Advertisements
Chapter 4 Reading Diddigar Kaya 1&2 Complete Hausa Novel Hausa Novels
Advertisements

Diddigar Kaya 1&2 Complete Hausa Novel

Author :  Fatima Category :  Complete Novels

Chapter   4 / 29

9K to 12K   out of 86.8K words

da ayoyi da hadisai masu magana akan neman ilimi musamman Addini, tana shiru bayan ya gama ya sallameta ta mi?e ta fice ba wai don ta Wauki ko abu guda da yace a cikin nasihohin shin ba.

Ya kamata ku san wani gida ne haka?
Wannan gida da mutane suka mata la?abi kala kala wasu su ce
"GIDAN F" dalili kuwa duka yaran da suke cikin wannan gida sunansu daga F ya fara.

Wasu su ce
"GIDAN PROF KAKA" dalili kuwa babu wadda be san waye PROF Ibrahim KAKA ba a faWin Nijeriya da ma kasashen ketare.
Dalilinshi ne ya sanya gabaWaya unguwan tasu ta tashi daga ainihin sunanta ta koma
"UNGUWAN ?AN BORNO"

Wannan unguwa na kafe ne a tsakiyar garin Yola na Adamawa state, zagaye yake da barebari Albarkacin dattijon arziki Baba Prof, asalin su ?an garin Maiduguri ne na jahar Borno, daga uwa har uba barebari ne, a garin Borno Zulaikha wacce yara suke mata la?abi da Jaddah ta haife su, su biyu ne rak wurin Mahaifinsu Abubakar Kaka, Baba prof wadda Asalin sunanshi Ibrahim Abubakar kaka da kuma ?aninshi Sulaiman Abubakar Kaka.

Mahaifinsu mutum ne me nagarta kuma babban malami a jahar Borno, karatu da karantarwa gadon su ne sbd abunda suka taso suka samu Mahaifinsu da shi kenan, a wurinshi suka fara karatu na addini ya basu ilimi me nagarta musamman ibarahim da kullum karfe biyun dare haka ze tashe shi ya makala mishi redio yana sauraran karatuttukan malamai tun yana gyangyaWi yana farkawa har ya dawo daga baya idan ze kwanta da kanshi ze cewa Mahaifinsu idan lokacin karatu yayi a tashe shi fa kar a manta.

Wani irin buWewa kwakwalwanshi tayi da Alqur'ani wadda har ya iya qira'o'i da riwayoyi iri iri, a tsakanin ya shiga boko wadda be hana shi yin karatun shi ba, duba da iyayensu girma ya fara kama su gashi shine Wan su na fari dayake Jaddah tana yawan haihuwa ne suna komawa, haka ta cigaba ko da bayan ta haifi Ibrahim ya tsaya.

Shi kaWai ya buWi ido ya gani a gidan hakan yasa ya ci alwashin gadar Mahaifinshi, wadda karantawar tashi wata rana yake fata ta zama sadakatul jariya ga Mahaifinshi, yana da shekaru goma sha biyu ya haddace Alqur'ani, hadda marar gargada bare kame kame, be dena karatun littatafai ba har ya shiga jss3 anan ne Jadda ta sake haihuwa bayan shekaru masu yawa inda ta haifi Sulaiman.

Shekarar su uku da Sulaiman ya samu scholarship sbd irin kwazo da ilimin shi da ya baza ko ina a cikin garin na Borno, har wasu state Win da idan be je musabaqa ba to ze je su debate, quiz, spelling bee da sauransu be kuma taSa Waukan na biyu ba.

Madina yayiwa tsinke inda ya dage ya maida hankali yayi degree Winshi na farko har kuma lokacin be dena neman ilimin addini ba, bayan shekaru huWu ya dawo Nijeria.

Alhamdulillah be bar iyayenshi haka ba ko da yake chan, ko da ya dawo ya cigaba da taimaka musu da karfinshi, yayinda Sulaiman ya fi maida hankali a boko Dukda dae ba laifi shima yana da iya nashi karatun na addini sede ba kaman Ibrahim ba.

A haka ya koma Madina yayo masters fannin kasuwanci, bayan ya dawo ya tafi America yayi degree Winshi na uku fannin halayya, anan ne ya dawo Nijeria lokacin Mahaifinsu na cikin hali na ciwo Sulaiman yana jami'a.

Wasa wasa Dr Ibrahim KAKA ya zama sananne a harkar musulunci, karantarwa da da'awa babu inda kafafunshi basu taka ba a Nijeriya, wani wurin har jifa suke sha, ruwa, rana, zafi, iska duk ya ?are a kansu amma basu karaya ba.

A haka Allah ubangiji ya karSi ran Mahaifinsu yana me alfahari da kaWan da Allah ya bashi masu albarka sede kuma da takaicin rashin ganin auren Ibrahim sbd har lokacin be maida hankali kan mace ba, ina ka fito karatu ina zaka karantarwa, me kaci karatu, me ka sha karatu haka Ibrahim yake.

Sulaiman na Bautar ?asa a Adamawa aka fara hare haren boko haram tashin farko kuma da matukar zafin su hakan yasa Sulaiman ya nemi Yayanshi Ibrahim da ya riga ya zame mishi uba sbd irin respect da yake bashi ya wuce na wa, akan su zo yola da Jaddah tunda apartment da shi baba prof Win ya kama mishi me girma ne.

Be ?i ba haka suka dawo cikin garin Yola wadda ya kasance dawowar kenan, wasa wasa Ibrahim yayi wani irin kafuwa sbd mutum ne me zafin nema Sam baya kwanciya kawai yaji daaWi, a tafiyan su wani kauye ne na mayo belwa ya samo Aisha(Mammi) gani Waya ya mata yaji nan duniya itace macen da ta dace dashi ko da ya dawo kan yayi magana Sulaiman ya tare shi da zancen ya samu mata, shima nan ya faWa musu yayi mata farin ciki wurin jadda harda hawaye.

fili babba ya saya ya samu architecture ya tsara mishi yadda yake so gidansu ya kasance na dindin din kuWi ya zube aka soma aiki, wata uku aka gama komai sashe uku ne se masallaci da islamiyya babba daga jikin gidan, a lokacin aka yi bukin su.

Yadda faWan boko haram ke tsamari a Maiduguri yasa yake ta sayan kananun Gidaje a unguwan yana saka ?an uwa da abokan arziki kusan almost rabin unguwan shi ya mallaka musu Gidajen su kuma in har ya kiraka akan ka dawo yola to wannan gida naka ne halak malak.

Wani irin buWi yake samu sbd alkhairanshi dake da matukar yawa, basu shekara biyu da Mammi ba ta haifi Yaron su na farko da ya ci suna FAIZAN(Genorous/Me karamci ko kuma beneficence wato me aikata mai kyau), bayan wata uku da haihuwar Faizan ruqayya(Matar Sulaiman) itama ta haihu ta samu Wiya mace wacce ta ci sunan Fadeelah(Virtuous wato tagari).

Ba'a rufa shekara ba Aka sake baiwa Baba prof mata Hussaina daga Wani kauye na jalingo da ake kira Sunkani, itama Fulani ce ba'a Sata lokaci ba aka yi bukin nasu, shekaranta Waya Mammi kaman yadda Faizan ke kira ta sake haihuwar Wa namiji Faahim(me ilimi or mai fahimta).

Ammi itama ta sake haihuwar Falaq(Ketowar Alfijir), Anan hankalin Ruqayya ya soma tashi, dama wani irin zama suke yi marar daaWi da Maa wadda musabbabin abun Ruqayya ce, tunda ta saka kafa gidan ta fahimci nisan dake tsakanin Ibrahim da Sulaiman kaman nisan dake tsakanin sama da ?asa ne, wai ba haka aka so ba kanin miji yafi miji kyau.

Bata kara shiga tunani ba seda taga irin girmamawar Sulaiman ga Ibrahim kai tsaye zaka iya cewa matsayin mahaifi ya bashi don ko ratar dake tsakaninsu rata ne me girma, randa ta haihu kuwa taga Sulaiman ya Wauki yarinyar musamman ya kaiwa Ibrahim shi ya mata huWuba ya sa mata suna alhali ta riga ta faWawa Sulaiman sunan da take so a sawa yarinyar, ba karamin rikici suka yi ba akan sunan Fadeelah sede Sulaiman ya fi karfinta haka ta bari, sede daga ranar maganan arziki ita da Mammi babu dama chan sama sama ne, se kuma gashi Mammi na jera maza Ita kuma tana jera mata alhali Ibrahim da Sulaiman basu bambanta dukiyar su ba.

Zaman doya da manja ake yi a gidan har Amaryar baba prof itama ta haihu ta samu mace, Falusha(Haske).

Bayan haihuwan Falusha Baba prof yayi tafiya Maiduguri inda ya dawo da Auren Zainab, ba karamin rikici aka yi da Hussaina ba kan ta saduda, Mammi kam fatan alkhairi kawai tayi mishi, a lokacin ma tana da tsohon ciki inda ta haifi Fahad(Damisa) ba'a Wau lokaci ba Ammi ta sake haihuwan Fadyaa(sadaukarwa).

Hussaina da yaran suke kira Maami ta sake haifan Farrah(Florence nau'in haske), har lokacin zainab bata haihu ba, Baba prof ya karo aure cikin ?an gudun Hijira Sakinah itama barebari ce usul, a tare suka fara haihuwa da Zainab wacce su Faizan ke kira Umma, ita ta samu Faraj(cure, waraka kenan) yayinda sakina ta samu Farzan(me wayau).

Daga nan dukkansu basu sake haihuwa ba seda aka Wau lokaci Ammi kuwa ta haifi maza biyu a tsakani Farhan(farin ciki) da Faris (horseman).

A lokacin Baba prof ya kara sashe a gefe da masallaci sbd matasan yaran da suka fara tasowa, Mammi ta sake haihuwar? Farida(ta musamman ko lu'ulu'u me daraja) daga nan har yau bata sake haihuwa ba.
Bayan nan Sakinah (umma) ta sake haihuwan Farhuddeen(farin cikin addini).
Sulaiman ya ?ara aure inda ya auri sumayya ta zo gidan da ?arta Fatima, sumayya sun haihu tare da Ammi(ruqayya), Ammi ta haifi Fauza (triumphant wato nasara) yayinda sumayya ta haifi fa'iza (Gain, wato samu).

Bayan su Fauxa, sumayya ta kara yara uku Fadiyah(me kyau), Fakiha(fruits) se Faazila(gaskiya) su kenan yaran gidan karan katakap.

Mammi na da huWu Faizan, Faahim, Fahad da farida.
Maami na da biyu Falusha da Farrah.
Umma na da guda biyu Faraj da Farhuddeen.
Daada na da guda Waya Farzan.
GabaWaya yaran na Baba prof guda 9 ne Allah ya bashi.

Se Alhaji wato Sulaiman.
Ammi na da shidda Fadeelah, Falaq, Fadyaa, Farhan, Faris se Fauxa.
Aunty Amarya na da huWu Fa'iza, fadhiya,Fakiha da Faazila.
GaSadaya yaranshi 10.

Gidan na da wani irin dokoki ne wadda duk tsari na addini ne, yaran kuwa akwai matukar shakuwa, tausayi da kauna irin ta ?an uwantaka a tsakaninsu Baba prof baya wasa da tarbiyar su ko na miskala zarratin, duk kuma abunda ze shimfiWa hannu bibbiyu Alhaji ke karSa.

Ya ?ara samun wani girma ne a unguwan sbd yadda baya banbance ?a?anshi da na dangin shi Dukda ba komai yake da iko akai ba sede fa ya san duka yaran don dole a islamiyya Winshi zasu yi karatu kuma shi da kanshi yake koyar dasu sbd dumbin falala dake cikin koyarwa da yara addini babban sadaqatul jariya ce wacce bata gushewa har se me wannan ilimi ya gushe idan kuma akwai wadda ya koya daga wurin Waya haka ze yi ta gudana har illa ma shaa Allah.

Wannan al'ada itace zaSarwa yara abokan zama masu nagarta, kawai ze kira ka a waya akan Zaku yi ba?o ze zo wurin wacce kaza, ko kuma wane kaza na gidan ka yaje wurin wacce kaza na gidan wane, a haka ya HaWa wani irin bond me girma tsakanin kaSilarsu ta barebari da suke nan unguwar, kuma duk zaSin shi suna alfahari dashi sbd baya taSa zaSin banza.

Mata da mazan gidanshi kan yi karatu har matakin degree ma idan har maneminki be fito ba, sbd ya san muhimmancin karatu ya kuma san karatu wani makami ne da zaka barwa yaro wadda ba ze taSa tagayyara ba hakan ne dalilin da ya sa ko maneminki ya fito baki fara makarantar gaba da jami'a ba dole akwai yarjejeniyar ci gaban karatun ki don gudun halin rayuwa.

Faizan pilot ne wato matu?in jirgi wadda aka fi sani da Captain Faizan matashi me jini a jika, kyaun fuska da na hali, ilimi both Islamic and western, his father's favorite, the first born to the house of F, har yau Allah be yi yayi aure ba kaman ba Baba prof ne ya haife shi ba.

Fadeelah tana auren wani businessman suna zama a Australia with kids.

Faahim Navy ne, an aura mishi Fadyaa suna da ?a?a biyu. Auren da saida aka kai ruwa rana da Ammi ta saduda.

Falaq har yau bata yi aure ba sbd rashin lafiya da take fama dashi.

Fahad na aiki da inland revenue with a wife and a kid.

Farida tayi aure some months ago with a costume officer suna zaune Lagos.

Falusha and Farrah duk tare aka yi aurensu su biyun duk suna yola suna auren ma'aikatan Gomnati.

Faraj, Farhan da Farzan duk suna final year of their studies a Apti American University mabanbantan courses.

Farhuddeen da Faris suna SS3

Fatima na SS2

Fauxa da fa'iza na SS1

Fadhiya js1, Fakiha pri5 and Faazila pri3.

Tou readers ya kuka ji GIDAN F? A tunaninku duk wani haWin kai da kaunar juna da zaman lumana dake wakana a wannan gida me cike da addini me Waurewa ne har abada? SheWan ze iya barin Waurewar wannan haWin kan da kaunar kuwa? Akwai wasu abubuwan da ban sa cikin tarihin gidan ba a hankali a hankali Zaku fahimta in shaa Allah, mu je zuwa @&? @&? @&?.

DIDDIGAR ?AYA...(Mai wuyar tsincewa) wannan littafi littafin kuWi ne..
Ze zo muku a Naira Wari uku kachal #N300.
Acc no. 0545475847
Acc name. Fatima Muhammad Gurin
Bank name. Gt bank
Se ki tura shedar biya zuwa wannan layin
09039206763
Ko ki tura katin waya ta layin na sama tare da shedar biya ta what'sapp.
Yi maza ki biya naki ki sha karatu cikin kwanciyar hankali, ina me tabbatar miki bazaki taSa nadama ba>?p?

Karku sake a baku labari.


=???Gureenjoh=???















DIDDIGAR ?AYA
(Mai Wuyar Tsincewa)

(3E DDG 'D1-EF 'D1-JE

FATIMA MUHAMMAD GURIN.
(Gureenjo)

ADABI WRITERS ASSOCIATION

Marubuciyar:
*Zuhraa*
*Hamrah*
*Igiyar Rayuwa*
*Noor Iman*
*Ruwan Sama..*
*Lelewal*
*GAMON JINI paid*
*Kowa Ya ga zabuwa..*
And Now..
*Diddigar ?aya... Paid*

*Shafi Na Shidda*

*PAID BOOK*

?AN?ANO

**WANNAN SHAFI SADAUKARWA CE GAREKI MRSJMOON GWANATA KUMA SHUGABATA>?p?d'?**

"Wa'alaikumussalam warahmatullah sannu da zuwa Mammi"
Cewar Fauxa tana me sakin murmushi.

Jaddah ma sannu Da zuwa ta mata, Seda ta amsa na Jaddah kan tace
"Fauxa ke kam ba zan amsa ba, ri?e kayan ki"

Dariya suka yi duka tace
"yi hakuri maa in shaa Allahu zan zo"

Tace
"na gaji da ji, ke kam gidan mu kaman wadda aka yiwa farraku dashi idan ba'a compound ba ko nan sashen Jaddah ba'a ganinki Sam?"

Dariya kawai take yi, wlh ita tana rasa dalilin da yasa take kasa shiga sashen na Baba prof, duk matanshi ma dama banda gaisuwa Mammi ce kawai take sakewa sossai, tana son matan ba tare da ta san dalili ba.

"Ina yini Jaddah? Fatan mun sameku lafiya?"

Cike da so Jaddah ta amsa mata, duk cikin surukanta babu mafi soyuwa a gareta irin Aisha, matar ta dabance cikin mata, tana da kawaici sossai gata da fara'a bazaka taSa ganinta bata murmushi ba, tana da son mutane da jan kowa a jiki bata damuwa da kai nata ne ko ba nata ba, tana da kirki fiye da zato, duk cikin matan na Baba prof babu me shiga kitchen da kanshi yayiwa Jaddah girki na musamman ya kuma tako ya kawo ya zauna suyi hira sossai irin Mammi.

Dukda tana yawan fama da matsanancin ciwon kafa se ta kwana biyu uku ma bata iya tafiya idan ciwon ya tasar mata amma hakan be sa tayi kasa a gwiwa wurin kula da mijinta da surukanta ba, kuma ita da kanta take taya baba prof kula da mahaifiyar tashi mace ce da a duk lokacin da mijinta ze shigo da wani abu a Leda bazata taSa karSa ba se ta tambayeshi ina na Jaddah? Idan har ya manta ko be saya ba sbd ganin ta girma da abun ko wani abu haka zata sa ya koma ya sayo, tana da wani ?ima na daban a zuciyar mutanen gidan musamman mijinta da surukuwarta.

"Aisha ya ciwon kafan? Fatan kin ji daaWin maganin nan na Gamborun gala?"

Tana murmushi tace
"wlh na ji daaWinshi sossai Jaddah, kafa yayi sau?i sosai"

Jaddah tace
"Toh Allah ya qara afuwa"

Suka amsa da Ameen.

Chan cikin hiransu Jaddah tace
"ni kam Aisha kina ji daga wurin wannan Miskilin nawa kuwa? Kwana biyu be kirani ba fa"

Maa tace tana murmushi
"eh Jaddah, ya ce min ze shiga ?asar da bashi da simcard Winta idan har ze fi kwana biyu to ze saya Sim Win sbd mu ji lafiyar shi idan kuma ba ze wuce hakan ba in ya bar ?asar in shaa Allah ze ?ira"

Jaddah tayi tsaki tace
"ba ga irin ta ba, mutum ne kullum a sama kaman tsuntsu fisabilillahi idan ya zo nan fa ya zube Sima simai se ki dauka kamfanin mtn ne, wani idan ya manta na wa???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ce kasa ce kuma be da lokacin gwadawa sede kiji katttt ya karya ta"

Mammi na dariya zata yi magana kenan Fauxa ta mi?e Tsam tayi Wakin Jaddah fuskanta babu yabo babu fallasa, da idanu duk suka bita Seda ta shige kan Jaddah ta zabga tagumi cikin jimami.

Mammi tace
"Jaddah Dan Allah ki dena sa damuwa a ranki sbd yaran nan kar kije wani ciwo ya kama ki, har yanzu dukkansu yara ne in Shaa Allah gaba ko ance su yi baza su yi ba"

Jaddah tace
"se yaushe kenan Aisha? Karki manta Faizan ya baiwa Talatin da biyar baya wannan ta fi sha shida amma ace se gaba? Wani gaban kuma bayan wannan? Wlh Allah ya gani babu abunda ke ci min tuwo a ?warya irin tsananin rashin jituwar yaran nan, har tsoro irin ?in da suke yiwa juna yake bani kwata kwata Waya baze taSa bada fuska ayi maganan Waya a gabanshi ba?"

Mammi tace
"ni na fi ganin laifin shi babban kwabon nasu ai, na yi faWa har na gaji amma ya kasa fahimtata"

Jaddah tace
"ya Allah ka kawo mana karshen wannan abun nasu"

Mammi ta amsa da Ameen suka kama wani hiran kuma se dab magrib kowa yayi alwala suka tafi masallaci a tare.

Bayan kwana biyu

Tunda ta tsefe kanta bata yi kitso ba gashi har yau Sunday, barta dae da neman tsokananta wadda bata rabo dashi, ita da fa'iza ce tafe suna hira sbd duk gidan babu wacce suke shiri kuma suke ?aunar juna kaman fa'iza babu wacce kuma ta tsana irin Fatima in ka cire Faizan.

Abun nata kaman jinnu, tana son fa'iza sbd ha?urin ta ta kan yi hakuri da duk wani halinta tana yawan kare ta, in kaga sun yi faWa to akan Fatima ne, Fatima na son nuna mata uwarsu Waya da fa'iza ita kuma ta tsani hakan, idan kuma fa'iza tace mata kar ta biyewa Fatima su yi ai jinin dake yawo a jikinta shine yake yawo a nata jikin tunda uba suka HaWa se ta ce ai fa'iza ta goyi bayan Fatima alhali Agola take a gidan Anan zasu yi faWa su Rabu Toh Fauxa da zuciya se ayi kwana biyu bata huce ba hakan yasa shirin su da fa'izan yake yawan ja baya.

Sashen Jaddah suka shiga tana zaune tana jan chasbi Fauxa ta zube kan kujera tace
"Jaddah wainar fulawa nake son ci na manja da yaji me tafarnuwa"

Jaddah tace
"se ki ci ai, ni kam ban

4 / 29