Advertisements
Chapter 106 Reading Kundin Kaddarata Book 1 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Kundin Kaddarata Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Huguma Category :  Complete Novels

Chapter   106 / 120

315K to 318K   out of 359.7K words

ta fada tana yatsina fuska
"Eesha shegiyar gari....wai ina bash ne?"
"Standby zaki ce,jeki dawo kizo na gaya miki"
"Alright"Amiran ta kuma fada tana bin bayan sumayya da tunitayi gaba.

       Suna shiga amira ta kama kafadar sumayya dake qoqarin daure gashinta don shiga wanka
"ke wai baki karanci komai tattare da eesha ba?,ba kya ganin irin kallo da take binki da shi" murmushi sumayya tayi duk da itama abun ya tsaye mata a rai,har yau kuma bai daina bata mamaki ba
"Kinsan wai yaya man take so?"amira ta fada tana kecewa da dariya ta fada saman gado,maganar ta daki sumayya,sai yanzu ta gano abinda ya sanya eesha bata qaunarta,amma sai ta dake
"to Allah ya tabbatar da alkhairi" harara amira ta watsa mata sannan tace
"Haka zaki fada?,ke yanzu fatar kishiya kikewa kanki banda waccar da take gabanki?" Cikin dakiya tace
"To meye?,bakiji abinda kema kika fada ba,nima wata nazo na taras"
"Amma wallahi baki son ya almustapha amira,da eesha da su'af meye banbancinsu?,qasar haihuwa ce kawai ta raba su,ai ko mata sun qare bazan masa fatan auren eesha ba wkh duk da tana 'yar uwata,amma duk dan uwa na gari zaya so yaga nashi na auren magartacciyar mace kaman ke"
"Lallai kam,idan rabonshi ce ai ba wanda ya isa ya hana ko?" Ta fada a fili tamkar ba komai,cikin zuciyarta kuwa kaman zata fashe
"Allah ya tsari gatari da saran shuka,kinsan ma duk cikin yaran family ba wanda sam basa hada inuwa da yaya almustapha irin eesha?,itafa ta sanya ya saka dokar hana samarinsu zuwa gidan nan matuqar suka zo hutu da sallah,tun randa ya ganta da wani cikin mota suna har harkoki"
"To Allah ya kyauta,kedai kwanta kawai kiyi baccinki"ta fadi tana daukar towel saboda ta sake watsa ruwa
"naqi din,kuma kamar a kunnen ya almustapha kin masa mugun fatan auren eesha"dariya ta baiwa sumayyan saboda yadda tayi kicin kicin kaman ance mata saif zai qara aure,toilet ta shige don ta tabbata ta biyewa amira sai su bata lokaci a wajen.


         Tana fitowa wayarta ta soma ringing,tana dubawa sunan almustapha ne a sama,murmushi ya subuce mata,halan yau 'yan rigimar ne a kusa,dududu awa uku fa da gama wayarsu,sai ta zauna bakin madubu ta daga kiran ta kara kunnenta tare da yin sallama
"kewarki nake" ya soma fada,murmushi ta sake masa mai dan fidda sauti har cikin kunnenshi
"Awa uku da rabuwarmu fa?"
"Jinta nake makan shekara uku,ummu abdallah kaman ma baki tausayi na,ashe haka so yake wahal da zuciyar mutum?,kinsan yanzhn haka wani asibiti ke buqatar taimakona za'a yiwa matan wani aiki amma na gagara zuwa,ko naje din ma nasan ba abinda zan iya aiwatarwa....please my summy kiji tausayina mana" ya qarasge zanacan a shagwabe,dariya ta saki salon magananshin ya tsumata
"Wallahi abu abdalla ka zama wami shagwababbe,anty su'ad ta lalata ka"
"Zaki gane hakan idan na kamaki a hannu,kinsan Allah....ranan ko babynmu bazan tausayawa ba bare ke,zaki zo hannu" ya fada yana katse kiran,murmushi ta dinga fiddawa,bata ajjiye wayar ba sai data tura masa sms da tasan zata haukatoshi sannan tayi switchoff din wayar yadda koya kira bazai sameta ba,ido ta lumshe tana sakin murmushi,ba qarta ita kanta tasan ba qaramin rashin mijinta tayi ba
"Laila majnoon,idan kun gama baqin sunzo" amira dake kwamce ta fada,ita kanta abun ma burgeta,wato haka yaya almustapha yake baje soyayyarshi,amma idan ka ganshi a waje sai kace wani zaki,musamman idan ya soma muzuran nan nashi ko bada umarni,baka ce ya taba dariya ba,amma yanzu ya wani narke kaman dan yaye,sam ita sumayya ma ta manta da ita sai da tayi magana
"To 'yar sa ido" dariya suka sanya baki daya,amira ta miqe daga saman gadon ta zauna sosai
"Seriouse amiran yaya musty....wai meye sirrin don Allah,salon soyayyarkun nan a bani nasha don Allah"
"Min indillah" ta bata amsa tana ciro kayan da zata saka
"Da gaske?"
"Biya sai na gaya miki"
"Ko nawa ne ko zan nada indai za'a gayan" dariya ta baiwa sumayya sosai,ita kanta wani lokaci ta zauna ta kanyi mamakin kansu,ita da kanta batasan akwai duniyar data qunshi zallar farinciki har haka ba sai yanzu,duba da irin bigire na nau'in rayuwa daban daban data afka,taso mukhtar a sanda bata mallaki hankalinta ba,a sanda bata banbance so qauna da shaquwa,wasu mata sun shiga rayuwarsu sun kawo naqasu wa farinciki da shaquwar dake tsakaninsu,sannan bayan duka wannan tazo ta rashi a sanda bata da kowa sai shi kadai ta mallaka,bata saba da kowanne namiji ba sai shi,tazo ta auri lukman bisa tsautsayi da qaddarar data hauta na dole sai ta shiga rayuwar wasu,daga qarshe ta samu almustapha,wanda ta sameshi ne a lokacin da hankali ya gama gameta,ta gama sanin zaqi da madaci,so qauna da shaquwa da kuma,tasan dama da hagunta.

         Aina da asma'u sune matan mus'ab da mahamoud,dukkaninsu basu fi sa'annin sumayya ba,koda zata girme musu bazata basu shekara ba,bare kana ganinsu zaka musu kudin goron sa'anni ne,dukkaninsu wayayyu ne masu matuqar kirki,karatunsi da wayewarsu bai hanasu kasancewa 'yammata nutsatstsu masu cikakkiyar tarbiyya ba,kowacce ta samu tarbiyya daga gidansu,kamar asm'u wadda makaranta daya sukayi karatu da mahmoud wata private university dake nan garin abuja,saidai tana matakin farko ne mahmoud yana matakin qarshe,kamun kanta da nutsuwarra shi ya fara jan hankalinsa,abinda bai fiya gani ba wajen 'yammatan dake manyan makarantu na jami'o'i,bare irin nasu makarantun na yaran masu da shi,kowacce ta dauki tabara da rashin tarbiyya rashin cikakken kamun kai a amtsayin wayewa,wannan ya zama ruwan dare cikin makarantunmu na walau na gwamanti ko kuma na kudi.

      Dukkaninsu suna da kyau  abinsu,faran faran da mutane,nan suka hadu suna hira abinsu,irin hiran farkon haduwa ba sakin jiki can da yawa,eesha na gefe tana hura hanci,ta dora qafa daya kan daya,ta san asm'u,duk da wuce asm'un da aji daya,hakan ya sanya ko ayanzun ka take jin ta fita,gidan 'yan uwansu take,bugu da qari ita dangin miji ce,su dinma da yake kowacce ta iya takunta daga gaisuwa basu damu da me take ba,a haka ummi tazo ta taddasu,hakan ya mata dadi qwarai,ta kuma yaba da tanadin da sumayya tasa aka musu,hatta da anty maamaa sai data ji dadi,duk da alkunya data yi tace baqin ummi ne dama,sunje dai sun gaisa da ita sannan suka dawo suka ci gaba da sabgoginsu.


         Basu tafi ba sai yamma liqis bayan sunyi musayar lambobin waya,cikin motar mus'ab duka zasu koma,sun tafi suna yabawa da sumayya,cikin qanqanin lokaci suka saba da hirarta suka a baki suka isa gida.

        Tunda suka tafin eesha ta dawo falon qasa ta zauna bayan data tabbatar ta gama shirya duk wani abu data tanada,rana saka ran cewa wani dalili ya sauko da ita daga dakinta zuwa kitchen din,hakan ya sanya ta kasa ta tsare ta zauna a falon,tana danne danne waya tare da kallon wani film a MBC action amma rabin hankalinta ja matattakala zuwa qofar kitchen din,duk wani ma'aiki da zai buqaci shiga kitchen din ta sallameshi tun yamma,ummi dama ita ke da girki taga fitarta zuwa sassan baba prof.

         Sajida ce ta sauko da sauri sauri,sannan da hazarinta irin mai tattare da quruciya ta nufi kitchen din,cikin hanzari ta dakawa sajidan wata iriyar tsawa data sanyata tsayawa cak
"Uban me zaki shiga ciki kiyi kanki na rawa?" Kaman zata saki kuka tace
"Anty amira ce tace na dauko ovaltine zata hadamin wani abu" sosai abin yayi mata dadi,da alama haqanta zai cimma ruwa,sai ta sake kaurara murya tana zare mata ido
"To koma kije kice mata nace ba zaki shiga ba,idan ta matsu ta sauko da kanta ta diba" tsayawa sajida tayi tana dubanta,don a ganinta ita kanta eeshan ta yiwa sumayya rashin kunya,bugu da qari ma gidan ba wanda akewa get na amfani da wani abu tunda basu gaji rowa ba,kowa na gaban kanshi je ciki kuwa harda ita eeshan
"Ba zaki wuce ba kika tsareni da ido ko sai na qaraso nan na babballaki na zubar" ganin hargagin da take mata ya sanya ta dole komawa saman da sauri.

        Sumayyan na zaune riqe da qaramin qur'ani tana karanta falaq da nasi da ikhlas tana qarashe addu'anta sajida ta dawo,maganan da eeshan ta gaya mata ta daure mata kai,bata ce komai ba ta gama addu'ar ta shafa,sannan ta miqe da hijabin jikinta tace da sajida
"Zauna,bari na debo miki"
"To" sajidan ta fada sumayya ta fice,dadi ne ya dinga ratsa eesha sanda taga sumayya ta shige kitchen din,tuni ta ajjiye wayar gefe ta miqe tsaye tana shirin ko ta kwana murmushi na fita a fuskarta.

        Sam sumayya bata lura ba har sai data dauko gwangwanin ovaltine din ta dauki hanyar fitowa,ji tayi ta tafi baki daya sululu zata kifa ta baki
"Hasbunallahu wa ni'imal wakil" ta furta,cikin wani irn hanzari ta saki gwangwanin ta dafe freezer dake daf da ita,duk da haka sai da qafarta ta amsa ta rintse ido tana sake kiran sunan Allah,da gudu taga shigowar eesha wanda hakan har yaso ya sake firgitata ta soma dudduba jikin sumayya tana cewa
"Innalillahi wa inna iliahi raji'un,me ya sameki?,kinji wani abu ne?,me ya samu jikinki?" Shigowar ummi cikin rudani wadda shigowarta falon kenan taga eesha ta runtumo kitchen din da gudu ta biyo bayanta,sumayya ta soma yu qurin tashi ummi ta nufeta,eesha ta dakatar da ita tana qarasawa wajen sunayya tana taka wajen cikin taka tsantsan ta kama sumayya tana dudduba qasan data fadj
"Ai babu ma abinda ya sameki" eeshan ta fada haushi na cikata,so tayi tazo ta ganta male male cikin jini,ta fadi kan cikinta tayi barin dan tayin dake cikinta,wani irin kallo sumayya ke bin eesha da shi wanda ita eeshan bata kula ba,baqincikin rashin cimma nasarar da bata yiba kadai ya cika mata qoqon zuciya,ta dora dukkan alamomin tambaya kan eeshan,zainab ce ta fara fado mata a cikin abdallah,take jikinta yayi sanyi,gabanta ya yanke ya fadi taci gaba da nazartar eeshan a fakaice,duk wasu abubuwa da take son gani ta samesu,tuni ta janye baya ta bar sumayya hannun ummi ummi na duban wajen
"Me ya kawo miyan kuka nan wajen har ya janyo miki faduwa,subhanallah" ummi ta fada tana janye sumayya daga wajen
"Ita tayi ta mai shegen warin daddawa" ta fada tana yatsine fuska,kai sumayya ta gyada
"Ni nayi,sai gata kuma ta taho har nan" ta ambata tana duban eesha,dauke kanta tayi ta juya ta fice daga kitchen din tana kumbura
"Bakijin dai komai a jinki ko?"
"Eh ummi,ba komai" ta bata amsa tana miqewa
"Bi a hankali,idan kina jin wani anu ki fada,don Allah nidai daga yau na yafe shigowa kitchen din nan" ummin ta fada cikin damuwa
"To ummi" ta fada tana nufar qofar kitchen din,zuciyarta cike fal da mamaki,me ta yiwa eesha,don tana son almustapha sai ta nemi rayuwar dan cikinta,d'an kuma wanda take iqirarin tana so,lallai dole ta sanya ido da takatsantsan da eeshan,don ba zata taba lamunta yaran da tun kafin ta haifesu su dinga shan wuya ba haka kawai ba tare da laifinsu ba,biyo bayanta ummin tayi,sai data sake tabbatarwa komai lafiya sannan hankalinta ya kwanta,saukowa qasa tayi,ta tara ma'aikatan dake kula da kitchen baki daya ta tsawatar musu,sannan taja kunnensu da kada ta kuma gani sun bar sumayyan ta shiga kitchen sannan ta sallamesu kowa ya koma muhallinsa bayan sun gyara gurin.




*mrs muhammad ce*👑

📚📚📚📚✍🏽✍🏽✍🏽✍🏽


✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
📖📖📖📖📖


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



9⃣9⃣


*Bismillahir rahmanir rahim*

*Allah S W T yana cewa*

*duk wanda ya aikata daidai da qwayar zarra na alkhairi(komai qanqantarsa) zai gani(cikin littafin ayyukansa,zai ganshi a rubuce kuma za'a masa hisabi da hukunci a kansa),hakanan duk wanda ya aikata dai dai da qwayar zarra na sharri zai ganshi.
__________________________________________







          Tun daga lokacin sumayyan ta zubawa eesha ido cikin nutsuwa,tana kula da takatsantsan da duj wanu taku nata,a bangaren eesha kuwa ko daya bata sauya qudurinta ba,ko da yaushe tunaninta daya na yadda zata illatar da sumayyan ne.

   ******    ******    *******

      Qarfe goma da rabi ranan ta sauko bayan farkawarta daga bacci wanda kusan almustapha ne ya tasheta,sai data gama biye masa sannan ta shiga tayi wanka ta shirya ta sauko don ta karya,bata da damuwa tasan cewa komai na shirye,tun daga randa wancan abun ya faru bash sake barinta shiga kitchen ba.

        Tare suka sauko da sajida,ummi na sashen anty maamaa,sajida ta wuce dining don ta karya,ita kuma kiran halima da ya shigo wayarta ya sanya ta wuce saman kujerun falon ta zauna tana amsawa,qarar sajida data jiyo shi ya sanyata sakin wayar ta miqe,bata jin nauyin jikinta haka ta nufi sajida da tayi zaman 'yan bori saman step na dining area,wajen ta isa tana dagata gami da tambayarta
"Faduwa nayi anty" ta bata amsa tana shirin sakin kuka saboda qafarta ta bugu sosai,idanunta sumayya ta kai wajen sai taga ruwa ne ya zube wajen
"Ya akayi kika zubda ruwa haka sajida?"
"Bani bace nima haka naga wajen,kuma ban kula ba har sai da na fadi" wani tunani ne ya darsu ran sumayya,ta sanya hannun ta cikin ruwa sai taji yana santsi da qanshin klien,to waye ya zubda ruwa haka?,tasan cewa babu yadda za'ayi ma'aikatan su zubda ruwan su tafi ba tare da sun gyara ba,ummi bata nan sajida ba ita ta zubar ba
"Eesha" zuciyar sumayya ta raya mata,kai ta girgiza,batason ta zargeta bayan bata gani da idanunta ba,riqe sajidan tayi don dawo da ita saman kujera,tana juyowa suka hada idanu da eeeshan,sai ta juya ta shige dakinta,mamaki ya kama sumayyan,wai me eeshan ke nufi,take ranta ya baci,ta zaunar da sajida saman kujerar ta kama qafarta tana mammatsawa,gefe guda ke mata ciwo,sai ta isa bakin dispenser ta tari ruwan zafi ta dawo kusa da sajidan ta gasa mata qafar sosai,cikin ikon Allah wajen ya saki,ta shafa mata man zafi a wajen sannan taje da kanta ta goge wajen sannan ta hada mata abin break din taci ta kwanta.

       Tana saman kujera zaune kanta a qasa,ranta a tsananin bace yake,don me zata dinga neman cutar da ita?,tana tunanin dai dai gaggawar unguwar zoma ta bari a haihu ko?,ta bari su hada miji tukunna,meye na hanzarin son cutar da ita tun yanzun,saqar data dinga yi kenan cikin zuciyarta,qara qofar dakin eesha tayi,itace ta bude ta fito,tana tafe dai dai ta hura hanci,idanunta da suka kada saboda bacin rai ta zuba mata
"Aisha..." Ta kira sunanta cikin kakkausar murya wadda ta sanyawa eeshan tsayawa ta kuma juyo tana dubanta
"Jan kunne nakeso nayi miki na qarshe....duk abinda zakiyi kiyi qoqari ya tsaya iya ni,kada ki bari sarkarcinki da haukanki ya sake taba wani cikin gidan nan,yanzun da kin karya musu yarinya kuma kice me?,haka rannan kika watso ruwan zafi saura kadan a fuskar sajida,kina gidan kakanninta kina cin arziqinsu kina neman salwantar musu da jikoki?"maganar sumayyan ta qarshe ta sosa mata rai,ita zata yima gori bayan ita ya cancanci ta yiwa gori
"idan kuma banji jan kunnen naki ba me zaki iya diyar malamai masu ci da buzu da tawada?"murmushi ta sake mata sannan ta bata amsa cikin nutsuwa
"alhamdulillah da na kasance diyar malamai magada annabawa,zancan rashin jin gargadina kuwa....koni zan iya miki hukunci.....amma da yake ni din mai uwace a gindin murhu,kunnen mutum daya maganar zata je kiga yadda dunuyarki zata gigita" ta fahimci sarai tana son hadata da almustapha ne ko shi ko baba,to har gwara ma baban akan shi din,kuma ta sani sarai qarshen lamarin bazai mata da dadi ba
"Duk abinda zakiyi baki isa ki hanani shiga gidan almustapha ba wallahi,baare ma ya sameshi bare kuma na gida" murmushi ta kuma yi
"Kan me zan hanaki dama?,nima fa wata ta taras,sannan kuma ba kanku na soma zama da abokan zama ba,abu guda kawai nakeso daga gareki.....koda zaki auri almustapha to ki kiyayi taba lafiyar jama'ar da basu ji basu gani ba.....ki taqaita haukanki....ki adana shashashanki har zuwa sanda zaki shiga gidan nashi"tana yunqurin maidawa ummi tayi sallama,hakan ya sanyata dole yin shiru,bata ji ke suke fada ba taga dai sajida kwance
"a'ah lafiya kuwa?" Ta tambayi sajidan tana dubanta
"Ruwa ne ya zube sai na fadi" ta bata amsa,gefe ummin ta samu ta zawa
"garin yaya ruwa ya zube a wajen?" Ta tambaya cikin mamaki,wannan karon sumayya ce ta karbi zancan
"Wallahi ummi,sashen dai ba kowa,ni da ita kuma tare muka sauko sai ihunta kawai naji" waiwayawa ummin tayi tana duban eesha
"Aysha ya akayi ruwa ya zube wajen?"
"Nima ummi ban sani ba"
"Bake na bari wajen ba kina karyawa?" Sai ta langabar da kai
"Tea ne ummi,ina so ma goge kuma na mance naje na kwanta"
"Amma ya kamata ki dinga kulawa tunda kinsan yadda wajen nan ke da santsi,ko su lami kika saka zash goge,yanzu da amira ce ta taka wajen Allah ne kadai yasan me zai faru,ki kula sabida gaba"
"To" ta fada tana zumbura baki ta koma daki,ranta cike fal da baqincimi,ita wacce iriyar mara sa'a ce,kuma wai ummin har take goyon bayan wata bare a kanta,lallai kam ba zata qyake wannan abu ba zatayi mai gaba daya ne kawai komai ta fanjama fanjam,ruwa ummi ta buqata ta gasawa sajida wajen,sajidan tace ai anty ta gasa mata,hakan yayiwa ummin dadi,daya daga cikin abinda yasa har kullum take sumayyan ke sake shiga ranta kenan sanin ya kamata,ba qaramin jin dadin zama take da ita ba,ba shakka da zaiyiwu riqe sumayyan zatayi wajenta har ta haihu,amma tasan hakan ba maiyiwu wa bane,ita kanta tasan alkunya almustapha kawai yake mata,wanda dukkan alamu sun nuna ya fara gajiyawa,don ya soma yi mata qananun qorafi,ko haka kawai ba gaira ba dalili sai ya dinga tashinta cikin dare yana sata kaiwa sumayya waya.


***** ******** ******


Kimanin takwas ne na dare yau ta kwanta da wuri,so take tayi bacci sosai,jin kanta take kamar wadda ta shekara batayi bacci ba saboda yau tayi tashin wuri,don haka yau tun magariba ta kashe wayarta don ta huta sosai,har ta kwanta qishirwa ta tasheta,ta miqe ta zura hijabinta ta sauko qasa,cikin sandata bude fridge ta dauki ruwa saboda duk saman babu ruwa mai sanyi,ummi ta hana ta sha shi yasa ake ajjiye mata mara sanyi,ita kuma qaunarshi take,idan bata sha ba har wani abu take ji ya tokare mata qirji.


106 / 120