Advertisements
Chapter 46 Reading Hukuncin Allah Book 1 Complete Hausa Novel Hausa Novels
Advertisements

Hukuncin Allah Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Aisha Aliyu Garkuwa Category :  Complete Novels

Chapter   46 / 46

135K to 136.1K   out of 136.1K words

bashi da yawan fitina ko gagara irin ta yara gashi da d'an karen wayo,
duk da yana yaro yasan masoyanshi ya kuma san wad'anda suke zare mishi ido in yaje kusa dasu mu samman Hajja inna mai zugeshi da carbi.

shiyasa baya zuwa inda suke,
tuni kuma ya fara tattaki.

Yau jumma'a da sanyin safiya Zahra ta shiga kitchen ta gama musu aikin breakfast,
bayan ta gama ne ta fito parlour inda ta samu Mama da Aryan suna zaune sai tsalle yakeyi a jikin Mama,
ganin Zahra yayi saurin sauk'a yabi bayanta tare da d'aga mata hannu alamar ta d'agashi cikin
lumshe ido ta sunkuyo ta d'agashi tare da cewa.
"Wash Aryan kayi k'atofa, yanzu na kusa in dena d'agaka."
Jafar ne da ya shigo yanzu yace.
"Uhummm gashi ke kuma kullum k'ara ramewa kikeyi duk kin canza yanayin rayuwarki ,
sam banajin dad'in abin."
Mama ce ta mik'e zaune cikin kula ta kalli Jafar d'in sai ta kuma kalli Zahra tare da cewa.
"Gata nan Jafar mafi akasarin ranaku sai tayi kuka,
ni kuwa damuwarta ke sani damuwa gata nan ko k'ofar gida bata fita tunda samu wannan matsalar."
ita kuwa Zahra kumatun Aryan taja wanda yaketa cewa.
"Mammama."
wai ta goyashi kenan.
kai tsaye bathroom ta wuce dashi,
wonka tayi mishi sannan tazo ta shiryashi cikin riga da wondo mai azabar kyau,
rigar orange wond'on kuma blue,
mai d'an ratsin orange daga can k'asan k'afafunta,
sai takalmanshi booth irin na yara masu azabar kyau,
mai ta tsiyayo a tafin hannunta ta k'ara shafawa suman kanshi datayi lib-lib,
shi kuwa turarenshi yaketa mik'o mata alamar ta sa mishi,
hannu tasa ta k'arba tare da fesa mishi sannan ta d'auko sabuwar wayarda Affan ya kawo mata jiya,
hotuna ta rink'a yi mishi,
shiko sai dariya yakeyi,
kiss ta manna mishi a goshinshi tare da cewa.
"Kaine farin cikina Aryan ina sonka,
domin nasan baka da laifin komai,
aka yadda kazo duniya."
murmushi yayi kamar yasan me take cewa.

Bayan sun fito parlour ne ta samu Jafar nanan har yanzu yana ganisu ya mik'owa Aryan d'in hannu cikin sauri ya zamo daga hannun Zahra da gudu ya nufi inda Jafar yake,
yana zuwa ya d'agashi sama tare da d'aurashi kan wuyanshi,
yayinda shi kuwa Aryan yasa hannu biyu ya rik'o kan Jafar d'in,
yanata kerketa dariya,
shi kuwa Jafar hannunshi yasa ya rik'o k'afafunshi,
sannan ya kalli Mama cikin kula ya kuma kalli Zahra yace.
"Zamu fita da Aryan,
zan saya mishi wasu kaya da na gani sabbin samfuri."
kai Mama ta jinjina alamar to,
ita kuwa Zahra cikin sanyi tace.
"Toh bari yasha kununshi kar yaje ya ta maka ihu."

to yace sannan ya sauk'oshi ya mik'e mata shi ya juya zai fita yana cewa.
"OK to kiyi sauri bari inje in gaida Ummi sai inzo mu tafi."
yana fad'in haka ya fice ya tafi yayi part d'in Ummi,
shi kuwa Aryan zamewa yayi tayi tare da k'ananun kuka alamun shi dai a barshi zaibi Jafar,
haka yasa dole ta sakeshi,
cikin tafiyarshi da bata gama nunaba yabi bayan Jafar wanda tuni ya shiga part d'in Ummi,
shi kuwa yana haura saman barand'ar takiyar gidan yayi tangak-tangal ya fad'i,
wani irin ihu yasa da k'arfi,
Aunty Amarya da Hajja inna da Nana da suke tsakiyar gidan ko inda yake basu kallaba,
ita kuwa Zahra da Mama kusan a tare suka fito,
jin ihunshi nan suka samu Zeenat ta d'agashi tana kad'e mishi jiki domin baiji ciwoba kukan tsorone kawai yakeyi,
da sauri Mama ta k'arbeshi ita kuwa Zahra sai kallon Aunty Amarya da tayi ko a jinkinta,
ita kuwa Mama Zahra ta mik'awa shi tare da cewa.
"Karb'eshi ki bashi nono."
amsarshi tayi tare da zamewa ta zauna kan bakin barandar ta fara fiddling inshi,

shi kuwa jiyo muryar Jafar ya sashi sakin nonon tare da zamewa ya sauk'a ya nufi wurin Jafar,
cikin kula ya d'agashi ya ruggumeshi tare da cewa.
"So sorry my boy."
yana fad'in hakane yayinda yake fita dashi ita kuwa Zahra sai hannu tasa tana share hawayenta.


Shi kuwa Affan kai tsaye Airport ya nufa,
ni kaina Garkuwa mmki nakeyi ko me zaije yi a Airport,
shi kuwa bayan ya isa cikin Airport d'in ne kai tsaye inda matafiya suke zaman jiran jirgi ya nufa,
daga bakin wurin naga masu jajayen kaya da alamar akwai jinin sarauta a wurin,
yana k'ara gaba sai ga Affan a gabanshi,
cikin kula Affan ya mik'a hannu ya karb'i Aryan da yaketa sauk'e ajiyan zuciya,
bisa dukkan alamu Aryan ya saba da Affan dan ba musu yazo gareshi,
sai kuma suka juya suka nufi wani sashi na musamman inda manyan matafiya suke zama in basa son hankalin mutane ya dawo garesu,
can gefe suka je kan wasu kujeru masu kyau,
Yusuf na zaune cikin shigar k'ananan kaya wad'anda kalarsu d'aya dana Aryan, yayi kyau sosai sai dai yanayin rama da k'uncin rayuwa dake tare dashi,
suna isa Affan ya mik'a mishi Aryan k'arami,
hannu mik'o tare da zubawa yaron ido,
shima Aryan ido ya zubawa Yusuf cikin gwaranci yayi dariya tare da cewa.
"Abeeh."
gaba d'aya Jafar da Affan dariya sukayi mai cike da mmaki,
shi kuwa Yusuf k'arb'arshi yayi tare da ruggumeshi gam a jikinshi sannan ya juya nufi hanyar da zata sadaga da inda jirgin yake...!

VISIT www.aihausanovels.com.ng For More Novel.

AIHAUSANOVELS is website consists of hausa novels note, the reason of launching this site is to Entetaint, Motivate and Educate our readers.



We provided hausa novels of many type, Such Adventure, love, romance, fiction, non-fiction, mystry, fantasy, action e.t.c from hausa Authors



We provided a new and old novels both softcopy and hardcopy from our Author with thier permission.



AIHAUSANOVELS shafin yanar gizo ne wanda yake ?auke da littattafan hausa, dalilin bude wannan shafin shine domin Kayatar masu karatu da kuma ilimantar da su.



Mun samar da littattafan hausa na nau'uka daban-daban, kama daga littafin, soyayya, tatsuniya, almara, Hikayoyi, gyara kayanki (yadda mata zasu kula da kansu a gidan mijinsu) da dai sauransu, daga Marubutan hausa.




By
*Garkuwar Fulani*


*By*
*GARKUWAR FULANI*


46 / 46