Advertisements
Chapter 2 Reading Sakacina Ko Halin Maza Complete Hausa Novel Hausa Novels
Advertisements

Sakacina Ko Halin Maza Complete Hausa Novel

Author :  Jamsy Category :  Complete Novels

Chapter   2 / 48

3K to 6K   out of 143.8K words

saka ta yadda tuwon ya zube ba,ta zabura ta mi?e hanyar gida dai dai sanda ta ji ya na faWin."Ni da kene a duniyar na baza ki taSa jin daWi ba matu?ar ina raye,haka kawai na yi sakaci har tunanina ya faru mu zu ba mu gani
Juwairiya na shiga cikin Waki ta fashe da kuka mai tsuma zuciyar mai sauraro,a ranta ta na jin ba?in cikin halinsa bata san mai ta tsare mishi ba,amma ya saka ma rayuwarta ?ahon zu?a.
Koda ta shigo Mama ba tace komai ba har ta sha kukanta ta ?oshi don tasan mai ya faru,tunna babu abin da za ta iya shi yasa bata tanka mata ba,sai ta jawo kwanon tuwon ta ba Ibrahim sannan ta bashi magani ragowar taci ta ragewa Juwairiya duk da babu miya kuma ta ji ?asa-?asa a tuwon.
Bayan ta gama kukan taji sanyi a zuciyar ta dama kukan shi ke sanyaya mata zuciya,duk lokacin da ya yi mata hakan don babu wanda yake ko tari a cikin iyayenta,su kansu tsoron sa suke yi duk da mahaifinta shine babba.
Mi?ewa ta yi ta Wauro alwala ta yi magariba sai ta yi zamanta ta na jan carbi yayin da hawaye ke zuba fuskarta,wani gefe na zuciyarta ta na hasaso mata lamura sosai game da Baba Sani.
Baba Sani ya yi tsaye a gurin bayan tafiyar ta ya na tunani sannan ya ?arasa dakalin ?ofar gidan ya zauna ya na gadin masu zuwa gurinta,ko da ka kira sallar isha'i ya yi sannan ya dawo ?ofar gidan ya ci gaba da gadin gurin.
Sai misalin tara na dare mahaifin Juwairiya ya yi sallama ya shigo da ?ullin leda mai Wauke da garin rogo gwangwani biyu da siga.Mama ce ta amsa sallamar ta ?arbi ledan tare da shinfiWa mashi tabarma,lokacin har baccin wahala ya fara Waukar ta don yunwa take ji matu?a kuma kamar zazzaSi yake son kama ta.
Jin sallamar ya sa ta buWe idanu ganin leda a hannun Mama ya sa ta mi?e tare da ?arban ledar bayan ta yi mishi sannu da zuwa ta fice dan ta ji?a garin.Ya kalli Ibrahim dake kwance ya na bacci ya shafa fuskarsa ya na faWin." Ya jikinsa?Ina can amma hankalina ya na nan kin san jiya ?afarsa ta bani tsoro."Yace ya na lasar bushashshen bakinsa dan rabon sa da abinci tun jiya da yamma da suka girka taliya leda Waya gashi ya wuni ya na faskare.
"Da sauki amma ya kama ta a maida shi asibiti gaskiya,yau ya bani tsoro ina ki kamar zan rasa Ibrahim saboda halin talaucin da muke ciki."Tace sai kuma ta rushe da kuka ta na fyace majina.
A sanyaye Juwairiya ta ije garin da ta ji?a ganin Mama ta na kuka ta koma gefe ta zauna ta na jin zafin Baba Sani dan ita gani take shi ya takurawa rayuwarsu da ya hana ta naimi aiki,in da ace ta na aiki rayuwar su ba ta yi muni haka ba,ga Mariya da take aikin suna jin daWi kuma matar ta na taimaka musu.
"Ki bar kuka dan Allah da kin san halin da na wuni da kin tausaya min!Na dage tu?uru ina faskare sai da na gama Malam Aminu yace bashi da kuWi sai gobe,da?yar na samu ya bani naira Wari biyu wai shima kwana biyu ba cinikin iccen.
Shuru sukai cikin jimamin rayuwar su kowa ya na takaicin yadda suke tsotsan tsamiya,ganin Baba ya dawo Juwairiya ta mi?e tare da yi musu sai da safe ta tafi Wakin da take kwana.
Washegari da safe misalin bakwai da rabi ta shafa addu'a,sannna ta mi?e ta nufi waje dan wanki zatai da aka kawo musu da safe kuma ana so anjima,murna sosai ta yi dan aka wo kuWin wankin za su sami su yi girki.
Da sauri ta ?arasa ta na faWin."La Mama har kin fara."Bata ce mata komai ba sai botiki da ta mi?a mata ta ibo ruwa a randa.
Basu gama wankin ba har misalin tara da rabi bayan sun gama Juwairiya ta fita tayo musu cefanen taliya suka dafa da mai da yaji.Bayan ya dawo daga sallar asuba ya kwanta don ji yake ko ina na jikin sa ya na ciwo,bai tashi ba sai da aka gama girki shi ma sai da Juwairiya ta tashe shi,dan tasan yunwa ce ke damunsa.
Bayan yaci abincin ya mi?e tare da fita ya na son ya ga kanin nasa,akan maganar komawa da Ibrahim asibitin da kamar yadda likitocin suka faWa.
Ya na ?o?arin shiga shashinsa suka yi kicibis saura kaWan su yi karo,Baba Sani ya matsa ya na kallon Wan'uwan nasa ya ce."Lafiya yaya baka da lafiya ne?Ji yadda ka koma kamar wanda ake iban shi ana miya."Yace da maganar shi ta izgilanci ya na karkaWe jakar zuwa aikin shi,dariya kawai ya yi mai kama da ya?e yace."A irin wannan rayuwar ka na sane da halin da nake ciki ni da iyalina,yanzu ko taimakon da kake yi min ka daina."Ya ?arashe magana da takaicin yadda Wan'uwan nasa ya daina taimaka mishi tun tsawon shekaru da irin butulcin da ya yi mishi.
Hannun shi ya watsa ya kalleshi ya na kallon agogo."Sauri nake yi yaya kaga na yi latti kuma kasan yanayin aiki na,yi sauri ka faWi abinda ke tafe da kai.Kuma da kake maganar ba na taimaka maka nauyi ne ya yi min yawa kowa ya ji da kansa."
"Haka ne Allah ya shige mana gaba,amma ya kama ta ka duba rayuwar Juwairiya kaga ni bani da shi da zan saka ta a makaranta,kuma kace ba aure zakai mata ba baka da ?uWin auren da ita."
"Haka na ce don ni yanzu ba ta aure nake ba,sabon gidana nake son na kammala.Ya bashi amsa a ta?aice sannan ya Wora da ce wa."Kuma da kake maganar na saka ta a makaranta baka ga yadda take mara kamun kai ba can zata dinga watsewa da mutane,ka na sane da irin ?orafin da nake maka a kanta ni nasan halinta da nake zaman gida."
Shuru ya yi ya na takaicin abinda ya faWa ransa ya yi zafi,shi dai yasan kawai ya tsaneta ne amma yasan wacece 'yarsa wani irin hali take dashi.
"Yaya na fa gaya maka aiki zan tafi amma ka tasa ni gaba kana ta wasi?ar jaki,ina sauri ne in kima baka da abin faWe na tafi imna dawo saimu tattauna."Ya ce dashi ya na ?o?arin fita da sauri ya tare shi sannan ya ce."A kan maganar komawa da Ibrahim asibiti ne,kuma gashi bani da kuWi dan Allah ka taimaka...."
"Haba yaya kasan fa bani da ?uWi nima hidima tayi min yawa kowa yaji da kansa,amma ga dubu Waya kuje Allah ya ba da lafiya."Ya mi?a mishi 'yan Wari biyar guda biyu ya fice ya barshi a tsaye kamar sanda ya na tunanin butulci irin na ?anin nasa.
A sanyaye ya shigo cikin sasan sa ya zauna akan turmi kamar babu laka a jikinsa,bai ce komai ba har zuwa wani lokaci sannan ya ja numfashi ya na kallon Mama dake ninke kayan da suka wanke har sun fara bushewa.
"Lailai Wan adam butulu ne."Yace cikin raunanniyar murya sannna ya Wora da cewa."Wai yau ni Sani yake wula?anta wa kan kuWi ya manta yadda na wahala dashi dan ya sami ingantacciyar rayuwa.Mama ba tace mishi komai ba sai gyaran murya da ta yi,dan babu wani abu sabo a cikin halinsa duka sananne ne a gurinta.
Juwairiya na kwance bayan ta tashi ta yi sallar nafila ta yi addu'a ta koma ta kwanta,idanunta babu alamun bacci sai juyi take yi ganin haka sai kawai ta janyo carbi ta na ja,idanunta a rintse zuciyar ta na fatan samun maslaha a rayuwar su tunannin ta inda za'a sami kuWi a mai shi asibiti,don likitocin suna tunanni aiki za'ai mishi a ?afar.
Kawai sai ta ji ana ?o?arin buWe ?ofar Wakinta tsoro ya kama ta,tunawa da ta yi ta manta bata saka sakata ba da ta fita zuwa alwala.Tsananin tsoro ya kama ta ta rintse idanunta ta na tunani ta ya ya kai wani ya shigo cikon gidan su,dan Baba Sani ya gyara gidan kuma akwai ?ofa na masu kuWi mai ?arfi gidan.
Ba ta gama wannan tunanin ba ta ji mutum ya shigo ya nufi makwancinta,ta buWe baki da nufin ta yi ?ara sai kawai taji an toshe mata baki da wata irin murya da nufin a Satar da tunanin mutum ga sanin mamallakin muryar aka ce."In kika yi ihu saina kashe ki?Ya faWa tare da soka zungureriyar wu?a dai dai cikinta,amma ta yadda bazai cutar da ita ba.
Wani irin tsoro da tashin hankali ya ziyar ce ta taji tam?ar numfashinta zai yi balaguro zuwa wata duniyar wacce take da banbanci da wacce take rayuwa a cikinta."Da gaske abin da sautin amon kunnnuwana suke gaya min muryar Baba Sani take amo a cikin dodon kunnuwana?To mai ya shigo dashi cikin Wakina a wannan sulusin daren?"Irin tarin tambayoyin da suke ta bijiro mata a cikin zuciyar ta wacce ba ta samu ko da amsar Waya ba.
_Kar dai ku manta sunan labarin "SAKACINA KO HALIN MAZA" Mu haWu a shafi na uku dan har yanzu shinfiWa ne har ba'a fara ba.Ga masu bu?atar shiga cikin group Wina na whatsapp ga numba 08144072423_.


Kuma ?ofa a buWe take na ?orafi gyara ko ?arin bayani ga zakakuran marubuta,har yanzu ni mai koyo ce.
Kar dai ku man da wannan lintafin sadaukar wa ne ga za?auran marubuciya,kuma ?awata (SUMAYYA NA'IGE) Allah ya ?ara fasaha ya sa ki fi haka,ina alfahari dake a cikin marubuta da irin taimakon da kike bani.




*FOLLOW, READ, COMMENT, SHARE*





*SAKACINA KO HALIN MAZA?*



*RUBUTAWA:-*
*JAMILA LAWAL ZANGO*

*SADAUKARWA GA:-*

*SUMMY M NA'IGE*
_(Aminiya)_


*FIRST CLASS WRITER'S ASSO....*

*SHAFI NA UKU*



Hannun Baba Sani ya sauka a ?irjin Juwairiya tare da wasu tagwayen hawaye masu tsananin zafi da ?una a fuska.Ta jin wani irin tsananin tashin hankali a zuciyarta yayin da take ji a cikin zuciyar ta tamkar za ta haWiye zuciya ta mutu."Da ma burin sa kenan a kai na ya hana rayuwata samun sukuni,kullum ya na bibiyata tare da da?ile farin cikina?Me na yi masa wanda ba zai iya Wauke mugayen idanunsa a kaina ba,a matsayina na ?ar wansa wanda suka fito ciki Waya?Wayyo Allah ina ma ace ranar mutuwa ta ce aka nuna min ba wannan ranar mai ba?in gani da muni a cikin zuciya ta ba.Ihu ya kama ta na yi ya kashe ni kamar yadda yace ko na yi shiru ya Sata min rayuwa?"Ta tambayi kan ta cikin tsananin ruWani dai-dai lokacin da ta ji saukar hannun sa a hurumin da ba na shi ba.Sai ta rufe idanunta ta na kiran sunan Allah tare da karanto duk addu'ar ta da fito daga cikin bakin ta.
Da sauri Baba Sani ya janye hannun sa daga ?irjin ta tare da fasa abin da ya yi ninya,jin motsi daga waje."Sannu Malam ka yi a hankali jikin ka babu ?arfi."Suka ji muryar mahaifiyar Juwairiya ta na magana cikin tausayi.
Hankalin Baba Sani ya tashi sosai ya daWe ya na dakon wannan ranar tun lokacin da Juwairiya ta fara girma ya saka kwaWayin sa a kanta,gashi ya sami dama amma kuma kamar hakonsa bai cimma ruwa ba.
Dai-dai saitin kunninta ya saita tare da raWa ma ta."In kika yi magana sai na kashe ki."Hakan ya sa Juwairiya kame bakin ta ta yi shuru sai hawaye dake zuba a fuskarta.
Ya tsorata iya tsorata ganin sun shige cikin bayin ya buWe kofar ya fice cikin sanWa,Juwairiya ta fashe da kuka tare da fita daga cikin Wakin a ranta ta ?udirta ba za ta ?ara kwana a cikin sa ba.Fitowar ta ya dai-dai da lokacin da suka fito daga cikin bayin.FaWawa kan jikin Mama ta yi ta fashe da kuka ta na wani irin kuka mai ?arfi da ta da hankali ba ta damu da daren da ya tsula ba.Cikin tashin hankali da tsoro Mama ta rungume ta ta na faWin."Lafiyar ki Waya Juwairiya dare ne fa?Ko kin yi gamo ne."Irin tarin tambayoyin da take mata amma ba ta kula ta ba sai kuka da take yi mai Waukar hankali,ganin kukan na ta ba na ?arewa bane Mama ta ja hannunta suka shiga cikin Waki lokacin Baba har ya shige ya kwanta,saboda gudawa da yake fama da shi ya kasa tsaya wa ya tambayi abin da ke faruwa.
"Mai ya same ki lafiya?"Mama tace don zuwa yanzu kukan ya fara ba ta tsoro ta na ganin kamar Juwairiya gamo ta yi,yayin da ta wani gefen ta fara ba ta haushi bacci ne sosai a idanunta.
Juwairiya ta kasa magana sai kuka haka Mama ta yi ta gaji ta koma ta kwanta yayin da ta barta zaune tamkar ta haWiye zuciya ta mutu.
Washegari da safe Mama duk lallashin da ta yi mata akan ta gaya mata abin da ya faru,amma ta?i ?arshe sai dai ta yi mata ?aryar mafarki mara kyau ta yi.Mama ba don ta yadda ba ta ?yaleta amma zuciyar ta ta na gaya mata a kwai Soyayyen lamari,kasancewar Juwairiya ba ta taSa kasa kwana ita kaWai ba.Hankalinta ya tashi musamman da Juwairiya tace mata ba za ta ?ara kwana a Wakin ita kaWai ba,sai dai a haWa ta da Ibrahim wanda Mamma bata iya kwana sai da shi saboda ciwon sa,gashi ta na da mugun bacci.Duk da jikin Baba da ya kwana babu daWi amma haka nan ya shirya ya fita bayan ya sha magani.
Wunin ranar Mama ta kasa gane kan Juwairiya duk irin tarin tambayoyin da take mata,don ko ruwan koko da ta dama ta?i sha daga ?arshe wani ?arya sake yi mata tace ba ta da lafiya.
******
Gidan cike yake da mutane kai da gani kasan ana farin ciki a dalilin bikin ?a?an gata, ga kayan abinci da na tsotse-tsotse da a ke ta fita da shi.Bikin na yaran manya ne waWanda duniya take hannun su kuma ta yi na'am da zuwan su duniyar,suke rayuwa a yadda suka tsara kuma suke ?urSar ruwan daWi a cikin ta.
Naira ta na tsala kuka tare da nai man taimakon agaji da son Soyeta domin ta adana kanta ga masu bu?atar ta.Ruwan kuWi kawai yake tashi da jerin gwanon motoci wanda ba zasu irgu ba.Wannan biki ne wanda ya amsa sunan sa kuma ya bu?aci a buga a jarida,wato bikin Muhammad Dawood Turaki da amaryar sa Zainab Abubakar mai shadda.Waye bai san waWaWnan hamsha?an masu kuWi da samu rayuwa mafi ?ololuwar daWi a gare su ba.
Muhammad Dawood Wa ne ga wani hamsha?in mai kuWi daga cikin turaki Family,wanda duniya ta san shi har da ?asashen waje don ma yafi gudanar da harkokin sa a can.Tsarin rayuwar su irin na turawa da zallar boko.Gida ne na ?anci da rayuwa babu ta?urawa da samun kwanciyar hankali.Suna da matu?ar kyau da asali mahaifin sa haifaffen garin Zariya ne.Ya gina katafaren gidan sa mai kyau a unguwar Zangon shanu,gida mai kyau na bene da tsari.Matan sa biyu Hajiya Khadija wato mahaifiyar A.m sai amarya Hajiya Binta Yaran sa bakwai Muhammad shi ne na farko wanda aka fi sani da A.m,sai kanin sa na miji sauran mata ne guda biyu sai kuma bangaren amarya ta na da uku.Suna zaman su lafiya kuma kan su a haWe yake.
A.m mutum ne mara daWin sha'ani ga rashin ha?uri ga saurin ?ulewa,ba ka taSa gane in da ya sa gaba shi kullum mutum a gurin sa bai iya ba kuma ba a yi mishi gwanin ta ba.Kannin sa suna shan faWa shi ya sa basa ?aunar ya zauna a gida in kayi magana,yace ka faye surutu in kayi shuru yace ya na magana an raina shi.Shi komai a gurin sa laifi ne sannan ba shi da fara'a ko wasa ba ya yi dasu.FaWin halin A.m abu ne mai wuya domin ya na da murWaWWen hali baka gane in da yasa gaba,wannan dalilin ne ya sa ba shi da wasu abokan sai A k wanda ya jure halin sa duk da wani lokacin shi ma hutsu ne,amma ya san yadda yake tafiyar da shi.Muhammad Wan gata ne a gurin mahaifin sa ga shi fari kyakykyawa dogo mai aji da tsafta.Wan mahaifin sa Alhaji Sama'ila ya na matu?ar ji da shi domin a hannun sa,ya tashi ya ma fi Daddy sa kuWi sai dai shi Allah bai ba shi haihuwa ba.
Ya na matu?ar son yaga ya haihu saboda ya samu magaji har ?asar waje ya kai matan sa uku a ka yi musu dashen kwai,amma Allah bai nufa cikin zai tashi ba,?arshe daga baya kan dole ya fauwala ma Allah lamuran sa ya na addu'ar Allah ya sa ya na da rabon haihuwa a duniya.
Tun kafin a haifi A.m mahaifin sa ya yi ma Yayan sa al?awarin ba shi duk abin da ya haifa,saboda haka ana yaye shi aka mi?a ma matarsa Karime.A.m ya taso cikin gata da shagwaba bai san damuwa ko a kasin haka ba.Duk karatun sa a ?asar waje ya yi in da ya karanci (Economis)bayan ya kammala ya dawo gida Nigeria amma ba ya wata yake fita waje.
Family Win Turaki mutane ne da ba ruwan su da harkan talaka ba sa hurWa dasu,kuma ba sa shiga sha'anin su.A.m da ya tashi Wauko tsanar talaka sai yafi kowa a cikin Family Win na su,don shi tunanin sa laifin sa ne da ya?i tashi ya nema ya tsaya lalaci.Saboda mugun tunanin sa akan talaka ya sa ya tsani ma'aikatan gidan su kullum cikin hantara da mari yake musu laifi kaWan zai kai duka,musamman masu aikin cikin gida.
Zainab Abubakar ?ar gidan wani Wan majalisa ne da yake tashe a yanzu kuma hamsha?in Wan kasuwa.Yarinya mai tashen kyau da ?uruciya ta na ji da kanta tare da alfahari da kyan da Allah ya yi mata,ga Wagawa da son nuna ita ma wata ce mai ilmi da kuma nera.Sannan ra'ayin ta yazo Waya da A.m na ?in talaka ba ta da kirki sosai,amma in baka shiga

2 / 48