Advertisements
Chapter 118 Reading Kundin Kaddarata Book 1 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Kundin Kaddarata Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Huguma Category :  Complete Novels

Chapter   118 / 120

351K to 354K   out of 359.7K words

su'ad din wasu abubuwan da take ganin ya kamata ace ta sani,sukan zauna suyi hira sosai da ita cikim sakewa kaman sun jima da soma mu'amala,jikin su'ad din da sauqi sosai,har takan iya zama sumayyan ta jinginata,ita ke gyara mata jikinta,ta bata abinci,ta daura mata alwala idan lokacin sallah yayi,tana yawan sanya sumayya ta jera mata amatullah da amatur rahman tayi ta magana da su kaman wasu manya
"Ki musu tarbiyya irin taki don Allah" hakan su'ad ke yawaita fada,murmushi sumayya keyi tace
"Tare zamuyi musu har ke,kema mamarsu ce"
"Zanso hakan" abinda takan fadi kenan wanda sumayyan ta kasa gane me hakan yake nufi.


Hatta almustapha yaga sauyi qwarai wajenta,da ya shigo takan gaidashi ko tayi masa sannu da zuwa,abinda bai taba gani ba,hakan ya masa dadi qwarai ua faranta masa,yakan zauna cikinsu ya bada wasu mintuna suyi hira su duka,duk da bai zama waje daya,ba wanda yasan inda yake zuwa daga shi sai Allahnshi,idan dare yayi yazo ya musu sallama shikenan sai gobe da safe.

Β  Β  Β Β  Wani dare bayan kowa ya tafi ya barsu,yan biyu na saman gado cikin neat suna bacci su'ad ta kalli sumayya
"Wai baki kewar maan,naga ko sau daya baki taba binshi ba" murmushi ta saki
"Kin manta jinyarki nake,ladan kuma da ake samu wajen yin jinyar mara lafiya ba kadan bane" kai take gayadawa cikin gamsuwa,duk wani furuci da sumayyan zatayi akwai qaruwa a cikinsa
"Wai nikam rannan kaman naji kina min magana kan rayuwarki,bani labari mana?" Dariya ta saki tana kallonta
"Kina son ji ne?" Kai ta kada
"Eh idan babu takura,don na tabbatar zan samu wani darasi a ciki"
"To qara kunne biyu" dariya ta saka
"Na qara" a nutse sumayya ta warwarewa su'ad labarinta,gyada kai kawai take,jikinta yayi matuqar yin sanyi qwarai,wato akwai mutane shigenta ko irinta da yawa a duniya
"Gaskiya rayuwarki baki daya darasi ce,ke din ta daban ce" ta fada tana jinjinawa yadda sumayyan ta fuskanci rayuwa haka,gyaran murya sumayya tayi wanda ya janyo hankalin su'ad daga duniyar tunanin data tafi
"Nikam in roqi wata alfarma mana wajenki"murmushi tahi,ki roqa ko mene idan baifi qarfina ba
" so nake ki yafewa mommy,kada ki manta uwa uwa ce komai lalacewarta,na tabbatar soyayyar da take miki ce ta kaita ga kasa tasawatarwa da tsayawa kai da fata wajen ganin ta hanaki aikata abinda kike so matuqar ba dai dai bane,ta kuma doraki kan dai dai din,ba zaka taba iya biyansu abinda suka yi maka ba har abada"murmushi ta saki ta kamo hannun sumayya
"Mummy,ina son mummy sumayya,saidai yadda ta tarwatsa rayuwata ta kasa gyarata tana qona min rai a duk sanda na tuna hakan,na jima da yafe mata sumayya,na mata haka ne ko don gaba,duk da cewa ko a yau na tafi na barta ba zata sake samun wasu yaran ba,amma wannan ya isheta izinar da zata bawa 'yan baya labari"kai ta kada
"naji,amma gobe ki furta mata cewa kin yafe mata,ki daina gudun ganinta don Allah" murmushi ta saka sumayya na sake shiga zuciyarta
"Naji in sha Allah zanyi,nasan tunda kika dage kan maganar kika gyaramin babu kyau abinda nake,zanso ace zan haihu da na sakawa 'yata sunanki" ta fada wani abu na taba zuciyarta,hawaye ya sauko saman fuskarta,goge mata sumayyan tayi tana cewa
"Ki daina kuka,ki godewa Allah da lafiyar da kike samu"
"Na gode" ta ce da sumayya
"Ba abun gode min,haqqina ne dama na kula dake din koba komai miji daya fa muke" murmushi suka sakarwa juna,ranar sunyi hira sosai da su'ad din har take gaya mata
"Naga amira na sonki,da fari haka nima ta soni,halina yasa ta gujeni,ki tayani bata haquri don na mata ba dai dai ba da yawa wanda yasa ta daina hulda da ni"
"Amira bata da riqo,kuma ke matar yayanta ce,na tabbatar komai ya wuce a wajenta,don kullum sai ta kirani ta tambayeni jikinki,abinda ya hanata tace na baki duk sanda ta kira kina bacci,ni kuma banson tada ke" murmushi ta saki don maganar ta mata dadi,sai da suka raba dare sosai sannan sumayya ta daura alwala ta tada sallah,ta baiwa su'ad carbi ita kuma taci gaba da azkar,sanda ta idar ta waiwaya sai taga carbin ya fadi hannun su'ad din,idanunta alumshe alamun bacci yayi awon gaba da ita.

*Bayan awanni uku*


Zaune take kawai a gabanta ta zuba mata ido tamkar mutum mutumi,sam kukan da yaran ke tsalawa bai shiga kunnuwanta bare tayi yunqurin daukarsu,dubanta kawai take lokavi bayan lokaci tana kiran sunanta,saidai babu wani alami dake nuna motsa bare ta amsa,tun kan ya qaraso dakin yake jiyo kukan yaran,hakan ya sanya ya qara sauri cikin hanzari ya isa qofar dakin ya bude ya tura,a kansu su biyun idanunsa suka sauka,sai ya sauya akalar tafiyar tasa daga wajen 'yan biyun zuwa inda su sumayyan ke zaune,kallo daya ya yiwa su'ad dake kwance gabanshi yayi mummunar faduwa,tamkar wanda aka bigewa gwiwoyinshi ya qarasa bakin gadon ya duba hannyenta zuwa saitin zuciyarta inda take aiki,abinda yaji ya tabbatar masa da cewa babu rai jikin su'ad din,duk da haka zuciyarshi ta kasa gasgata masa,take ya hautsina kayan aikin dake dakin,ya dinga gwaje gwaje,wanda yana tsaka da aikin abokinsa mai asibitin ya shigo dakin da niyyar duba mara lafiyan,kallo daya ya mata ya tabbatar ta mutu,hakan ya sanyashi janye almustaphan cikin harshensa na turanci yace
"Kayi haquri,ta rigamu gidan gaskiya man,Allah ya jiqanta" tuni sumayya ta qarasa rushewa da kukan dake cinta,suka hadu ita amatullah da amatur rahman suka gauraye dakin,baya almustapha yayi ya jingina da bangi yana furta innalillahi wa inna ilaihi raji'un.


*bayan awa daya*

Dukkansu suna zaune a babban falon dake asibitin wanda na likitan ne ya basu su zauna,kowanne ka dubi fuskarsa cikin baqinciki take,hatta da mazan dauriya kawai suke,saidai almustapha bai iya daurewar ba,karon farko da suka soma ganin hawaye kan fuskarshi,abinda basu taba gani ba tsahon rayuwarshi da su,ummi ma hawaye take sharewa lokaci zuwa lokaci,yayin da sumayya ke kuka tuburan,idanunta da fuskarta gaba daya sun kumbura,yayin da fuskar ta hadu tayi jazur,ummi dake gefanta ita ke lallabata ta bawa yaran nono,tana shayar da su cikin hijabin tana kuka,ba shakka mutuwa kota wanda baka sami bane tana da ratsa jiki da sanya wani sabon imani a zuciyar dan adam,ballantana wadda ta sani sun zauna tare tsahon shekara nesa da juna,gab da zata tafin kuma sukayi zama irin na yaya da qanwa,yaushe zata manta haka?,haka mutuwa take,takan dauke mutum a sanda bai shirya ba hakanan masoyansa basuyi sallama da shi ba,sai mutuwar mukhtar ta fado mata,kukanta ya sake daduwa,wanda hakan ya sake karya zuciyar duka sauran,ba shakka sunga irin zaman da sukayi a tsakaninsu cikin sati uku kacal kafin ta mutu,haka suka dinga bata baki kafin su fara tattauna abinda ya zaunar da su din bayan an kai gawar su'ad mutuware.


Alhj abdus samad ne ya fara magana
"Zamu wuce nigeria da gawarta,bama gawarta ba har maman tata ma"
"Amma alhj kaji fa sunce ita khaulat ta samu stroke,haka zamu tafi da ita" cikin tsantsar baqinciki yana goge qwallarsa yace
"Daga rana irin ta yau professor na bar zaman qasar nan har abada,zamu koma qasarmu ta gado da zama,babu abinda na tsinta a zaman qasar nan banda baqinciki da tarwatsewar iyalina tunda har na kasa control dinsu,kowa yana vin gashin kanshi,Allah ya jiqanki su'adah ya gafarta miki" ya qarasa fada yana shafe sabbin hawayen da suka zubo masa da tafin hannunshi
"Hakan yayi,a mata suttura cikin dakin mijinta" inji ummi,da wannan shawarar suka soma neman izinin tafiya da gawar su'ad,cikin kwana biyu rak suka samu kasancewar abun na masu da shi ne.


Cikin dakinta dake abuja aka mata wanka aka shiryata,almustapha na tsugunne gaban gawarta yana mata addu'a,sosai yayi mata addu'a tare da jaddada yafiyarshi a gareta,sannan ya bawa sumayya guri,alhj abdus samad da duk wani makusancinta,inda aka turo mommy a keke,kuka ta saka ta soma magana,saidai maganar bata fita ba'a jin abinda take fada,sakamakon bakinta daya karkace tun faduwar data yi sanda tayi ido hudu da gawar sy'ad tana ihu tana ita daya ta mallaka ya zata yi mata haka,daga nan ta sume,bayan ta farfado kuma ta gamu da wannan cutar,sosai sumayya ta qunshe kanta a tsakanin qafafunta tana sakin kuka sanda aka dauki gawarta aka fice da ita zuwa gidanta na gaskiya,tabbas duk wanda yayi damara don duniya ya kwanceta,Allah ya bamu sa'ar tafiya,kasa mu riskeka sanda kake farinciki da mu ya Allah.


A nan gidan dake abuja suka zauna karbar makoki,kaf 'yan uwan sumayyan ba wanda baizo mata ba,haka yan uwa da abokan ariziqi suka dinga zirya,har eesha ba'a barta a baya ba,tazo jikinta cikin matuqat sanyi,tana tuna yadda suke takun saqa da su'ad din,tana tuna yadda su'ad ta dauki rayuwarta kusan dai dai da yadda itama take jin kanta,hakan ya qara mata mutuwar jiki,sai data dangana da sumayya tayi mata gaisuwa,sannan ta roqi gafararta kan abinda ta nata a baya,murmushi kawai tayi,mutuwa kadai ta ishi mai hankali aya,me ya mata zafi da zata tsaya saka wani mutum a ranta,itakam mantawa ma take da faruwar abin sai idan wani abu ya taso da zai tuna mata da hakan,tace ya wuce har abada,'yan biyu sun jima hannunta,sosai yaran suka shiga ranta,bul bul da su cikin tsafta gwanin sha'awa,duk da mamarsu na cikin alhini amma fes suke,don ummi ke sawa baba uwani ke kula da su akai akai,ba'a maidasu wajen sumayyan sai sun buqaci nono.


Kwanaki bakwai akayi kaman yadda al'ada tace kowa ya watse,aka fidda duk wani abu na su'ad din aka miqawa iyayenta,don almustapha cewa yayi ya yafe,bazai iya amsar komai nata ba,ranan mummy khaukat tayi kukan da bata taba makamancinsa ba,tayi nadamat da bata taba tsammanin akwai kamarta ba,ta dinga kallon sumayya tana son gode mata amma babu baki,iya jinyar su'ad kawai zuwa mutuwar nan ta karanci irin kyakkyawar zuciyar da take da ita,da hannu ta dinga mata godiya haka aka turata kan keken guragu suka fice a gidan.


Washegari kwana takwas kenan almustapha ya taddata tana gyara dakinta,ita daya ce su amatullah suna wajen ummi,duban junansu suke kowa na kallon irin sauyawar da dan'uwanshi yayi,shaida mata yayi zai koma america,amma baya so ta gayawa kowa can ya tafi,din su dubai yace zai koma,fatan alkhairi ta masa don ta fahimci me zai komar da shi din,itama tana goyon bayanshi,bai kamata mutane irin doctor james ace sun kubuta ba haka nan akwai.


Qasa ce da bangarorinta suke da wariyar launin fata da qyama ga musulmai,amma hakan ko kadan bai karya masa gwiwa ba,bai wani tuna cewa shi din baqo bane,ya dan sha wuya amma bai haqura ba sai da ya tabbatar an kamo doctor james an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya,sannan an qwace duk wani license nashi tare da rushe asibitin da ya gina,wanda hakan ya dauki almustaphan tsahon watanni biyar,bai waiwayi gida ba sai bayan wadan nan watanni,satin guda da kammaluwar lamarin,da wani yammaci wanda a wannan lokacin sumayyan na kwance,bata taba jinta cikin matsi da takura irin na wannan lokacin ba,rashin ganin almustapha har tsahon watanni biyar bata zaci ma zata iya jureshi ba,a kusan kullum sai taci karo da saqonshi ta email dinta na ban haquri da alqawarin dawowarshi nan kusa,bata da amsa face Allah ya bada sa'a,ta tsawaita haqurinta qwarai da gaske,saidai har zuwa yau shiru kake ji,duk sanda ummi ko professor sukayi qorafi,takan nuna ita ta bashi dama babu komai yana gab da dawowa.


Qarar wayarta ita ta dawo da ita daga tunanin da take,ta miqa hannu ta daga ta kara a kunnenta ba tare data damu da duba mai kiran ba
"Assalamu alaikum warahmatullah" muryar nan mai daraja da qima a wajenta,muryar nan da take bawa girma,muryar nan da babu tamkarta ita ta ratsa dodon kunnenta,tamkar an cire duk wata laka dake jikinta haka taji wata muvuwar kasala,zuciyarta ta karye,take qwalla ta cika idanunta
"Wa'a laikumussalam warahmatullah" ta amsa masa bayan ta sauke ajiyar zuciya,idanunsa ya lumshe daga can bangaren yana duban kansa a madubi,ya sauya kaman bashi ba,ya rame saidai ya fara cikowa cikin sati guda,zaya so ace sai daya murmure sosai kafin ya koma mata saidai dauki da son ganin ahalinsa bazai barshi ba,sautin yaji kaman na sheshsheqar kukanta
"Ya salam" ya furta yana zama gefan gado
"Ummu abdallah ki yimin rai don Allah ki daina kukan nan" ya fada a tausashe,a hankali ya dinga tsarata cikin kalamai masu taushi da di,har sai daya sauke mata duk wani abu dake cikin zuciyarta sannan ya jefeta da albishir mai dadi
"Rana ita yau,ki jirayi mijinki masoyinki,ki masa kyakkyawan tanadi da tarba ta musamman,ki gayawa daughters(amatullah da amatur rahman)duk wanda nazo na tadda ya fara gwada tafiya shine best friend dina" murmushi mai dauke da sauti ya qwace mata,ba qaramin dadi albishir din yayi mata ba,uwa uba takan yi dariya duk sanda yake magana da yaran kaman sa'anninshi,saboda tsabagen wayo hat sun soma shaida muryarshi da fuskarshi ta hanyar hoto da kuma waya da sukeyi
"In sha Allah" ta furta cikin tsantsar farinciki,a qalla sai da suka kashe awa daya cikakkiya yana sake wa soyayyarshi service kafin suyi sallama,ya jiqata ya tsumata da kalamanshi qwarai da gaske,wanda ta dinga sakin murmushi ita daya kaman tababbiya,kasa zama sashen tayi,ta zura hijabinta ta miqe zuwa sashen ummi,inda su amatallah suke can tun sassafe.


Sanda ta sanarwa da ummi zancan dawowar cewa tayi cikin zolaya
"To sai a fara shiri da kyau ko?" Kunya ta kamata ta sadda kai tana gyarawa amatallah kalbarta data soma zamewa.


In sha Allah last page na zuwa muku nan da anjima,ku zama ready........




*mrs muhammad ce*πŸ‘‘

πŸ“šπŸ“šπŸ“šπŸ“šβœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½βœπŸ½

✍ *~KUNDIN QADDARATA~*✍
πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“–πŸ“–


*~NA~*

*~SAFIYYA ABDULLAHI MUSA HUGUMA~*

*WATTPAD:HUGUMA*

*_HASKE WRITERS ASSO_*
(HOME OF EXPERT AND PERFECT WRITERS)



1⃣0⃣7⃣

*bamu kasance masu azaba ba har sai da muka aiko da dan aike(manzo)*

*haqiqa mun aiko ka manzo(annabi muhammad)kan al'ummah,Allah ya isa shaida*

*wanda ya yiwa manzan Allah biyayya haqiqa yabi Allah*

*haqiqa mun shiryar da shi hanyoyi biyu(dan adam)kodai ya zamantoΒ  mai godiya ko ya zamto mai kafircewa*

*haqiqa mun halicci mutumΒ  daga digon maniyyi dake cakude da ruwan mace da namiji muna jarrabashi da takhlifi(nauye nauye na shari'a Allah na nufin jarrabarsa a sanda ya dace)saboda haka muka sanyashi mai ji mai gani*

*haqiqa wannan gargadi ce ga talikai to wanda yaga dama sai ya riqi hanya izuwa ubangijinsa*

_____________________________________




Sosai ta shiga gyara cikin satin bata zauna ba,ummu kam ta daure mata qarqashi ta kwashe mata su amatallah,duk wani abu daya kamata ta aiwatar da shi,har kwaskwarimar bangarenta sai data yi,kafin ranar dawowarshi komai ya zama neat.


Ranar da zai dawo din mahmoud ne zaya je dauko shi,kafin isowarshi ta shirya tsaf cikin shigar cikakkiyar bahaushiya atamfa,ga mata cas a jiki dinkin ya zauna mata,yaran duka ta shiryasu cikin kaya iri daya komai da komai,sun fito sak a twince dinsu,sunyi wani kyau da girma,sanda taji isowar tasu sai ta kasa zaune ta kasa tsaye,kai tsaye wajen baba ya wuce,ya taddashi tare da matan nashi,ba wanda baiyi farinciki da ganinshi ba,sai a sannan ya yiwa baban bayanin me ya zaunar da shi,shiru baban yayi yana jinjinawa namijin qoqarin da yayi cikin qasar daba tashi ba,aqalla ya kusa mintuna talatin kafin ya wuce sashensu.


Awa uku da shigowarshi amma ta kasa zama,sai qirqirarwa kanta aiki data yi,zirga zirga take tsakanin kitchen da falo,duk wani motsinta yana kan idanushi,ya ganeta sarai,tana nufin sai ya sake sabon yaqin neman soyayyarta?,kunyarta keson musu shamaki,yana zaune ne da boxer da singlet fara qal bayan yayi wanka,ba abinda ke fita jikinsa sai qamshi mai taushi na turaren safirul hubb da wasu nau'in turarukan,tuni amatallah da amatur rahman sukayi bacci kan qafarshi dake miqe,sai ya yunqura ya miqe da su saman kafadarsa sanda ta sake zuwa ta kwashe duk abinda yayi amfani da shi zuwa kitchenbda alama wanke wanke zata yi,sai da yaje ya kwantar da su din sannan ya nufi kitchen din.


Tana tsaye gaban sink kuwa tana wanke wanken,taji shigowarshi amma sai ta kasa waiwayowa,a hankali ya qarasa bayanta,ya sanya hannayenshi ya kamo qugunta ya manna da nashi,sannan ya hade bayanta da qirjinsa ya dora habarshi saman kafadarta,nannauyar ajiyar zuciya ta saki saboda wani saqo na musamman da jikinsa ya aikata mata
"Wani abu kake so" ta furta qasa qasa
"Ke nake so maman 'yan biyu?,wai baki da labarin nayi kewarki ne?" Sai ta ajjye kwanukan alamar tabar wanke wanken,abinda ahi bai sani ba kunyar shi take ji sosai ta rasa dalili
"Um um ci gaba da wanke wankenki,zamuyi hirar a haka....bani labarin bayan rabuwa baby....nikam nayi rayuwa ne kawai,gani nan tamkar mutum mutumin,ina rayuwa ne tsahon wata biyar ba tare da nasan nau'in dandanonta ba,amma alhamdulillah,tunda alwashin da naci na cikashi" ajiyar zuciya ta saki tana dauraye wani kwano
"Bansan ya zan misalta maka ba noor,rayuwa babu kai ashe tamkar gangar jikin da babu ruhi ce,kullum sai nayi kukan rashinka,raba dare nake ina kokawa da tunaninka,sai inji kaman ka tafi kenan,kaman ba zaka dawo ba kaman yadda anty su'ad ta tafi...." Sai ta saki kwanukan ta juyo tana kallonshi,sannan ta lafe a qirjinsa kaman mai tsoron wani abu
"Don Allah noor.....kada ka sake tafiya ka barmu haka,ni da yara duka muna buqatarka" dagota yayi suna duban juna kafin ya sakar mata qayataccen murmushi mai kwantar da rai
"Ba zata sake faruwa ba my summyyy,ni dinma ina tsananin buqatarku cikin rayuwata....,bari in nuna miki kadan wani dan yanki daga cikin yadda nayi kewarku" bai saurari komai ba ha dagata baki daya tana dariya da roqon ya sauketa zata taka amma ya qiya,yace baiso tayi komai wannan karon shi zai sarrafata yadda yaga dama,zai kuma dauke duk wani aiki daya zama nata ya hada da nashi duka yayi.


Tun da suka haura saman sai kukan amatur rahman ne ya sauko da shi,bako kunya ya daukesu duka ya kaima ummi,baga ce komai ba ta

118 / 120