Advertisements
Chapter 34 Reading Me Kamar Sarki Book 2 Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Me Kamar Sarki Book 2 Hausa Novel

Author :  Yusrah Musa Category :  Complete Novels

Chapter   34 / 67

99K to 102K   out of 200.4K words

domin koma maye haka kawai bazai daketa batai masa komai ba tunda dai abun yazo da haka saimu jira ta farfad'o za kuwa taci ubanta daga lokacin dana gane cewa itace mai laifin zata yabawa aya za'kin da take dashi".

"Shikenan Allah ya rufa asiri tunda haka ta sakance zuwa dare idan su Ameer sun dawo duk abinda likita yace sai ayi idan kuma sun gagara nema sai mubi shawarar Ameer a fita da ita wajen".

"To yaya dama ni akwai inda zanje kafin yanzu gashi lokaci yana neman fita min nima sai daren zan dawo".

Kai mai martaba Alhassan ya d'aga yana cewa "ok ba matsala ka kula" yana mi'kewa Sultana Shafi'ah ma mi'kewar tai suna fita tare yayin da Sultana Hadizah ta tashi cikin kishi ganin sun fita buguzun buguzun tana hararar Mami tabi bayansu sai tsinewa Asad take a ranta d'an tsaki Mami tai itafa dama harga Allah Sultana Hadizan nan tun ba yanzu ba ta fahimci inda ta dosa sosai bata son laifin 'ya'yanta sannan ta maida d'an wani banza nata kuma dukiya hummm kullum tayi sallah tana ro'kon Allah yasa Khimiyyah ta farfad'o kodan Sultana Hadizah taji kunya ta gane 'yarta ce mara gaskiyar da bataso a fad'a..............................

"Hauwa'u kinyi magana da Asad ne"? Jin saukar muryar mai martaba yasa ta dawo daga duniyar tunanin data fad'a tana maida hankalin ta kansa tace.

"Na'am Allah ya baka nasara me kace"?.

Da mamaki mai martaba ya sake kallon ta yana cewa "tunanin me kike yi haka har nai magana bakiji ba ko abun ya damaki ne"?.

Kai Mami ta girgiza tana murmushi tace "a'a mai nasara babu abinda dake damuna kawai dai banji me kace ba".

"Ok cewa nai kinyi waya da Asad ne jiya ko yau"?.

"Eh munyi magana dashi jiya munkai kusan karfe sha biyu na dare a online yana fad'a min cewa sun ma fita operation ne cikin wani daji zasuyi kusan wata guda kafin su fito yanzu baida lokaci sosai kuma ba damar kiransa ta shiga saita chat dole wajen babu network".

Da murmushi a fuskar mai martaba yace "Tofa Asad d'ina yana can a daji gurin ma'kiya tab umh Allah ya fito dasu lafiya shiyasa Ajeeb yace bazai soja ba akwai wahala ya za'bi doctor馃懇鈥嶐煍 Annur ya za'bi banker馃懇鈥嶐煆 Ameer yace lawyer馃懇鈥嶐煄 amma Asad ya d'age sai soja馃懏yafi son a ri'ka marmarinsa daga nesa balle abina yana da kwarjini ko bai soja ba da gani ba raini".

Dariya Sultana Fatima tai tana cewa "ra'ayi kenan cin d'an wake da diga kowa aikin daya kama zaiyi mana amfani Annur ba ruwan mu da wani harkar zuwa banki ciro ko sa kud'i Ajeeb yana duba lafiyar mu babu ruwan da hospital ga Ameer lawyer kaga shima zaiyi mana amfani ko".

"Humm zaiyi kam tunda ga Sultana Hadizah tana zancen zuwa kotu saboda rashin tunani" mai martaba na rufe baki Mami tace.

"Oh wai da gaske take sai takai 'karar da take magana"?.

"Lallai hauwa'u amma kin manta wace ita idan ana neman mace mara kirki da kara azo wurinta itace karshe".

'Dan ta'be baki Mami tai cikin rashin nuna damuwa tace "Allah ya kaimu lokacin fatana Khimiyyah ta tashi Allah yasa yarinyar nan karta mutu kawai ina so Sultana Hadizah ta fahimta ta gane abinda ya dace da wanda bai dace ba domin yawancin lokuta tana yin abu da ka kuma a gurin ta daidai ne".

"Humm bari kawai tabi a sannu duniya makaranta wanda bazai bama jiransa take balle wanda yake cikinta ya d'au rayuwa da fad'i" Mami ta karasa maganar tana jijjiga kai d'orawa Sultana Fatima tai da cewa.

"Ke kam kibar batun kawai kinsan tun farko Sultana Hadizah tana da jin kai馃檮 idan kin lura"?.

"Eh ina kule da ita amma miye ruwana a ciki ta kiyayi duniya da zataji shawara da nace mata duk lokacin da taji girman kai yana shirin kamata tayi sauri ta kalli 'kasan 'kafarta maimakon haka sai take sake d'aga kansa sama tana shar'kar iska shiyasa akan ta samar da zaman lafiya sai take neman jefa fitana a cikin ahli" Mami tana rufe baki Sultana Fatima na shirin magana mai martaba ya katse ta.

"Wannan maganar ta isa haka ya kamata a sauya wani zancen ba wannan ba idan kasan halin mutum saika sha maganin zama dashi kun gane nasan kun fini sanin halayenta da d'abi'unta tunda kullum kuna tare nifa sai ranar da muka had'u nake jin irin wannan damuwar na dama min masarauta amma na kusa kawo 'karshen komai Allah ya baiwa Khimiyyan lafiya so nake sai sun had'u guri d'aya dukkan su hudun zanyi magana dasu naga babu wanda hankalin sa yake kan sarauta kowa harkar gabansa kawai yake ina so nasan waye zai gaje ni".

Baki Mami ta ri'ke "to babbar magana anya a cikin su akwai wanda yake sha'awar sarauta kuwa umh amma ban sani ba sai munji ta bakin nasu tunda kansu d'aya rana d'aya aka haife su babu babba ba yaro shiyasa suke ganin daman juna musamman Asad rigima ta masa yawa nasan baya ra'ayin sarauta dama babu shi a ciki ukun za'a tambaya Asad da sarautaa? wai da anga cakwakiya馃槀".

Murmushi mai martaba yai yana cewa "Hauwa kin raina min Asad d'in nan nawa komai sai kice shi gaskiya ban yarda ba karfa ya dawo yace zaiyi mulki ki bari zamu baki mamaki idan kika ganshi cikin kayan sarauta saikin rud'e kin kasa ganeshi kiyi tunanin ko daga Ethiopia yake tsabar kyau da d'aukar hankali".

Dariya Mami da Sultana Fatima sukai dan kuwa Mami ta tabbata Asad bazai kar'bi sarauta ba domin ya ta'ba fad'a mata a shekarun baya tun lokacin daya had'u da Amatu malam Habu zai kaita makaranta ya shiga part d'in ta take tsokanarsa tana cewa "Asad tunda kaine ka fara ganin matar aurenka ai kaine zaka gaji Abbanku ko" kaiya girgiza mata da sauri yace "a'a ba son mulki Mami bazan iya ba babu ni a cikin saidai ko Ajeeb ko Annur da Ameer amma nidai na yafe aikina nasa a gaba" dawowa daga tunani tai tana kallon mai martaba da suke zance da Sultana Fatima sai kawai tai murmushi zaman su yana matukar burgeta Sultana Fatima bata da wata matsala tunda suke tare bata ta'ba yi mata wani abu dataji haushin ta ko ta munana mata ba shiyasa take sonta da Sultana Hadizah ce tasan da yanzu sai daya ko ita ko kuma ita domin bazata d'au raini ba "Hauwa'u tunanin me kike"? Ta sake jin mai martaba ya mata tambaya kai ta girgiza har lokacin da murmushi a fuskarta tace "babu komai u're highness" daga haka bata sake cewa komai ba ta bud'e wayarta tana shiga chat saboda tasan maybe Asad ya mata magana.

馃彆锔'KAUYE馃彆锔

Asabe ce zaune sai kiran wayyo Allah wayyo na shiga uku take bayan mai gara tazo ta duba mata targad'en kafarta wanda Dalah tai mata shegen duka Balarabe yana zaune a gefenta da mafici a hannunsa kamar zaiyi kuka sai cewa yake.

"Sannu Asabe sannu kinji Allah ya sauwake Allah ya baki lafiya sannu bi a hankali wai taya ma kikaji targad'en ne ko fad'uwa kikai naga fuskarki ta kumbura kuma gefen bakin ki a fashe"?.

Wata uwar harara Asabe ta sakar masa jin abinda yake cewa wato fad'uwa tai amma zatai irin wannan raunikan a 'kule tace.

"Wanne irin munafirci ne zakace maye ya kumbura min fuska wato ka nuna bakasan komai ba saboda matarka ce tai min duka ko"馃ぃ?.

Zaro ido Balarabe yai cike da mamaki yace "wacce matar tawa amma dai ba Dalah ba itace tai miki haka kuma kika zauna garin yaya"?

"Garin ban sani ba aikin banza aikin wofi kawai na rantse da Allah bazan yarda ba ko kadau mataki kona huce haushi na a kanka dan ba'a ta'ba Asabe a 'kare lafiya ni zafin wuta ce nafi maciji dafi"

Kallon ta Balarabe yai "to yanzu me kike so ayi"?.

"Oh tambaya ma kake kwarai Balarabe ni yaushe nema nayi sake harka samu baki da damar fad'i in fad'a dani ina cewa kayi zaka kana maida min? Eh lallai Dalah ta sake sabon shiri amma ba damuwa bari nima na warke zanci uban ubanta ne ni roba ina daidai da 'kugun kowanne shege".

Saroro Balarabe yai yana kallon ta ya kasa cewa komai cikin tsawa Asabe tace "kallona kake nace kallona ka tsaya yi Balarabe bazaka dau matakin ba kenan"?.

A susuce Balarabe daya zabura murya na rawar tsoro yace "dan Allah kiyi hakuri fad'a min me kike so bansan me zanyi ba umarninki nake bi"?.

Asabe bata kulashi ba saida ta d'ono ruwan zafi a tsumma ta danna a gefen fuskarta tana yamutsewa da'kyar saboda azaba tace "so nake ka saki Dalah yanzu ta tattara yanata-yanata tabar gidan nan".

Kallon ta Balarabe yai "idan na miki haka shikenan kin huce"?.

A fusace Asabe tace "ban sani ba d'an sakalai馃槵馃槯 maza kaci gaba da tambaya ta Allah yasa karkayi abinda nace wallahi yau zaka sha mamaki".

Jin abinda take fad'a yasa Balarabe jiki na'bari ya mi'ke yana zunduma kira "DALAH KE DALAH gidan uban wa kika shiga zonan yanzu munafika mara mutunci zaki fito ko saina zo na fito dake a tsiyace"?.

Jin abinda yake fad'a yasa Dalah tashi daga kwancen da take ta fito waje domin ita dama wannan gurin take so azo inda zata bar masa gida yaje ya 'karata zai gane idan tana da amfani a gurin sa durkusawa tai a gaban sa cikin ladabi tace "gani".

A masife Balarabe yace "au gaki? gaki? Shine abinda zaki ce saboda ke ba mutuniyar arziki bace? To yanzu ki tashi ki had'a tsummokan kayanki ki barmin gidana na sakeki Dalah tunda kin zama muguwar mace mai ba'kin hali idan naci gaba da zama dake wata rana nan gaba bansan bala'in da zaki kwaso min ba".

Mikewa Dalah tai tana cewa "alhamdulillah dama nima kullum wannan ranar nake jira kuma ina so kasani nangaba sai kayi nadamar abubuwan da kake aikatawa a yanzu sannan bazan tafi ba saika bani shedar sakina a hannu na".

"Au saurin me kike yanzu ma kuwa zaki kar'ba d'aki ya shige yana masifa Dalah data kalli yadda Asabe take d'und'uma jiki tun d'azu tayi dariya tana cewa "ashe duk cika bakinki na 'karya ne gashi zarrata tai miki aiki? Ai banyi tunanin idan kika sha duka tsoro zaisa kice a sake niba na dauka zakii warke mu d'ora akan inda muka tsaya ne"?.

Wata uwar harara Asabe ta sakar mata tana cewa"ke dallacan gafara ban guri uban waye ya fad'a miki tsoro yasa na nace ya sake ki nayi haka dan na ba'kanta miki ne".

Murmushi Dalah tai "au haba wai dan gaske kike? Ta fad'a tana kallon Asabe ganin tayi shiru yasa tai dariya tana cewa "humm Asabe kenan nifa hasken rana ce baki isa ki kare niba kuma abinda nake bukata ne kullum yau na samu kina tsoro ne kawai domin kin ganki yanzu a zaune kada malam ya fita na take 'kafar ciwon na dawo miki da sabuwar karaya shiyasa kike so nabar gidan kwantar da hankalin ki badai gida bane gashi nan na bar miki saiki dafa ki cinye maiya kawai".

Daidai Balarabe ya fito a d'aki yace "uban waye maiyar kinga Dalah ki kiyaye ni uwar me kika tsaya jira kizo kibar min gida nace" ya karasa maganar yana cillo mata farar takarda wacce yai rubutu da ajami d'auka Dalah tai tana shiga d'aki ta sako hijab ta fito zata fice dakatar da ita Balarabe yai "ina zakije baki d'ebe kayayyakin kiba"? Juyowa Dalah tai tana kallon sa tace "saurin me kake jira ka gani yanzu ma kuwa zan d'ebe an gaya maka ina sha'awar sake zama a gidanka ne"? Mstttthhh taja tsaki tana 'kwalla kiran "Indo ke Indo fito mu tafi" zunbur Balarabe ya mi'ke yana cewa "tazo ku tafi ina? Inace 'yata ce bada ita kikazo min gida ba to wallahi babu inda zata biki kinji na rantse ko fita min a gida" Dalah bata sake ce masa komai ba ta fice yayin da Balarabe ya juya kan Indo data fito daga d'aki da hijab a hannunta tana shirin sakawa jin kiran da Dalah tai mata wani kallo Balarabe ya bita dashi tare da d'aukar sanda dake gefen Asabe yana cewa.

"Oh munafika wato da yake kinji kiran uwarki shine harda fitowa da sauri ko da Asabe ce sai tana kumfan baki kice baki jita ba saboda ke matsiyaciya ce kin gado ba'kin hali irin na dangin Dalah uban ki zakici ai yanzu bata gidan".

Ran Indo a 'bace ta tsaya tana kallon Balarabe sai kace ba ubanta ba zai ri'ka yi mata irin wannan tsinuwar ganin shi ta tsaya kallo yasa ya wurga mata sandan hannunsa yana cewa.

"Dan ubanki me kike kallo maiya ko cinye ni zaki d'anye馃"? Da gudu Indo ta fad'a d'aki sandan daya wurgo mata saura kad'an ya sameta a baya tana shigewa ya daki kofa d'akin ji kake kararau ya fad'o kasa huci Balarabe keyi yana nuna kofar d'akin da hannu.

"Zakici uban kine shegiya la'ananniya mai ba'kin jini babu wanda ya ta'ba zuwa yace yana sonki duk garin nan nidai wallahi ba jinina kika biyo ba saidai dangin Dalah dangin tsiya aikin banza nayi danasanin aurenta har abun ya min ciwo ya zama tabo tsinannu kai duk kunbi kun burkita min 'kwa'kwalwata da halinku bari nabi bayan shegiyar uwar taki tazo ta d'ebe daud'ar ta da bolarta a gidana" ya fad'a yana yin hanyar fita sai sambatu yake yayin da yabar Asabe yau ba bakin magana sai d'und'uma jiki take tana ya'kewa saboda azaba.

馃彊锔廗ANO馃彊锔

Nurain na zaune a parlor bayan ya gama waya da Nafisa sai kallon secreen din yake yana murmushi fitowar Zainab kenan daga part d'inta cikin shiri zata tafi office tana ri'ke da hannun Auta dake sanye da uniform Amnah tana binsu a baya ganinsa a zaune yasa cikin mamakin meya tsaya yi har yanzu bai tafi gurin aiki ba ta karaso zatai magana abinda yake kallo a cikin wayar ta kalla wani irin 'kara ta saki tana jifa da handbag馃憸 d'in dake hannunta muryarta na rawa tace "My choice me zan gani haka photon wata budurwar ka zubawa ido kana gani wacece ita a ina take meye ala'kar ku"? Ta fad'a hawaye na zubo mata tana kallonsa zuciyarta na girgiza da tsoron karfa ace budurwar sace data shiga uku yadda bata son kishiya.

Shiru Nurain yai bai bata amsa ba a rud'e ta zauna a gefensa zata kar'bi wayar ya zame hannunsa kuka ta saki da karfi tana cewa "dan Allah ka fad'a min gaskiyar wacece ita a gurin ka kafin kasa zuciyata ta buga wallhi bazan iya jurewa ba ina da matukar rauni ta wannan bangaren bazan iya jurar kishi ba my choice ka fad'a min ka hutar dani 'kunci" ta fad'a tana kifa kanta a kafad'ar sa fitowar mai aikinsu Falmata ganin abinda yake faruwa yasa da sauri taso juyawa Nurain ya dakatar da ita.

"Fatima zoki raka su Amnah school kada lokaci ya'kure".

Jiki a sanyaye Falmata ta juyo kanta a sunkuye tace "to mai gida muje Amnah" wucewa sukai Amnah tana sake waigowa ta kalli yadda Zainab d'in take kuka suna fita Nurain ya sake jawota jikinsa yana rungumeta sosai cikin lallahi yace.

"Kiyi shiru mana haba baby zaki tada min da hankali na".

'Ko'karin fisgewa Zainab take tana ture shi da dukkan 'karfin ta tace "ka sakeni bana so ba wani baby ka rabu dani".

"zan rabu dake but fad'a min abinda ya 'bata miki rai"?.

"Ai kana jin tambayar danai maka ka shareni kasan irin kishin da nake maka amma wanne irin sake nayi har na bari kake kallon photon wata jakar".

Zaro ido Nurain yai "jaka dai?.

Zainab data gama ciki tayi fam a lamarinsa 'kara had'e rai tai tana cewa "eh jaka akuya na fad'a idan kaji haushi ka fad'a min wace ita"?.

"Kina so kisan wacece ita"?.

"Eh ina son sani".

"Baza kiji haushi ba"?.

Kallon sa zainab tai cike da zarguwa tace "ni kawai ka fad'a min bana son kwane-kwane".

"Zan fad'a miki shiyasa na tambaye ki baza kiji haushi ko ki tada hankali ba"?.

Jitayi zuciyarta na harbawa amma ta dake tace "eh ka fad'a kawai zan tafi office I don't want to be late".

Kai ya jinjina yana kunna wayarsa ya nuna mata photon yana cewa "nasan baki ta'ba ganin ta ba ko kalleta dakyau" karewa photon kallo Zainab keyi na wani lokaci kafin taja dogon tsaki tana d'auko karamin towel cikin handbag馃憸 d'inta ta tsartar da yawu tana cewa "wannan me kamar aman fa daga ina ka samu photon da gani 'yar asalin tantagaryar 'kauye ce bata san komai ba" 'yar dariya Nurain yai yana kallon Zainab bai bata amsa yace.

"Kije ki tafi office karki makara maybe patient馃樂馃泴 d'inki suna can suna jiranki".

Mi'kewa tai tana kallon sa tace "kaifa bakaje office ba ko yau hutu ka d'auka d'azu Daddy ya kirani yace ya kira wayarka a rufe sai kuma yanzu na ganka anan"?.

Shima mi'kewar yai suna fita harabar gidan tare yace "eh jiya na rufe ta da wuri kuma yau ban bud'e ba sai yanzu zanje na sameshi" "ok shikenan ni na wuce ka kula" tana fad'in haka ta shiga mota shima tasa ya shiga yana kallo ta fita $annan yabi bayanta yana tunanin tashin hankalin dake gaba daga ranar da Zainab ta fahimci son auren Nafisa yake akwai damuwa dazai iya ha'kura to daya ha'kura din saidai maganar gaskiya bazai iya ba turbar lafiya a bita da shekara a zahirance bason Nafisa yake ba kawai yana jin sha'awar tane yana son kasancewa da itane idan harba haka yai ba kuma yaci gaba da zuwa 'kauyen yana ganinta komai zai iya faruwa za'ai abun kunya wanda shi hakan ne baya so duk rintsi gara ya aureta zaifi da ace yadda mahaifin sa sukeyi da mahaifin ta abin kunya kamar haka ya faru yasan Daddy bazai ta'ba yafe masa ba zai lalla'ba Zainab kota halin 'ka'ka tayi hakuri ta bari ya aureta yasan ba'kin

34 / 67