Advertisements
Chapter 17 Reading A Rubucetake Book 2 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

A Rubucetake Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Mamuhgee Category :  Complete Novels

Chapter   17 / 33

48K to 51K   out of 97K words

ita,hatta da kayan sawarta yanzun ya hanata saka wasu muddin fita zatayi,yafi ganewa kowanne dinki ma ayi mata doguwar riga sakakkiya.

Abbas sun tattauna sosai da kawu hassan harma da yaaya sa'id da Bashir akan batun hafsat din,sun tausheshi sosai sun bashi haquri,yace yaji,amma su qyaleshi,ko zai maidata ba yanzun ba,ya fara gajiya yana son shima ya huta,ba wanda ya tilastashi a lokacin,babban wansa yaaya sa'id ne yace

"Shikenan,zan nema kawun nata zamuyi magana,amma dai ka daure kaci gaba da haquri ko don zuriar da Allah ya qaddara a tsakaninku"

"In sha Allah" ya fada cikin girmamawa,sun qyaleshin,suka ajjiye batun suka shiga tattauna sauran maganganun da ya shafesu.

Kafin yabar gidan ya bawa umar key din motarsa yace ya dauko masa su mimi,saboda yanason su koma kaduna tare,ko don makarantar yaran.

Abinda yayi matuqar bata mamaki da daga mata hankali kenan,a dauko su mimi fa?,to me yake nufi?,kada fa ya zamana ta fita kenan a gidan gaba daya,kada yarinyar ta zama sanadiyyar fitarta haihata haihata a gidan,ta kadu don irin hakan bata taba faruwa a tsakaninta dashi ba,amma ummanta ta kwantar mata da hankali

"Kada ki damu,ki bada yaran,kinsan muddin ina raye bazan bari irin haka ta faru dake ba" hakanan ta daure ta hada musu tsummokaransu.

Kafin abbas din ya dawo ita ta rigasu dawowa,ta gyara bangarenta da nashi,ta dora abinci,sanda yaran suka iso ta gyarasu fes ta canza musu kaya,sai gashi sun sake sunata walwala abinsu,musamman mimi data dinga fadin

"Nidai wajenki zan zauna anty", murmushi kawai widad tayi

"Dama ta wajena ce ke" abbas na zaune yana binsu da kallo,sai yakejin gidan nasa ya sake masa dadi, widad nata kai.kawo tana hidima dasu,affan yana hannun su mimi suna masa wasa,wanda inda mahaifiyarsu na nan basu isa su samu wannan damar ba.

Waya ta shiga daki ta amsa,koda ta fito sai ya tsareta da ido,daga bisani kuma murmushi ya kubce masa

"Madam.......tsakani da Allah ban yarda dake ba,me kike shiryawa silently" dariya takeson yi amma bataso ta bashi qofar da zai gane plan dinta

"Siyar dakai zanyi" tayi maganar tana kashe masa ido daya,wani qawataccen murmushi ya subuce masa yana jin kansa fes cikin wata irin walwala

"Girmanki ne,don kin siyar da DSP,har IG ma zaki iya siyarwa,duka girmanki ne" sai dariya ta qwace musu su duka biyun.

Washegari bayan ya fita ta kuma tambayarsa zasu fita ita da yaran gaba daya,ya langabe kai a inda yake zaune

"Babyn uncle.....ki jirani zuwa dare na kaiki please,wallahi banaso...... inajin kishin ki fita a kalleki,banason kihau motar haya"

"Allah uncle ba zamu jima ba,kuma inda zanje din basa fitowa ai da daddare,don Allah ka turon umar ko ko muneer,saika bamu aron daya motar taka ya miqamu ya dawo damu"

"Shikenan nan,amma awa biyu kacal na baku"

"In sha Allah bazan wuce haka ba" ta amsa masa a ladabce.

*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02

Page 23

Wankin kai da qunshi akayi mata,haka suma yaran duka,sunata murna don ba'a taba musu gyara da lalle irin wannan ba,bata wuce awa biyun ba ta dawo,koda ya dawo gidam ya samesu da gyaran bai kawo komai ransa ba,tunda yasan dama already ita kullum cikin gyara take ta saba (qalubale gareki, keda bakya komai sai sallah ko idan zakuyi biki ko wani sha'ani na taro ya kama,mai gida har ya gane hakan,yara suyita tambayar umma unguwa zamu?,umma biki za'a yi,ba lalle ba gyaran kai babu kitso).

*******Karfe hudu na yammacin washegari tayi wata kyakkyawar shiga cikin wani tsadajjen crystal swarovski lace,duk inda ta motsa ko ta gifta daddadan qamshi ne yake fita daga jikinta da wani irin qyalqyali mai daukan hankali.

Ta nutsu ita daya daga can bakin gate,ta yadda abbas data kirashi gida urgently bazai gane abinda ke faruwa cikin gidan ba har sai ya shigo.

Daga waje ya kashe motar,ya bude ya fito ya kulle yana kallonta cikin mamaki,tace yazo gida yanzu yanzu,yazo kuna ya tarar da ita cikin ido me narkar da zuciya da idanunsa

"Wow......amma kin kyauta da kika kirani naga wannan kwalliyar kada nayi missing nata" ya fada yana murmushi,batace masa komai ba sai kama hannunsa da tayi suka shiga cikin gidan.

Mutuwar tsaye yayi sanda yaga yadda aka maida harabar gidan nasa kamar wani event center,har yaushe akayi hakan bayan fitarsa daga gidan duka duka bai wuce awa uku ba,ko ina ya daga kai manya banners ne masu dauke da hotonsa cikin full police uniform a tsaye,da wasu rubututtuka na nuna murnar tayashi qarin samun promotion da yayi,ga family saman kujeraru da shigowarsa ta saka kowa miqewa yana masa maraba,a lokacin wani irin sassanyan abu yaji yana tsarga masa akan widad din

"Ya rabbb,wacce irin yarinya Allah ya azurtashi da ita?"

"Surprise?" Ya fada yana sauke idanunsa a kanta yana lumshesu cike da wani irin shauqi,saita jinjina kai lallausan murmushi yana kubce mata,shima kan ya jinjina,ya kuma kama hannunta da kyau cikin nasa ya fara takawa zuwa ciki suna riqe da hannun juna ya nufi yan uwa dake dakon isowarsa don a gaggaisa kafin a fara ciye ciye na abinda aka tanada a wajen.

Cikin wani yanayi me kyau da qayatarwa aka kammala taron lafiya,abu yayi masifar qayatarwa,ya burge masoya, abokan adawa kuma da masu taya hafsat kishi kamar su mutu

"Yar qanqanuwar yarinya ta iya kidifiri da iyayi,ta kora sa'ar uwarta uwar gida cikin yaranta gida tazo tana shimfida abinda taga dama" ire iren abinda su gwaggwo hassana da gwaggwo fanteka suke fada kenan,saidai babu bakin cewa komai saidai gulma daga gefe,hakanan kuma sukaci suka sha suka watse.

Sai data tabbatar an sallami kowa harabar gidan ta barwa su shazali zasu qarasa gyarawa sannan ta dawo cikin gidan duba yaran,tasan bata da matsala don suna tare da aminatu,tare suka taho wannan karon.

Aminatun kam akwai hidima,ba qyuya sam,harta sake musu wanka,affan da nawwara sunyi bacci,ita da mimi ne kadai suna kallo a ipad din widad da abbas din yabar mata kwanan nan,don dama itace bata da ita,hafsat nada tata duk da ta bari yara sun tsoma tatan a ruwa.

Bayan ta tabbatar sunci abinci sai ta dauki affan tayi musu sai da safe,don ta gaji tubus,ta kuma ji shigowar abbas din tun kusan dazun ma tana waje tana sallama da mutane.

Tana tura qofar suna hada ido,waya yake amsawa,da alama kuma mai tsaho ce,don haka ta daga masa hannu kawai,ta ajjiye masa affan ta kitchen ta hado musu baqin shayi me kayan qamshi sosai,don ya koya mata itama,sanann ta wuce toilet ta hada ruwa mai zafi tayi wanka.

Daure da towel ta fito,fatarta sai sheqi takeyi,ya ajjiye wayar gefe ya miqa mata hannunsa,batayi qasa a gwiwa ba ta miqo masa nata hannun,yayi mata mazauni saman cinyarsa yana sansanarta,yana bala'in son qamshinta,ba qaramin burgeshi yakeyi ba

"Sannu da hidima madam" murmushi tayi tana saqalo wuyansa da hannunta

"Kaine da sannu yallabai,don dukka aikinka ne wannan" da mamaki ya daga kai ya dubeta,don dai shi yasan sisinsa babu a ciki,hasalima baisan zata shirya ba sai daya shigo gidan.

"Aikina kuma?" Gira ta daga tana murmushi

"Sosai,mun samu kyakkyawar kulawa daga gareka,ka sauke dukkan wani haqqi naka dake wuyanmu,wanann yasa har a cikin zuciyata naji ka cancanci fiye da haka ma,donma ni din ba wata bace,da fin haka naso ya kasance" cikin jikinsa ya qanqameta yana cusa kansa tsakanin qirjinta,abinda ya sanya tsigar jikinta tashi,ya sauke mata zazzafan numfashin da dole ta riqe kansa da hannunta tana 'yar dariya

"Ji nakeyi kamar na maidaki cikina na boyeki,zuciyata har wani irin zafi takemin saboda sonki" yana kaiwa nan saiji tayi ya watsata saman gadon ya kuma maye gurbin towel din jikinta.

Washegari ta tsinci alert a wayarta da sunan mijin nata har na naira million daya,ta sameshi a bayan gidan shi daya da wasu takardu data tabbatar ayyukansa yake,da alama za'a baza komar kama wani mai laifi ne

"Yallabai kudinka sunyi batan kan shigowa account dina fa,da saninka?" Takardun ya aje gefe,ita daya duk duniya yakema haka idan yana aiki irin wannan

"Zonan" yace tana bata hannunsa,saita qaraso din ta zauna

"Ba batan kai sukayi ba,sun shiga inda ya dace ne,nawa kika kashe jiya." Fararen idanunta tadan juya kadan

"Bazance ba,amma dai bazai wuce three hundred thousand ba" kai ya jinjina

"Kice duka tattalin arziqinki kika kwashe" saita saki dariya,kome zata bawa abbas din batajin zatajishi a matsayin asara

"To yayi,kudin dana tura duka naki ne,inason ki zauna kiyi tunani ko kiyi shawarar sana'ar da kike sha'awa,inason ki fara kasuwanci cikin gida" sosai ya bata mamaki kamar yadda itama ta bashi mamaki jiya,ta sauko saman gwiwoyinta ta fara masa godiya,ya kamata ya tayar da ita

"Ban miki komai ba,saboda ke din kin bani komai"

*H A F S A T*

Kai kawo taci gaba da yi,wayar hajiya habiba tana hannunta,duk hoto daya da zata bude tashin hankali ne yake sauko mata mara adadi,kamar ta hadiyi zuciya ta mutu,abbas dinta mijinta da kuma yaranta,duka under control na widad,wacce irin asara take shirin tafkawa?.

"Nidai gaskiya kin bani mamaki,am totally disappointed wallahi,ni duk sai kunya ta kamani ma da naga irin abinda akeyi a wajen,sai lawal ne ya bani address na gidan nan,shima yana daga gefe takaici ya isheshi,don dai bashi da yadda zaiyi ne".

Kananun qwalla ce suka kubcewa hafsat,tana jin tata ta qare,duk wani abu da zatayi akan widad tayi amma jiya iyau

"Aah,ai kuka bai ganki ba,mafita ya kamata ki nema" komawa tayi ta zauna,don gaba daya jikinta babu sauran qwari ko karsashi

"Meye ma banyi ba,kissar nayi babu ci,malaman nabi amma sai abun yayi kamar zaiyi tasiri saiya wargaje" murmushi haj habiba ta saki

"Malamai kika bi ko muna malamai?,hajiyata kiqi kudinki kizo na kaiki inda zaki mori kudinki,kissa kuma iri iri ce hakanan iyawa ce,ki fita batun yarinyar koda an miki aiki yayi,ko agabansa ki dinga nuna bata gabanki shine kawai"

"Wallahi na shirya,ko nawa zan kashe a shirye nake,ai ranar biyan buqata rai ba'a bakin komai yake ba" murmushi ta saki

"Gwara da Allah ya ganar dake ai" (hmmm,kodai shaidan ya batar da ita,Allah yasa mufi qarfin zukatanmu,muje dai zuwa masu karatu,aci gaba da haquri,so nake mu sauke dukkan darasin dake ciki,saboda labarina yafi rinjaye da true life story)

*H U G U M A*
*Arewabooks:Huguma*

*_A RUBUCE TAKE_*
(K'addarata)
Part 02

Page 24

Kafin su gama hutunsu a bauchi ta tattauna da mutanen da suka zame mata tamkar fitila a rayuwarta,su anty deena hajiya sha'awa dasu hajiya fanna,anty deena tace

"Kina 'yar kano cibiyar kasuwanci ai baki da matsala,kaya kawai za'a yita kawo miki kina saidawa kina maido kudin ana sake miki sari" su hajiya fanna dake 'yan kasuwa ne suma sukace ba matsala zasu dinga karba,ta zauna tayi shawara da tunani ta zabi kayan da zata dinga saidawa,bata bar bauchi ba saida kayan suka iso,ta raba wasu suka wuce kaduna da wasu.

Abu kamar wasa saiga kaya sunata shiga ana hada mata kudinta,hakan yayi mata dadi sosai,a cikin lokaci qalilan ta fara gane amfanin sana'a ga mace.

Ta maida kanta sosai ga kulawa da mijinta da yaronta dake shiga watanni takwas,gasu mimi da takejinsu kamar yaran cikinta,bata da sauran matsala sai godiya ga Allah.

Watansu daya da dawowa ya dauki su mimi ya maidasu bauchi kan mamarsu ta dawo,bata wani damu ba tunda zuciyarta babu wani mummunan nufi a ciki,saidai bataji dadin tafiyar yaran ba,don hatta mimi taso a barta amma hakan bai yiwu ba.


*R U B U T A C C I Y A R K' A D D A R A*


K'arfe hudu na yammaci,tana kitchen tana aikin abincin dare,affan yana goye a bayanta,don aminatu bata nan tana islamiyya,yau din ta dauko aiki me dan wahala,favourite foods na abbas din takeyi har guda biyu,don ma aminatu ta rage mata wasu ayyukan kafin ta wuce islamiyya.

Knocking taji anatayi sosai,kamar za'a balla qofar,mamaki ya kamata,sam bata qaunar bugu me qarfi haka,taha tsaki ta share bugun ta qarasa juya miyarta sannan ta ajjiye ludayin ta nufi qofar tana tambayar waye da dan qarfi,saidai ba'a amsa mata ba har ta bude qofar.

Tsananin mamaki ya kamata ganin abbas a tsaye,ya kafeta da ido kafin ya sanyo kai ciki,saita rabe gefe tana bashi hanya hadi da binsa da kallon mamaki,a hankali kuma ta taka ta bishi a baya jikinta na wani irin mutuwa.

Sai da ya gama qarewa falon kallo tsaf sannan ya kalli wayarsa dake hannunsa ya maida dubansa gareta da murtukekkiyar fuskarsa

"Ina kika je?"

"Ni kuma?,ina zan fita ba tare da saninka ko izininka ba?,ina kitchen ina girki"

"kina kitchen kuma?" Ya sake tambayarta cikin yanayi na rashin yarda sosai kwance a fuskarsa,abinda ya bawa widad mamaki sosai

"Eh mana,uncle na taba yi maka qarya?"

"Amma naketa kiranki baki dauka ba?,kamar kin fita ko kin tafi Wani wajen?" Idanu tadan zuba masa sannan ta sauke ajiyar zuciya mai qarfi,sai kawai ta kama hannunsa suka wuce zuwa bedroom dinta inda tabar wayar a ajjiye.

Cak ta dauko wayar ta danqa masa a hannunsa,ya dubeta ya dubi wayar sannan ya bude

"A silent take,ni na sakata saboda inason affan yayi bacci,kada kira ya shigo ya tadashi" wayar yadan juya a hannunsa kadan yana sauke ajiyar zuciya a jejjere,sai ya koma da baya ya zauna a bakin gadonta.

A matuqar sanyaye ta fice,ta shiga kitchen ta bude fridge ta fiddo zobo me sanyi data hada masa da yaji kayan hadinsu abarba,daya daga cikin nau'ikan zobon data koya a class dinsu da deeja Berver (the best online class da na taba shiga da ya burgeni qwarai qwarai 0907 927 4454).

Tason yana matuqar sonshi saboda taste dinsa na dabanne da ba ko wanne gida zaka shiga ka samu irinsa ba,shi yasa bata rabo da yi masa.

Gabansa ta dawo ta durqusa ta soma zuba masa sannan ta miqa masa idanuwanta a kansa,bai musa ba ya karba ya kuma shanye tas ya miqa mata cup din,saita koma gefan gadon ta kwantar da affan sannan ta dawo gabansa ta zauna tana tattara nutsuwarta a kansa

"Uncle,me yake faruwa?,kwanakin nan gaba daya idan ka kira wayata baka sameni ba sai hankalinka yayita tashi,sannan duka ka gaza nutsuwa a wajen aikinka,me yake faruwa?" Idanunsa ya lumshe yana kada kansa da yakejin ya masa wani nauyi,zuciyarsa kuma tana rabuwa gida biyu

"I don't know,kawai dai.......ina tsananin kishinki" shuru tayi tana nazarin maganarsa,a baya yana kishin nata amma ba ta irin hanyar da yanzu yakeyi ba,ya canza kwata kwata,wasu irin halaye yake mata da suke sakata shakku,kamar zargi zargi,to amma tunda ya bata wannan hanzarin bata da hurumin masa hukunci kai tsaye

"Ka kwantar da hankalinka uncle,ni taka ce har abada" qaramin murmushi ya subuce masa wanda baikai har zuciya ba,ya waiwaya yana kallon affan dake bacci abinsa hankali kwance cikin cikakkiyar tsafta da kulawa.

Bayan wasu kwanaki da yammacin wata litinin,a yau din ba ita keda girki ba,don haka tun bayan kammala sallar la'asar ta gama komai.nata tana zaune,sai kiran ummu ya shigo mata,suka shiga hirarsu sosai tana wasa da hannun affan dake zaune saman cinyarta yana wasa da teether.

A qalla sun kusa awa guda,suna gamawa kuma kiran anty fanna ya shigo,suka hau hirar kasuwanci da lissafin kudaden kayan widad din da aka saida wadanda suke hannunta.

Daga qofar falonta taji ana knocking,ta dauki excuse tace zata kirata ta aje wayar ta miqe tana bude qofar,aminatu ce sanye da kayan islamiyya,hannunta riqe da waya

"Aah,har an taso?" Widad ta tambayeta

"Aah anty,yau korar school fees akeyi" dan bata rai tayi kadan

"Amma sau nawa zan gaya miki,duk sanda wata ya qare ki dinga tunamin ina baki?"

"Mamace tace na qyaleki hakanan,wancan watan kin kawo kayan abinci,yanzu kuma......" Sai maganarta ta katse saboda ringing da wayar hannunta ta fara,duka suka kalli wayar a tare

"Wayar waye wannan?"

"Wani ne,da uniform irin nasu abban affan,yace sunanshi samuel,oga ne yace wai a kawo miki wayar zakuyi magana" ta gane komai a dan bayanin aminatun,amma sai mamaki ya kamata,tasa hannu ta karbi wayar,kafin takai ga dagawa ta yanke,saita saki qofar ta juya cikin falon jikinta a matuqar sanyaye,abun na abbas har ya fara kaiwa haka?,meye haka mai qarfi ya shiga zuciyarsa dangane da ita?.

Tana shirin zama amintu ta sunkuya ta dauki affan tana masa wasa sai gashi ya sake kira,batayi qasa a gwiwa ba ta daga wayar ta sakata a kunne tare da

17 / 33