Author : Maman Teddy Category : Complete Novels
bashi labarin ta Sai yaga ai Sam Bata iya fasalta mutum ba.
Afnan na ganin Daddy ta shiga irin rawar murnar kaga abinda kake so din nan da Yara sukeyi tana zillo gurinsa zahrar ta nufa da nufin ta kaita.
Ita da duk saura ba Wanda yaga lokacin da mahmud ya diro gabanta Dan ja da baya tayi da sauri tana fad'in.
"Subhanallahi! Lafiya meye faru?".
Baiyi wata wata ba ya rungumosu ita da Afnan din dake hannunta.
Kici kicin kwacewa take Dan Bata taba tunanin zeyi irin wannan danyan aikin ba.
"Na shiga uku! Aunty ku taimaka min Dan Allah ku janye shi inaga bashi da lafiya kada yayi Mana illah Ni da yarinyar nan".
Ta fada tana kuka.
"Wallahi bazaki sakamin ciwon zuciya ba kin hanani sakat tun safe kin Hana ko fuskarki na gani,kinki yarda muje asibiti, me nayi Miki Mai zafi haka har kike ikirarin Wai mijinki ya Hana kije Asibiti, waye mijin naki bayan ni? Fada mini!!!..????"
Ya fada Yana hargagi abinda Bata taba gani ba kenan a iya zamanta dashi,kuka Afnan ta kwallah saboda yanda ya matsesu ga Kuma hayaniya da yake musu.
Da sauri Abbas ya taso yaga mahmud din kamar baya cikin nutsuwarsa.
Hannunsa Daya ya kamo sai yaji jikin nasa na tsuma.
Daidai kunnensa Abbas yayi magana.
"Pls sakarta kaga ka saka yarinya kuka, ka nutsu ta fada maka me yasa tayi hakan kowa ai yasan taka ce Ina ga da abinda kayi Mata Mai ciwo".
Da kyar ya yarda ya saketa ita da yarinyar. Zaunar dashi Abbas yayi ai Zahra na Dora yarinyar a cinyar uwarta lokacin Abbas na can Yana bashi Baki ta fice.
Tana shiga tayi locking din door tana sauke numfashi tare da goge 'yan hawayenta na karya data kakarosu.
"Wallahi saina rama zakayi bayani da bakinka guy ni zaka yiwa cin fuskar da ze Zubar min da daraja da kimata sai zuciyarta da Bakinka sun Fadi gaskiyar da kake boyewa, Kuma Wallahil Azim addu'ar tsamiya yanzu na Fara har FAHAZAMUHUM BI'IZIMILLAHI YA WADUDU YA JAMI'U MALIKIN NASI MALIKI YAUMIDDIN zanta zabga maka sai ka Raina kanka kasan Dan an baka kyautar zahra ba Yana nufi Zan Zama matar shige ba, sai duniya ta shaida zahrar Zahra ce, tayi kwafa ko yanzu na rage tension ko ya yake tunda kaima kaji a jikina ka Kuma karyata maganar daka fadawa 'yar uwarka jiya, Wai bakaga wadda tayi maka ba, sai kasan bayanin da zakayi musu Kuma tunda magana zarar bunu ce bata komawa.
Lokacin da Abbas ya juyo da zummar yiwa Zahra magana yaga sai filin gurin kallon Ina take ya yiwa Aishat..
"Ta gudu Ina zata tsaya ya nakasa ta yayiwa mijinta asara,kuma saboda Allah sai ka kakume Matar mutane da yammacin gari yaushe ka Zama haka yarinya da aurenta da komai wannan kasan haramun ne basai an fada maka ba, Ina cewa gida Daya kuka zauna ba diyar malaminka bace me yasa kasan kana sonta kayi shiru har wani ya aura ni Naga kokarinsa Daya amince ka taho Masa da irin wannan diamond baby din wata uwa duniya baya tsoron sharri shaidan ya gitta tunda gashi a gaban mutane ka iya rungumeta yaya idan daga Kai sai ita ne ai labarin ba irin wannan bane ki.."
"Stop!!!..... Aisha, ni kike fadawa abunda yazo bakinki? to Zahra halaliyata ce matata ce ta sunna".
Ya fada a zafafe tashi yayi ze fice da sauri Abbas ya riko shi.
" Dawo magana zamuyi ta fashimta".
Baiyi gardama ba ya dawo ya zauna, ita dai Aisha rasa ta cewa tayi wai barawo a hannun Mata.
Very close dashi Abbas ya zauna ya riko hannun mahmud Yana fadin.
"Munji matarka ce amma yanda sweetie ta fada min kace matar ubangidanka ce me yasa ka boye mata Bata cancanci haka ba, kasan irin wahalar Dana Sha da ita lokacin da case din Nan ya taso? yanda kasan zata zautu wallahi Amma sai ka dawo Mata da wata fuskar daba taka ba duk rintsi bakwa rufewa junanku komai, kasan ta fada min cewar wallahi matarka ce Dan ta shaida bazaka taba yarda kayi tafiya da mace irin wannan da mace kamar wannan babu alaka Mai karfi a tsakaninku".
Mahmud ji yayi duk ruwa ya cinye shi yarinya karama ta dagula masa lissafin da tasa ya saki layi duk yanda yake shirya nasa planning din ta rusa a lokaci daya yayi amansa ya lashe.
"To tayi hakuri ni kaina bansan me yasa na kasa fada Mata ba Ina Jin nauyin yanda Zan tunkari Ammi da Abbie da wannan maganar ba wallahi, sai Naga nayi wani Abu Daya sabawa al'adar mu ta Malam bahaushe, Kuma ita na rasa abinda nayi mata lafiya kalau mukazo gidan Nan Amma ta sauya min na rasa abinda yake min dadi wallahi Ya Abbas yarinyar nan itace weakness dina a rayuwa ni kaina nasan hakan, itace fa wadda nake fada maka na gani da dadewa a jirgi ita da Abbanta ka tuna?".
"Off cause anyi haka,Amma how comes hakan ta faru?".
Furzar da iska yayi daga bakinsa.
"It's long story, idan ka huta zamu tattauna akai, yanzu dai ki tashi like kiyi min Biko tunda Naga alamar kina da masaniyar laifina".
Baki Aishat ta dafe da hannu Wallahil Azim ban sani ba, nifa duk abin Nan hasashe nake yi ban tabbatar ba sai yanzu, ni wannan aikin ba nawa bane Kai zaka gyaro kayanka da abinda kayi Mata tunda Naga Bata da kwaramniya Sam, Kuma ya zakayi da ita kenan? Zakaje kace ga matata nan tsaraba fushin da nayi ko Yaya za'a kayi?".
"Ki Bari kawai alkawarin da nakeso kuyi min mu rufe maganar nan a nan duk da Faruq ma ya sani amma nasan tunda na kada Masa warning bazeyi karambanin fadawa kowa ba, nina taro match dina Ni zanyi playing din kayana kawai kuyi min addu'ar samun nasara kada Ammah tayi min nak'i".
Ya fada Cikin raunin murya.
[19/02, 11:46 pm] Abu Saleh: *AUREN HUCE HAUSHI*
MAMAN FATEEMAH
09062432330
Or
O8055362975.
Page 72
........... Cikin kankanin lokaci mahmud yaji ya Dan samu nutsuwar Daya rasa, yarinya karama ta saka shi sakin layi a gaban mutane, ita dai Aishat sai jijjiga Afnan takeyi wadda har lokacin take 'yar mita, tashi Mahmud yayi da nufin barin gurin, Ya Abbas ne ya riko Masa hannu Yana girgiza masa Kai.
"Dawo magana zamuyi ta fashimta, baiyi gaddama ba.
"Kana ji yanzu ka Bata sarari ta huta ta Kuma Huce daga fushin da tayi da kai, idan so Samu ne ka koma gidanka ka kame kanka, kada ka Bari ta Kara ganinka Nan kusa har sai an Kai wani limit da zata nemeka ruwa a jallo ta rasa yanda ko kun hadu babu saura fishi sai dokin ganinka dole ba Zama very strong a fannin soyayya Kaine namiji kada ka yarda ta gane itace rauninka, sannan dole ka koyi takatsantsan kasan inda na dosa idan ba haka ba za"ayi amfani da wannan damar a cutar maka da ita Koda ta furucin Baki ne".
Shiru mahmud yayi Yana saurarensa wato shi kansa zaman takewar auren sai an shirya mata, Dan rausayar da Kai yayai yana fad'in.
"Anyway shike nan,Amma da so nake ta yarda muje asibiti su dubata tukunna sai na wuce din".
Wani kallon me yake damunka Ya Abbas yayi Masa.
"For God sake! Ashe bazaka Zama Mai karfin ba kenan? Tunda nace ka kame kanka ai sai kayi yanda nace ko, tashi mu fita ja rakani na dubo patient din namu ma ida discussion din a hanya tunda Naga alama ka rifta da yawa".
Ya fada Yana Masa dariya, sumar kansa ya shafa shima Yana murmushi.
Bayan fitarsu Aishar Goya Afnan tayi so take tayi barci, Bata Kara bi takan Zahra ba ta shige kitchen ta Dora ruwa ta dauko kaza ta Fara gyarawa ta Dora a wuta ta debo fresh fruits ta wanke ta Fara hada fruits salad ta saka a fridge tayi lemon kankana da Madara pepper chicken tayi da chicken rice sai coslow data hada ta dafa ruwan tea Mai hadin spices masu Dadi na dafa tea kafin magariba ta Gama komai, Babban tray ta hadawa zahra kayan bude Baki ta aje a gefe sannan ta ringa fita da nasu zuwa dinning tana jerawa Saida ta Gama komai ta dauki na zahra lokacin har duhun magariba yayi, knocking Daya tayi Zahra ta bude Mata ta matsa gefe tana fad'in.
"Sannu Aunty da aiki Aunty".
Ta fada tana karbar kayan Amma taki yarda su hada Ido.
"Zanje nayi sallah idan na Gama zamu zauna dake Ina so mu tattauna wasu abubuwa".
Aishat ta fada tana juyawa.
"To Aunty zanzo basai kin dawo ba".
Dan dakatawa tayi da tafiya ta waiwayo.
"Kiyi zamanki ai Amare 'yan lalashi ne, ni zanzo on behalf of my beloved brother".
Ta fada tana dariya, itama zahra murmusawa tayi.
******Daga gida direct Asibiti su Mahmud suka nufa, sun samu Habib da Abubakar, Ya Abbas yayi mamakin ganin Abubakar a gurin sosai Amma baice komai ba kenan da wadanda mahmud yayi hijirar dasu.
Lokacin Baba malam Yana zaune suna Hira, har gabansa su mahmud suka karasa suka gaishe shi da Kara suba shi, sannan su Habib suka gaishe dasu mahmud, Ya Abbas ne ya kalli Abubakar Yana fadar.
"Wato har Kai gurin kufe Mana gaskiya ko? Kana ji ana ta Fadi tashin nemansa kayi fumfurus kana kallon kowa daga karshe ma akace ka canza gurin aikine".
Sadda Kai yayi yana Dan sosa gefen wuyansa, gyaran murya Baba malam yayi Dan duk da bayanin matsayin Ya Abbas da mahmud yake basa baisa ya dauke hankalinsa daga maganar da Abbas din fada ba.
Jin gyaran muryar Malam yasa suka juyo gaba Daya suna kallonsa.
"Ayi Masa Afuwa shima Mai bin umarni ne,sai yanda akayi dashi kada aga laifinsa amanar kenan da baya da Amana baze yarda dashi irin haka ba. Allah yayi albarka ya kiyaye gaba, ai karfin addu'a ne yasa komai ya Zama tarihi naji dadin ganinka sosai Malam Abbas Dan Allah kayi min aikin Dana kasa ka maida min Dana gida tare da iyalinsa ka bawa mahaifinku hakurin karambanin da mukayi musu wallahi nagarta muka duba ba komai ba tunda Bamu San gaibu ba, in Sha Allah idan lafiya ta Samu Ina Nan zuwa sokoton da kaina".
Waje su Habib suka fice, ya Zama daga Malam din sai su Ya Abbas.
"Babu komai Malam Allah ya baka lafiya, muke da godiya ya fada min duk dawainiya da kayi dashi tunda kuka tsince shi har kawo yanzu ai kaima ubane ka Isa kayi yanda kaga dama dashi, Allah ya Kara lafiya da sutura yasa kaffara akeyi in Sha Allah amanarka Zan idata, ai mu bamu da Bakin godiya sai dai ubangiji ne ze biyaka".
Sun Jima suna tattaunawa anan Malam yake farawa Abbas yanda kayiwa mahmud makaru abinda Bai taba fada Masa ba sai yanzu yakeji, har wasu hawayen gefen Ido Mahmud yaji sun taro Ashe haka akaso a kassara Masa rayuwa Allah yayi Masa gada da Rahama ya kawo Habib ya gashi a gurin da yake a yashe a kasa.
Anan sukayi magariba sukayi insha'i sannan sukayiwa Baba malam sallama, mahmud ne yace suje su duba jikin Alhajin su Aunty surayyar uncle Mustaphan Shima Yana nan.
Shima sun samu 'ya'yansa maza biyu sunzo duba jikin nasa, sun gaisa tare da jajanta musu, shima Alhajin jikin da sauki sosai Dan har Yana takawa shima da karfe.
Gida suka koma mahmud yayi dinner tare dasu, haka Nan yayi ta maza bai nemi zahra ba Suma babu Wanda yayi maganar ta har suka gama, Mahmud Bai wani zauna ya shiga dakin da ya mayar nasa tun ba yanzu ba ya dauko laptop din da wayoyinsa ya fito.
"Ka Bari na saukeka Nima Ina son fita ne".
Ya Abbas ya fada.
"No, ka barshi kawai nayi waya da Mr salahuddeen Yana kusa da isowa, kawai dai Alfarma za'ayi min twins zasu shiga Nigeria a tsakanin kwanakin nan harna Fara musu processing na visa harda yaran duka".
"Ba damuwa Nima Ina son suje Nigeria din to saboda makarantar Abulkhairi ne, Amma yanzu dole suje tunda ta Kama amma naji kana fadar kana nemar musu visa Kai kana Nan kenan?".
Kai ya girgiza Yana fadar "A'a akwai dalilin raba tafiyar ne jikina Yana bani wani Abu da bansan ko menene ba".
"To Allah ya rufa asiri, Zan fadawa sweetie ka wuce tana can gurin 'yar daru ita da dare take tata rigimar amma da Rana lafiya kalau za'a wuni da ita".
Dan murmushi Mahmud yayi Yana ayyana Wai babyn su ce da zahra suna tarairayarta.
Yana fitowa harabar gidan motar sayyid tana shigowa, dai dai gurin Mahmud ya tsaya ya kashe motar ya fito da sauri ya rungime Mahmud Yana fad'in .
"Ina ka shiga a duniyar nan ka barmu da tashin hankali? Munyi nema har mun godewa Allah kasan Umma cewa tayi a saka nemanka a jaridu da mujallu da kafafen sada zumunta na zamani,Su uncle Mustaphan ne suka Hana sukace abun ze zama tonon sillil Wanda Bai sani bama ze sani".
Dan zare shi daga jikinsa mahmud din yayi Yana fad'in .
"Ai gashi Nan dawo sayyid ya karatu ace ka koma PhD ko?"
"Wallahi kuwa".
"To Masha Allah. Allah ya taimaka, Nima Zan wuce ne matar abokina na kawowa Aishat su zauna a Nan asibiti sukazo zataga likita".
Ya mika Masa hannu yayi gaba, sayyid Yana da kirki amma fa gurin lamarin Mata sai a hankali, ko baya Zina ta zahiri akwai 'yan tabe -tabe.
Yana fita ya turawa Aishat text message a waya.
Amma fa karfin Hali kawai yakeyi Sam zuciyarsa Bata nutsu ya tafi yabar zahra da wannan Karen farautar a gidan ba, amma dole ya kauda Kansa yayi kawaici da Kara kada Ya Abbas yaga Bai dauki maganarsa ba.
Koda ya koma su Habib suna gida Suma sun baro asibitin, coffee ya bukac Mr Ajey ya kawo Masa ta wuce ciki Saida yayi wanka ya bude laptop dinsa Yana aiki Yana sipping din coffeen, ya Kai kusan biyun dare Yana Abu Daya Saida ya tabbatar da komai ya dai daita sannan ya kwanta zuciyarsa da gangar jikinsa suna mararinta, filo ya rungime a haka barci yayi awon gaba dashi.
Bayan sun sallar Asuba barci mahmud ya koma knocking din da ake a kofar bedroom dinsa ya tashe shi daga barcin da yake Mai Dadi Wanda ya saka shi nishadi.
Umarnin budewa ya bada Yana daga Cikin blanket dinsa.
Mr sunny ne Mai yin share share da goge goge.
" Good morning Sir"
Ya fada Cikin ladabi daga Bakin kofa sannan ya Dora da fadin.
"Akwai Baki daga Nigeria".
Wani smile yayi Yana tashi zaune yasan za'a Rina sai yanzu ya gane hikimar ya Abbas na cewa ya dawo nan shi kansa baze so zahra taga dabin da za'ayi ba".
"Kaje ayi musu duk abinda ya kamata, Mr Ajey ya Basu abinci kafin na fito".
Toilet ya shige yayi suk abinda zeyi sannan ya fito Yana tsane sumar kansa da Karamin towel a nutse ya Gama shirinsa ya fito a Mahmud dinsa, ya riko wayoyinsa hannu ya nufo main parlour.
Da uncle Mustaphan ya Fara yin tozali kafin ya sauke idanunsa a Kan uncle saminu, nan da nan ya hade girar sama data kasa tamkar yaki ya rigshi kofar gari.
A ciki ya gaishe su duk da shafi ce ta shafi uncle Mustapha sai yayi musu kudin goro, neman guri yayi ya zauna Bai Kara cewa komai ba, uncle saminu ne yazo iya wuya Dan ba haka yayi zaton zega Mahmud ba l,Dan an Bashi assurance na ya Gama lalacewa,dan a yanda a kayi Masa aikin rigar sawa ma sai tafi karfinsa, bare wani arzikinsa sai dai komai ya lalace masa, sai ya Zama abinda zeci ma saiya fi karfinsa, sai Kuma yaga sabanin haka Dan yanda yake da kyawun gani a yanzu ko kafin faruwar matsalar da suka Zama asasin fatuwarta Bai Kai haka kyaun gani ba.
A zuciye ya taso yana fad'in.
"Kai din banza har yaushe kayi arzikin da zamu tako har inda kake ka wulakantamu eyeh? Ka maida mu 'yan iska Wanda Basu San ciwon Kansu ba ko a Nan ma halin akuyancin kake tabawa shi yasa ka makale kana gyallin goshi?'
Uncle Mustapha ne ya taso da sauri yana fadin.
"Meye haka kakeyi saminu? Daman abinda ka shirya kayi kenan? Amma kaji kunya wallahi Dan zumunka? ko abinda kuka kitsa kaida munafukarka kuka lankaya Masa sharrin da gaske Yana yinsa ai ka rufa Masa asiri ba kazo kana wannan shirmen ba Wanda Allah ya daga ya daga shi sai dai mahassada suyi kuka, dai dai gwargwado meka nema ka rasa da yawa ta taka suke nema Basu samu ba wace irin sutura ce Ubangiji baiyi Mana ba Amma ka tsaya kana yiwa dan Dan uwanka hassada saboda Allah ya daukaka shi a cikin family din kace ya auri 'yarka yace baya so to nuna kin jini na me Kuma wani ya taba auren matar daba tasa ba ka ragewa kanka wannan walahar Dan babu inda zata kaika sai fagen Dana sani, Ashe 'yar burumburum kayi min ka nuna komai ya wuce muzo mu tafi dashi gida".
Sadda Kai saminu yayi baiyi zatom Mustapha zeyi masa haka ba Dan Saida ya shirya ya taho da zummar duk abinda yayi babu Mai iya tanka Masa.
Maganar Mahmud uncle Mustapha ya tsinkayo daga bayansa.
"Ka daina Bata Bakinka uncle Wanda yayi nisa baya Jin kira,ni Mahmud ta zamar Masa kadan garen bakin tulu ya barni na Bata ruwa a karni a Kar tulu, babu abinda ya Isa yayi min tinda bashi ne ya halicceni ba Kare ya canza min kaddarata kuma har abada Bazan taba auren wannan karyar 'yar tasa ba, yaje yayi bincken wacece ita kafin ya samu bakin fadawa mutane maganar suna Zina aje asibitin tugar barau ka nemi solomon kaji sau nawa ya zubarwa da 'yar taka ciki? Ko an fada maka bamu San haka ba Dan anyi shiru an kyaleta ba' a fasa maganar a family ba idan kace karya ne yanzu na nuna maka hujjata Mai karfi, kaci gaba da abinda kake kada ka fasa Dan Allah mu Zuba sharri dai Dan aike ne kada ka rufe kofa ze dawo Komai Daren dadewa, uncle Mustapha kayi hakuri wallahil azim Bazan bika ba yanda na fito ni kadai haka Zan koma indai da wannan mutumin zamu tafi Saida na mutu ban koma ba, bani da wani Hadi dashi Wanda ze shige min gaba a dukkan lamurana.
Uncle Mustapha baiyi yunkurin Hana shi ba saboda yasan irin bakin Cikin da yaron ya kunsa a wancan lokacin.
Juyawa mahmud yayi ze fice daga parlourn,