Advertisements
Chapter 20 Reading Goran Duma by Maimuna Idris Beli BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Goran Duma by Maimuna Idris Beli

Author :  Maimuna Idris Beli Category :  Action Novels

Chapter   20 / 28

57K to 60K   out of 82.5K words

Bata
Karbekiba Ki Caje Maganar Nan Da Kyau Zaki Tarar Da
Kure A Cikinta, Domin Ubangiji Bai Hukunto Kaddarar
Mutum Rataye Da Gurin Zama Ba,jikinta Sanyaye Ta Ce
Astagfurullah,
yadago Ya Ce Yauma Zansake Zuwa Miki Da Kokon Barar
Alfarma Ina Mai Cike Da Yakinin Jincewa Alkhairinki Da
Tawakkalinki Bazai
Saki Gaza Yimin Ba Gabanta Yafadi Aranta Ta Ce Allah Yasa
Alhji Ba Komawa Gidan Yushau Zaice
Ya Ce Lallai Kinzo Kano Cikin Farinciki Da Wani Abu Na
Koshin Lfya Abubuwa Dayawa Sunfaru Wadanda Allah Ya
Tsarasu Danai Sila Kamar Auren Yushau Wandayake Cikin
Kaddarorinki Marasa Dadi Har Yanzu Ina Nadamar Da
Kasa Yafewa Kaina
Kuma Na Tabbatar Nadamata Bazata Gusheba Idan Ba
Ganinki Nai Cikin Farinciki Ba Amma Yanzu Ruma Saiki
Kinkimi Min Maganar Komawa Gida?
Kiyi Hakuri Kimin Alfarmar Ki Bani Lokaci Mui Addua
Mumika Wa Allah Kokenmu Mujira Hukuncinsa
Nayi Alhji Tafada Cikin Tawakkali Da Rarrauniyar Murya
Hakikatan Bataji Dadin Yadda Yake Dora Wa Kansa Laifi
Ba Acikin Abinda Yushau Kemata Dantana Da Yakinin In
Ana Bada Numfashi Alhji Zai Iya Bata Nasa Saboda
Damuwa Da Kulawa Ta Ce Masa Amma Inason Kai Ziyara
Wannan Ba Bu Laifi Kijekiyi Wata
Daya Ko Biyu Ki Dawo Allah Yaimiki Albarka Amin Kwana
Biyu Tsakani Ta Hada Kaya Ta Nufi Abuja,
******
Yushau Yadawo Kasuwa A Gajiye Karfe Shida Amma Har
Shida Darabi Ba Bu Alamar Sumayya Allah Kana Gani
Cikin Tausayin Kai Goshin Magaruba Ta Shigo Tare Da
Almajirai Uku Ta Ce Ma Almajiran Kai Sharemin Tsakar
Gidan Da
Kicin Kai Gyaramin Falo Ka Goge Tayil,kaikuma Yimin
Wanke Wanke Ka Feremin Doyannan Don Wancen
Hayatun Saiya nemi Dagamin Hankali Akan Abinci,wata
Bakar Zuciya Tataso Masa Amma Haka
Yashare Yai Alwala Yatafi Massallaci Dan Yatuna Lokacin
Ruma Ko Adama Bata Isa Ba Shi Abinci Ya Ci Ba Amma
Gashi Yanzu Ashe Har Girkin Almajirai Yakeci,
Bismillah Ga Abinci Yaduba Soyayyar Doya Ce Mai Fulawa
An Kawata Ta Da Farin Kwai Dajan Tumatir Tai Shar
Kamshi Maidadi Natashia Amma Saiyarufe Yana Toshe
Hanci Lfya Kake Wani Toshe
Hanci Hayyatar Tawa Batakainan Ba Dahar Zanci
Jagwalgwalon Almajirai Nandai Suka Hau Sama
Suka Fado Ita Tana Korafin Yaki Kawo Mata 'yar Aiki
Shikuma Ya Cemata Ke Wannan Dama Zamanki Kikai
Agidanku Kika Mutu Ba Bu Aure Da Gangan Ake Cutar
Mutane Ake Damfarar Musu Kudi Azuwan
Ba Aso Kui Zurfin Ilimi Ashe Rabuwa Da Ja'ib Ake,
tuni Sumoli Ta Barke Da Kuka Ayya Inza Ai Wasa Ayi
Darling Amma Banda Tsikarar Uwar Miji,
yanzu Dan Allah Audine Zaiwa Talle Gori?
Ai Wallahi Garani Iyayena Suna Sona Har Ma Zasu Inganta
Rayuwata Sun Damfara Wa Wani Amma Kaifa?
In Bandani A Duniyar Nan Kafadamin Wake Sonka,?
Kuma Wallahi Sweety Barikaji Ba Fa A Kauye Muke Ba
Dazan Zauna Kadinga Cin Zarafin Iyayena Shi Zaman
Duniya Susar Jakine Yimin In Maka Allah Inka Ci Gaba Da
Zagin Iyayena Zan Rama Don Iyaye Basufi Iyaye Ba,kaima
Danaka Iyayen,kewofintar Dakai Kaso Abinka Bareni Da
Nawa Ke Lelena,
ai Kuwa Zanfara Turamiki Ashar Daga Karamin Alhaki
Sweety Da Darling Dindakike Cemin
Tamike Tana Dariya Har Da Sunkuyawa Har Takai Dakin
Baccinsa Ta Ce To Honey Turamin Ashar Din Mana
Iyayenmu Daya
Haka Dai Rayuwa Tadinga Tfya Kwanaki Suka Dinga
Karewa Har Takai Watara Na Yushau Ya Zarce Gidansu
Wanda Rabonsa Da Zuwa Tun Rasuwar Ahmad Dakuma
Niyyar Gyara Dangantakar Sa Da
Iyayansa Kafin Tunanin Hukuncin Dazai Duka Akan
Sumoli,
Gaisuwar Sa Ma Da Kyar Hajiya Ta
Amsa,yajima Zaune Gabanta Kala Batasake Ce masa Ba
Yatuna Ba Buwani Abinda Zai faranta musu Rai Irin Ruma
Dan haka Yai Niyyar
Yaudarar Su Hajiya Ina Rumaisau Banji Motsinta Ba?
Hajiya Kamar Ta Kifa masa Mari Saboda Haushi Anan
Tahadiye A Takaice Ta Ce masa "Bansaniba".....
Ya dubo dayan gefen yace Dan Aunty ina Ruma?
Hehehe... Jama'a wace irin amsa zan ba Yushau?
.
Dan Aunty.GORAN DUMA (P 46)
.
.
Yai Dif Jiki A Mace Yanufi Kicin Wajen Talatu, Rumaisau
Sunje Unuwane?
Eh Suna Abuja,
da Mamakinsa Kwana Nawa?Watansu Hudu,yakarajin
Rudewa An Tafi masa Da 'ya Batare Da Saninsa Ba,ziyara
Ko Zaman Dindin?Daga Ziyarar Wata Biyu Gata Tana
Neman Haure Wata Hudu Saboda
Kaguwa Da Tambayar Atakaice Take Amsamasa,
Saidai Naji Hajiya Nafadin Kila Cikin Watan Nan Su Dawo
Yai Sallama Ya Bar Gidan Ya Wuce Gidan Maikudi
Abokinsa Yakaimasa Koken Sumoli Yaimasa Nasiha Da
Shawarwari Akan Haka,
hakadai Sumoli Taci Gaba Da Gara Yushau Yarame Ya
Lalace Hartakai Watarana Hatsaniyar Takai Ga Yushau Ya
Zageta Tarama Da Kaima Tir Dakai,kawai Kaita Tsinemin
Mugun Mutum Kawai Tunda Na shiGo Gidanka Nakasa
Gaba Na Kasa Baya Kullum Cikin Zulumin Bala'inka Na Ke
Ashe Duk Zakin Bakinka Damin Ina Waje Na Yaudarane
Aurenka Cike Yake
Da Rashin Kwanciyar Hankali
Kayan More Rayuwa Ba Bu Saita Fashe Da Kuka,
to Fita Fita Nasake Saki Daya Kitafi Gidanku Ta Ce Wallahi
Tallahi Baka Isa Ba,ba Bu Inda Zani Na Rantse Da Allah
To Ki Zauna Watarana Zanyi Ajalinki Don Bazan Jure
Wannan Rashin Tarbiyar Ba
*****
Innar Ruma Ta Kware Dasanin Hanyoyin Hilatar Mutum
Da Tattalinsa Ruma Kam Da Hamida Suna Samun Kulawa,
Duk Azaman Da Ruma Tai A Abujane Karance Karancenta
Yadawo Kuma Daidai Wannan Gabarne Tasami Damar
Zama Marubuciyar Tauraruwa Jaridarta Ta Aminiya Tun
Tana Abuja Bisa Sahalewar Mominta
Alhji Ya Gaji Da Kawaici Yatanka Mata Rumaisau Kin Saba
Alkawari Fa Tai Dariya Cikin Satin Nan Ko Na Sama
Zandawo,
Dazaki Hakuri Kidawo Danafi Kowa Farinciki,
Wallahi Zandawo Alhji Amma Ina Neman Alfarmar Barin
Hamida Wajen Momin Domin Ta Saba Da Ita Harma Tafi
Damuwa Daita Akaina BaBu Laifi Inkin Tsayar Da Ranar
Dawowa Kisanar Dani Nazo Na Daukeki Na Gaisa Da
Hamida Tunda Nan Za A Barota Sukai Sallama
Ranaku Suka Dan Wuce Inda Rayuwar Sumoli Da Yushau
Bata Canza Daga Yadda Take Ba Shidai Baikulata Itakuma
Tanasan Yamaidata Yushau Kam Baidawo Wa Gida Sai
Cikin Dare Itakuma Sumoli Data Lura Da Hakan Safiya
Nayi Yafita Itama Ta Dasa Kwalliyarta Ta Shiga Dakinsa
Tadauki Kudi Ta Shi Ga Gari Adalci Daya Yaimata Bai
Kullemata Sito Ba,kuma Yana Ajiye Kayan Abinci DaiDai
Bukata Sannan Yasan Tana Zarar Masa Kudi Dari Biyar Ko
Dubu Daya, Duk Yashare Danyaga Bata
Daukar Wanda Yafice Kima Sumoli Sunyi Wata Daya A
Haka Tafara Laushi Tare dayin Girki Dashi A Wani
Rana Ta Boyewata Kawarta Da Sukai Rikici Da Mijinta
Yakoreta Gidansu To Tana Tsoron Mahaifanta Kawai Sai
Sumoli Ta Bata Mafaka A Gidan Yushau Baisaniba, Inda
Bayan Mahaifinta Yagano Tana Gidan sukazo Tafiya Da Ita
Da Cewar Zasui Karar Sa Saboda Aje Matar Aure Da Yai A
Gidansa
Kaitsaye Falon Yushau Ya Dosa Tare Da Iyayan Samira Ya
Kwankwansa Kofa Yana Kwada Mata Kira Ta Fito A Firgice
Yadaka Mata Tsawa Ina Yarinyar Danagani A Gidan Nan Ta
Ce Ai Batanan Tunjiya Au Shekaranjiya Tatafi Yasheketa
Da Mari Yashige Falon Ya Tadda Mata Sama Da Goma
Sunata Cashewa
Duka Yakorasu Itakuma duk Aranar Yushau Yakara Ma
Sumoli Saki Daya Takara Daukan Alwashin Bazata Je Koina
Ba Ranar Kam Yushau Bai Runtsa Ba,kuma Yatabbatar
Alhakin
Rumane Yakamashi Ita Yakewa Kallon Masifa Ashe Ita
Rahamane In Aka Jerata Da Sumoli,haka Sukaci
Gaba Inda Sumoli Takara Canza Salon Karkato Da
Hankalin Yushau Gareta Amma Yagagara Haka Yushau
Yakara Komawa Ga Abokinsa Maikudi Wannan Karan
Gurin Mahaifiyar Ta Sukaje Amma Me Bata Wani Daraja
Koken Nasu Ba,tadai Ce Zatai Mata Fada
****
Maman Ta Cemata Dazu Da Safe Sai Ga Mijinki Yakawo
Kararki
Sumoli Ta Ce Ashenan Yayo Aima Haryasakeni Ummanta
Ta Ce Ashe Munafikine Inaganinsa Haka Ta Ce Karkidamu
Suka Zarce Can Wajen Wani Boka Sai daf Da Magariba
Tadawo Tagama Abinci Aka Bade Masa Abinci Da
Magunguna Haka Dai Zaman Nasu Ya Ciga Ba Har
Suka Sake Share wata Uku Batare Da Anji Kansu Ba Sai
Halin Sumoli Yafi Nada Tambaya Zuwa Anguwa Kullum In
Ma Bai Barta Ba Zatatafi ,
Kayan Abinci Taiyanda Taga Dama Dashi Hartakai Sumoli
Tanason Yushau Ya Biyamata Makaranta Tadora Daga
Indata Ta tsaya
To Ashe Dai Tana Jika Tunda Har Sumoli Ta Furta Maganar
Komawa Makaranta Hakan Dai Baisamu Ba Danko A
Mafarki Bazan Lamunta Ba, Na Lura Idan Na Biyemaki
Kwanan Nan Zanyi Mutuwar Tsaye,
Awata rana Sumoli Takaremasa Rashin Mutunci Da Gori
Kan Kayan Abinci Ya Ce Mata Tir Tir Dake Sumoli Kin
Munana Halinki Ni Allah Yayemin Jidalin Aurenki Idan
Dagaskeni Bana Rufamiki Asiri Ki
Sami Mai Rufamiki Idankuma Ni Ni'imane Atare Dake
Allah Na rokeKa Daka Janye Miki Ni Kozaki
Hankaltu,na Tabbata Matukar Inatare Dake Kece Ajalina
Ya Fice Yafada Motar Sa Yatuno Ruma Yadda Yake
Munana Mata Da Dukkan Gabbansa,ya Hantareta,ya
Bautar Da Ita,ko Bata Da Lfya,yaki Kula Da Lfyarta,yaki
Taimaka Mata Alokacin datake neman Taimakonsa,yaha
na Kudin Cefane Koda Bai Aje Kwayar Hatsiba Amma Ko A
Fuskarta Bazata Nuna Fushiba Balle Harshenta Ya
Furta,kuma Bata Kasa Kyautata Masa Ba Bare Ta
Kauracemasa, Unguwa Kamsaita Share Wata Biyu Bata
Leka Kofar Gidanba,kuma Dukda Tana Da Alaka Da Masu
Hannu Da Shuni Bata Taba Ganin Abu Ta Ce
Asaimata Ba Ahaka Take Binsa Saudakafa Har Lokacinda
Gangandinsa Takadamasa Kidan Watsar Da Ita Yazabi
Sumoli Ya Biyemata Yawatsar Daduk Dangi To Yau Ga
Kangin Rayuwar Dayashiga Ya Bata Dakowa Nasa Adalilin
Sumoli Waidamezaiji?
Da Fushin Mahaifinsa?
Ko Da Matsin Rayuwa?
Ko Kuma Masifa Da Balain Ta Na Cikin Gida?
Yaukam Da Tunanin Ruma Yawuni Musamman Dayake
Ganin Akwai Sauran Damarta Nakomawa Tunda Saki
Daya Yaimata Kuma Ba Maganar Aurenta Da Wani Allah
Yadubeshi Tadawo Rayuwar Sa Ko Farinciki Yadawo
Rayuwar Sa Har Yake Ganin Zai Cire Nauyi Da Kunya Da
Tsoro Ya Tunkari Alhji Da Hajiya Har Ita Ruma A Gobe
Yana Iya Yiwa Abuja Tsinkesu Yanke Masa Duk Irin
Hukuncin Dasukeso Indai Zasu Dawo
Masa Da Ruma
Yaje Gidansu Da jin Kumajin Zai Motsa Kwanji Amma Sai
yatarar Da Alhinin anyi Rashi A Rogo Saboda Haka
Yahadiye Abinda Ya kawoshi Da Safe Yanufi Rogo Ashe Da
Rabon Zai Tsinka Dami Akala Wato Tsinto Ruma...
<==KAN DUTSE!==>
Karasowar Yusha'u gare ta da 'karar shigowar sa'kon
murya karo na biyu a wayarta ya katse mata tunanin
JIYANTA wanda ba ta dire ba.
Ta kasa hankalinta biyu, kallon Yusha'u da damuwa da
sakon wayarta. Ta san sa'kon MAHAUKACIN MASOYI ne,
mahaukacin da wani lokaci zuciyarta ke hararo basajar
Yusha'u, amma yanzu yana son 'karfafa shakkar in shi din
ne, don ga shi a tsaye, ga kuma sakon ya shigo.
Yusha'u ya gyara tsayuwa lokacin da ya gaji da cika da
dokin abin da ke ranta game da shi ya zarce wannan
kallon 'kurullar da ta ke masa.
Kamar ta san abin da ransa ya raya masa, ta kawar da kai
a sannu tare da shan kunu, sai ya shiga taitayinsa, amma
da yake kamar bai gaji iya rarrashi da siyen soyayya ba,
iyakar maotsinsa sai ya 6uge da son kyautata murya ya
ce. "Ban san al'adar da ke tilasta miki zuwa kan dutsen
nan ba, kuma duk sanda kika zo sai an biyo
bayanki".
Ko kadan ba ta yi niyyar zata amsa ba, sai kawai ta 6uge
da zuge jakarta ta zura wayarta, sannan ta fara tafiya tana
cewa. "Dan ma ba a dare a gida".
Ya biyo ta cikin daga 'kafa saboda son su jera.
"Kin fada za ki kwana ne?"
Har zata amsa da fatar baki sai kuma ta ga asarar hakan,
ta girgiza kai tare da duba agogo..
.
Chakwakia..
Ga Yushau ga Mahaukacin masoyi ga kuma Dan Aunty?
Ko ya zata kare. Amma dai ni hankaki na akwan ce yake
tunda tace in ba niba sai rijiya, lol.
Sai kuma gobe idan Allah Ya kai mu.
Dan AuntyGORAN DUMA (P 47 )
.
.
Karfe shida saura kadan za su kai wajen isha'i ke nan
kafin su je gida. Ba wannan ya fi yi mata ciwo
ba, sai yadda Yusha'u ya yi damarar dole sai sun tafi tare,
ba dan Hajiya ta yi mata kashedin kwana ba da babu abin
da zai hanata kwana, saboda kawai kar ta jera da shi.
Yana ta fuffurzo mata magana da 'karfin hali da na kwanji
har suka 'karaso gidan Goggo tana cika
tana batsewa suka yi sallama da Goggo mai yi mata
nasihar ta saurari Yusha'u a fakaice. Suna fitowa kofar
gida dan babur din da ta yiwa maganar ya dawo ya kaita
tasha ya karaso.
Cikin dakewa kuma ta doshe shi ya karkata mata mashin
din a gaban Yusha'u ta haye.
Duk yadda ya zo wuya sai ya rasa matakin da zai dauka
wanda ya wuce binsu a mota har tashar. Ta salllami mai
mashin shi kuma ta yi d'amarar share shi, sai da ya matsa
mata da hon sannan kamar dole ta zo ta shiga motar.
Sai da tafiya ta fara nisa sannan ya tsinka shirun
tsakaninsu.
"Na yi miki.....mtsw..... Abu dan gayya, abin da kika yi yau
nayi masa kallon gayya..."
Wannan karon yana sauke numfashi ta amsa.
"Ba gayya ba ce, kamar matsa min ka yi sai mun taho
tare, na yi kokarin in hana zuciyata nuna ba ta
son biyoka ta gaza, wannan shi ne abin da ka dauka
gayya".
"Shi ne kika za6i ki sa6i Allah?"
Ya fada yana nacin kallonta.
Ita ma ta dan yi masa zuru na rashin fahimta, ya mayar
da kallonsa ga titi.
"Kin ba ni haushin da kika yi niyyar ki ba ni na kuma
kar6a cutar da yadda kika so. Wai a gabana ki haye bayan
wani 'kato ya goya ki... 'kazantar ta wuce 'kazanta..."
Ta tare shi ba dan zuciyarta ta fara zafi ba, sai dan kar ta
ba shi sararin da zai ci gaba da nuna mata iko.
"Ka daina fadar wani a gabanka, dazu ma da babu kai shi
ya dauko ni, kawai ka kaddara rayuwa ce ta
'yanci da rashin mafadi...."
Mamaki ya ishe shi, ya juyo yana kallon ita kuma ta maza
ta shiga binciko wayarta a jaka saboda 'karar shigowar
kira, kafin ta gama fito da ita kiran ya katse. Da ta duba
lambar kiran sai ta tarar da 6oyayyar lamba (hidden
number).
Ta shiga juya wayar tana kallo, shi kuma Yusha'u ya sami
sararin magana.
"Ni kike fadawa haka Rumaisa'u?"
Ta yi saurin dagowa ta dube shi ba tare da fuskarta ta
sauya ba. Ta yi saurin dagowa ta dube shi ba tare da
fuskarta ta sauya ba.
"Ban dauki maganata wani cin fuska ba, na fada ne dan
ban ga abin 6oye-6oye ba...
In dai mutum ba ya iya hanzartar da wani akan wani abu
da zuciyarsa wanin ta 'kulla masa, to kai tsaye gara ya yi
abin da ya shiryawa kansa, ya kuma fito da shi
kowa ya gani, Allah basshi duk wanda yake jin an shiga
hakkinsa sai ya fito ya nema".
"Allah Ya ba ki hakuri".
Abin da ya ce mata ke nan, ita ma cikin ko'in kula ta ce.
"Amin".
Ta ciro bututun sauraren magana na kunne (earphone)
daga jakarta tana zurawa a wayarta dan ta ji sakon
muryar Mahaukacin masoyi, wanda ya shigo mata dai-dai
da zuwan Yusha'u kan dutse.
Ammma sai Yusha'un ya katse mata hanzari da tambayar.
"Ina Hamida?"
Ta kuma dagowa ta kalle shi fuskarta babu alamar wasa
ta ce.
"Wace ce haka?"
Cikin bayyana mamaki ya ce. "Hamida nawa kika sani?"
Ta dan d'aure gira ta yi 'kasa da ido.
"Wadda na sani ba mu ta6a lurarta da kai ba, ban san
akwai wata ala'a tsakaninu ba shi yasa na yi mamakin
yadda aka yi ka san da rayuwarta a doron 'kasa".
Ya yi kasa'ke lokacin da zuciyarsa ta fara bugawa,
Rumaisa'u ta sauya matu'ka ba kamar sanin baya
da ya yi mata na rashin kullaci da 'kankantar da laifi ba,
sannan yanzu harshenta ya yi kaifi, zuciyarta ta yi 'kwari
yadda ba ta shakkar fada masa duk wata
magana da ta zo bakinta. Hamida 'yata cikinsa Rumaisa'u
ke keta idonsa ta fada masa wai ba ta san da wata ala'ka a
tsakaninsu ba.
Sai dai dole ya share saboda ya fi kowa sanin dalilin da ya
sa ta fadar hakan.
Dalilin da ba ya son ya tuno bare ya fadi abin da zai sa ita
ta tunatar masa.
Sai ya watsar da wannan maganar ya kamo wata, duk da
a kan Hamidar. "Ya ya jikinta?"
Ta juyo masa da fushi, sai dai ya yi dai-dai da latsa
ma6allin sauraron muryar Mahaukacin Masoyi da ta yi.
--
''Kamar kina cikin fushi yau, na dame ki ko?
In kin dauki abin da nake miki damu kar ki dauke shi
zalunci, ko zuciyarki ta raya miki zaluncin ne ki
tunatar da kanki fadin Manzon Allah (S.A.W). 'Kada ku bi
mutane ku ce in sun kyautata ni ma zan kyautata, in sun
yi zalunci ni ma zan yi zalunci...
ku tsaya da 'kafafunku in suka yi zalunci ku ku kyautata".
Ta yi tsuru idonta akan wayar Yusha'u da ke ajiye lokacin
da sa'kon ke maimaita kansa a kunnuwanta. Hakan kuma
ya yi tasirin sauke fushin da ta 'kunso a radadin da zata
yiwa Yusha'u, 'kari a kan sa'kar da zuciyarta ta yi mata na
ta binciki Yusha'u Mahaukacin Masoyi da sa'konninsa.
A 'kagauce ta amsa masa tambayarsa.
"Da sauki". Zai yi wata maganar ta riga shi cikin sar'kewar
murya.
"Me yasa kake damuna da yawan turo sa'konni?
Duk abin da kake son sanar da ni ai gara ka tunkare ni kai
tsaye ka fada min".
Wato ta yi masa basaja ke nan. Ya tare girar da ke
bayyyana mamaki tare da dafe kirji ya ce.
"Ni?
Ai kuwa kin san rubutu ba dabi'ata ba ce, layi biyu na
rubutu akan na yi shi gara na kashe dari biyar a waya
balle na dame ki da wanda zai gundure ki Rumaisa'u".
Ya kare da tausasa murya yana dan kallonta.
Ta yi saurin kawar da kai tana da na sani.
Ta gamsu da ma'anarsa, mawuyacin abu ne ka ganshi
yana rubutu, kai ko karanta sa'ko ba cika yi ba, in ka yi
masa sa'ko ma ka yi a wofi, koda yake ita kanta ma
basirarta ce ta toshe, sakonnin Mahaukacin Masoyi sun yi
kama da na dan leken asiri ko wani mai gani har hanji.
Ta ci gaba da raba hankulanta uku, kan kallon wayarta
sanan ta daga kai ta dubi Yusha'u tarwai, alhalin kuma
zuciyarta ta kwarzaheta da haske mata fuskoki kala-kala
wadanda ta ke zatawa Mahaukacin Masoyi tare da
zuciyoyi iri-iri wadanda ta ke hasaso niyyarsa da
manufarsa a kanta,
wannan ya yi dalilin da har suka 'karaso Kano ba ta
fahimci sabon kundin da Yusha'u ya bude ya fara karata
mata ba, kundin da yake son nuna shi ne wanda ta ke
'karkashin mulkin mallakarsa shekaru kusan uku da suka
gabata ba, ba shi ne wanda kamar a tsohuwar rayuwarsa
ta ke zaton lokacin da aka raba maganganu masu dadi da
taushn furuci an manta da shi ba.... Ba shine kaza ba
shine kaza ba!
Wannan da suke tafe yanzu kamar Yusha'u ne a fuska da
riga kawai, amma ayyuka wani ne daban...
.
Dan Aunty.GORAN DUMA (P 48)
.
.
Lokacin da ta fara barin kunnuwanta su saurare shi sai
zuciyarta ta cika da dokin ta san makasudin wannan
sauyawar, ga6a kawai ta ke jira ta nemi ba'asi, kuma ta
tabbatar masa ita fa ba a sauyata ba, ba a sauya
Rumasa'u daga kasancewarta sickler ba, kuma ba ta
daina laulaye-laulaye ba, sannan ba a kwashe mata zurfin
karatun da yake ganin shi ne tsanar da ya yi mata ba.
Ga6ar da zata nemi ba'asin ta zo dai-dai lokacin da suke
jiran danja a Gadon Kaya kan titin B.U.K zuwa Ibrahim
Taiwo Road, sai dai abubuwa biyu ne suka faru a dai-dai
lokacin, wato Yusha'u ya nuna mata Yahya Guasau Road
ya ce mata.
"Kin ga hanyar gidan da nake gina miki, na san ba zaki so
zama gida daya da kishiya ba..."
Ta ci gaba da raba hankulanta uku, kan kallon wayarta
sanan ta daga kai ta dubi Yusha'u tarwai, alhalin kuma
zuciyarta ta kwarzabe ta dahaske mata fuskoki kala-kala
wadanda ta kezatawa Mahaukacin Masoyi tare da
zuciyoyi iri-iri wadanda ta ke hasaso niyyarsa da
manufarsa akanta, wannan ya yi dalilin da har suka
'karaso Kano ba ta fahimci sabon kundin da Yusha'u
yabude ya fara karata mata ba, kundin da yake sonnuna
shi ne
wanda ta ke 'karkashin mulkin mallakarsa shekaru kusan
uku da suka gabata ba,ba shi ne wanda
kamar a tsohuwar rayuwarsa take zaton lokacin da aka
raba maganganu masu dadi da taushn furuci an manta
da shi ba.... Bashine kaza ba shine kaza ba!
Wannan da suke tafe yanzu kamar Yusha'u ne afuska da
riga kawai, amma ayyuka wanine daban.Lokacin da ta
fara barin kunnuwanta su saurareshi sai zuciyarta ta cika
da dokin ta
san makasudin wannan sauyawar, ga6a kawai ta kejira ta
nemi ba'asi, kuma

20 / 28