Author : Mamuhgee Category : Complete Novels
kalleshi,amma a kallo dayan ta karanci bacin ran dake kwance cikin qwayar idanunsa,saita miqe da wani irin qarfi tana kade jikinta,amma kuma ya dakatar da ita ta hanyar cewa
"Ki miqomin key din motarki yanzun nan" ya bata umarni nakai tsaye ba tare da ya ko dubeta ba
" a mamakance ta juyo tana kallonsa,amma ko kallon inda take baiyi ba,ta dauke kai ta jinjina sannan ta taka zuwa ciki,ta dauko key din ta dawo ta ajjiye masa ta wuce daki wasu hawaye masu zafi suna qwace mata.
Koma wanne karin magana bahaushe yayi akan kishiya,koma meye aka fada akan kishiya tabbas ya dace da ita,wasu baqaqen dabi'u da halaye da batasan dame zata kwatantasu ba abbas din ya koyo,saidai koma meye ita ba zata taba bari widad din taga faduwarta ba.
*_A N K U M A M A C E T A H A I F I M A C E inji bahaushe_*
Watan affan bakwai dai dai wanda yayi dai dai da samun qarin matsayin abbas din ya sake samun wani promotion din daga DSP(deputy Superintendent of Police) zuwa SP(superintendent of police) din gaba daya,wani irin ci gaba da budi yaketa samu tako ina wanda bai zaci samunsa haka a kurkusa ba.
Randa aka saki signal sunansa ya fito widad din na falo a kwance,sanye take da wata armless chiffon gown,yatsunta na hannu da na qafa sunsha jan lalle jajir gwanin sha'awa,basu jima da dawowa daga wankin kai ba ita da aminatu,ta dauki affan suka fice sai ita kadai a gidan,gashinta mai tsaho santsi da baqi yayi kyau sai sheqi yakeyi,wannan gyara ne daya zame mata jiki jiddin zaka sameta cikinsa.
Yau din ba ranar girkinta bane,sai a gobe zata karba girki,amma ta gama shirya tarbar abbas din tun a yau din,ta gama komai,zuwa yanzun yadda abbas din keyi a kanta ya daina damunta,ta riga ta saba,ya zamar mata jiki,hasalima tausayi yake bata,don ta tabbatar inda yana samun kulawa yadda ya kamata daga wajen hafsat itama zata samu sauqin wani abun,to amma ita daya ce ke iya kashe masa qishirwar komai,ita kadai ke tsaye a kansa take samar masa nutsuwa da kwanciyar hankali.
Tunda ya duba sunansa yaga ya fito yaji har cikin jiki da zuciyarsa ita yafi dacewa ta fara sani,a nutse yake tuqa motarsa bakinsa dauke da hamdala da godiya ga Allah fili da badini,don yayi masa dukkan wata baiwar da rufin asiri,kuma dama a rayuwa baka taba samun komai cif cif dari bisa dari.
A kofar gidan ya kashe motarsa sannan ya fito,yasa key ya buda gidan yana sanya kai,yau gaba daya aiki ya sashi a gaba,ko zuwa ya dubasun da yakeyi baiyi ba sai yanzun da ya samu break,amma da yake gwanar alkunya ce tare da yi masa uzuri,da sukayi waya ita ta fara bashi uzuri ma kafin ya bata.
Lumshe idanunsa yayi sanda ya tura qofar falon,sassanyan qamshin nan na kullum da kullum dai shine a falon cakude da sanyin ac da aka daidaitashi dai dai da buqatar dan adam.
A duniya gidanta ne waje na farko da yake fara saukar masa da nutsuwa a rayuwarsa,bazaiqi ya dawwama a cikin gidanta ba kaf rayuwarsa,yasan bazai rasa komai ba,ba kuma zaiyi kuka da Komai ba.
Tana daga kwancen ta daga fararen idanunta masu girma ta.kalleshi,ta sakar masa murmushi tana miqewa daga kwancen ta zauna tana dubansa
"Welcome home sir" tsaiwa yayi ya moqe kafadarsa kamar qaramin yaro yana kallonta
"Ban yarda da wannan qwangen da akeson yimin ba" saita miqe da sassarfa ta isa gareshi,ya buda mata hannuwansa kamar yadda suka saba ta fada jikinsa,ya maida hannun ya lullubeta gam cikin qirjinsa yana sauke ajiyar zuciya,kamar yaron da yayi kuka ya qoshi
"Alhamdulillah ala kullin ni'am.......na samu promotion,now am SP abbas" wani irin qanqameshi ta qara yi cikin wata siririyar qara
"Seriouse abbin affan?"
"Da gaske nake sarauniyata" ya fada a tausashe yana shafa sumarta da taja hankalinsa sosai,qamshin jikinta kuma yana neman birkitashi,yana jin yadda bugun zuciyarta ya qaru saboda murna,zamewa tayi a jikinsa ta kama hannuwansa dukka biyun,ta dinga jera masa addu'ar samun nasara tare da fatan alkhairi mai yawa a rayuwarsa,har sai da qwalla ta cika idanunsa,zuciyarsa ta tabu sosai.
Mutum daya...... mutum daya ke tsaiwa tayi masa irin wannan,hajiyarsa,zayaso ace yau tana raye taga abinda ubangiji yaketa yima rayuwarsa.
"Zan samu abinci madam" ya fada yana langabe mata kai,a gabanta kawai yake komawa hakan,inda zaka ganshi a fagen aiki zaka dauka bashi bane.
Kafada ta noqe tana tura baki gaba
"Girkin mummyn mimi ne fa daddyn mimi" girarsa ya daga
"Yes i know....amma kinsan banason cin abincin waje baya ina da mata har biyu,gida kuma yanzun yamin nisa,infact ma abincinki nakeson ci,in kuma ba za'a bani ba to shikenan" ya fada yana komawa kamar wani abun tausayi,dole ya sanyata ta saki wata shagwababbiyar dariya
"Ni na isa na hanaka abinci?,zauna sosai na zubo maka" tayi maganar tana miqewa,saiya riqo hannunta ta baya,ya kashe mata ido daya
"Zafi nakeji,hadamin ruwa nadan watsa tukunna,yau aiki zai riqeni inajin har wajen isha" kai ta jinjina masa,saita sauya akalarta zuwa bedroom dinsa ta hada masa ruwan kamar yanda ya buqata sannan ta fito ta gaya masa ta wuce kitchen.
Tana tsaka da shirya masa abincin taji yana kiranta,ta ajjiye warmer din ta fito.
Tana tura qofar toilet din unexpected kawai taji an fincikota,ko kula dashi ma batayi ba,bata zame ko ina ba sai cikin bathtub,ta jiqe jalaf har saman kanta,tabi jikinta da kallo sannan ta waiwaya tana kallonsa ta gefe,don tuni ya mata masauki cikin jikinsa
"Daddyn mimi......"
"Shshshs....."ya fada yana dora yatsantsa saman labbansa
"Karkice komai,minti biyar kawai zakiyi ki tafi,ba abinda zan miki,kawai ina buqatar ki a jikina kamar haka" bata iya masa musu a wannan bangaren,saboda tasan koda ransa bai masa dadi ba bazai nuna mata ba,uwa uba kuma tasan ba inda zai samu hakan sai wajenta,saita lumshe ido kawai ta jingina da jikinsa.
Sun kusa mintuna goma a haka sannan ta samu ta zame,haka ta fita da kayanta suna diga,sai data shiga bedroom dinsa sannan ta ciresu,ta dauki bababn towel dinsa ta daura ta nufi qofar fita don ta koma nata bedroom din ta saka wasu kayan.
Gabanta yayi mummunar faduwa sansa ta bude qofar dakin,don kwata kwata bata tsammaci ganin mutum cikin falonsu ba,ta kafeta da idanu wani bacin rai yana taso mata,ita din wacce irin dabba ce?,don ta wuce a kirata mahaukaciya,haka kawai saika buda gidan mutane ka shigo babu sallama babu komai?,ba neman izini kamar naka gidan,yau kuwa zata nuna mata ta fita hauka da danyan kai,idan akace ta sake zuwa mata gida ba zata qara ba,saita fasa shiga nata dakin,ta tako a hankali ta nufi gurin tv dake aiki.
*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*
*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02
Page 22
Gifatatan da tayi shi ya fahimtar da hafsat dake zaune tana huci fitowar ta,ta bita da kallo daure da towel din daya bayyanar da kyakkyawar surarta da farar fatarta dake ta glowing mai daukan hankali saboda gyara da mai da sabulan wanka masu kyau data samu.
Qamshinta ya cika mata hanci,ta gaza dauke idanunta daga kanta har zuwa sanda ta isa gaban tv din ta kasheta.
Kashe tv din tayi sannan ta dawo ta sake wuceta kamar batasan Allah yayi wata halitta ba a wajen,ta sake nufar bedroom din abbas din cikin takun na isa,tana shiga ta maida qofar ta rufe hankalinta kwance.
Gefan gadon ta koma ta zauna tana qissima abubuwa da yawa cikin ranta,bata taba ganin mace kidahuma irin hafsat din ba,sau tari idan ta zauna tana nazarin rayuwar abbas din tausayinsa kamata yakeyi,yana da matuqar kirki sanyin hali da qoqarin sauke haqqin da ya rataya a wuyansa,yana da mugun haquri,mutum ne mai nisan haquri sosai da kuma idan aka qureshi fushinsa yakanyi tsahon da ba kasafai yake sakkowa da wuri ba,tako ina babu digon match atare dasu,idan ka kalleta ka kalleshi ba zaka taba zaton miji da mata bane,to amma kuma kowanne bawa da kalar tasa qaddarar,TASHI QADDARAR KENAN.
Yayi mamakin ganinta a zaune daya fito,yana goge jikinsa sa towel yana tsokanarta
"Ko nazo na qarasa aikina ne kawai mu samu ladan me gaba daya?" Ya fada yana kashe mata ido,saita dan jefa masa hararar wasa yana karya wuya
"Naqi wayon.....na yarda ka kashemin jiki,kazo dai ka rakani kitchen saimu debo kayan abincin gaba daya"
"As you wish maaaa" yadda yayi maganar sai ya bata dariya,gefe guda kuma tausayinsa ya kamata,tasan yanzun nan jahilar matarsa zata jagula lissafi da kuma nutsuwar da ya samu.
Tana gaba yana biye da ita daure da towel shima,yadda widad din ta tsara ma ranta kuwa haka ya kasance, idanun hafsat din a kansu ya fara sauka,saita miqe tsaye cak kamar wadda aka yiwa barin wuta,yayin da abbas ya dubeta cike da mamaki,take zuciyarsa ta fara tafasa
"Da izinin waye kika fito?" Ya tambayeta da kakkausar muryar,maimakon ta amsa shi saita sauke dubanta ga widad
"Shegiya la'ananniya,dama nasan yana wajenk......."
"Dakatamin......karki qara kuskuren kirana da wannan sunan,idan ba haka ba wallahi zakisha mamaki na......tunda kike haukarki kinga na taba bi ta kanki?,saboda ni ba take nake ba,ta mijina nake,shine a gabana,ya samu farinciki da nutsuwa daga gareni,ta yadda zan tsaya gaban kowa na amsa suna na na mace,bawai muna mata ba,sannan zanji gamsuwa ba mata na rako duniya ba" ta qarashe maganar tana watsa mata wani banzan kallo,kallon da ya kusa fin maganar da widad ta yaba mata zafi,sai ta fige mayafinta ta watsar da jakarta
"Yau saina nuna miki wace mace wace muna mata"
"Karki kuskura ki sake taku ko guda daya idan ba haka ba yau zakiga abinda baki taba gani ba daga gareni" abbas ya fada idanunsa na sauya launi
"Wuce" ya juya yana gayawa widad,saita fara taku a nutse fuskarta fes da murmushin d hafsat taji kamar ta watsa mata garwashin wuta a fuska.
"Kana gani fa......kana kallon gaskiya kake taketa?,sau nawa ina kamaka a gidan nan abbas?"
"Tunda kwartanci nazo yi saiki tsayarmin da haddi,da izinin wa kika fito nace miki!!!" Ya daka mata tsawar da sai da cikinta ya kada,amma taurin zuciya da tsaurin rai ya sakata ci gaba da tsaiwa tana dubansa
"Dole ne ka fake a bayan na fita baka sani ba,tunda idonka ya rufe ka manta sanda na gaya maka bani da lafiya ko" kallonta yakeyi yana jin kamar ya yanke mata hukuncin da zuciyarsa ke raya masa ko zai samu sassauci daga abinda yakeji a ransa na zallar bacin rai
"Idan kika qara minti daya tsaye a nan wallahi saikin raina wayonki" abinda ya fada mata kenan ya juya ya koma dakinsa.
Tana kuka wurjanjan ta fita a gidan ta wuce titi ta samu abun hawa,bata jin zata iya jurar ci gaba da zama a garin kaduna,bata da sauran amfani a wajen abbas,ba wata soyayya ko qauna data rage tsakaninsu.
Tsaf ta shirya abincin ta fito dashi bayan ta sauya kayan jikinta,da taga baya falo saita wuce bedroom dinsa.
Ko towel din jikinsa bai cire ba,yana zaune a gafen gadon dafe da kansa,ta ajjiye abincin a nutse tausayinsa yana kamata,ta tako a hankali ta zauna gefansa tana dafa kafadarsa hadi da kiran sunansa a tausashe.
Hannunsa dake dafe da kansa ya sauke, sannan ya dagashi zuwa gareta yana duban fararen idanunta da nashi idanun da suka rine
"Kayi haquri....."
"Na gaji widad.....na gaji,nayi duk iya bakin qoqarina,na kuma yi irin haqurin da nake ganin zan iya,shekara nawa?,shekara nawa amma har yau babu sauyi?,har yau jiya iyau,sai yaushe zata canza?"
"Mai haquri baya taba tabewa daddyn mimi,kaci gana da haquri ko don yaranka" dan shuru yayi sannan ya fara magana a sanyaye
"Ina da dubban hanyoyin da zan hukuntata,amma ta kowanne fanni idan na duba mafi yawan hukuncin da duk zan mata sai ya shafi yarana,inda ace bamu da zuri'a ko daya da ita,wallahi wallahi bazan zauna da ita ba" maganar ta daki widad sosai,don duk wanda yake wajen yadda maganar ta fita daga bakinsa zai fahimci tun daga qasan zuciyarsa ne.
Sosai tayi qoqarin kwantar masa da hankali da dadadan kalamai da ban haquri,ta tayashi sukaci abincin tare duk da ba yunwa takeji ba,sannan ta taimaka masa ya sake shiryawa cikin wasu uniform din,don idan ya watsa ruwa da rana kamar haka baya maimaita kaya,takan tsokaneshi da cewa
"Ban taba ganin police din da kayan aiki sukewa kyau irinka ba,hakanan ban taba ganin dan sanda mai tsafta kamar ka ba" murmushi yakeyi sannan yadan harareta
"Kina nufin qazamai ne kenan?" Takan maida masa murmushin hadi da salute nashi
"Afwa nake nema yallabai,ni na isa na fadi haka,kada kasa hukumar 'yan sanda ta kamani"
"Waya isa,wane mutum,kina da Abbas turaki" ire iren hirarrakin da suke sakawa basa gajiya da junansu.
Relief din da ya samu daga wajenta yasa zuciyarsa ta sauka sosai,ya kuma yi aikinsa cikin sukuni,sanda ya tashi komawa gida sai yaji kamar ya koma gidan widad din,amma hakan bashi yiwuwa,kodon yaransa da kuma hakkin Allah dake kansa.
Daya koma din kamar wancan lokacin,baibi takan komai nata ba,hidimarsa yayi dasu mimi,gefan abincinta ma bai kalla ba,saida sukayi baccin ua debesu ya wuce dakinsa dasu,yabar musu gadon ya kwanta saman sofa bed.
Da safe da wurwuri ya shiryasu ya wuce aiki,ya ajjiye mata kudin cefane,bayan ya zabge fiye da rabin abinda ya saba batan,yana sane yayin hakan,don yanason ko yaya ne ya horata taji a jikinta.
Koda aka tashi daga aikin gidan widad ya wuce,bai koma ganinsu ba yadda ya saba,bai kuma kirata ba,baisan ya akayi ba washegari suna waya da lawal kawai yaji muryar su mimi,tsananin amaki ya cikashi
"Suwa nakeji kamarsu mimi?"
"Eh....eh sune" yadan fada a daburce,saboda yasan yadda akayi tahowar,baiso kuma yaji wani bayani daga bakinsa ba
"Ok,shikenan yayi" abinda ya fadi kenan,don ba hurumin yaron bane suyi kowacce magana dashi ba,suka gama maganar da zasuyi ya kashe wayar.
Duk yadda yaso yayi controlling fushinsa amma ya gaza,tattarawa tayi ta koma bauchi ba tare da izininsa ba kenan kwatankwacin abinda tayi masa wancan karon da yayi sanadiyyar haramta mata kaduna kwata kwata kenan?,sai ya sake daukar wayar ya fara kiranta.
Sai da yayi mata miscal biyar bata daga ba,abinda bai taba yiwa wani dan adam ba,ya sauke wayar ya shiga gurin rubuta saqo ya aika mata da saqo kamar haka
_Ki wuce gidanku har sai na nemeki_
Abinda ya aika mata kenan a taqaice,saqon da yayi mugun gigita mata hankali,ta fara kiransa babu qaqqautawa,amma sai shima yayi biris,daga qarshe ma da kiran yayi yawa sai ya kashe wayar gaba daya,widad dake zaune gefansa tana tayashi shigar da wasu bayanai system dinsa batasan abinda yake faruwa ba,sai da taji yana ta jan tsaki sannan ta kalleshi
"What's...."
"Shshsh....."ya fada yana dora yatsantsa saman labbansa yana dan lumshe idonsa,saita dage kafada da gira tana murmushi,bata sake cewa komai ba taci gaba da tayashin,yayi qoqarin shima tattara duk wata damuwar hafsat din ya watsar.
Kwana uku rak kawu hassan yayi kiransa,yace a jirashi sai ya shigo weekend,weekend din da baije ba sai da bayan wata guda cif!.
Widad sam batasan me ake ba,taga dai ya dawo gidan gaba daya,ta kuma sake samun wata sabuwar zazzafar soyayya da kulawar data dinga sakata jin kunya muddin cikin mutane suke,takan tambayi kanta wai wacce irin soyayya abbas din yake mata?,tasha tambayarsa amma shima baida amsa illa yace
"Min indillah" daga qarshe itama haka ta barwa ranta daga Allah ne,saidai tabbas ZUCIYA TANA SON ME KYAUTATA MATA,TANA KUMA QIN ME MUNANA MATA KOMAI SOYAYYAR DA ITA ZUCIYAR KE MASA.
Suna sauka a bauchi ya wuce gidan kawu hassan din,don akwai maganganun da zasu tattauna,yanason wannan karon su halarci bikin qara musu girman da akayi,itama bata zauna ba tace zata je gidan uncle muhsin,da fari ya hana don mugun kishinta yakeyi,yace ta jira ya dawo ya kaita.
Amma ta kafe da roqo da nacin ya barta,don akwai abinda take shirya masa,batason kuma ya sani sai ranar,daga qarshe da qyar ya yarda idan ya isa gida zai turo umar ya dauki motarsa guda daya ya kaita,ta saki murmushi sanda yake fita
"Uncle dina" ta fada qasa qasa cikin murmushi,wani kaffa kaffa yakeyi da