Advertisements
Chapter 190 Reading Abban Sojoji Takun Karshe complete by Boss Bature BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Abban Sojoji Takun Karshe complete by Boss Bature

Author :  Boss Bature Category :  Complete Novels

Chapter   190 / 231

567K to 570K   out of 690.9K words

atare suka haɗa baki wurin cewa"mun fi ƙarfinsu,kai ke buƙatarsu kai daga ganin mu kasancewa ba matsiyata bane,"
"Wow," ya furta yana tafa hannunshi "abu yayi kyau ƴa'ƴan billionaire,karfa kuce zaku gayamin magana!ku fuce mun daga ɗaki cikin salama,"
Jahan yace"ba sai ka kore mu ba, mukan mu aƙagare muke da mu fita mubar maka wannan ƙazamin ɗakin naka wanda ko numfashi mutun daƙyar yake iya fitarwa!!kuma inaso ka sani Haroon baka ci bulus ba, zamu rama duk wani wulaƙancin da kayi mana!!
yana kai ƙarshen maganar tashi ya ruƙe hannun ayaan suka juya zasu fita daga ɗakin karaf idonsu ya sauka akan mutumin dake shigowa cikin ɗakin, A wani irin firgice suka ja da baya gaba ɗayansu, shi kanshi Haroon ya sha jinin jikin shi saboda basu son da mutun ba, gaba ɗaya duk abunda suka tattauna acikin kunnanshi kaf ya gama naɗar komai,
hankali tashe suke kallon shi,kamar yarda shima hankali atashe yake kallon su



Follow my tiktok acct 👇
https://www.tiktok.com/@boss_bature?_t=8WKx0lm4jaP&_r=1

Atare suka sauke ajiyar zuciya lokacin da suka shaida cewa junaid ne,sai faman murza idanunshi yake yi da hannunshi,da alama magagin bacci ne ya shigo dashi,hakan ya basu tabbacin ba lallai in ya fahimci komae ba,
    cikin sauri Jahan yace"junaid tun yaushe kake anan?me kake yi har yanzu baka yi bacci ba"?
  Cikin shagwa6a yace"nima bansan ya akai na shigo ba,dan Allah kutaimaka mun ku kaini ɗakin abbanmu in kwanta,wurin shi nake son zuwa,"
 Shu'umin Murmushi haroon yasaki yana kallon shi,
  ganin yarda yake binshi da kallo yasa su twins saurin ruƙe hannun junaid suka fuce dashi daga ɗakin,
    "Ayaan kaje kawai ka kwanta,ni bari nakai shi ɗakin Abban namu,"
Amsa mashi yayi da toh,sannan ya wuce bedroom ɗinsu,
  Shi kuma jahan zuƙunnawa yayi tare da ce mashi"ka hau na goya ka karka faɗi,"
   daddagewa junaid yayi ya haye bayanshi tare da ƙanƙame shi,sannan jahan ya miƙe ɗauke dashi abayansa ya wuce bedroom ɗin Abban nasu,
   A hankali ya tura ƙopar bedroom ɗin Abban nasu,yana kwance sai faman sharar bacci yake yi asaman royal bed ɗinshi,shiga da junaid ciki yayi a hankali ya sauke junaid saman gadon daga gefen abban nasu,
     gyara kwanciya junaid yayi tare da rungumo Abban nasu da hannunshi sannan yace ma Jahan"thank u,"
  murmushi jahan yayi ba ƙaramin burge shi yayi ba,sam junaid bashi da wata damuwa,sai yaji dama shine ke irin rayuwar shi,
   "Sleep well," ya furta tare da juyawa ya fuce daga bedroom ɗin yana sauke ajiyar zuciya,ɗakinsu ya koma lokacin daya shiga a kwance ya samu Ayaan har bacci yayi awon gaba da shi,shima wucewa yayi tare da haurawa saman gadon ya kwanta daga gefenshi,
Yaushe rabon da suyi bacci irin na daren nan harsun manta,saboda fargabar haroon kullum da damuwarshi suke kwana,yau dae sun huta ma rayuwarsu tunda sun sallame shi,

A 6angaren haroon kuwa tun bayan da suka fita ranshi ya raya mashi cewa tabbas akwai alamar tambaya game da zuwan junaid bedroom ɗinshi,saboda tun da yake junaid bai ta6a faɗowa ɗakinshi ba irin haka,duk irin magagin baccin da junaid yake yi bai ta6a zuwa ɗakin shi ba,amma sai yau kwatsam zai faɗo mashi ɗakin shi adai² lokacin da suke tattaunawa dasu twins kuma? Anya ba turo shi akayi ba❓
   zama yayi daga gefen gadon nashi yana tunani,dakyar ya iya tashi yakai hannu ya kinkimi jibgegiyar jakar kuɗin,wuri yayi mata acan cikin ɗakin nashi ya 6oyeta,
   Sannan ya koma tare da hayewa saman gadonshi ya kwanta,

     *********************
Washe gari

A hankali ya buɗe idanunshi da su kayi mashi nauyi saboda bacci,hannu yasa tare da yaye blanket ɗin daya lullu6a dashi,miƙa hannu yayi tare da ɗaukar wayarshi dake ajiye saman bedside drawer dinshi,missed calls ya gani nasu hossana da jahad,tashi yayi daga zaune yana kallon screen ɗin wayar tashi,jiya yaso yaje ya duba su amma bai samu time ba,
   danna musu kira yayi tuni tashi ga ringing,
  A lokacin Jahad ce acikin falon zaune saman 2 seater tana ta jiran kiranshi,hossana kuwa tana can tana sharar bacci,
    har ta fidda ran cewa zai kirasu saiga kiran nashi ya shigo,cikin sauri ta miƙe ta nufi telephone ɗin tasa hannu ta dauka tare da karata a kunnanta,
   Cikin sanyin murya tace"Assalamu Alaikum ya Omar an tashi lafiya,"
  murmushi yasaki tamkar yana agabanta yace"lafiya lou Alhmdlh,nayi laifi ko?jiya banzo na duba ku ba,ayi mun afwa ina busy sosai,amma kuna araina,"
   "Babu komai ya Omar,dama mun damune akan rashin zuwan naka,kuma mun kira wayarka jiya da safe,baka a kusa sai dai matarka Aunty zainab ta ɗaga kiran,"
   "What!matata kuma? Wacece kuma aunty zainab?pls explain to me ni bangane me kike cewa ba,"
   murmushi jahad tayi tare da cewa"Ya omar meyasa ba ka sanar damu cewa kana da aure ba?baka so mu sani ne?
  Sam Omar baisan inda zanjen nata ya dosa ba,
   "Jahad nifa bansan me kike cewa ba! Wacece kuma matata?
  kafin jahad tace wani abu,sai ga hossana ta fito da saurin gaske jikinta sanye da kayan bacci,tana ƙarasowa tasa hannu ta kar6i telephone ɗin tare da karata a kunnanta cikin shagwa6a tace"eh mana ya omar ashe kana da aure,jiya da safe mun kira wayarka,mace ta ɗaga kiran tace mana kai mijinta ne kuma baka a kusa,sannan kuma tace mana tana ɗauke da juna biyu,kuma sunanta zainab amma kana kiranta da Hayaty,"
   tunkan ta ƙarasa maganar Omar yashiga 6a66aka dariya,natsuwa su kayi gaba dayansu suna sauraron sautin dariyarshi,
  "Ya omar kayi shiru baka ce komai ba," muryar hossana ce ta katse mashi dariyar tashi,daƙyar ya tsagaita tare da cewa"Am sorry na fahimci abunda kuke cewa,bazan iya yi maku bayani anan ba,insha Allah bayan na kammala breakfast dina zan shigo sai muyi magana ta fahimta ko?
  Atare suka haɗa baki wurin cewa"Eh muna jiran zuwanka,sannan in ka tashi zuwa kazo mana tare da Hayati ɗinka muganta,"
   murmushi kawai yayi tare da rejecting call ɗin,sai lokacin ya duba kiran nasu da sukayi mashi jiya acikin wayarshi,cike da mamaki yaga kiran da sukayi mashi jiyan da safen kuma already an ɗaga kiran,natsuwa yayi yana tunanin wanene ya daga mashi kira harya tsara wannan ƙaryar,tabbas junaid zai iya yi mashi wannan aikin,. 
  Miƙewa yayi tare da saukowa daga saman gadon nashi,ya wuce cikin toilet dinshi,within 15 mins ya fito ya wuce wurin closet ɗinshi,tsaf ya kammala shiryawa cikin shadda purple colour ba ƙaramin kyau tayi mashi ba yabi jikinshi duka ya feshe shi da turare,
  Bayan ya ɗauki wayar shi ya fito tare da wuce wa part ɗin Rafayet,da sallama ya shiga ciki,baya acikin falon shi don haka ya wuce cikin bedroom ɗin shi,
  Yayi mamakin ganin shi a kwance saman shimfiɗeɗen gadonshi,jikin shi na'a sanye da bathrobe da alama bai jima da fitowa daga wanka ba,
   Shiga ciki omar yayi tare da samun wuri daga gefen gadon ya zauna sannan ya ambaci sunan shi a hankali"Rafayet wai haryanzu bacci kake yi?
   Yamutsa fuska yayi alamar idonshi biyu sannan yace"Omar,yau lalaci nake ji ajikina,duba fa ka gani tun ɗazu nayi wanka amma nagaza tashi in shirya kaina,"
   sakin baki Omar yayi yana kallon shi tare da jinjina kai yace"nasan meye matsalarka,wato har yanzu abun nan bai bar jikinka ba ko?
   "Mekenan"? Sgr ya tambaya yana kallon shi daga kwancen da yake,
   Murmushi Omar yasaki batare da yace komai ba,
   Miƙewa Sgr yayi tare da tashi daga zaune suna fuskantar juna shi da Omar yace"Na fa tuna duk abunda ya faru jiya a tsakanina da yarinyar nan,"!
  "dagaske"? Omar ya faɗi da ɗan mamaki a fuskarshi,
  "yeah,amma bakomai na tuna ba,so nake ka faɗamun gaskiyar abunda ya faru,time ɗin da ka tarar damu asaman gadon nan,shin na cire shorts ɗin jikina ko ban cire ba"?
   tunkan ya ƙarasa maganar omar ya soma sakin dariya,
  Ɗaure fuska sgr yayi tare da cewa"pls Omar banason wasa,just tell me the truth,cos banaso yarinya ta raina ni,"
    tsagaitawa omar yayi sannan ya zayyana mashi dukkan abunda ya faru tsakanin shi da Sehrish,

   hannu sgr yasa tare da dafe forehead ɗinshi yace"OMG!Omar ashe kaine ka katse mun jin daɗina a wannan lokacin!meyasa baka bari na ƙarasa aikina ba"? ya ƙarasa maganar yana jifar shi da harara,
   dariya omar ya kuma yi kafin yace"nifa taimakonka nayi,kisan kai fa zakayi,"
   tsuke fuska yayi tare da cewa"babu wani nan,ni narasa meyasa kake mun haka,"
  Yayi maganar tare da kai hannu ya dauki pillow ya wurga mashi shi a fuskarshi,tarbe pillow ɗin Omar yayi a hannunshi tare da cewa"Am sorry bro,bansan abun yayi hurting ɗinka ba,amma ae ko yanzu bata 6aci ba,kasan inason farin cikin ka,bari natashi naje na kira maka yarinyar sai ka ƙarasa aikin naka,"
  Yana kai ƙarshen maganar tashi ya mike tare da nufar  hanyar fita daga bedroom ɗin  yana  karashe dariyar shi,yana jiyo muryar sgr cike da zolaya yana cewa"Am waiting,"

Kai tsaye bayan Omar ya fito daga sashen sgr down stairs ya sauko tare da fuce wa daga main palour din,ko breakfast din bai tsaya yayi ba ya wuce wurinsu hossana,

Wuraren ƙarfe tara kiran Amrish ya tashe ta daga dogon baccin daya ɗauke ta tun bayan sallar asuba,dakyar ta iya buɗe idanunta da sukayi nauyi saboda bacci,hannu takai tare da daukar wayar dake ajiye asaman side drawer ɗinta,picking call ɗin tayi tare da kara wayar a kunnanta a kasalance tace"Assalamu alaikum Amrish irin wannan kira haka tunda sanyin safiya"?
   daga can 6angaren Amrish tace"Sleeping sickness wai kina nufin har zuwa yanzu baki tashi daga bacci ba?duba time ki gani kusan 9 fa yanzu,"
  Jin haka yasa sehrish sa hannu tare da janye blanket ɗin jikinta ta tashi daga zaune tana kallon clock, ɗan xaro ido tayi tare da cewa"subhanallahi wai har 9 tayi?meyasa aunty azmee bata tashe ni ba,ya ilahi,"
  dariya amrish tayi tare da cewa"kin cika bacci reeshi yakama kije kiga psychiatric doctor ya duba brain ɗinki,"
   ɗaure fuska sehrish tayi kamar tana agabanta tace"oh ashe dama kallon da kike mun kenan ko?
     muryarta cike da dariya tace"no ba haka bane inason lafiyarki ne shiyasa na baki shawarar kije aduba ki,"
   "Okey thanks for ur advise amma fa ni ba inda zanje,da raina da lafiyata bazan kwasa na tafi asibiti ba,salon su ja man bala'e,"
ƙarasa maganar tayi tare da cewa"pls inason zan shiga kitchen yanzu,i wll call u later bye,"
   sallama su kayi da amrish sannan ta mayar da wayar saman side drawer ta ajiyeta,
saukowa tayi daga saman gadon cikin sauri ta wuce cikin toilet, brush tayi tare da wanko fuskarta sannan ta fito ta wuce wurin wardrobe ɗinta,buɗewa tayi tare da ɗauko mayafi ta daure shi akanta kamar ɗan kwali,

Lokacin da fito har azmee ta kammala jera masu breakfast ɗin asaman dining,junaid ta samu tare da fawan zaune suna yin breakfast dinsu,kamar waɗanda yunwa ta koro sai faman turawa suke yi abakinsu suna ci,
   dagowa junaid yayi tare da kallonta nan take ya sakar mata murmushi tare da kiran sunanta"sehrish,"
  Juyowa fawan yayi tare da kallonta yace"ke zo nan,"
  nan da nan taji gabanta ya faɗi dama basu ta6a magana dashi ba,
  jiki asanyaye ta ƙarasa inda suke dai dai kusa dashi sannan ta tsaya tana faman ƴan kame kame,
   cikin sanyin murya yace"jira kike na fara gaishe ki ne"?
  cikin sauri sehrish tace"ina kwana,ka tashi lafiya,"
  fashewa da dariya junaid yayi yana kallonsu,harara fawan ya watsa mashi tare da mayar da idonshi kan sehrish yace"lafiya lou,haka yadace daga yanxu basai nace ki gaishe ni ba,daga zarar kin ganni kiyi hanzarin gaidani amatsayina na yayanki,"
  Murmushi sehrish tayi tare da amsa mashi da"toh,"
    junaid yace"bismillah ki zauna muyi breakfast atare mana," girgiza kai tayi tare da cewa"a'a inaso zan shiga kitchen ne wurin aunty azmee,"
  Amsa mata yayi da"okey,"
  Sannan cikin sauri ta juya tare da nufar kitchen din,
   time din da taƙarasa kitchen ɗin azmee ta kammala gyare kitchen din tsaf, dakyar ta iya cewa"ina kwana aunty azmee,"
   sai lokacin ta lura da ita,murmushi tasakar mata tare da cewa"lafiya lou babyn junaid,sai yanzu kika tashi daga baccin naki?dazu nashiga ɗakin naki na sameki kina bacci,
   ciki sehrish ta shiga tana cewa"Aunty azmee ae da kinsani kin tashe ni,nikaina banasan yawan baccin nan da nake yawan yi,"
  Azmee tace"ai baida amfani atlease yakamata ace duk in kika kammala sallar asuba ki daure kina karanta al'qur'ani, sannan ki dinga yawaita yin azhkar,insha Allah duk wani abu dake damunki Allah zai yaye maki shi,"
  "Insha Allah zan yawaita yinsu kamar yarda kikace,yanzu inaso in kaima babban yaya breakfast ɗinshi,bansani ba ko kin kai mashi,
   Azmee tace"a'a ban kai mashi ba,bari na haɗa maki sai ki kai mashi,"
   Tsayawa sehrish tayi tana jiranta,
  Bayan azmee ta kammala shirya mata breakfast din nashi acikin tray ta miƙa mata,hannu biyu tasa ta kar6a tare da kama hanya ta fuce daga kitchen ɗin,
  Da sallama abakinta tashiga part din nashi,
    har time din bai fito ba,yana acikin bedroom ɗinshi,ƙarasawa ciki tayi tare da ajiye mashi tray din asaman table,sannan ta wuce izuwa bedroom ɗinshi daga bakin kopar ta tsaya tare da maimaita sallamar,
   daga cikin bedroom ɗin tajiyo muryarshi yana cewa"wanene nan"
  tuni tasha jinin jikinta,musamman data tuna abunda ya faru jiya ba ƙaramin tsoro ya bata ba,
   murya na rawa tace"Ni ce,breakfast nakawo maka,"
   "Okey,come in,"
a hankali tasa ƙafa tare da shiga ciki zuciyarta nata faman ɗar ɗar,
  tsayawa tayi daga bakin ƙopan tana kallon shi,har lokacin yana kishingiɗe kamar yarda Omar ya barshi,
   ganin ta tsaya abakin ƙopar yasa shi cewa"lafiya?
   cikin sauri tace"bakomai,"
"Okey shigo ciki,ki fara gyara min toilet ɗina,"
  ƙarasawa ciki tayi a hankali take tafiya tana satar kallon shi,eyes ɗinshi na'a rufe tamkar mai jin bacci,duk wani motsinta acikin kunnanshi yake jinshi,tura ƙopar toilet ɗin tayi tare da shigewa ciki,
   Sai bayan da ta shiga ciki sannan ya buɗe idanun shi tare da bin ƙopar toilet ɗin da kallo,tunawa da abunda ya faru jiya tsakaninsu yayi,mayar da idonshi yayi tare da lumshe su,
   ba da jimawa ba sehrish tafito daga cikin toilet tare da cewa"na kammala gyarawa,saura bedroom din,"
   buɗe idanunshi yayi ba tare da ya kalleta ba yace "okey,ki duba cikin closet ɗina,ki ciro mun kayan da zan sanya,"
  Cike da mamaki ido waje sehrish tace"dani kake"?
  "Ni da waye" ya tambaya a ataƙaice,d'an murmushi tayi tare da wuce wa can ciki wurin wardrobe ɗinshi,mai girma da faɗin gaske gaba ɗaya glass ne ta gabanta,daga waje kana iya hango kayan sawarshi dake aciki gasunan abun kamar a company jeri jeri komai a tsare,tana ɗauke da sliding doors ajikinta,
  Hannu sehrish takai ajikin wardrobe ɗin nan take ƙopar ta zuge da kanta,abun ba ƙaramin burgeta yayi ba,ruwan ido ta tsaya yi tama rasa wanne zata ɗauko mashi,saboda kowanne acikin kayan sawar nashi kyau suke yi mata,wata ƙopar ta zuge anan taga jerin kayan hausawa ta jima tana mamakin ashe yana dasu amma bai ta6a sanyawa ba,hannu tasa tare da ɗauko mashi haɗaɗɗiyar shadda gezna sky blue mai ɗaukar ido,
   ruƙowa tayi a hannunta tare da dawowa wurin gadon Shi a lokacin harya gaji da jiranta ya sauko da ƙafafunshi ƙasa yana ƙoƙarin tashi,jin takon tafiyarta yasa shi ɗagowa yana kallon kayan data ruƙo a hannunta,
  tsayawa tayi dab dashi sannan ta miƙa mashi,
    ƙin kar6a yayi saima nuna mata hanya da yayi tare da cewa"basu nakeso ba,ki canza mun wasu bana sa kalar wannan,"
     Jiki asanyaye sehrish ta koma ta maida shaddar sannan ta ɗauko mashi jeans da t shirt baƙa,
  
  Komawa tayi tare da miƙa mashi,hannu yasa ya kar6a tare da furta"thanks" a gefen shi ya ajiye kayan sannan ya miƙe tare da kai hannu ya zame bathrobe ɗin jikin shi,cikin sauri sehrish tayi hanzarin barin bedroom ɗin takoma daga waje tana faman sauke ajiyar zuciya,ƙiris ya rage sgr ya saki murmushi don ba ƙaramin dariya ta bashi ba,ita duk atunaninta babu shorts ajikinshi shiyasa tayi saurin guduwa daga ɗakin nashi,
  Tsaf ya kammala zura kayan ajikinshi bayan ya gama ya koma gaban dressing mirror ɗinshi tare da kai hannu ya ɗauki kwalbar turarennan nashi shumukh yabi ko'ina na jikinshi ya feshe shi da shi,sannan ya koma wurin shoe rack ɗin shi tare da zaro takalma ya zura a ƙafarshi,
   tana atsaye tana jiran fitowarshi muryarshi ta ratsa kunnanta da cewa"ki shiga ciki ki gyara mun,"
  Sannan ya wuce ta izuwa cikin falon nashi,
   Shiga ciki sehrish tayi anatse ta soma gyara mashi bedroom ɗin nashi,

    **************
A hankali motarsu tashiga cikin gidan abusufyan major ne ke driving ɗinshi yayin da yake zaune a back seat na motar,
  Bayan yayi parking ɗin motar omar ya fito tare da wuce wa ciki,
  Koda yashiga cikin falon samun su yayi azune saman 3seater sun haɗa kai sun kurawa plasma tv ɗin dake manne abango suna kallon tashar bollywood,
   ba ƙaramin burgeshi su kayi ba,gyara muryar yayi tare da yi masu sallama,atare suka dago tare da kallon shi,hossana na ganin shi ta miƙe da gudun gaske ta tunkare shi,dakatar da ita yashiga yi da hannun shi amma ina sai da ta faɗa mashi,sosai ta rumgume shi tare da kwantar da kanta a saman wide chest ɗinshi,lokaci guda yaji wani irin yanayi atattare dashi,
  Jahad kuwa a fusace tace"hossana menene haka wai?ba zaki bari ya ƙaraso ciki ba?
   tamkar bata jita ba,haka ta ƙara ƙanƙame shi tana cewa"ya Omar nayi missing ɗinka sosai,jiya ko isasshen bacci bansamu ba saboda ban saka a idona ba,
  hannu omar yasa tare da janyeta daga jikinshi suna kallon juna ido cikin ido yace"Am sorry pls,amma yanzu ae gashi nan nazo ko?
  daga mashi kai tayi alamar eh,sannan tasanya hannunta cikin nashi suka ƙarasa ciki atare suka zauna kusa da Jahad saman 3 seater ɗin da take,
  Cikin sanyin murya tace"sannu da zuwa ya omar,yasu abba da sauran mutanen gidan,
  Fuskarshi dauke da murmushi yace"yawwa jahad,duk suna lafiya,ina fata kuma nasame ku cikin ƙoshin lafiya,"
  Amsa mashi tayi da eh,sannan tace"namanta ban tambayeka ba,yasu Aunty zainab,"?
   kafin yace wani abu hossana tace"ya Omar wai dagaske kana da aure"?a shagawa6e tayi maganar tamkar zatayi kuka,
   cikin natsuwa ya soma kora masu jawabi"Ni banta6a aure ba,saurayi ne ni,ko budurwa ban ta6a ajiyewa ba,"
  Jahad tace"amma ya Omar wacece ta ɗaga kiran wayarka da mukayi a lokacin?
    shiru ya danyi kafin yace"ina tunanin younger brother ɗina ne Junaid,ya cika zolaya

190 / 231

Chapters