Author : Aysha A Bagudo Category : Complete Novels
ya'yan gatan da zaka gansu da tarbiya da kamun kai idan dai kana sonta na bada goyon baya dari bisa dari Dan gaskiya yarinyar tayi da kace aurena bai Jima ba Dana k'ara ta biyu daita idan kai baka da ra'ayinta ..
"Dan iska to yaya zakayi da minal ?
"Yaya kuwa zanyi daita Karka fa manta nmj nake inda daidai da auren mata hudu "to kuma duk Dubin matan dake garin nan basu yi maka ba sai bakuwar gidanmu ,hisham cikin dariya yace" ita naga ta min kasan nafi son auren yayan Hutu shiyasa nake sha'awar in tara matan Hutu agidana nayi ta hutawa dasu "to kuwa kwalelenka anan ,wannan tafi karfinka "ta yaya kake tunanin tafi karfina? Ince abun ba kokuwa bane ya k'arasa mgnr yana kwashewa da dariya "
alameen yace "ka hakura kawai Dan ba baka zamuyi ba "idan Baku bani ita ba zaku jikata ku sha ne ?
"No no saurayi dai zamu bawa danye sharab Wanda ba'a cirewa yanar kaciya ba domin yarinyar bata dace da auren nmj mai mata ba "
Hisham yayita dariya har da rike ciki "kai nafa San inda zamceka ya dosa Amman kake son yin wani kwana kwana kai kace min hasashena gaskiya ne ...
Wallahi duk wani kauksucenka Nasan kana son yarinyar nan so kuma mai girma ,tun zuwana gidan na nasan za'a rina, a duk ruwan idonka da wuya ace baka sota ba ,ba zanga laifinka ba domin kuwa yarinyar akwai ruwan kyau Amman karka manta kmr a kunnen latifa domin ni zan fara bata labari za'a yi yar gida cikin murmushi alameen yace "sai kabari dai sai na fad'a da bakina sai kaje ka sanar mata dayake mamatace "to meye maraban dambe da fad'a ?
Alamen yace" zage zage sukayi dariya hisham yace "tunda uwar lafita ta rigada tace Tabaka ai tamkar tazama matarka ce fatiha ce kawai da za'a shafa ba .
Alameen yace " kai ni rabani da zanceta ba ita nakeyi ba yanzu " sai ta muwaddat ba ,ai nasan za'a rina tunda kai ba mutumin kirki bane.."ni wallahi tausayi yarinyar take bani itama hjy mantawa tayi da halinka shiyasa ta nanika maka yarinyar ..
Suna ta hira har suka iso gidan suna shiga parlour'n suka iskesu suna hira ,muwaddat kishigid'e Akan kujera kanta ko d'ankwali babu ana iya karewa dogon gashinta kallo Wanda ya sha gyara yagaji ,sai kyalli yake,da alamar hirar tayi mata dadi domin hankhankalinta baya kan komai sai tautaunawar da suke ita da minal Dan haka bata lura da shigowarsu ba sai da hisham yayi magana tana waigowa taga duk ita suke kallo ..
Littafin muwaddat page 17
bismillahi rahmani rahim
Da sauri ta tashi zaune sosai tare da gyara zamanta ,basu daina kallonta ba hakan ya ankarar daita a she fa kanta babu d'ankwali sai lokacin tayi hanzarin d'auka ta d"aura gaskiya irin gyaran da muwaddat takewa gashinta ba namiji ba hatta mace 'yaruwarta zai iya burgeta bare nmj .
Hisham ya d'an juyo ya kalli abokinsa ya lura shima ita yake kallo minal ce ta katsesu ta hanyar yi musu sannu da zuwa sai da kowa ya zauna sannan muwaddat ma tayi musu sannu al'ameen ya amsa idanunsa akanta yace "yau dai kun sha hira ,tun sanda suka shigo muwaddat bata sake yin magana ba saboda tsarguwa datayi da irin kallon da al'ameen ke binta dashi haka minal ta fahimci muwaddat batason yin magana agaban al'ameen da tunda suka shigo ta kasa sakewa hisham ne ma yake d'an janta da magana amman Sam taki saka bakinta acikin surutun da suke .
Al'ameen ya Mike da kanshi ya nufi fridge ya bud'e ya d'auko lemo mai sanyi ya zauna yana sha, sai da ya gama sannan ya sake dubanta "mu tafi ko kar muyi dare ,batayi magana ba sai kawai mikewa datayi ta lalubi Jakarta ta rataya minal ta dubi al'ameen "gaskiya banso dawowarku da wuri ba domin hirar da muke bamu gama ba "to ko zama zanyi ku karasa ?
"Kai ma kasan bakuwa bazata iya sakewa a gabanku ba ,gashi daga shigowarku ta d'auke wuta ko magana bata iya yi ..
Muwaddat dai gaba tayi abunta har gaban mota suka yi musu rakiya minal tayita rokon muwaddat akan ta dinga zuwar mata hira muwaddat tace "bazan iya miki alkwari ba amman idan nasamu lokacin da kuma mai kawoni zan dinga zuwa ...
Hisham ya d'an kalli inda Al'ameen yake yana.dariya domin jin abinda muwaddat tace shi kuwa al'ameen shiru yayi kmr bai ji ba d'an Jan ajinta yasoma bashi haushi ya bud'e mota yashiga ya juyo ya d'n zubawa muwaddat ido domin yaga inda zata shiga amman sai yaga hisham yana k'ok'arin bud'e mata gidan gaba shiru yayi bai yi magana ba sai data shiga ta zauna sukayi sallama dasu minal har ya tadda motar sun fara tafiya sannan yace "na d'auka direban zaki sake meidani irin na d'azu"haba dai ta yaya zan maida kai diteba"eh mana gashi nan da zamu zo kin wani kwanta abaya ina janki tayi shiru ,da yaga bazata yi mishi magana ba sai cewa yayi "halan nayi miki kama da direbanki ne da d'azu ki wani rashi rashi abaya ?
"Ba kayi kama ba, tabashi amsa a agajerce dayake bata fiyye son doguwar magana kamarsa ba ,sukayi shiru gabad'aya can kuma ya sake janta da wata hirar da alamun muryata yake son ji, kallonta yayi tare da cewa "amman fa nayi mamakin yadda kuka dade kuna hira da minal musamman yadda kike ba ma'abociyar son magana ba ,"kasan ita magana zuwa take bawai ayita zuba kmr ruwa ba yace "ko ?
"Tace kwarai kuwa tun daga nan basu sake magana ba har suka iso wani katafarin mail na sai da kayan makulashe yayi parking din motarsa acikin harabar wajen sai daya bud"e ya fito kana ya zagaya ya bud'e mata yace "bismillah fito mu shiga ko, ta d'an yatsina fuska kmr kar ta fito sai kuma taga hakan bai dace ba ko babu komai d'an'uwanta ne yakamata ta nuna kulawarta.
ta fito tana yatsina fuska saboda kai tsaye gida taso taje ta kira bunayya dan tun safe take expecting kiransa amman ko miss call dinsa bata gani ba .
Duk yadda taki son jerawa dashi sai daya saita kafad'unsu suka jera suka nufi kofar shiga mail din suna gota wasu matasa da suke tsaye kusa da kofar shiga mail din ,dayan ya zunguri sauran da suke tare yana yi musu nuni da muwaddat.
"kai kai kai had'uwa ji wata hadaddiyar zalziyya suka kalleta gabad'aya, dayan yace "gaskiya da ba dan wancan gayen da suke tare ba, da sai na d'an latsa ko zan yi sa'ar ta sairareni ,daya daga cikinsu yace "kai tafi can kana ganin yarinya wata muguwar yar hutu amman har kake zaton zata iya sauraronka ..
"Ai ba'a anan take ba ,su irin wad'an nan yammata da suke furgitamu in akayi sa'a sunfi saukin kai in Allah ya doraka akansu ,babu wuya sai kaga kun daidaita "kai dan Allah karya ne ba dai irin wannan kalar ba wannan ko acikin yayan talakawa ta fito bazata saurareka ba bare kana ganinta kaga masu gidan Rana kaga mace na takun kasaita, ko gwal din dake wuyanta ya isa ya sayi motarka .
Suka kyalkyale da dariya yayinda duk maganar nan da sukeyi acikin kunnen al'ameen amman baya zaton muwaddat taji su ,saboda ita tarigashi shiga ciki, da sauri ya k'arasa ya sameta suka jera tare "ki shiga ciki sosai ki duba abinda kike bukata kai kawai ta gyada masa sannan ta fara zagayawa tana bada baya, wasu samari suka shiga dubanta suna magana kasa kasa "kai Anwar dubi yarinyar dake gabanka kaga wata halitta da kyan diri mai d'aukar hankali ,cikin hanzari wanda aka kira da Anwar ya d'aga kai yana duban muwaddat" kai gsky cikar nan ta hadu da yawa Allah yayi halitta a wannan guri ,ina ma ina ma ..saif yace ina ma me ?
"Ina ma yarinta ce gsky Dana more rayuwar duniya ",to ai yanzu baka makara ba kana iya latsawa ,ko zan maka sallama daita ne
ai baasan inda rana zata fadi ba?
" ,lallai kuwa ka kawo shawara dan gaskiya ina sonta ,ya kake ganin zamu bullowa abun .
Jira zamuyi sai tagama tsiyayarta ta kai idan za'a yi mata bill sai kayi sauri ka biya mata,kaga daga nan nasan zata maka godiya kaga mu km mun samu hanyar gaisawa daita ko ba haka ba ?
Al'ameen na jin tautaunawar da samarin keyi akan muwaddat kawai ya tsinci kansa da jin matsanancin kishi akan magana ,cikin hanzari ya matsa gaba kusa daita yace "am har yanzu baki ga abinda kike so ba ne?
"Uhmm ina dai dubawa yace "Jimana ta d'ago da sauri ta dubeshi "idan bazaki damu ba ki koma cikin Mota ki zauna zan zabar miki duk abinda kike so ..
Mamaki ya kama muwaddat domin ita bataga dalilin da zai ce ta koma mota ta zauna ba ,kamar ta tambayeshi sai kuma tayi shiru har ta juya zata tafi sai taji yace kmr dame dame kike so?
Batare data juyo ba tace chocolate kawai nake bukata "da kuma me "shikenan nan suna maganar ne ahankali yadda duk munafurcin mutun bai isa yace yaji abinda suke cewa ba ,musamman yadda al'ameen ya lura da hankalin mutane wurin yana kanta ,duk sanda ya d'ago idanunsa sai yaga maza da suke ciki ita suke kallo hkn ya sake k'ara masa kishi a zuciyarsa ,tana fita daga ciki yaji ya D'an samu natsuwar zuciya .
Ahankali take taka kasa kamar batason takawa Yayinda duk wani matashin dake tsaye agurin hankalinsa da natsuwarsa ke kanta, wasu suyi magana azahirance ,wasu kuma acikin zuciyoyinsu a irin wannan lokacin da tasan da tare take da Auwal da yanzu sunyi fad'a yafi sau babu adadi domin cewa zai yi ita ke kiransu da jikinta ta hanyar rausaya wacce ita Sam batasan tana yi ba ,haka ta taso ta samu kanta da tafiya a natse kamar bata son yi , shi yasa duk lokacin da fita takamasu tare baya yarda ya barta ta fito ,sai dai tajirasa a mota shi yaje ya dawo idan kuwa tayi masa magana sai yace"bazai iya kasada da rayuwarsa ba ,sannan bazai jurar wasu kwaratan banza na kallar masa mata ba ,tana isa harabar gurin wayarta tashiga k'ara ,a natse tasoma k'ok'arin bud'e Jakarta batare da ta kai dubata ba ta ciro wayar tana d'aura idanunta akan screen din wayar ganin sunan dake yawo ajikin screen din wayar ne yasa take gabanta ya fad'i ,gefe daya na cikin zuciyarta sanyi taji acikin ranta jikinta har rawa yake lokacin data d'auki kiran ta manna wayar a kunnenta "hello Auwal dina "babu wani Auwal dinki ,tun jiya rabon muyi magana dake ko araye nake ko mace baki da matsala kawai kin tattara kin shareni kina harkokin gabanki ko"?
Yadda yayi maganar cikin shagwa'ba da tsigar isa yasata ta murmusa "kai my auwa ka fiye rigima , mai ma akayi daka d'auki zafi dayawa ?
"Tun jiya nake tura maka sako babu respond sai yanzu dakayi ra'ayi kirana ..
"Ai bazaki sani ba sai ki min laifi amman idan na nuna fushina ki fini fushi tun daren jiya rabon da muyi waya ban kiraki ba why not ke ki kirani ?
"To kayi hakuri, kadan bani minti goma zan shiga wanka ne idan na fito zan kiraka ta fad'i haka tana istigifarin karyar datayi domin idan ta bari yasan bata gida kuma tana tare da al'ameen mai rabata dashi sai Allah "ban yarda ba, adaidai wannan lokacin nasan abinda kikeyi ba wanka ba ,idan kuma wanka ne ki turo min nonona nagansu nayi kewarsu .....
ya k'arasa fad'ar haka yana buso mata iskar bakinsa ta cikin wayar,take numfashi nta ,ya ne mi d'aukewa ta dafe saitin zuciyarta "Auwal zaka kasheni fa "idan na kasheki nayi rayuwa dawa ?
"Ga matan nan dayawa a duniya sai ka zaba ka durje.
"no no Sam bazasu min ba ,karki manta inda nayi karatu cikin kyawawan matan turawa Wanda yawo tsirara agurinsu bawani Abu bane duk banji daya daga cikinsu Sumin da zan iya rayuwata dasu ba ,ni kece macen Da zuciyata ta yarda ta amincewa rayuwa daita .
Ta k'arasa jikin mota taja ta tsaya tana cigaba da sauraransa gabadaya ta manta da inda take saboda yadda maganarsa ke shiga cikin jikinta da zuciyarta .
Al'ameen kuwa tafiyarta ya bashi damar yi mata tsiyaya sosai sannan ya fito ya sameta jikin motar tana waya ,bai ji komai ba aransa saboda tunaninsa ita da iyayen goyonta ne ,batare da yayi magana ba ya bud'e mato yashiga ya zauna itama ta bud'e ahankali tashiga ta zauna tana jin zai tayar da motar tayi saurin katse kiran gabadaya ,koda ta gama katse wayar batayi magana ba suka wuce .
M.A kuwa yayita k wayar taki d'auka akalla sai da yayi mata missed call biyar bata d'aga ba, sai zuciyarta dake dokawa saboda fargaba tasan tana d'auka wayarsa ta saka kanta cikin matsala,Dan zai fahimci inda take , daidai sun kai wani traffic al'ameen yace "ki d'auka mana ko kiran bashi da mahimmanci ne ?
"Sannan ma waye mai kiran ?
Yayi mata tambayar batare daya juyo ba yana taka motar saboda danja ta tsaya Kan layinsu tace "karka damu da kowaye kacigaba da tukinka kawai "
Bai ji dadin abinda tayi masa ba, dan hk ya sake wani magana ba ya maida hankalinsa kan tukin dayake ita kuma tana kallon gefen titi shi kam jifa jifa ya kan juyo ya kalleta, yanayin yadda take yin magana yana bashi sha'awa ,ta d'an juyo ahankali ta kalleshi suka had'a yayi saurin kawar da idanunsa tamkar ba ita yake kallo ba ,tacigaba da kallonsa yanayin yadda yake tukinsa taji ya burgeta saboda wannan karon Jan motar yake sannu ahankali cikin natsuwa da kwarewa da nuna ganintar tuki kowa yaga yadda yake sarrafa sitiryarin yasan ya kware da tuki ,agaskiya tukin nasa ya burgeta tunda har taji tana sha'awar itama taja mota da kanta dan dai abi ne bayason can al'amen kamar yasan abinda yake zuciyarta ai ya d'an waigo ya dubeta "kin iya mota kuwa?
Ta d'an kada kai "eh to Auwal ya fara koya min amman har yanzu hannuna bai fad'a ba "ya had'e rai dosai jin ta ambaci sunan Auwal ya cigaba "ai ina jin ko kin koyi tuki ina ganin dady'nki bazai barki kija mota ba da kanki ba, "nima ina tunanin haka shiyasa ban maida hankali wajen koyo ba .
"Amman yana da kyau ki iya koda bazaki dinga ja ba, cikin murmushi tace " zan yi kokari naga hannuna ya fad'a suka dan yi shiru ,sai dai muwaddat ta damu da yadda ya takura mata da kallo can ya sake takalota da magana "Amman tunda zaki dade agarin nan me zai hana ki dinga yawan kaiwa minal ziyara kmr yadda ta bukata?
"ba damuwa duk sanda na sami lokaci zan rinka zuwa "idan kin samu lokaci ko idan mai kaiki yasamu lokaci?
Jin ya jefa mata tambaya sai tace "daga ni har mai kai ni din ."amman ai ke kina da lokaci tunda ba karatu kikeyi ba kina cikin Hutu ba kuma aiki kike zuwa ba ..
"Haka ne amman ina karatu saboda wannan zango gabadaya zan rubuta jarabata ta karshe ta bashi amsar tana had'e fuska saboda ta lura hira yake son suyi ,ita kuma bata fiyye son hira dashi ba ,haka suka cigaba da tafiya yana janta da magana tana d'an sharesa har suka iso gidan tana shirin fita daga motar yace "am...aysha.
Ta waigo da sauri "kin mata kayanki ta kai ganinta ga kayan manya ledoji ne guda biyu shake da kayan ciye ciye ta d'an yi murmushi "nagode sosai amman chocolate kawai zan d'auka aciki daman kuma ita nace ina so ..
Yace "shikenan naji amman ki d'aure ki shiga dasu ko su eiman da mamana suna so ,ta d'an yatsina fuska saboda bata son kinkimar kaya tace "bari idan nashiga sai na turo su d'auka ,ta fita ta fara tafiya zata shiga cikin gidan yana zaune a motar har tashige gidan ba abinda yake banda kallon tafiyarta taku take cikin natsuwa irin na matan da suka amsa sunansu mata ,shi kansa yasan tana da mugu kyau kmr yadda mutane suke fad'a kuma ya yarda da had'uwarta da ajinta ,yasan bazata ta'ba d'aukar kayan tashiga dashi ba ,da haka da kansa ya kinkimi kayan ya bita dashi cikin gidan ya tadda kannenta zagaye daita kowa na tambayarta guraren daya kaita ,ita kuma tana cewa su bari sai ta huta ..
Al'ameen nashigowa parlour'n ya ajiye mata kayan gefenta ya tafi abunsa ta bi bayansa da kallo Wanda batasan dalilin hakan ba ,Allah sarki ta furta cikin zuciyarta tana jin rashin dadin abinda tayi masa ,tasan da Auwal ne sai dai abar kayan ,amman ko sama da kasa zasu had'e bazai d'auko mata ba ,ta ina ma girman kai da miskilancinsa zai sa ya biyota dashi "my Muhammed Auwal kenan yaro da izzan , shi Sam baya d'aukar raini ga kowa ga tsabar miskilanci Wanda yake daya daga cikin abinda yasa take naci akan kaunarsa .
Tana son Auwal tamkar yadda take son rayuwarta ,tana son shi tana son su rayyu tare muddin rai Auwal daban yake acikin maza bazata gaji da furta hakan ba....
Tunda take kallon maza bata taba ganin mai irin yanayinsa ba komai yafisu ,ba dan tana son shi ba ,sai dai tasan ummi bazata bari aurensa ba saboda kaninta ne ...
Tasan dakace auwal yayanta ne ,tasan sai inda karfin ummi ya kare amman sai ta mallakamusu juna
Mummy ta fito daga d'akinta tana fara'a "aa yan yawo kun dawo ?
Muwaddat tayi murmushin tace "Eh momy mun dawo "kece yau wata yarinya tasha yawo har ina da ina kukaje?
Mmn sudais ce....
Muwaddat page 18
October 23, 2020 Muwaddat Complete
bismillahirrahmanirrahim
page 18
Muwaddat tayi shiru tare da tsurawa kannenta fararen idanunta tana