*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/EEiLcD9ZnpbFRLSjSOZozT
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaBJBOr8vd1H4qb9rd1a
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
Allahumma Salli Ala Sayyadina Muhammad Wassalim.
Written by ✍️
Jagabar Jajirtattu
(Ta Batulu)
Chapter 8️⃣
Da asuba ta shirya ta saka uniform sannan ta ɗau Qur'ani ta nufi hadda yau bata tsokani kowa ba, ta bayar da karatu sannan aka ƙara musu wani gab da za a tashi aljannun wata suka tashi, sanadiyar dukanta da wani mallami ya yi akai.
Duka ta ringa kaiwa duk wanda ya matsa kusa da ita, a hankali ƴan ajin suka fara bigewa abin yafi ƙarfin mallamai, duk wannan abin Hajiyar Allah bata motsa ba, tana zaune ta duƙar da kai kamar bata cikin ajin, mai aljannu ta zabgawa Kuluwa mari ta riƙo hijjab ɗinta har Qur'ani na neman faɗuwa.
Kuluwa ta fasa ihu ta fara fari da ido ta haye ruwan cikinta, ta ringa kai mata duka tun aljannu suna nan har suka gudu yarinya ta ringa kuka, tana faɗin a taimaka mata amman Kuluwa jibgarta take yi kamar ta samu jaka.
Da ƙyar aka ɗaga Kuluwa a kan yarinyar mutane, ta ƙwace Qur'anin ta tayi waje bata jira an tashi ba.
Yau ko sallama ba tayi ba Kaka ta ganta kamar daga sama, tana shirin magana ta wuce zuwa bedroom kaya ta loda a jikinta guda huɗu, sannan ta ɗaura uniform a saman kayan ta ɗau jakan makaranta.
Kaka ta shigo ta kalli fuskanta gabanta ya faɗi, domin idan har ta ganta a wannan ya nayin bata barinta fita ko ina, domin wallahi tana fita sai an kawo mata ƙara sama da biyar.
"Kulun majadun waya taɓa mun ke." Kaka ta faɗa tana shigowa.
Kuluwa ta raɓa zata wuce Kaka ta riƙo ta, juyin duniya taƙi sakin hannunta.
"Tun da so kike in faɗi in mutu shike nan jeki." Kaka ta faɗa tana sakin hannunta.
Kuluwa jikinta ya yi sanyi ta kalli Kaka, hawaye ya zubo mata, domin ta tsani taji Kaka ta ce zata mutu.
"Kaka marina fa akayi, kamar ni za a mara."
Koma waye wannan mai ƙaddarar na tausaya mishi da masifar Kuluwa, Kaka tayi zan cen a cikin zuciyar ta.
Kaka ta rarrashi Kuluwa tayi breakfast sannan ta bata labarin abinda ya faru a hadda.
Kaka ta rarrashi Kuluwa sannan ta faɗa mata ai ta rama marin, amman ita bata yarda ta rama ba.
Kuma tayi alƙawarin sai ta yiwa yarinyar mugun duka, duk yanda Kaka tayi da ita amman bata haƙura ba.
Ta ɗauko madubi ta yi kwalliya harda lipgloss red, fuska yasha powder.
Kaka ta bata hamsin Kuluwa ta ce.
"Daga yau na yanke miki bayar da kuɗin makaranta, Mallam zai rinƙa biya."
"To ki amsa wannan domin kin makara yanzu." Kaka ta faɗa tana miƙa mata kuɗin.
Kuluwa ta amsa ta fita bayan tayi addu'o'i, yau babu tsokana gidansu Ummi ta nufa.
Matar baban su tana zaune tana danna waya Ummi na wanke wanke.
Kuluwa bata kalli kowa ba ta cewa Ummi.
"Mallama shirya mu tafi makaranta."
Ummi ta miƙe ta shiga ɗakinta, bata jima ba ta fito sanye da uniform suka nufi ƙofar gida.
Hassana ta miƙe ta tare ƙofa cike da ɓacin rai ta ce.
"Wallahi babu inda za taje sai ta gama wanke wanken nan."
Kuluwa ta raɓa zata wuce Hassana ta riƙo ta.
"Ummi wuce ki jirani a waje gani nan zuwa." Kuluwa ta faɗa tana miƙa mata jakan makarantar ta.
Ummi ta wuce Kuluwa ta dawo da kallanta gurin Hassana, ta kwashe da dariya ta karkace ido ta mayar da bakinta gefe ɗaya, ta shanye ƙafarta guda ɗaya hannun ma haka, sannan ta nuna Hassana ta maƙale murya kamar na kutare ta ce.
"Kin yi babban kuskuren da kike hana Ummi zuwa makaranta, kuma daga yau ba zaki ƙara tafiya ba."
Hassana gabanta ya faɗi ta ƙara kallan yanda lokaci ɗaya halittar Kuluwa ta sauya.
"Dan Allah dan Annabi ki yi haƙuri wallahi ba zan ƙara ba." Hassana ta faɗa jikinta yana rawa.
Kuluwa ta daka mata tsawa ta ce.
"Karƙi ƙara kirana mace, sunana Ƙudus sarkin kutaren duniya."
Hassana ta nemi hanyar gudu, amman jin abinda Kuluwa ta faɗa ya dakatar da ita.
"Kina shiga ɗakin nan ba zaki ƙara tafiya ba har abada."
Hassana ta ƙame guri ɗaya.
"Zan gindaya miki sharaɗi, kuma idan kina san zaman lafiya dole ki yi biyayya, ko kuma na mayar dake duniyar mu."
"Wallahi zan yi biyayya duk abinda ka ce Baban mu." Hassana ta faɗa tana share hawaye.
"Daga yau duk aikin gidan nan ke zaki rinƙa yi, sannan kuma idan kika ƙara hora Ummi da yunwa daga rana irin ta yau kin yi bankwana da wannan duniyar." Kuluwa ta faɗa tana zagaye gidan.
Kuma idan kaga Kuluwa zaka ɗauka naƙasashiyar gaske ce. 😂
"Kuma duk lokacin da kika ga tayi ba dai dai ba ki tsawatar mata a matsayin ki na uwa." Kuluwa ta faɗa tana nannaɗe jikinta, daman gata siririya.
Hassana dai hawaye yaƙi tsayuwa.
"Idan mahaifinta ya ƙara yin mata wani abin kika riƙe." Kafin Kuluwa ta rufe baki Hassana ta katse ta.
"Wallahi ba zan ƙara komai ba dan Allah ayi mun afuwa."
"Zamu tafi kasar mu dan haka, a bamu kuɗin shan ruwa a hanya." Kuluwa ta faɗa tana gwallo idanunta.
Kuluwa ta tabbatar da idanunta yana razana mutane, shi ya sa take zaro su idan tana neman tsokana.
Kuɗi da yawa Hassana ta ɗauko Kuluwa ta zari dubu biyar, ta watsa mata sauran.
"Idan kika gayawa wani abin da ya faru, daga nan ki fara shirin tawowa duniyar kutare."
Hassana ta rufe bakinta.
"Bani guri ga ƴan masarauta na nan sun zo."
Da rarrafe ta shiga ɗaki ta kulle Kuluwa ta daka tsalle ta bar gidan.
Ummi tana zaune tayi tagumi.
Suka tafi makaranta, a hanya Kuluwa ta siyawa Ummi doyan ɗari biyar da ruwa.
Suna zuwa bakin makarantar suka samu an tare makara, Ummi ta miƙa hannunta aka yi mata bulala goma, sannan ta ƙara miƙa ɗayan hannun a yi mata na Kuluwa.
Mallam Usman ya daka mata tsawa ya ce.
"Wallahi ko mutuwa za tayi, yau sai na zaneta."
"Mallam daga duka sai mutuwa." Kuluwa ta faɗa tana miƙa mishi hannunta.
Ya daketa sannan ya ce ta share jan bakin data saka a lips ɗinta.
Kuluwa ta matsa gefe shi kuma yaci gaba da tare makara, ta duƙa ta share a jikin rigan shi kuma rigan fari ne.
Ta samu ƙasan rigar tayi mishi kiss kuma ya fito sosai, sannan ta share raguwan jan bakin a hijjab ɗinta.
Suna shiga makarantar, taga ƴan ajinsu gaba ɗaya suna tsaye a cikin rana.
Tayi kamar bata gansu ba zata shige taji an fincikota ta baya.
Yau nayi typing da yawa, sauran likes da yawa.*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/EEiLcD9ZnpbFRLSjSOZozT
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaBJBOr8vd1H4qb9rd1a
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
Allahumma Salli Ala Sayyadina Muhammad Wassalim
Written by ✍️
*Jagabar Jajirtattu*
(Ta Batulu)
Chapter 9️⃣
Kuluwa ta juyo suka haɗa ido da mallama Ikilima ta ce.
"Gidan uban wa za kije, ko baki gansu bane a can." Kuluwa ta kalli gurin sannan ta kama hannun Ummi suka nufi gurin.
Ta nemi gurin zama ƴan group, suka kewayeta suna bata labarin abinda ya faru tayi murmushi ta miƙawa Ummi doyan ta ce.
"Ki yi maza ki ci kafin mallaman su zo."
Ummi ta amsa tayi musu bismillah suka ɗau guda ɗai ɗai, wasu kuma suka ce alhamdulillahi, Ummi ta kalli Kuluwa ta ce.
"Ba zaki ci ba.?"
"Idan zan ci ai ba zan baki ba, dallah mallama ki yi sauri." Kuluwa ta faɗa tana hararan ta.
Ummi ta cinye doyar tasha ruwa, Kuluwa ta kallesu gaba ɗaya sannan ta ce.
"Na san maganar Nazifi ne, wanda muka yiwa jifan shaiɗan."
Suka amsa gaba ɗaya.
"Ni dai yau bana ƙaunar hayaniyya dan haka, ku nemowa kan ku mafita." Kuluwa ta faɗa tana miƙewa.
Gaba ɗaya suka bita a baya ɗaya bayan ɗaya, kuma babu mallamin da ya gansu har suka fice.
Sun yi tafiya mai tsawo kafin su tsaya a bakin lambu, Kuluwa ta leƙa ciki sannan ta shiga bishiya ta haye kamar ƙadangare ta fara jefo mangwaro inibi da sauran kayan marmari, komai akwai na kayan marmari Kuluwa har tsalle takeyi zuwa bishiyar kusa da ita.
Tana shirin saukowa ta hango mai lambu yana tawowa.
"Kowa tashi ta fishe shi." Kuluwa ta faɗa tana dira daga bishiyar, ai tana rufe baki suka watse Kuluwa ta ɗaga murya tana cewa.
"Wallahi idan kuka bari ya kama ku to kamar damisa ne ya samu nama." Suka ƙara gudu mai lambu yana biye dasu, shi da wasu mutane guda uku kamar samudawa.
Ganin an kusa cin musu Kuluwa ta ce.
"Bibbiyu ta cikin window."
Suka rabe kowa bibbiyu Ummi da Kuluwa suna tare, kayan yana hannunta.
Sai da suka tsere musu sannan Kuluwa ta ciro riga ɗaya daga cikin rigar jikinta, ta zuba kayan marmarin ta haƙa rami ta ɓoye daga nan suka nufi makaranta.
Sai da suka leƙa ta window suka tabbatar babu mallami sannan suka haura, a hankali sauran suka ringa shigowa ta window su goma.
Mallam Usman ya shigo cike da mamaki yake kallan tawagar Kuluwa, domin ɗazun an yi ta cigiyarsu amman ba a gansu ba.
Ya umarci Kuluwa ta fito ta tsaya gaban allo, ta tsaya ta ɗaure fuska suka haɗa ido da Nazifi tayi murmushi ta kau da kai.
"Daga ina kuke.?" Mallam Usman ya faɗa yana rubutu a saman allo.
"Babu inda muka je." Kuluwa ta faɗa tana hararan ƴan ajin, ganin sun zuba mata ido.
"Kun gansu a cikin ajin nan tun ɗazun.?" Ya tambayi ƴan ajin, suka amsa da eh.
Mallam Usman ya dakata da rubutu yana ƙare musu kallo, yana mamakin yanda suke jin tsoran ƙaramar yarinya, amman yau duk sai ya yi maganinsu.
"Kowa ya miƙe tsaye ya ɗaga hannu sama." Mallam Usman ya faɗa yana zama a kujeran zaman mallamai.
Kowa ya miƙe ya ɗaga hannu mallamin ya ce.
"Kowa ya rufe ido." Ya faɗa ba tare da ya kallesu ba.
"Wannan ai iskanci ne." Kuluwa ta faɗa ƙasa ƙasa, amman sai da yaji abinda ta faɗa.
Ta shige tsakiyar ɗalibai ta zauna ganin haka ya yi saurin cewa.
"Maza dawo ki zauna a farko." Kuluwa ta fito tana hararan shi.
Sai da suka yi tsayuwar awa ɗaya sannan ya ce zu zauna.
Mallaman makarantar suka shigo gaba ɗaya harda shugaban makaranta.
Suka umarci Nazifi ya fito ya tsaya gaban allo, ya fito hannu maƙale da igiyi an naɗe ta wuya.
Shugaban makaranta ya ce.
"Duk wanda ya san yana ɗaya daga cikin masu jifan Nazifi ya fito gaban allo."
Kowa ya yi shiru babu wanda ya fito juyin duniya sunƙi fitowa kuma ya tambayi ƴan ajin sun yi shiru.
Nazifi ya ce.
"Ranka ya daɗe na yafe musu."
"Ko ka yafe musu dole ne makaranta ta hukunta su." Mallam Usman ya faɗa.
Sallama suka ji a bakin aji, mai lambu ya shigo suka gaisa sanna ya ce.
"A cikin ɗaliban wannan makarantar an samu wa inda suka yi mun ɓarna, bayan kun yi mun alƙawarin babu wanda zai ƙara shiga mun lambu."
Shugaban makaranta ya dafe kai ya kalli Mallaman gaba ɗaya ya ce.
"Ku sameni a officer." Ya fita mallaman suka bishi a baya.
Mallama Ikilima ta cewa Mallam Usman.
"Da alama yau madam bata so fitowar ka ba."
"Banganeba.?" Mallam Usman ya faɗa cike da mamaki.
Mallama Ikilima tayi shiru suka ƙarasa officer ɗin shugaban makaranta.
Ɗaya daga cikin Mallaman makarantar ya janyo Mallam Usman gefe ya ce.
"Ka duba ƙasan riganka."
Cike da kunya da mamaki yake kallan ƙasan rigar, wato wannan dalilin ne yasa Mallama Ikilima tayi mishi magana ɗazun, kuma ya san wannan aikin Kuluwa ne lallai ta ɗibo ruwan dafa kanta, wallahi yau sai ya sauke mata abin da yake kanta.
Ya kama ƙasan rigar ya riƙe suka zauna aka tattauna akan yanda za a ɓullowa lamarin, bayan sun samu mafita suka kira mai lambu suka bashi haƙuri, kuma sun tabbatar mishi wannan shi ne na ƙarshe.
Bayan fitan mallamai ƴan group suka haɗe kai Kuluwa ta ce.
"Wallahi yau makarantar nan akwai ƙura, dan haka kuzo kuji mafita."
Suka haɗe kai baka jin abin da suke cewa, sai da suka gama tattaunawa sannan Kuluwa ta miƙe ta kalli ƴan ajin gaba ɗaya ta ce.
"Kowa ya san yau babu mai ƙwatar mu a cikin makarantar nan, dan haka ina da shawara." Kuluwa ta cigaba da magana.
"Duk wanda yake tare dani yazo kusa dani, kamar wasa gaba ɗaya ajin suka miƙe duk yawan su.
Mazan suna zaune suna jin daɗin yau za a yi musu maganin Kuluwa.
Kuluwa ta fita waje suka bita, sun jima kafin su shigo suna dariya kowa ta nemi gurin zama.
Mallaman makarantar gaba ɗaya suka dawo cikin ajin, Kuluwa tana hangosu ta ce.
"Kowa ya shirya."
Mallaman na shigowa cikin ajin.
Ta Batulu ce.........✍️*KULUWA*
*(Ƴar bala'i)*
Group 👇
https://chat.whatsapp.com/EEiLcD9ZnpbFRLSjSOZozT
Channel 👇
https://whatsapp.com/channel/0029VaBJBOr8vd1H4qb9rd1a
*JAJIRTATTU WRITER'S ASSOCIATION*
Written by ✍️
Sa'adatu Ta Batulu
Chapter 1️⃣0️⃣
Ɗaliban duka suka miƙe shugaban makaranta ya ce.
"Hukuncin da muka yanke muku, shine kamar haka gyaran toilets ɗin makaranta na wata ɗaya, sannan sharan ajujuwan makaranta gaba ɗaya zuba ruwa a roban toilet na wata ɗaya."
"Ka ce gidan yari aka kawo mu." Kuluwa ta faɗa tana ƙarshen aji.
Duk da cewar sun ji abin da ta faɗa amman basu kulata ba, Kuluwa ta ɓuya cikin ƴan aji ta fara kukan jariri idan tayi kukan jariri sai tayi na kare.
Tun Mallamai basu lura da abin da yake faruwa ba har suka fahimta, Kuluwa ta nannaɗe jikinta kamar ƙadangare ta fara rarrafe, ƴan aji suka fara watsewa fuskanta yasha baƙin kwalli tako ina, gurnani ta fara tana bin ƴan ajin idan tabi wannan sai tabi wan can, ɗalibai suka fara fita ajin wasu ta window suke dira ganin Kuluwa ta nufo gurin Mallamai shugaban makaranta ya fita yana cewa.
"Ku riƙe ta."
Ɗaya bayan ɗaya Mallaman suka