Advertisements
Chapter 8 Reading Goran Duma by Maimuna Idris Beli BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Goran Duma by Maimuna Idris Beli

Author :  Maimuna Idris Beli Category :  Action Novels

Chapter   8 / 28

21K to 24K   out of 82.5K words

da kana da niyyarsa ba,
wannnan ne yasa ya daure ya ce.
"Abin har ya yi zafi haka Auwal? Ba zaka iya
fitar da yarinyar nan a ranka cikin ruwan
sanyi da dalilin matsalarta a rayuwarka da ta
'ya'yanka ba?"
Auwal ya muskuta da murmushin ya'ke
alamar akwai magana fal a cikinsa, sai dai
yadda zai furta ya yi girma, don haka ya
hadiye ta kawai ya bi mahaifinsa da shiru,
har mahaifin nasa ya gaji da jiran cewarsa
ya nemi guri ya zauna idonsa akan Auwal.
"Tun farko ka san Rumasa'u sickler ce?"
Auwal ya kad'a kai, mahaifin nasa ya dora
wata tambayar.
"Wanne mataki ka dauka akan yadda za ku
rayu tare, ko kaucewa yadda za ku haifi
'ya'yan sicklers?"
Auwal ya jima kafin ya tattaro abin cewa.
"Ta yi 'kokarin hana ni aurenta tun ranar da
muka had'u na dage. Duk matsalolin da ka
lissafo min da bakinta ta lissafo min su,
amma ba su gigita ni yadda suke gigita ku
ba... Da ta ga haka sai ta shawarce ni yin
gwaji dan sanin makomar 'ya'yanmu, na
amince a sannan amma sai na ga gwajin
6atawa kai lokaci ne da tanadar wa kai
fargaba, don na ji a raina ko wane irin
sakamako gwajin zai haifar ba zan iya
barinta ba, saboda haka na ce ta bar
maganar gwaji".
Mahaifinsa ya jima cikin shiru yana jiya
maganganunsa, kafin ya yanke hukuncin d
ayake jin shi ne na 'karshe.
"Gaskiya ta yi hange mai kyau saboda haka
shawararta ita ce abin bi. Ka je ka yi gwaji
idan akwai matserar 'ya'yanku sai ku yi
aure, idan kuma babu, to ku dubi girman
Allah ku ceci 'ya'yanku ta hanyar ha'kura da
juna".
Duk da Auwal ya ji maganar mahaifinsa da
kamar maimaici kawai, ma'ana babu wani
sassauci haka ya cije a ladabce ya gyad'a kai.
"To na gode Abba".
Ya m'ke kuma salin-alin ya fice ya shiga
'kwan'kwasa falon Innarsa.
Auwal bai 6oyewa Rumaisa'u komai ba
dangane da yadda suka yi da mahaifinsa da
hujjarsa ta sanin kukanta nasa ne, kukansa
ma nata ne. Tuni suka yiwa juna wannan
al'kawarin na tarayya akan matsalolinsu dan
nemo hanyar araka.
Rumasa'u ta jima ba ta yi magana ba, ba dan
rashin abin cewa ba sai dan saisaita
maganar don gudun kada tayi muni a
kunnen Auwal ko kuma ya zama wani
mataki na karyar masa da gwiwa.
"Kin 'ki cewa komai Rumasa?"
Ya fada bayan ya gaji da jiran cewar tata.
Ta gyara tsaiwarta ta 'kara jingina sosai da
motarsa saboda tana jin jiri. Ta yi
murmushin 'karfin hali ta ce.
"Abin da Abba ya yi shi ne ya kamata Auwal,
so ne tun farko ya ke runtse mana ido
alhalin wani dad'in gushi ne kawai a cikin
rayuwar aure, wanda ake 'kulla si domin
kammaluwar iyali. Ya wajaba ne mu
samarwa iyalanmu makoma ta gari, ba ya
kamata ba Auwal".
Shi ma ya yi murmushin 'karfin hali bayan ya
ji a ransa kawai 'karfafa masa gwiwa ta ke
so ta yi ba ainihin abin da ke cikin ranta ke
nan ba, ya ce.
"Kamar ke da Abba kuna mantawa ba a yiwa
Allah wayo, ke kanki aya ce Rumasa'u,
Innarki da Abbanki babu sickler ciki, amma
suka haife ki..."
Ta tare shi da dariya.
"Ba 'kokarin yin wayo ba ne, 'ko'karin
amfani da hankali ne, wanda Ubangiji Ya
hore mu da shi dan za6ar abin da zai
amfane mu da gujewa abin da zai cutar da
mu, abin da ya faru da mu cikin akasi mun
yarda daga Ubangijinmu ne ba tare da
sakacinmu ba, sai mu yi fatan zamowarsa
kaffa".
Auwal ya yi zuru kawai yana kallonta sannan
ya nisa ya ce.
"Ban sna me yasa duk cikin lissafinku ba
kwa duba uban yaran da samun su yake
'kila wa 'kala ba, sa ku kuka himmata
sarayar da shi alhalin shi ne a hannunku. To
zan fada miki abin d ana fada Abba jiya na
kwana da 'kokarin lissafa yadda zan yi
rayuwar da babu ke, na ji kamar
numfashina zai yanke daga lissafin kawai ba
tare da fitar da sakamako ba, amma dai ban
cire rai daga rahamar Ubangiji ba, duk za6in
da ya yi min ina fatan rahma da jin 'kanSa a
ciki".
Ta zuba masa ido, dauriyarta na kokarin
'karewa. Kasa gajiya da kalonsa da ta yi ne
ya sa ita ma ta tabbatarwa kanta wa'ka
kawai ta ke, amma tursasa kanta za6ar
tsaka-tsakin al'amura, sai dai kuma ta kasa
hana zuciyarta rauni da son nuna gazawa
da ta tsaya kawai ga bayyanawa ta hanyar
'kura masa ido cikin hawaye.
Haka suka tsaya ita kuka, shi hawaye, har
daga 'karshe ya zagaya mota ya shige yana
cewa.
"Zo mu je asibitin".
Ta yi saurin duba agogon hannnunta da ya
nuna 'karfe sha daya da mintoci sha hud'u.
Ta bude motar ta sunkuya a tausashe ta ce
masa.
"Bari na sanar da Hajiya".
Ya yi saurin tare da fadin.
"Rumaisa'u kar ki sanar da kowa
matsalarmu fa, umarni ne da kuma kokarin
kwantar da hankalinku ke da Abba zai kai ni
gwaji, ba dan na yarda da iya raba ni da ke
ko ya yi wani abu a cikin sonki ba. Ya
kamata ki ri'ke wannan kada ki yi 'kokarin
raba ni da kanki, son da nake miki mutuwa
ce kawai zata iya raba ni da shi".
Ta sororo cikin sanyin jiki tana kallonsa. Ta
hadiye kwallarta ta ce masa.
"Auwal wai me yasa ka damu da kira mana
mutwa? Ai ba sai ka kirata zaka bayyana min
kana sona ba,.."
Ya tareta cikin kyalkuala dariya.
"Me yasa ba kya so na kirata? In akiranta ne
dan na sna ita ce mai YANKE 'KAUNA, duk
yun'kurin raba mu da kuke ni dai na
tabbatar ita kadai ce zata iya raba ni da son
da nake miki. Amma na san ba ni da karfi ko
dabara a cikin aurenki yadda Ubangiji Ya so
haka zai yi".
Ta murza yatsu tana dariya, ita ma ce.
"Shikenan. In Allah Ya so ni da kai mutu ka
raba".
Ba ta jira cewarsa ba ta wuce. Ya bi ta da
kira, ta tsaya ba tare da ta juyo ba, ya dan
daga murya.
"Na fa gaya miki kar ki fad'a".
Sai kawai ta kad'a kai ta wuce tana dariya.GORAN DUMA 15
.
.
Dr. Hadiza ta gyara zama ta janyo wani fayil
cikin murmushi ba tare da dubansa ba ta ce.
"Soyayyar da kake mata da amincewarka na
aurenta a matsayinta na mai sikila shine matakin
farko na magance matsaloli ko yi musu kallon
'kanana a cikin aurenku, idan duk kun yarda da
wannan to kamata ce ku zo min tare, duk abin da
zan fad'a tare zai amfane ku, idan ma 'karfafa
gwiwa ne tare zai 'karfafa muku".
Auwalu ya jima bai tanka ba, sannan ya ja
numfashi cikin kasa hankula barkatai ya amsa.
"Haka Allah ya tsara na riga na taho ni kadai d'in,
amma na daura damarar zantar da ita komai
kamar yadda kika zantar da ni, hikimia ko ta aro
ce zan aro in yi 'kokarin fahimtar da ita".
Ofis din ya dauki shiru sai 'karar takardun da
likitan ke bud'awa da kuma bugun zuciyarsa da
ya cika masa kunne da rud'u.
Likita ta dago kai ta dube shi da wata takarda a
hannunta tana juyawa.
"Sakamakon gwajinka ya nuna cewa, kai AS ne,
ma'ana zaku iya haihuwar mai AS za kuma ku
iya haihuwar mai SS, wato ranar da ka bayar da
A ta bayar da S dinta za ku samar da d'a irinka
(AS). ranar kuma da ka bayar da S din ka dama
ita abin da zata bayar ke nan, to za ku samar da
d'a SS (sickler) irinta.
Abin da zan 'karfafa muku gwiwa da shi a nan shi
ne, ku shiga cikin hankalinku ku kyautata zaton
alkhairi ga rayuwar 'ya'yan da zaku samu a gaba,
wanda Ubangiji ne kadai Ya san yadda za su
kasance. Idan Allah Ya ga dama sai ya azurta ku
da 'ya'ya goma babu sickler ko daya a ciki,
ikonSa ne Ya umarce ka ka yi ta bayar da A
dinka har ku gama haihuwarku, idan kuma Ya si
zai iya jarabtarku da haihuwar sickler, Allah babu
yadda bai iya ba. Kai kanka zaka iya haifar
sickler ba tare da ka auri Rumaisa'u sickler ba.
Idan wadda ka aura din AS ce kamai ai za ku iya
tarayya wajen bayar da S zalla ku samar da
sickler. Abin da ya ke a rubuce dai babu wanda
ya isa kankare shi, dukkanmu ba dan ba
damarmu muke, Ubangijin da Ya yi ka AS shi ya
yi A. Ba don ya fi sonsa da kai ba. Kuma shi ya
yi S.S ba dan Ya yi masa laifi ba, sai dan haka
Ya so, haka Ya ga dama. Dan haka babu wani
dalili da zamu dogara da shi wajen hana aurenku
ina fatan ka fahimce ni?
A 'karshe ina shawartarka da kwantar da hankali
da mayar da lamari ga Allah, na tabbatar zai
saka maka da dubun alkhairi idan ka dogara da
shi ka auri wannan baiwar Allah ba tare da ka
guje ta ka gadar mata da takaici a zuci ba, kai
kuma ka saka 'karfi da dabara a cikin taka
rayuwar ba, yadda kake nuna wa ina fahimceka
da cewa ka dauki ciwonta naka, wannan ko
wanne sickler ke bu'kata. A yarda da rauninsa, a
tausa masa idan ciwonsa ya taso, a yi masa uziri
a taimake shi ta wadannan hanyoyin kula da
maganinsa, kaucewa abin da zai motsa ciwonsa,
hana shi aikin wahala tare da 'karfafa masa
gwiwar cutar da yake bautar Ubangiji ce. Idan ya
yi tawakkali ladansa ba zai lissafu ba. A yarda in
an haifi d'a sickler da shi ba shi kadai ya haifa
ba, da sauransu.
Duk wadannan dabi'un taimakon na zace su a kai
malam Auwalu dan Allah ka yi 'ko'kari kar ka ba
ni kunya".
Tunda ta ke magana hankalinsa ya kasu uku,
daya a kanta, daya akan batun mahaifinsa (ka je
ka yi gwajin idan akwai matserar 'ya'yanku sai
ku yi aure, idan babu to ku dubi girman Allah ku
ceci 'ya'yanku ta hanyar ha'kura da juna), daya
kuma wanda ya ke da kawo mafi tsoka akan
'kauna da tausayin Rumaisa'u, wanda a yanzu shi
ya sa shi fitar da 'kwalla bayan Dr. Hadiza ta
dire, zuciyarsa ta dame shi da son ya fad'a mata
'dama can ba ni ne matsala ba, mahaifina ne'.
Sai kuma ya ga fada matan wani rage karsashi
ne a dogon lokacinta da ta 6ata tana ba shi
shawarar rayuwa da Rumasa'u, wanda ko ba a
shawarce shi ba, abin da burika da ra'ayoyinsa
ke zartarwa ke nan.
Ya hadiye duk wata damuwarsa ya yi mata
godiya sosai, tare da nuna 'karfin imanin babu
abin da zai raba shi da Rumasa'u, suka yi
sallama dukkansu suna yiwa juna godiya.
Bayan ya fito asibitin ya yi mazantakar wucewa
ofis dan gwada 'karfin hali da na zuciyarsa da
koyawa kai jarumta cikin lamarin d ake fin 'karfin
iyawa, mahaifinsa ne abin jinsa, wanda alamu ke
nuna yana son saka 'karfinsa wajen taruwar
iyalai da babu tahalikin yadda za su samu.
Rayuwarsu zata kai ga haihuwar ko zata gaza, za
su haifa din ko ba'kararru ne su? Duk wadannan
gaibu ne babu wanda ya san shi sai Allah, idan
ya sa wa kansa damuwar rana guda a kansu ya
had'a wautar da zata kamanta shi da rashin
hankali.
Suna zaune a falon da suke hira, idan sun so
jimawa suna hirar ke nan, idan ba za su jima ba
dama a motarsa suke jingina su yi tad'insu.
Rumaisa'u ri'ke da takardar sakamon gwajinsu
tana juyawa, idan akwai abin da ya fi 'kunci da
d'aci to ranta shi ya yi. Abin da ke shirin faruwa
da ita zuciyarta ta 'ki yarda zata iya daukarsa
duk yadda ta yi 'ko'karin gwadawar.
Auwal ma ko da gwaji ya kasa ce mata wani
abu. Tunda ya ba ta takardar har sai da ta gaji ta
tsinka, cikin yi masa kallon kai tsaye.
"Auwal ban ta6a jin kaico da nadamar
kasancewa ta sickler ba sai a yau. Na tsani kaina
da duk wata tawaya da ta ke son raba ni da kai
Auwalu..."
Ya tare ta cikin dakewar 'karfin hali.
"Kar ki yi sa6o Rumasa'u, wannan wacce irin
wauta ce? Ki shiga cikin hankalinki, duk yadda za
ki so ni bayan Ubangijin da ya halicce ki ya
wajabta in bi. Tsanar kanki da tsanar
kasancewarki yadda Ubangiji Ya tsaro ki tawaye
ne da butulci gare Shi..."
Ta dam'ke bakin da ya yi mata amfani biyu, hana
sautin kukanta fitowa da nuna nadamar abin da
bakin ya fad'a, cikin raunanniyar muryar kuka ta
ce.
"Astagfirullah, Allahumma gafirni war hamni..."
Ta zare da shesshekar kukanta.
Shi ma duk yadda ya so ya daure sai dauriyar ta
fi 'karfinsa ya fara hawaye, ba dan yana zatar
musu rabuwa ba, sai dan shaukin yadda suke son
juna da tausayin Rumasa'u wadda ake son raba
su ta dalilin aibun da ba ita ta 'kaga wa kanta
ba. Mace mai sanyin halin da ta kasa fitowa kai
tsaye ta ga laifin mahaifinsa da ke son raba su,
'karfinta da yaji ta ke juyawa aibata mahaifinsa
baya.
Sun jima suna 'yan koke-kokensu kafin ita da ta
fi shi sharafin damuwa ta kuma soko wata
kato6arar.
"Da za a ba ni za6in rayuwar da babu kai ko
mutuwa, Auwal da gudu zan za6i mutuwar, har
yau ni ban san ta inda zan fara rayuwar ba, shi
yasa ka ji na kasa 'karfafarka bin umarnin Abba
don Allah ka yi min wannan uzirin... Ina sonka
ban san babu a kanka ba Auwal, wannan ciwon
ya fi sickle cell ciwo a raina..."
Ya tare ta cikin kasa tattara kalaman da za su
fidda ma'ana sosai, saboda rud'ani.
"Ba zamu rabu ba Rumasa'u ki daina ambato
mana rabuwar... Ni duk maganar nan ma ta
gundure ni wallahi".
Ta dago ta bi shi da kallo cikin hawaye.
"Haka ne burina Auwal, amma ba zan yaudari
kaina na dorar da shi da fatar baki ko ture abin
da ya kamata na duba ba".
Suka kuma daukar shiru sannan ta goge
hawayeta 2a fuskance shi
"Ka sanarwa Abba?"
Ya yi saurin girgiza kai yana kallonta sararo. Ta
'kokarta ta ce.
"Sai ka yi gaggawar sanar da shi, ya yanke mana
hukuncin da Ubangiji Ya za6a mana, fara shirin
zama tare ko kuma shiga makarantar koyon
juriya da rashin juna, ko wanne Ubangiji Ya za6a
mana muna fatan ya zama alkhairi a gare
mu".Ba ta jira cewarsa ba ta mi'ke zata bar
falon....
.
Dan Aunty
August 4 at 9:12 PM · PublicGORAN DUMA 16
.
.
Ya yi saurin dakatar da ita da cewa" Duk kurin da
na gama yi na cewa babu abin da zai sauya a
cikin soyayyarmu da auren kin fayalar da shi
kenan, dama kin tura ni gwaji ne dan ki rabu da
ni Rumasa'u?"
Ta yi saurin dawowa gabansa ta dur'kushe tana
girgiza kai cikin hawaye. Ta kasa magana sai
kallonsa da hawayen, shi ma ya motsa baki, ya yi
maganar amma ya kasa, har sai da ta gama nata
alayin ta riga shi samo abin cewa.
"Ina sonka Auwal... aurenka shi ne babban burin
da da ace ina da iko zan kusantar da shi tunda
ba ni da ikon na yi imani aurenko rashinsa da ni
kaina da kai duk muna shawagi ne cikin hukuncin
Ubangiji, zai iya kusantar da shi dan rahamarsa a
gare mu da ni'imarsa. Zai iya tankwa6ar da shi
dan isarSa a kanmu da zartar da abin da mu ba
mu san da shi ba, dan haka duk abin da ka ji na
fad'a kar ka yiwa ubangiji biyayya da faranta ran
Abba, a wani hannun kuma da 'kin biyewa zuciya
sakokinta... Ina sonka Auwal"....
Ya kai 'kololuwan rauni da tausayin Rumaisa'u
wanda ya 'kara masa miliyoyin kaunarta,
ma'kogwaron ya cunkushe da shu, shi yasa duk
yadda ya yi 'kokarin ya ce wani abu ya kasa,
kawai sai ya dauki takarda ya nemi hanyar fita.
"Ba zamu rabu ba Rumaisa'u ki daina ambato
mana rabuwar... Ni duk maganar nan ma ta
gunudure ni wallahi".
Ta dago ta bi shi da kallo cikin hawaye.
"Haka ne burina Auwal, amma ba zan yaudari
kaina na d'orar da shi da fatar baki ko ture abin
da ya kamata na duba ba".
Suka kuma daukar shiru sannan ta goge
hawayenta ta fuskance shi.
"Ka sanarwa Abba?"
Ka yi saurin gaggawar sanar da shi, ya yanke
mana hukuncin da Ubangiji Ya za6a mana, fara
shirin zama tare ko kuma shiga makarantar
koyon rashin juriya da rashin juna, ko wanne
Ubangiji Ya za6a mana muna fatan ya zama
alkhairi a gare mu".
Ba ta jira cewarsa ba ta mi'ke zata bar falon.
Ya yi saurin dakatar a ita da cewa.
"Duk kurin dakatar da na gama yi na cewa babu
abin da zai sauya a cikin soyayyarmu da auren
kin fatalar da shikenan, dama kin tura ni gwaji ne
dan ki rabu da ni Rumaisa'u?"
Ta yi saurin dawowa gabansa ta dur'kushe tana
girgiza kai cikin hawaye. Ta kasa magana sai
kallonsa da hawayen, shi ma ya motsa baki, ya yi
maganar amma ya kasa, har sai da ta gama nata
alayin ta riga shi samo abin cewa.
"Ina sonka Auwal... aurenka shi ne babban burin
da da ace ina da iko zan kusantar da shi tunda
ba ni d aiko na yi imarin aurenko rashinsa da ni
kaina da kai duk muna shawagi ne cikin hukuncin
Ubangiji, zai iya kusantar da shi dan rahamarsa a
gare mu da ni'imarsa. Zai iya tankwa6ar da shi
dan isarSa a kanmu da zartar da abin da ba mu
ba mu san da shi ba, dan haka duk abin da ka ji
na fada kar ka danganta shi da kanka Auwal,
danganta shi ga son yiwa ubangiji biyayya da
faranta ran Abba, a wani hannun kuma da 'kin
biye zuciya sakokinta... Ina sonka Auwal".
Ya kai 'koluluwan rauni da tausayin Rumaisa'u
wanda ya 'kara masa miliyoyin 'kaunarta,
ma'kogwaron ya cunkushe da su, shi yasa duk
yadda ya yi 'kokarin ya ce wani abu ya kasa,
kawai sai ya dauki takardarsa ya nemi hanyar
fita.
Ba ta takura kanta da binsa ko kiransa ba, kawai
sai ta raka shi da mafi sau'ki cikin abin da zata
yi, wato binsa da kallo har ya fice, sannan ta
durkushe ta fara kuka mai dalilin.
Kwana biyu babu labarin Auwal, babu wayoyinsa.
Ta yi 'kokarin kira duk a kashe. Ta yi tunani ta yi
issafin duk ta kasa cankar dalilin 6uyansa ko
kuma abin da ya 6oye shi, duk canki-cankin da ta
ji yana neman tafiya da numfashinta.
Auwal ya janye neman aurenta, hasashen da ke
kusan tafiya da numfashinta. Auwal ba shi da
lafiya, zargin da yake tilasta mata son lallai ta
san halin da yake ciki.
Kwana na uku ya kama alhamis, ba ta yi shawara
da kowa ba ta wanke 'kafa da yammaci ta dauki
Hafsat suka tafi Na'ibawa gidan su Auwalu.
Tun a hanya Hafsat ke tambayarta abin da ke
faruwa, musamman ganin yadda hankalinta ya yi
matu'kar tashi ba kamar a lokuta baya ba, inda
ko ya shafe kwanaki bai zo ba bata damuwa.
Rumasa'u ba ta 6oye mata komai ba ta zayyana
mata yadda suka yi.
Hafsat ta ce, "Ina ganin gara mu fadawa Inna
gaskiyar lamari idan muka je".
Rumasa'u ta dafe 'kirji ta ce, "Wai rufa min asiri,
kada a ga za'kewata da wawancina."
"Ba wawanci ba ne, Rumasa'u, yarda ce da nuna
bu'katuwar al'amarin nan."
Kallo daya Innar Auwal ta yiwa Rumaisa'u ta
gane ta, duk da ba su ta6a haduwa ba. Amma ta
yi mata farin sani a hotuna dan haka ta sauke su
da rawar jiki kamar zata goya su. Kasala da
kunyar da Rumasa'u ke bayyanawa ya sa Innar
Auwal jin wani irin tausayinta ya ishe ta.
Ta zauna suka gaisa cikin girmama juna.
"Duk manyan naku lafiya ko?"
Inji Innar Auwal, Hafsat ta amsa
"Lafiya kalau".
Rumaisa'u kai na 'kasa. Suka dauki shiru kowa
da abin da zuciyarsa ke sa'kawa, Rumasa'u na
jin tsanar kanta da kankambar zuwa gidan
surukai, surukan ma wanda auren d'an nasu da
damuwa da 'kila wa'kala, amma 'kaunar dan nasu
da sanin halin da yake ciki ya kore nadamarta
mai taurin kan da ta 'ki 'karuwa, sai ta tsaya
suke ta damun zuciyarta tare. Yanzu abin da ta
fi d'ko shi ne, ta ina labarin Auwal zai 6ullo
mata?
Can Inna ta nisa ta ce.
"Ku sha lemon don Allah, Nuraddin nake jira ya
shigo ya dubo shi ko ya farka, yanzu da
abokansa suka zo duba

8 / 28