Advertisements
Chapter 14 Reading Goran Duma by Maimuna Idris Beli BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Goran Duma by Maimuna Idris Beli

Author :  Maimuna Idris Beli Category :  Action Novels

Chapter   14 / 28

39K to 42K   out of 82.5K words

sanar da ni
ba. To don Allah ina rokon arziki kar ka yi wasa da
lafiyarrta ku je asibiti a shirya mata fayil, kuma abi
dokokin likita".
A sanyaye ya ce mata. "Babu komai, in Allah Ya so za a yi,
Allah Ya inganta, Ya sauke ta lafiya".
Momi ta amsa, "Amin". Sannan suka yi sallama.
Ya wuni da abubuwa biyu, tsabar murnar cikin Rumasa'u
saboda dokin samun magaji, da kuma
takaicin yadda Rumasa'u ke yawan hada shi da iyayensu.
Da ya dawo gida da yamma ya jima a dakinsa Rumaisa'u
ba ta shigo ba, saboda haka ya sameta a
dakinta, sai ya tarar da ita a bandaki tana kwara amai,
dole ya sassauta 6acin ransa ya yi tsaye a
bakin kofa yana mata sannu, har ta gama aman, ta gyara
wajen ta wanke baki sannan ta wuce firji ta
ciko tambulan da ruwa ta zuba glucose ta shanye sannan
ta dawo ta zauna yana bin ta da kallon da
ya sanya ta tsarguwa shi yasa ta kasa hada ido da shi, shi
kuma ya 'ki tanka mata.
Can ta mi'ke ta kawo masa lemo da fura sannan ta koro
masa bayani.
"Don Allah ka yi hakuri yaya Yusha'u, wallahi na sha
ciwon 'kafa dazu shi yasa ban sami sararin yin
abincin ba".
Ya jima cikkin shiru sannan ta tsinka bayan ya tsiyayi
leman ya sha. "Ya ya zan yi Rumasa'u, tururuwa ta yi
jidon banza ma ballantana ranar garar 'yarta".
Tana 'kila wa 'kalan fahimtar inda maganarsa ta dosa duk
da ko ta fahimta din ba ta da kalmar amsa
masa dan haka ta kyale kanta da damuwa da sai ta
fahimta. Sai da ya gama shan furar sannan ya dubeta da
kyau, ya ce.
"Yanzu tsakani da Allah Rumaisa'u kina dauke da cikina in
rasa arzikin ki sanar da ni?
Duk lamurana ba kya daukarsau da muhimmanci idan ba
wandanda ba ki 'kudurta kai ni 'kara wajen mahaifanmu
ba".
Ta yi shiru 'kirjinta sai bugawa yake saboda tsoro, bakinta
sai rawa yake ta kasa samo hanyar kare kai saboda haka
shi kuma ya sami sararin fitar da dukkan zargin da
zuciyarsa ta sa'ka masa.
"Tun kafin auren nan fargabar a ta dame ni ke nan, ni na
san zurfin iliminki ba zai barki daukata wata tsiya ba bare
ki kimanta ni, duk wani abu na ha'k'kina ko naki kina
ganin na yi tsororo ki cika min shi ko ki gabatar min.
Babu wani abin arziki da nake tsinta a wajenki sai na
'korafi da kaiwa iyayenmu magana... Takardar jarida ko
mujallarki ta fi ni kima da daraja..."
Yanzu kwallar da ta taru a idonta ta fara saukowa,
cikinta kuma ta dago ta dubi Yusha'u murya a raunane ta
tare shi.
"Wallahi Yaya Yusha'u ban ta6a kai 'korafinka ko 'kararka
ba, wannan kuma da na fadawa Momi ba 6ata ka nake
nufin yi ba, kawai dai na yi tunanin ita zata fi iya fahimtar
da kai matakin da za a iya dauka a kaina. Yadda aurenmu
ya zo bagatatan ne duk ya janyo wannan matsalar, tun
kafin mu yi aure ya kamata ka san yadda rainon cikina zai
kasance..."
Ya tare ta a zafafe. "Karki sauya min magana ko ki yi min
gori Rumasa'u, yadda aurenmu ya zo ni ban ta6a
daukarsa wani daban da yadda ya kamata aurena ya
kasance ba, Allah ne Ya za6a min ke ban kuma yi butulci
ba na kar6a, na ri'ke ki da iyakar adalcin da zan iya. Duk
wani abu daban sai dai in a wajenki ya ke, ba kuma a
baibi kike ba ni yadda na kabari ya fi ni daraja a wajenki
ba..."
Sai ta bude baki cikin tashin hankali tana dubansa, kuka
ya dinga fizgirta, amma ita ma ta dinga hadiye shi, a
karshe cikin rawar murya ta ce.
"Yaya Yusha'u me nake yi na zafi haka?"....
Dan Aunty.
GORAN DUMA (P 32)
.
.
Ya tsare ta da ido, ya ce. "Tsakaninki da Allah idan Auwal
ne za ki zauna da cikinsa tsawon wata biyu ba ki sanar da
shi ya yi
farin ciki ba?"
Takaici da rauni ya cikata, dan haka ta saka masa ido ta
kasa tanka masa.
Ya ce. "Ki amsa min mana!"
Ta girgiza kai tana dubansa kai tsaye da alama ya fara
'kure ta.
Ta ce masa.
"Idan na amsa wata'kila kai tsaye ka yiwa amsar tawa
kallon wautacciya, in daga zuciyata kai tsaye amsa zata
fito."
Cikin gadara ya ce.
"Idan ma a haukace zata fito ina jiranta. Na kuma
tabbatar ba zata sauya daga yadda na zace ta ba".
Hawayen idonta ya fara gangarowa, tana kallonsa kai
tsaye ta ce.
"In da Auwal ne ba zan kai tsawon wata biyu da ciki ba
tare da ya binciko da kansa da kansa ba,
cikin wata biyun nan wanne irin amai ne bana yi, wanne
irin zazza6i ne ba na yi, wacce irin kasala ce bana yi?
Yaya Yusha'u duk sanda zan gabatar maka da wadannan
matsaloli 'kar'kari ka ce min ok Sannu, Allah Ya sauwa'ke
sai ka ga na galaibata ne kake kawo min maganin
shawara, ko kuma
tarkacen magunguna daga kyamis...
Saboda haka ne sam ba ni da 'karfin gwiwar sanar maka
da wani abu da ya dangance ni..." Rumaisa'u bata kula ba
ne, tuni Yusha'u ya zo wuya taf! Tana direwa kuma ya fara
zubar da bala'in da ya 'kunshe.
"Ka ji ba! Rumasa'u ni kike fadawa wannan maganganun
saboda rashin ladabi ko?
Saboda tsabar ke butulu ce wacce irin kulawa ce bana yi
miki?
Duk namiji ne zai jure wannan jarabar laulayin naki
amma ina iyakacin kokarina kina nuna min na gaza,
kuma saboda tsabar raini ki keta idona ki nuna Auwal ya
fi ni matsayi a gurinki?...
Dadin abin ya gama yi miki nisa, duk yadda kike jin fitsara
dai ba zaki dauko gawarsa ki gina mata daki a cikin gidan
nan ki ce kishiya ne shi ba...."
Bai ko saurareta ba fuuu! Ya fice ya bar dakin sai ya bar ta
da binsa da kallo, lokaci guda kuma hawayenta ya dauke
saboda maimaita kalmar
KISHIYATA da Yusha'u ya ambata tare da tuno yadda
Auwal yake ambaton kalmar da KISHIYI.
Kusan sati guda Yusha'u na gaba da Rumaisa'u, ba gabar
magana ba har da na dauke hannu a shigo
mata da abubuwan masarufi dangin ciye-ciyen kayan
gina jiki, kaza, balangu, kifi da kayan itaciya, ''Inko hakane
gwara ya daina fita. Don ni ban ga amfanin dukiyar da
iyalina ba zasu
amfaneta ba'' wadanda su kadai ne ba ta rasa ba a abin
da ya kamata kada sickler ya rasa su, saboda haka 'kan-
jikinta ya 'karu, ga nata na asali ga na raunin ciki sannan
ga na 6acin rai.
Suka sake share wasu sati biyun a haka, bayan muguwar
rama yanzu ta fara d'ashewa alamun jini ya yi mata
'karanci, babu ciwo dai sosai, sai yawan kwanciya da bin
sanyi wanda shi ma alamu ne na
'karancin jini a jikin sickler.
A karo na hudu da Innarta ta kirata dan ta ji batun
zuwansu asibiti, sai ta fada mata gaskiya don 'karya ta kan
fada mata cewa 'mun je', yau cikin kuka sai ta fada mata.
"Wallahi Momi ko soron 'kofar gida ban taka da sunan
asibiti ba, a halin yanzu kuma ina cikin wani
hali dan ina ganin alamomin rashin jini... Amma don
Allah Momi mu nemi wata shawarar kar ki yiwa Yaya
Yusha'u magana, tuhumata yake da kai 'kararsa."
Momi ta rasa abin da zata ce saboda mugun takaici,
kawai sai ta ja numfashi ta ce.
"Shikenan, ba ni awa daya na yi tunani zan kira ki".
Ba ta ko jira cewar Rumasa'u ba ta kashe wayar, kai tsaye
kuma ta kira Yusha'u cikin tsananin fushi, ko
gaisuwarsa ba ta amsa ba, ta ce.
"Yusha'u ka tuna na ta6a fada maka cewa, ina da juriya
akan komai amma ban da akan Rumasa'u?
Zan iya yi maka kawaici akan komai amma ban da na
wasa da ranta, mun shiga sati na uku a maganar da na yi
maka ba ku nemi hanyar asibiti ba, yanzu da na
tuntubeta ta tabbatar min tana tare da alamomin
'karancin jini. Wallahi Yusha'u ba zan iya zuba ido ka yi
min sanadin Rumasa'u ba..."
Muryarsa a tausashe, amma maganarsa zazzafa dan cewa
ya yi. "Ai babu mai iya kashe wani sai Allah!"
A fusace Momi ta ce masa.
"Au haka ka ce?
Shikenan Allah Ya kaimu gobe ni kuma zan zo in nuna
iyawata akan hanawa ka zama silar Rumaisa'u, in ma ka
6oye manufar shirya
kasheta ne saboda an aura maka ita bisa tilas ni zan yi
maka gatan rabaka da aurenta..."
Ba ta ko jira cewarsa ba ta kashe wayar, nan take ya hada
gumi kashir6an dan ya san Momi ba wa'ka take ba,
zazzafar mace ce shigen mahaifinsa. Tsab zata zo kuma ta
dauke Rumaisa'u dole kuma maganar ta je kunnen
mahaifinsa, wanda zai iya mummunar sa6a masa.
Bai yi dogon nazari ba ya hau kiran Momi tana 'kin amsa
kiran nasa, shi kuma ya nace cikin tsabar dakan zuciya,
amma yana mita. "Mahaifin Rumasa'u ya zama hoto,
dama yawancin masu d'amarar nan matansu ke juya su,
haba me za a yi da auren 'yar mace?"
Ire-iren mitar da ya dinga yi ke nan yana nacin kiran
wayar Momi, kusan sau ashirin sannan ta
daure ta daga. A ladabce ya ce.
"Don Allah Momi ki yi hakuri, wallahi za a yi yau din nan
ba zamu kwanta ba sai an je asibiti, na rantse miki".
Ta sauke hucin 6acin rai, sannan cikin lumana ta ce.
"Yusha'u ka yi tunani da kyau, bai kamata sai an yi
yun'kurin gwada maka 'karfi zaka tausaya wa 'yar
uwarka ka yi mata abin da ya kamata ba, ko babu igiyar
aurenka akan Rumaisa'u ai abar ka tausaya mata ce,
yanzu ta ce min jininta ya yi 'kasa sosai,
idan aka sake nan da kwana biyu, sai dai ka ji batun yi
mata 'karin jini".
Cikin 'kas'kantar da murya ya ce.
"In Allah Ya so ba za akai wannan matakin ba Momi, ki yi
hakuri". Cikin sakewar Murya ta ce."To na yi, Allah Ya yi
muku albarka".
Da ya koma gida da yamma,
Rumasa'u ta kawo masa abinci a dakinsa sai ya dinga
satar kallonta. Ta yi mugun ramewa, sannan
ta yi wani irin fari, idanunta kuma sun yi wani 6ulu-6ulu
sun kukkunbura. Ta zauna jim amma kafin ya 'karasa cin
abincin sai ta tashi ta koma dakinta ta kwanta, yanzu
babu abin da yake mata
dad'i sai kwanciya, hatta dan karance-karancen jaridu da
mujallun da ta ke samun yi a da yanzu gagararta yake,
duk da ma dai Mubarak me daukar nauyin kawo mata
jaridun jarabawa ta 6oye shi. A haka ta jiyo motsin
shigowar Yusha'u, haka kawai sai ta ji gabanta na faduwa
dan ta
ha'ki'kance da kyar idan ba gadar mata da wani takaicin
ya kawo shi ba.
Sai dai ya shigo dakin cikin sakin fuska ya nemi stool ya
zauna idonsa a kanta, ta dan dube shi da kyau sannan ta
lumshe ido.
Ya yanke shirunsa da cewa.
"Kwanciyarki ta yi yawa, ko yaushe ke kenan a akwance".
Ta bude ido ta dube shi, amma ta kasa cewa da shi
komai. Ya sauke numfashi ya ce. "Jaridancinki dai a gidan
aurenki da mijin aurenki
kike sauke shi. A zamanmu dad'i da wahalarmu gaba
daya babu na sirri kunnen iyayenmu da 'kawaye kaiconki
Rumaisa'u, wallahi ba ki morre hali ba..."
.
Dan Aunty.GORAN DUMA (P 33)
,
,
Ta kokarta ta tashi zaune ba tare da ta shirya ba ta ji kuka
ya kwace mata babu kakkautawa, yana kallonta zuru yana
dokin ta yi shiru har kukan nata ya fara ta6a ransa,
babu shiri ya cimmata ya fara rarrashi. "Ki yi hakuri ni
ban fada dan cin fuskarki ba, na fada ne dan ki ankara da
laifi da cutarwar da ki ke min fisabilillahi ina mutunci a ce
duk sirrin gidanmu a kunnen Hajiya, Momi da sauran
dangi da 'kawaye..."
Ta dakatar da shi cikin kuka. "Ba gudun cin fuska ya ba ni
kuka ba Yaya Yusha'u, illa mummunar shaidar da ka yi
min a matsayinka na mijina har kana tir da halina....
rayuwar nan ba ta da garanti musamman ta mutum
irina... Idan Allah Ya kar6i raina yanzu wannan shaidar
'kila ta yi tasiri a kaina... Dole in yi kuka dan ban san
yadda zan gyara ka yarda da ni ba".
Ya 'kara tausasa murya ya ce. "Ki daina kai 'karata gurin
Momi ko Hajiya, ki dinga 6oye sirrin gidanmu ba fa jahila
ba ce ke Rumasa'u, kin sani yana daga nagatar mace 6oye
sirrin mijinta..."
Ta jima tana kallonsa cikin hawaye, sannan ta kwace
kafadarta ta koma ta kwanta alamar ta ma rasa abin da
zata ce.
Ya yi saurin dagota ya ce. "Babu abin da zaki ce?"
Yana rufe baki ta amsa.
"Idan in ce dan in kare kaina ne ba zan ce din ba,
dan kar mu ci gaba da 6atawa juna lokaci, amma zan iya
cewar da zata iya zame maka wani nauyi a
ayyukanka biyu na duniya da lahira cewar tawa ita ce,
duk matsananin halin da zan shiga kuma duk yadda
Momi zata kwakkwafe ni ta ji matsalata ba zan kuma fada
mata ba, in ka kula da ni kanka Yaya Yusha'u, in ka yi
sakacin da na rasa raina sai ka shirya amsa tambaya
wajen Ubangiji fa'kat!"
Yusha'u ya yi wuri-wuri ya rasa abin da zai ce mata, sai da
kyar ya lalubo shi.
"Abin da kika fadawa Momi ke nan ina sakaci da ranki?
Amma sam ba ki yi min adalci ba Rumaisa'u".
Ta goge hawayenta duk da wasu sun kuma kunnonwa, ta
dube shi ta ce.
"Kana dai so sai na kare kaina ko? To ka san dai mutum
ba zai rayu ba sai da jini?
Dube ni".
Ta shiga gwale idonta fatar ba'kinta tare da nuna masa
tafukan hannayenta, sannan ta dora.
"Jinina ya yi 'kasa sosai, da ko ba ni da ciki dab nake da
shiga mawuyacin halin da zai kai ni matsayin 'karin jini.
An yi maka batun fa'idar zuwana asibiti tun sayi biyu da
suka wuce ba ka dauki batun da muhimmanci ba, ban yi
tsammanin zai zama laifi ba dan Momi ta binciki halin da
nake
ciki na sanar mata ina da matsalar rashin jini, ko babu
komai ya fi sama ta ka a ce musu ga ni kwance ana 'kara
min jini... ko su zo su bayar da jini a 'kara min".
Da ya rasa bakin magana sai ya fanshe akan kalamanta na
'karshe.
"Lokacin da ba ki karkashin ikona ma na ba ki jini
Rumasa'u bare ki yi min gori... in leda goma ne zan
iya baki ba leda daya ko biyu ba". Yana rufe baki ta amsa
masa.
"Rigafi ai ya fi magani".
Ya ce, "Me kike nufi?"
Ta amsa masa, "Ka yi tattalina kar na rasa jini ya fi
burgewa akan ka bar ni na rasa ka bayar da leda
goma a 'kara min".
Yanzu ya rasa abin da zai ce mata bilha'k'ki, sai ya 6uge
da duban agogo lokacin da aka rera kiran sallar magriba,
ya wuce kai tsaye batare da ya kare kansa ba.
Abin mamaki ba ya 'karewa a duniya, karfe tara na dare
Yusha'u ya shigo mata da Dan'Isiya mai kyamis a nan
unguwarsu dauke da akwatin magunguna da allurai.
Dan Isiya ya tsare ta da lacca da hudubobi bayan ya gama
karade ta da tambayoyin da ake wa sababbin zuwa awon
haihuwa, mata masu lafiya ba sicklers ba. Kallonsa kawai
ta ke kamar wani duron ya'kin
neman za6e, wani lokacin kuma ta sauke ganinta akan
Yusha'u wanda ya hakimce shi a dole ya yi abin arzi'ki.
A karshe Dan Isiya ya ce, tun da cikin bai kai ko wata uku
ba ba sai an yi awo ba, yanzu zai dauki jininta ya tafi da
shi lab. gobe zai kuma yi mata allura yanzu sannan ya
bata magunguna musamman na 'karin jini.
Duk Rumaisa'u na kallonsa bambarakwai har ya fito da
sirinji ya zu'ki jininta, sai da ya zu'ko allurar da zai mata
ne sannan ta magantu. "Tun safe ban ci abinci ba bai
kamata a yi min allura ba, zai fi kyau a bari sai gobe".
Dan Isiya ya mayar da ruwan allura cikin kwalba yana
cewa.
"Eh gaskiya ne, in Allah Ya kaimu goben sai na zo na yi
miki".
Yusha'u kuma ya ce.
Amma kina kallonsa ya zu'ko?
To ya zauna ya jira kici abincin mana ya yi miki..."
Ta girgiza kai ba tare da ta dube shi ba, ta ce. "Nidai sai
gobe".
Dole ya kyale ta, ya mayar da hankali ga Dan Isiya da ke
zube masa magunguna yana masa bayaninsu.
Yusha'u ya ce.
Ina fatan akwai na 'karin jini?"
"Akwai".
Yusha'u ya ce masa.
"Yauwa, ka hada mata da maganin kasala da na 'karfin jiki
ba ta da aiki sai kwanciya".
Nan ma Dan Isiya ya ce.
"Duk akwai".
Ya dure musu magunguna tuli a leda ya mi'kawa Yusha'u,
shi kuma ya mikawa Rumasa'u ya wuce
raka Dan Isiya. Ya dawo mata da gasasshen nama da
nonon roba
mai sanyi. Da kansa ya nemi faranti a kicin ya zuba
naman ya kawo ruwa da lemo ya zube, sannan ya ce
mata.
"Ki zo ki ci ki samu ki sha magani".
Tun da ta ga 6arin jikin da ya ke ta san ba na Allah da
Annabi ba ne, tattalin raya darensa kawai yake,
dan haka ta zage ta yiwa naman cin 'koshi cikin 6oye
6acin zuciya, dan ta san idan ma ba ta taimaki
kanta ta ci ba babu abin da Yusha'u zai raga mata,
gara ma ta kori yunwa ko ta rage wa kanta wahala.
Har ta gama cin naman da fargabar abubuwa biyu, wato
yadda zata ji jiki a shimfidarsu da kuma yadda zata
gujewa shan wadannan magungunan da wata
'kila in ta sha su yi ajalinta.
Bayan ta gama ya dauke farantan da tarkacen kayan da ta
sha lemo da yagot, sannan ya dawo ya janyo ruwa ya
janyo ruwa ya tsiyaya mata a tambulan kana ya janyo
ledar magunguna ya fara 6alla. Kijrinta sai dakan uku-uku
ya ke ta dube shi ta ce.
"Yaya Yusha'u har na gaji da gaya maka ba na shan
maganin da duk ba likita ne ya rubuta min ba".
Ya tsayar da 6allo maganin sororo yana kallonta, cikin
hadiye bacin rai ya ce.
"Da yake nan ya ba ki wadannan magungunan?
Dauko miki shi da na yi har gida bai zama garkuwar da
zaki zarge ni da shi ba musan abin da muke ba?"
Ta girgiza kai a raunane, tace. "Likita daban mai kyamis
daban Yaya Yusha'u, in ya san abin da yake yi na tabbatar
ba lallai ya san yadda ya kamata tafiyar da sickler ba...."
Ya tare ta da alamar rarrashi, Rumaisa'u bata zargi karya
ba, ya yi kewarta yana kuma son ya fanshe a yau, dan
haka ya 'ki su yi fada, ya ce mata. "Tun da kin iya karatu
kin kuma san kan magungunan me yasa ba zaki dube su
ki gani idan ya yi miki ganganci ba?"
Tun da an ce Mutum ba ya 'kin ta mutane, ta mika hannu
ta kar6i magungunan na farko da ta dago
sai ta tarar capsil ne na 'karin jini. Ta daga maganin tana
duban Yusha'u fuskarta cike da takaici ta ce.
"Daga inda ya dauki maganin karin jini ya ba ni na san bai
san aikinsa ba..."
Yusha'u ya tareta cikin tsabar mamaki.
"Amma dai ke kika ce kina da 'karancin jini ko?"
Ta amsa masa cikin sabawa da takaici.
.
Abbas Abdulkadir Hada Hada ( Dan Aunty.)
GORAN DUMA (P 34)
.
.
Ta amsa masa cikin sabawa da takaici.
"Ba zan iya 'kirga sau nawa na yi 'karancin jini daga
haihuwata zuwa yau ba, amma ko sau daya likita bai ta6a
ba ni maganin 'karin jini ba, sickler ba ya bu'katar
maganin 'karin jini, domin cikin kowanne irin maganin
yana dauke da sinadarin Iron, su kuma sicklers suka sha
maganin 'karin jini to
jininsu zai daskare kamar gasara, abin da zai faru da su
kuma Allah ne kadai zai iya faru da su kuma Allah ne
kadai zai iya iyakance shi".
Yusha'u ya yi shiru kawai yana kallonta, ba wai bai yarda
a ita ba, amma in ya bi ta kamar ya fadi, sai
dai dole faduwar zai yi, dan

14 / 28