Author : Hafsat Bature Category : Action Novels
kuma tana da kyau" murmushi duk suka yi Abbas yace "yau da alama Mom Zarah ta tafi da hankalinka shiyasa ko ta baban naka bakayi ba balle ka gaidashi ko" da sauri ya nufi Haisam yana fad'in "Good Evening Baba Zakee Ango" gaba d'aya suka sa dariya daga haka suka nufi ciki hannun Abdul cikin na Haisam, cike da Farinciki Feenah ta tarbi Fatuu don sun kwana biyu basu had'u ba bayan sun gaisa tace bari ta shirya table dama Abbas d'in bai ci Abincin rana ba shima tana shirin mik'ewa Haisam yace mata a koshe yake tace ma Fatuu ai ita zata ci ko tace mata a'a itama a koshe take ganin yamma ne tasan dole sunci Abinci yasa ta k'yalesu Abbas ma yace ba yanzu zai ci ba, d'aki Abdul yaja Fatuu wai suje suyi game su ci kayan dad'in data kawo mashi Feenah ma tace baza'a barta ba da ita za'a ci tabi su Abbas na dariya yana fadin da girmanta zata cinye ma yaro abu, bayan barinsu parlon hirar tafiyarsu Haisam d'in gobe suka shiga yi can ya tambayeshi yadda akai suka koma Normal da Mom Zarah anan ya bashi labari yace ba abunda yake tunani bane kawae ta damu da tafiyar da zaiyi ne don basu ta6a hirar Aurenshi da ita ba so abunne yazo mata unexpected kuma gashi bazata je bikin ba, da mamaki Abbas ya tambayi dalili yace mashi zasu fara final Exams ne Next week d'in, shiru Abbas yay kaman mai tunanin wani abu lokaci guda ya tuna da ba Next week ake fara Waec ba sai Upper week wato sati na sama nan take ya fahimci Fatun k'arya tay ma Haisam hakan kuma ya tabbatar mashi da zarginshi akanta duk da ba zargi bane duk alamu sun tabbatar da son Haisam take kawae shima don bai da experience kan hakan yasa yak'i fahimta shiru yay kawae bai ce komai game da hakan ba sai da sukayi Magrib sannan sukae masu sallama suka rako su gaba d'aya har bakin Mota anan Feenah ke ce ma Fatuu "Mom Zaraah sai mun had'e Abuja ko" Abbas yay saurin cewa "Mom Zaraah bazata samu zuwa ba don lokacin sun fara Waec" kallonshi fatuu tay suka had'a ido ya saki wani murmushi da yake akwae haske sosae sam Feenah bata ji dad'in hakan ba haka ma Abdul daga haka suka shige Mota Abbas nace ma Haisam sai sun had'e goben suka tafi bayan ya bud'e masu gate, akan hanyarsu ne yake ce mata zadae ta raka shi Airport gobe ko tunda da yamma zai tafi har saida gabanta yay wata kalan bugawa kafin da k'yar tace mashi eh ai bazata ma je Makarantar ba ta fad'i mashi hakan ne don kar yama zo daukarta, tambayarta yay dalili tace mashi ba komae kawae shiru yay bai ce komae ba har suka iso gidan ba wanda ya k'ara tankawa, jiki a mace tace mashi ta gode ya jinjina mata kai kafin yace ta d'auki ledan baya tace to, bayan ta d'auka ta nufi gida ko juyowa batayi ba ya bita da ido har ta shige ya lura da canjawar da tayi nan take zuciyarshi ta ayyana mashi saboda zancen tafiya da yayi mata ne d'age kanshi yay a fili ya furta "I too gonna miss u Zaraah" iska ya d'an fesar ya d'ago ya kai hannu ya ja Motar.
Next Day........
Bayan sallar juma'a misalin k'arfe 3:30 sun gama shirin tafiya tsab Hajiya tasha adon lifaya haka ma Saude tana sanye da doguwar rigar Atamfa da babban gyale don da ita za'a tafi Tk kuma zai tafi garinsu ne gobe daga can zai tafi tare da iyayenshi, gaba d'aya Tk ya gama fita da kayayyakinsu yasa acikin Mota, lokacin da suka k'araso parking space Gwaggo ta shigo cikin gidan tana ta sauri ta nufesu tana fad'in ayi Hakuri ta taushe hannu don ta sanar da Hajiyar zata raka su dama suna haka sai ga Haisam da Abbas sun fito daga part d'inshi sun nufo parking space din Haisam na sanye da wani d'anyen bak'in voile haka hular kanshi da takalman kafafunshi da agogon hannunshi suma duk bak'ak'e ne wato shigar complete black yay just Ma sha Allah, suna isa Abbas ya gaishe da Hajiya don bai shiga wurinta ba sannan ya gaishe da gwaggo tanata fara'a ta amsa Haisam ma ya gaishe da ita har zai bud'e Mota sai kuma ya dakata ya kalli gwaggo yace "Zaraah fa?" shiru ta d'anyi Hajiya tace "wllh nima inata son in tambayeta nasan dae yau ba islamiyya ai", ganin duk ita suke jira tayi Magana yasa tace "d'ana Haisam kar ka damu mu tafi kawae" jimm yay haka Abbas ma Hajiya tace "wani abu Dije, ina Fateemar take?" Da yar damuwa tace "tana can tun jiya da daddare take abu guda yau ko Makaranta bata je ba sai aikin kuka ba irin lallashinta da ban yi ba amman a banza tunda ba jin Magana take ba" yar dariya Hajiya tayi sai kuma ta d'an girgiza kai tace "Allah sarki kinsan yadda sabo yake dole ta shiga damuwa Yayanta Handsome zai tafi gashi ba samun zuwa bikin zatai ba ko ni banji dad'in hakan ba itace ya kamata ace k'irjin bikin" gwaggo tace "to amman ai saitai hak'uri tunda kukan ba canja komae zaiyi ba kuma don an tafi ai ba shikenan an rabu ba ko" gyad'a kai Hajiya tayi tace suje kawae duk suka shiga Jeep d'inta Tk na niyyar shiga wurin driver don ya jasu Haisam ya tsaidashi yace ma Abbas ya kaisu shi zai taho tare da Tk d'in ya d'aga mashi kai da murmushi kan fuskarshi ya shiga mazaunin driver ya tashi Motar suka tafi, kallon Tk yay yace ya shiga shi kuma ya zagaya ya bud'e mazaunin driver d'in ya shiga daga haka yaja Motar Suka tunkari gate Officer na mashi Allah ya tsare sai ya zo suka wuce, A daidai gidan su Fatuu ya taka burki yace ma Tk yana zuwa,bud'e motar yay ya fita ya maida kopar ta rufe ya nufi cikin gidan................
********************** ⬇ **************************
********** Ai Hausa Novels ****************
*************************⬆ **********************
DOWNLOAD More complete Hausa Novels, Education Books, Adventure, Drama, Mystery, Religion, Fiction, Non-Fiction, Romance, Meimor, True Life Stories & Others from our blog.
Visit > https://www.aihausanovels.com.ng
Ka tura mana sako ta adireshinmu na email, domin tuntubarmu ko turo mana hausa novel ko kuma post.
Email > aihausabooks@gmail.com
******* FOLLOW US ******
Facebook: Ai Hausa Novels
Twitter: Ai Hausa Novels
Telegram Channel: https://t.me/Aihausanovels
WhatsApp Number: 08138873799
Haka kuma domin shiga kowanne daga cikinsu za ku iya ziyartar shafinmu ku yi search na AI HAUSA NOVELS, hatta facebook group dinmu ma za ku samu.
********************** ⬇ **************************
*************** Ai Hausa Novels ****************
********************** ⬆ **************************
*ASM Bk2016*
_Destiny may be delayed but cannot be changed...._
*This page is dedicated to Hajiya Kubra (Mommy) Allah ya k'ara girma da daukaka da nisan kwana Amin🤲🥰*
*DA SUNAN ALLAH MAI RAHAMA MAI JIN KAI*
.........Yana shiga gidan Parlor ya nufa ganin ba kowa yasa ya wuce direct d'akinta tun kafin ma ya shiga ya jiyo shesshekar kukanta ya kai hannu ya d'aga labulen,tana zaune a k'arshen gado ta had'e kai da gwuiwa ga gashinta duk ya tarwatse, har ya shigo ya tsaya a tsakiyar d'akin yana kallonta bata sani ba goya hannuwan shi yay a k'irji idonshi akanta yama rasa mi zaice mata, a hankali k'amshin turaren shi ya fara kurd'ad'awa yana kai ma hancinta ziyara tun tana jinshi sama sama har ya cika mata hancin ta tabbatar k'amshin Ya Haisam ne hakan yasa ta d'ago a zabure idanunta suka sauka akanshi, zare ido tay tana kallonshi da idanuwanta da suka canja kala sunyi jawur gashi sun kankance sosae tsabar kuka duk a tunaninta sun ma tafi, lokaci guda ta kama kanta ganin kallon da yake mata ta fara jan jiki tana matsowa ta zo bakin gadon cikin hard'ewar murya tace "Y..ya ha.i..sam" shiru bai amsa ba yana cigaba da kallonta sai yan kame kame take tana kallonshi can yay sigh da wata irin murya yace "is this the Promise u ave made to me Zaraah" girgiza mashi kai tay tana yamutsa fuska kaman zata sa kuka,
"Why, why all dis Zaraah kina son in tafi da damuwa ne?" tun kafin ya rufe baki tafara girgiza mashi kai ganin yadda yake Maganar da damuwa kwance akan fuskarshi shiru yay yana kallonta cikin muryar kuka ta fara fad'in "Don Allah kayi hakuri Ya Haisam wllh kukan ne yake zuwa da kanshi nayi nayi ya daina yak'i" ta k'arasa tana had'iye kukan wani irin tausayinta ne ya kamashi slowly yay moving zuwa gaban gadon ya samu wuri can gefenta ya zauna da sauri ta sunkuyar da kanta don duk kamshin turaren shi ya cika hancinta shiru ya d'anyi yana kallonta can yafara Magana Slowly "am so sorry Zaraah I caused u pain am sorry" ya k'arasa da breaking voice ya d'an cije baki d'agowa tay ta kalleshi hawaye na sauka daga idonta da sauri ya kai hannu cikin pocket d'in rigar shi ya fiddo farin hanky ya mik'a mata ta amsa ta fara goge kwallan yana ta kallonta yama rasa tunanin da zaiyi ji yake kaman kar ya tafi ko don ta daina damuwa but he knows isn't possible ita kuma ga exams d'inta kuma yasan ko taje ma in ta dawo still sai ta damu na wani lokaci saboda rashin shi sai faman dirzar ido take bata da niyyar tsayawa a hankali ya kai hannuwanshi ya kamo duka hannayenta ya sauke su k'asa suka kalli juna cikin ido picifically yace "kiyi Hakuri Zaraah am feeling almost d same thing am not happy zamu yi nisa da juna after being together for gud 3 years but we can still be together though we're in distance right?" Jinjina mashi kai tay alamar eh, yace "ok ki daina damuwa pls" nan ma kai ta jinjina mashi shiru ya d'anyi sai kuma yace "tunda baki son rakani ba wani abu lokaci na tafiya zamuyi Magana" daga haka ya saki hannuwan nata ya mik'e har ya juya yaji ta kira sunanshi da disasshiyar murya ya juya ya kalleta ta saukko daga kan gadon ta mik'e a hankali tace "zan raka ka" fuska a d'an sake ya d'an bud'a ido yace "really?" Kai ta d'aga alamar eh d'an murmushi yay ya nufeta yace ina ribbom d'inta ta juya kan gado ta d'aukko tana kokarin sawa ya mik'a hannu ya amsa yay mata alamar ta duk'o da kan kallonshi tay cikin ido sai kuma a hankali ta duk'ar da kan ya matsa dab da ita ta yadda har kan nata ya d'an gogi broad chest d'inshi a nutse ya fara tattara gashin don ba kaman na Fanan bane nata yafi cika hannu sosae bayan ya gama ya d'ago da ita yana mata murmushi ita kuma tana mashi wani kallo a hankali ta furta "I will miss u Ya Handsome" kawae sai ya janyota yay hugging nata very tight ya d'aura ha6arshi saman gashinta, sosae itama ta k'ank'ameshi idonta a rufe wata kalan natsuwa taji tazo mata yayin da scent d'inshi ke k'ara narkar mata da zuciya tana cikin hakan taji cool voice d'inshi yana fadin "I will miss u too Zaraah, I will miss ur everything ur smile,jokes and d whole moment we spend together......" Yadda Maganar ke sauka acikin kunnanta yasa ta k'ara kankameshi yana jin yadda kirjinta ke sama da kasa saboda numfashin da take da sauri da sauri hakan kuma yasa Haisam d'in jin wani bak'on yanayi a tattara dashi wanda sam bai ta6a jin irin hakan ba a tare da Fanan, ita da bai ma jin komae in ya had'a jiki da ita don koda Maganar Aure ta shiga tsakaninsu tana nan a matsayin da ya d'auketa cikin ranshi sai daga baya ne data k'ara girma ya fara jin canji game da hakan shiyasa yake kokarin kiyayewa bai cika son suna had'a jiki da ita ba sai ta kama ita ce dae in zai biye mata to kullum suna manne, jin abun na k'aruwa sosae yasa da sauri ya d'agota don shi kanshi yasan bai kamata ya had'a jiki da ita ba har saida ya nemi tsari yay istigfari cikin ranshi, sam ta kasa kallonshi don da k'yar take ma bud'e idonta wani bak'on yanayi take ji a jikinta, shima juyar da kanshi yay gefe trying to get ease kafin ya kai hannu ya kamo hannunta ya kaita gaban mirror bai iya tanka mata ba da hannu yay Mata alamar ta gyara fuskarta ta kai hannu ta d'auki puff d'in powder tana goge fuskar idonta akan shi suna kallon juna ta cikin mirror d'in suna haka wayarshi ta fara ringing ya kai hannu cikin pocket d'in rigarsa ya fiddo yaga Hajiya ce ke kiran nasa yay picking yana d'auka tace mashi yana inane yasan dai jirgi bai jiran Mutum ko yace mata he's on his way heading there d'aga haka yay cutting ya maida wayar Fatuu na kallonshi yace mata ina veil d'inta ta matsa wurin wardrobe ta ciro hijab tasa ya kama hannunta suka fita, back door ya bud'e mata da kanshi bayan sun fita ta shiga ta zauna ya rufe shi kuma ya bud'e gaban ya shiga ya ja Motar, a kai kai yake kai ido kan mirror ya kalleta wani lokacin su had'a ido wani lokacin kuma ta duk'e tana goge kwalla can ta d'ago kawae taga yana mik'o mata hanky kallonshi tay kafin ta mik'a hannu ta amsa, a hankali take kai hanky d'in fuskarta ta d'an goge kwallan in suka had'a ido dashi sai ta sadda kan kasa, basu d'au tsawon lokaci ba suka k'araso Airport bayan sun yi parking sun fito ya nufi inda su Hajiya suke Fatuu da Tk na bayanshi, Hajiya na ganinshi ta sha mur ganin Fatuu yasa bata dae ce mashi komae ba gwaggo ma tunda suka had'a ido da ita sau d'aya bata yarda sun k'ara ba don taga kallon da tay mata mai kaman harara Abbas kuwa sai murmushi yake mata a sanyaye ta gaishe dashi kafin ta nufi wurin Hajiya ta gaidata tana kallon fuskarta ta amsa kafin ta dafa shoulder d'inta tace "kiyi hakuri kinji Fateema ai ba an rabu ba kenan da zaki damu kanki har haka, dubi idanunki yadda suka kumbura kukan ya isa haka kinji" kai ta d'aga mata lokacin kuma aka fara sanarwa nan da mintuna biyar jirgi zai k'araso don haka matafiya su shirya Hajiya ta juya tana k'ara yin sallama dasu gwaggo da Abbas suka ce sai sun zo daga haka suka nufi cikin departure Haisam ya mik'a ma Abbas hannu suka yi sallama shima yace mashi sai yazo haka Tk da gwaggo duk suka yi mashi fatan a sauka lpy, juyawa yay side d'in Fatuu ya d'an kalleta for few seconds sai kuma ya tafi ba tare da ya ce mata komae ba har yayi kaman taku ukku zuwa hud'u yaji ta kira shi hakan yasa ya dakata ya juya nufo shi tay tana zuwa gaban shi ta mik'a mashi hanky d'inshi da ya bata a cikin Mota kaman bazai amsa ba sai kuma ya amsa ya juya yana niyyar cigaba da tafiya yaji Muryata tana fad'in "Thank u Sweetheart Ya Handsome, thank u for all dat u have done to me May Almighty Allah reward u Abundantly, ina rokon Allah ya dawwamar da kai cikin farinciki har abada kamar yadda kake sa bayinsa farinciki, Allah ya jibanci lamuranka ya baka y'ay'a wanda zasu ji k'an ka, Allah ya....." Kasa k'arasawa tay ta duk'e a wurin tana wani irin kuka mai cin rai duk abun nan yana tsaye cak ba tare da ya juyo ba yana jin yadda take Maganar cikin breaking voice dake bayyana she's in serious pain runtse idonshi yay can kuma ya bud'e yaci gaba da tafiyar saida zai shige wurin sannan ya dakata ya d'an juya suka had'a ido tana a durk'ushen sai kuka take can ya juya ya shige, kowa ta bashi tausayi har gwaggo saida jikinta yay sanyi ta sani sabo ba abunda bai sawa ba kamar su sabonsu na Musamman ne, Abbas ne ya nufeta ya duk'a ya kamo hannunta ta d'aga kai ta kalleshi tana gunjin kuka ya jinjina mata kai alamar ta mik'e, Mota ya nufa da ita ya bud'e baya yace ta shiga gwaggo ma ta bud'e d'ayar kopar ta shiga yace ma Tk ya taho da Jeep d'in yace to, tunda suka taho hanya take aikin kuka kanta na kan kafafunta ta rufe fuska Abbas sai bata hakuri yake har dae ta k'ule gwaggo ta fara surfa mata fad'a cikin harshen fulatanci Abbas na bata hak'uri duk da baisan mi take cewa ba amman daga ji yasan fad'a take mata, suna akan hanyar jirginsu Haisam d'in ya wuce, Allah sarki Ya Haisam d'in mu shikenan ya tafi wayyo Fatuu I feel ur pain ko baki son Haisam dole ne ki ji zafin tafiyarshi🥹, suna k'arasowa kopar gida gwaggo ta bud'e Motar bayan tayi ma Abbas godiya ta wuce gida abunta da k'yar ta iya bud'e Motar ta fita sakamakon k'afafunta da sukae mata nauyi sai faman shessheka take tana niyyar tafiya bayan ta rufe Motar Abbas ya bud'e ya fito har ta juya ya kira sunanta ta juyo da runannun idanunta ta kalleshi ba tare da ta amsa ba cikin muryar lallashi ya fara Magana,
"Am so sorry Zaraah, i know how are feeling but I want u to know Allah yana jarabtar bawa ba don baya son shi ba and if u'r destined for sadness there is always a reason all u need is to put ur trust in Allah, shine kadae mai maida abunda ake tunanin bai ta6a yuwuwa ya yuwu cikin tsananin sauki, so all I can say to u is kiyi HAKURI kiyi HAKURI" kai ta jinjina mashi tasa hannu tana goge kwallan ya kuma cewa "Da