Author : Mamuhgee Category : Complete Novels
taji a cikin ranta itama tabar taka sassanta.
A nan waje ta watsar da batun,kamar yadda baba tabawa bata sake daga batun ba,ta wuce bedroom dinta tayi wanka,ta shirya cikin dinkin doguwar rigar atamfa A shape,ta dora baby hijab dinta saman kanta bayan tayi sallar magariba,tasha magungunanta sannan ta fito falon,tana ji a ranta zuwa yanzu wayarta ta cika da chargy.
Ta samu baba tabawa ta gama shirya musu abinci
"Na zuba sauran yana dumama don kada ya huce kafin yazo ci" baba tabawa tace da ita,sai ta amsa mata da to,ba tare data fuskanci ma'anar maganarta ba,tare suka zauna da ita sukaci abincin,suna ci suna hira,baba tabawa na bata labarai iri iri da suka shafi rayuwa,zamanta da kishiyoyinta da kuma mijinta,yadda mijin ke ji da ita saboda tafi duka sauran kula dashi,a fakaice take shigar mata da darasi.
Sosai take jin dadin labaran,tunda take tsahon watanni sai yau ne takejin gidan a matsayin gida,sai yau ta taba jin dadin zaman gidan,sun jima sosai suna hira,harta soma jin bacci yana fusgarta,don haka ta miqe ta bada faralin sallar isha'i,ta dubi baba idanuwanta na lumshewa
"Inajin akwai maganin dake sanya barci cikin magungunan da nasha"
"Bacci ko?" Kai ta gyada mata
"Eh wallahi,zan je na kwanta"
"To Allah ya tashemu lafiya" da kallo tabi maimunatu sanda take shigewa dakinta,tana jinjina kai tare da sake tabbatarwa kanta akwai matsala,bata ga ya shigo ba,bata ga taje nemansa ba,koda kuwa ba kwananta bane,tana kuma da tabbacin zuwa yanzu ai yana gida,don ba mai yawon dare bane shi tun asali,amna zatabi komai a sannu,koda yau da gobe ba kwananta bane,dole jibi ya zamanto kwananta,jinjina kai tayi tana ci gaba da kallonta,saidai kuma gefe guda na zuciyarta tana ayyana mata yadda zata tafi da komai.
******washegari ta kunna wayarta,ta kuma dauko number afra fatima da ayman ta sanya,tayi saving number kowa,sannan ta fara kiransu daya bayan daya,duk wadda ta kira sai ta yi mamaki,cike da murna da farincikin samun number aminiyar tasu,afrah ce a qarshe,don tasan dole sufi dadewa da juna akan kowa.
Da tsiya afra ta fara yi mata
"Kin yiwa kanki fada kenan?" Dariya maimunatu tayi
"Na gaji da kewarku ne" hira sosai suka sha da afrah din,har sai da katinta da hisham ya taba lodawa layin ya qare,afran ta biyota
"Ina fata kin fara shawo mana kai captain" dan shuru tayi tana son tuna waye captain,sai kuma tadan saki fuska
"Manta da wannan batun"
"Seriously you are doing wrong fa maimunatu,kina nufin a haka zaki yita zama,meye ma'anar auren kenan?"
"Karfa ki damu,ni dashi duka bamu damu ba"
"Amma kin sauke amanar anni da amma kamar yadda suka baki?" Tambayar da ta sanya maimunatun yin shuru kenan,har sai da afrah tace
"Qarshen term na ss 2 nima za'a karbi kudin aure na da farid,lalurar abba tasa uncle kamal yace a daga,amma abban da kansa yace a karba,babu wata damuwa,sannan hajja ma tace itama tafi nutsuwa nayi auren,naci gaba da karatun a dakina,tunda shima farid din yana da ra'ayin karatun"
"Allah sarki,Allah ya bashi lafiya kafin lokacin bikin,Allah yasa za'ayi damu,qawata kice na fara shiri tun yanzu" hararar gefanta afrah tayi,kamar maimunatun tana kusa da ita
"Nifa mun kusa raba gaari dake,muddin ba zaki tsaya kiyi abinda ya kamata ba" murmushi maimunatun tayi
"Nifa baki fahimta ba,wai ta yaya kukeso na mu'amalanci mutumin da babu soyayyata ko digo a ransa sai ta marigayiyar matarsa,sannan kuma nima din babu qaunarsa ko qanqani a rai na,hasalima ni wani kallo na daban nake masa,ko inuwa daya idan muka hada Allah Allah nake yabar wajen ko kuma ni nabar wajen,infact ma kallon mugu nake masa,tunda na ganshi yana smoking,bansan ta inda zan fara sonshi ko sakashi ya soni ba" wata qaramar dariya afrah ta saki
"Ban yarda dake ba,ban kuma yarda da dukka hujjojinki ba,kece number one a cikin mu hudu da kika fi kowa son kallon k-dramas na soyayya,har turkish drama kin koya kallo....."
"Kin tunamin ma,akwai wani da naga talla,zanje na kalla" taka katse afran tana miqewa daga kwanciyar da tayi
"Ahaf,kyaji dashi,kici gaba da zama,zaki mamaki idan kk ga wata tayi muku wuf dashi" dariya maimunatun ta saki,idan hakan ta faru batajin tana da asara,saidai unaisa,don ta fuskanci tana da damuwa sosai a kanshi.
Agogo ta kalla sanda suka gama waya,sai taga lokaci yaja,abinda ya sanyata miqewa kawai ta shiga wanka,so take ta shirya ta fita su gaisa da baba tabawa.
Dai dai lokacin da yake shigowa sassan nasu,cikin shirin office kamar kullum,slim fit three pieces suits ne a jikinsa Dim gray color dake da ratsin butter color,kwantacciyar fatarsa dake nuna zallar hutu da gayu tayi kyau cikin shigar,jikinsa ba abinda yake sai fidda sassanyan qamshin turaren prive rose George armani dan qasan turkey,kwantacciyar sumarsa sai fidda qyalli take kamar qura baya tabata,komai nashi me kyau tsari da kuma tsafta ne.
A nutse baba tabawa dake gyara abinci saman dining hannunta kuma maqale da carbi tana ja ta waiwayo tana amsa sallamarsa
"Barka da fitowa" ta fada tana sakin murmushi,taji dadin ganinsa sosai,don ya soma wanke zato da zargin dake ranta,kadan ya motsa fuskarsa,abinda ke alamta yanayin nasa murmushi ko fara'ar kenan
"Barka da asuba"
"Barka kadai manya,mun tashi lafiya?"
"Alhmdlh,jiya na gaji sosai,kuma na dawo late,ban leqo ba" murmushi tayi
"Ai babu komai,ta warware ma" agogon daure a tsintsiyar hannunsa wanda yake mix da zallar ruwan gwal ya kalla
"Zan wuce office,akwai wani abu da kuke buqata?" Kai ta girgiza
"Babu komai,amma ga abinci ko zaka ci" wajen ya kalla,ya sani baba tabawa is the best cook a duk gidansu,tana cikin list din mutanen da yake iya zama hankali kwance yaci abincinsu,amma yanzun sai yakejin bazai iya zaman ba,baima saba cin abinci cikin gidan ba, infact ma bai taba ba
"Ina sauri ne,zan makara"
"Amma akwai kunun gyada irin wanda kakeso,ka daure ko cup daya kasha" ta fada tana hada masa da sauri,bayan ta saka madara da suger madaidaita,don tasan bai cika sonsu ba
"Na gode" ya fada yana karba,har cikin ransa yaji dadin hakan,yayin da baba tabawan ke karantarsa a fakaice,babu wadda ke girki a cikinsu ta bashi kenan?,abinda ya fara zuwa kanta kenan,lallai akwai aiki jazur a gidan,akwai kuma gyara.
"Tana ciki,ina tsammanin ta tashi,zan shiga ciki na watsa ruwa" tayi masa tayin shiga wajen maimunatun a fakaice,tanason haifar da kyakkyawar alaqa a tsakaninsu,tanason tayi wani aiki da anni zataji dadinsa,sannan kuma ba zata manta dashi ba. Bashi da wani sauran zabi face soma takawa a hankali zuwa dakin,tunda har ta fahimci bashi da nufin shiga,bayaso ta zargi wani abu a ranta game dashi,ya kuma tabbatar kome yayin kamar yayishi ne gaban idanun anni,tunda da ita da anni duka abu daya ne,hannunsa guda daya cikin aljihun wandon suit dinsa,daya hannun kuma cup din kunun ne yana sipping a hankali,ya masa dadi qwarai,ya kuma yi masa yadda yakeso.
Daure da babban towel ta fito daga bandakin,ta dora qarami saman kanta da yadan jiqe ya kuma bawa sumarta daman kwanciya a bayanta da gefan fuskarta,yau din sakayau take jinta,da alama lafiya tana sake samuwa a gareta,kai tsaye ta isa gaban mirror taja dressing chair ta zauna tana kallon fuskarta data yi wani irin haske ta kuma yi fresh har ita da kanta abun yana bata mamaki,kamar zaka taba ta jini ya fito,ta canza totally,irin canjin da ita da kanta yake bata mamaki.
Towel din saman kan nata ta cire ta fara goge fuskarta dashi tana maida sumartata dake son shige mata idanu baya,bayan ta miqa hannunta ta jona hand drayer amma bata kai ga kunnata ba,tana goge gashin nata tana dan rera karatun qur'ani,haddarta ta qarshe da bata baiwa ya shaik nasu ba,saboda zazzabin da ta dinga fama dashi kafin tafiyarsu hutu,ta miqe tsaye tana ture kujerar baya,ta kunna hand drayer din ta soma busar da kanta in a low heat.
Dai dai sanda ya murda qofar dakin ya kuma turo cikin cikakkiyar nutsuwa,tashin farko qamshin hair mist dinta dana hair oil da take amfani dashi wanda ya cika dakin saboda zafin hand drayer din dake kadoshi,ya kuma cakude da qamshin turarenta daya kama dakin suka buso saman fuskarsa.
Wata ajiyar zuciya ce ta qwace masa ba tare daya shirya hakan ba,bai kuma san dalilin faruwar hakan ba,ajiyar zuciyar data wuce da idanunsa suka lumshe na wasu gajerun sakanni sannan ya budesu tarwai,basu sauka ko ina ba sai santala santalan qafafunta da suma fito ta qasan towel din da take daure dashi,wanda ya tsaya mata iyaka gwiwarta,soma yawo yayi da idanunsa zuwa samanta,faffadan qugunta ya fito sosai ta cikin towel din,kallo daya zaka masa kasan daya daga cikin baiwar da Allah yayi mata ne,ci gaba yayi da kallonta zuwa sama,bayanta dake dauke da farar fata me sulbi da qyalli ya bayyana muraran,da wasu daga cikin gashin kanta da suka kwanta luf a kansa.
Cikin nauyin zuciya da kuma mutuwar jiki ya daga qafafunsa yaci gaba da shigowa dakin ba tare da maimunatu tasan an shigo ba,don zuwa sannan ta tattaro sumar tata zuwa fuskarta tana tajewa bayan ta kashe hand drayer din,tana kuma ci gaba da rera karatunta da qaramar muryarta mai zaqi da sanyi,karon farko ya sake sakin boyayyar ajiyar zuciya,qira'arta sak irin ta shaheeda,qira'ar malami guda suke bi,sai ya maida qofar ya rufe ya sake matsowa ciki sosai sannan yayi sallama idanunsa bisa kanta.
44
Sosai ta tsorata kamar yadda ta saba,comb din hannunta ya sulale a qass,bugun zuciyarta kuma ya sauya,zuciyarta ta fara tantama shine ko muryarsa ke mata gizo?,don gusar da tantama sai ta waiwayo cike da fatan ya zaman bashi bane.
Ido hudu sukayi dashi sanda yake kurbe kununsa,wannan tsoron dake haifar da wani kyau cikin qwayar idanunta ya bayyana muraran,hakanan yadda gashin kanta ya sauko ya qawata fuskarta ya kuma yi mata ado sosai,ba tare data qara tunanin komai ba ta laluba hanyar toilet,ta manta da cewa qofar toilet din yafi kusa dashi akan inda take tsaye.
A nutse ya dire cup din a saman side drower din dake gefansa idanunsa a kanta yana jiran isowarta,goye hannayensa yayi a qirji yana kallonta har xuwa sanda ta qaraso dab dashi da niyyar wucewa a rude,babu zato kuma babu tsammani taji an ruqo dukka hannayenta gaba daya,sannan kuma ya jata zuwa cikin jikinsa,ya rungumeta ta baya,hannuwansa riqe da dukka hannayenta biyu,rungumar data sanyashi cikin nadama bayan ta samu kyakkyawan masauki cikin jikinsa,gashin kanta ya musu rumfa gaba daya shi da ita,sahihin qamshin hair mist din da yake ji daga nesa bayan ya shigo dakin a yanzun yaji ainihinsa,lallausar fatarta data gama mulketa da wani body lotion mai wani irin sulbi da qamshin rose ta gogi jikinsa,saura kadan yayi missing numfashinsa na gaba,dukka gabbansa suka saki,wani irin yanayi da bai taba zata ko kawowa zaijisa daga kowacce mace ba macen ma irin maimunatu da yakejin zai iya haifar kamarta lokaci daya ya saukar ma kowanne lungu da sawo na sassan jikinsa.
A jikinta ta dinga jin kamar jinin jikinta ke daskarewa saboda tsoro.
Tun daga tafin qafarta zuwa hannayenta dake cikin nasa sunyi wani irin sanyi saboda tsoro da mamaki,kasantuwarta a jikinsa sai takejin kamar cikin wani mafarki take,ire iren mafarkan da suka takura mata kwanakin baya,har ta dinga tsammanin tana da wata lalura data shafi jinnu,amma kuma bayan sun karanta a fiqhu cikin alamun balagar mace da suke nuna kaiwarta munzali irin wannan mafarkin sai hankalinta ya kwanta ta kuma fuskanci abinda ke faruwa da ita.
Tsigar jikinta ce tayi wani mugun zubawa,kanta kuma ya sara sanda hannunsa ya shafi wuyanta a qoqarinsa na tattare gashin nata gefe guda,bata warware ba daga wannan taji ya juyota gaba daya tana fuskartarsa cikin hanzari,tashin hankali!!....ta fada qasan ranta,ta fiddo idanunta dukka waje tana jin yadda towel dinta ya kunce daga daurin data masa,ya kuma fara warwarewa a hankali a hankali,ta kuma yi imanin nan da wasu sakanni zata iya kasancewa tsirara kenan?.
Ta bangarenshi baisan me yake faruwa ba,yadda ta zare idanun nata ya sake haifar masa d wani abu ya kuma gasgata masa tsananin tsoronsa da takeyi
"Why all this fear?Am I a monster?" Yayi maganar yana kafeta da ido,da mugun hanzari ta girgiza kanta,tun kafin ma yakai aya,cikin shagwabarta data zame mata jiki,shagwabar da a baya idan inna furera ta daketa ta fara bata haquri sai tace da ita ba tare da duba da cewa haka yanayinta yake ba tun usuli
"Shegiya karuwa,wannan,irinku ne idan kuka kama mazan jam'a a bariki ba matarsa ba,haar uwarsa saidai ta sallama muku shi"
"Kayi haquri don Allah" maganar ta fito da wata siririyar qwalla daga idanunta,saboda yadda taji towel din naci gaba da ware kansa.
Idanunsa ya lumshe kadan sannan ya sake budesu,hawaye.....hawaye,he hated it,me yasa kuka baya mata wuya?,shagwaba kamar 'yar fari ko auta?,yayi qiyasin hakan a ransa ba tare da yasan ita din bace
"Nooo,dole ki nunan abinda yake baki tsoro a jikina" kai ta shiga gyadawa
"Babu komai"
"It's a lie kuma ban yarda ba" ya fada yana tsuke fuska tare daci gaba da kallonta
"Allah....wayyo Allah daadata!" Ta fadi kukanta yana qaruwa tana kuma neman durqushewa a wajen saboda jin ya fara salube mata.
Dubansa yakai ga jikinta,sai a sannan shima ya karanci meke faruwa,wani mugun shock yaji sanda idanunsa suka kai kan saman rabin dukiyar fulaninta da suka fara fitowa,ba tare da tunani na biyu ba ya sakar mata hannuwanta da gaggawa ya kuma juya mata baya,sannan a hankali ya nufi inda ya aje cup dinsa ya dauka yana ficewa daga dakin ba tare da ya jira komai ba.
Bai samu baba tabawa a falo ba,sai ya fice kawai daga sassan ya kuma wuce parking lot,inda ya samu drivernsa yana jiransa,bai jirashi ya bude masa qofar ba ya bude ya shiga,sannan ya bashi umarnin tafiya.
Sosai yayi relaxing a bayan motar bayan ya kulle idanuwansa yana sauraren yadda bugun zuciyarsa ya sauya cike da mamakin faruwar hakan a gareshi,fuskarta da gifta duhun idanuwansa sanda take kukan,wanne irin tsoronsa take haka?,idan ta bayyana hakan gaban mutane akwai wanda zai yarda dashi kan ba wani mummunan abu yake aikata mata ba?,bude idanun nasa yayi a nutse yana duban hanya,a hankali qamshin jikinta yake yana tashi ta gaban suit dinsa da hannayensa,sai yaja dan qaramin tsaki,yana ji a ransa he's totally wrong.
Ta jima a duqe a wajen tana sharar qwalla,don batasan ma ya fita a dakin ba sai da taji shurun yayi yawa,a hankali ta daga kanta,ta tabbatar baya dakin,sannan taja jikinta daga wajen,tana riqe da towel din nata gam,kamar wadda aka ce za'a qwacewa shi,saman gadonta ta nufa ta zauna,amma sai zaman ya gagareta,wani irin mutuwan jiki takeji da kasala,gaba daya kamar an samu abu an buge mata gabbanta,gefe daya kuma zuciyarta kwata kwata babu dadi,musamman idan ta tuna a yau din wani namiji ya ganta a rabin tsirara,sai wasu sabbin qwallar su sake zirto mata,saidai ta saka hannu ta shafesu.
Ta kwashe awanni masu yawa a haka,ita ba me lafiya ba ita ba mara lafiya ba,bata tashi ta shirya ba hakanan bata fita a bedroom din nata ba,abu daya ne ya tsaye mata a rai yake ta mata yawo,duk juyin da zatayi sai abinda ya farun ya wulga mata a idanunta,hakanan duk motsawar da zatayi sai mayataccen qamshin da ya bar mata ya kada har qwaqwalwarta,tamkar a yanzun ne yake tsaye cikin dakin,tafukan hannuwanta gaba daya sun rune da qamshin wani dan mitsitsin oily pen perfume da yake amfani dashi,idanunta ta lumshe tana shaqar qamshin har cikin qwaqwalwarta,yana silalewa a hankali zuwa zuciyarta,sai ya tuna mata da handkerchief dinsa dake wajenta,d same qamshin da yake jiki kenan,best scent ever data taba ji me wani irin yanayi,duk da yadda zuciyarta keta qyamatar qamshin amma ta kasa daina shaqarsa,daga qarshe bayan ta gama shafe awanninta,haka ta janyo mataccen jikinta ta sauko daga gadon ta nufi toilet ta sake wanka,waiko zata samu ta raba fatarta da mayen qamshin dake qara mata kasala.
Koda ta fito ma tsaiwa tayi gaban mudubi tana duban yadda fuskarta tayi jaa saboda kukan da tayin,ta sauke idanunta saman qirjinta tana tuna a yadda ya ganta,sai ta dan zame towel din tana iya dai dai yadda ya kufce mata a dazun,dukka idanunta ta qwalalo waje,indai towel din yakai haka sakkowa tabbas yaga fiye da rabin jikinta,wasu qwalla masu zafi suka sauko mata,amma kuma sai tayi hanzarin gogesu sanda taji muryar baba tabawa tana knocking qofar gami da tambayarta lafiya ta jita shuru?,ta fito ta karya kada abincin ya huce
"Gani nan fitowa baba" ta amsa mata,sannan taja lotion dinta da hanzari tana sake sabon shafa.
Cikin doguwan rigan wani material mara nauyi ta shirya,ta gyara sumarta ta hadeta waje daya,sannan ta yafa dankwalin kayan,har tayi gaba ta dawo ta dauki wayarta sannan ta fito.
A zaune a falo ta samu baba tabawa,daga kanta tayi da niyyar cewa wani abu sai suka hada ido da maimunatun,tadan zuba mata idanu kadan saboda yadda fuskarta take nuna tayi kuka,kamar zata ce wani abu sai ta fasa,saboda ta tuna dazun,shima taga fitarsa daga dakin da wani mugun hanzari,hakan yasa taji bai kamata tace komai ba,don tsakanin miji da mata sai Allah,fatanta kawai ubangiji yasa ba wani abu mara dadi baje ya faru a tsakaninsu ba,kuma Allah ya kawo daidaito tsakaninsu nan kusa.
Kadan ta zuba abinda baba tabawan ta dafa ta fara tsakura,saida kadan taci ta tashi,saboda tana jin cikinta gaba daya ya cushe,kamar babu wani sauran space na zuba abinci,data dawo saman kujera ma kwanciya tayi,yau ko hirar da sukanyi da baba tabawan jifa jifa ta dinga yinta,tans ankare da ita,lokaci lokaci sai tayi kamar ta tafi tunani,sai kuma ta sauke ajiyar zuciya taci gaba da abinda takeyi.
Kafin azahar jiki da zuciyarta yayi laushi qwarai,sanda