Advertisements
Chapter 43 Reading MUWADDAT by Aysha A Bagudo BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MUWADDAT by Aysha A Bagudo

Author :  Aysha A Bagudo Category :  Complete Novels

Chapter   43 / 53

126K to 129K   out of 157.9K words

yayi shiru ya gagara karasa maganarsa yana mai runtse idanunsa ,kusan minti goma suna zaune a haka sannan ya cigaba da maganarsa a tsanake "abinda zan fad'a maka Aminu ka bar zance muwaddat saboda ina da dogon buri akanta ban tashi aurar daita yanzu ba ,amman ga faiza nan na baka aurenta ,ko yanzu ka tashi aure ka sanar min ,nayi maka alkwarin zan ajiye karatunta na aura maka ita...

Shiru ne ya ziyarci parlour'n ,yayinda gumi yashiga tsatsafowa ala'meen ta koina ajikinsa , gabad'aya jinsa ne ya nemi d'aukewa ..
Ya yunkura tamkr wani zararre yasoma k'ok'arin barin parlour cikin tashin hankali dady ya bi bayansa da kallo ,tunda yake bai furta abinda taji ya damesa ba sai yau..

kai tsaye al'ameen bangarensa ya nufa kmr wani mahaukacin sabon kamu , yana shiga yashiga Kira ummi byn ta d'auka ya zayyano mata yadda sukayi da dady ,ummi tace " Banda abunka ala'meen meye nayi wannan zance da dady ?
"Yaya ne zai aurar da muwaddat ko mu ?
Kawai idan ka tashi ka turo magabatanka nan gurinmu ,na tashi aurar da diyata ....
da wannan furucin yasamu karfin gwiwar ajikinsa dan haka batare da Bata lokaci ba ya turo iyayensa zuwa ga abi domin nema masa auren muwaddat me zai yi da wata faiza shi zuciyarsa muwaddat tagani take so ba faiza ba , kafin iyayen ala'meen suzo ,ummi bak'ara min fama ta Sha da abi ba kafin ya yarda yace" suzo"

Dady bashi da masaniya ala'meen yayi gaban kasa ya turo iyayensa ,bayan sun gaisa cikin fara'a da mutuntaka abi yayi shiru ya zubawa sarautar Allah ido ,Banda murna da farincikinki babu abinda iyayen ala'meen suke, amman Banda abi da yake jin kmr an d'aura Masa dutse ne bisa kirjinsa , duk safiyar ranar haka ya dinga ji fad'awar gaba ..
An kawo baki abinci iri iri da abun Sha ,da kayan marmari iri daban daban daga ummi ,byn sun gama cin abinci suka soma magana akan abinda ya kawosu, Basu tafi ba sai da aka saida magana mai karfi tsakani, inda iyayen ala'meen suka ce Nan da wata goma cif suke son ayi biki ......

MUWADDAT PAGE 35


Shi dai abi duk abinda iyayen al'ameen suke tautaunawa akai na batun aure, kasa cewa komai yayi ,illa zuciyarsa dake wani irin harbawa da sauri , babu abinda yake tunani da fargaban a halin da yake ciki facce halin da tilon d'ansa zai shiga ,yasani bunayya zai shiga matsanancin tashin hankali idan ya riski wannan labarin ,koma ya nemi zaucewa saboda shi kansa ya lura da irin mahaukaci kaunar da yake wa muwaddat
,itama Kuma muwaddat din ya lura tana mugu mugun sonshi .

gabad'aya acikin lamarin sai yaga duk kuskurensa ne ,da tun lokacin da bunayya ya nuna masa yana bukatar ya aura masa muwaddat, yayi wani Abu akai da yanzu da muwaddat din zai koma karatu a matsayin matarsa ...
"to yanzu shi mai zai iya cewa Kuma ?
"Ya zabi son zuciyar matarsa ya hana d'ansa abinda yake kwakwar so, to idan wani Abu ya faru dashi a sadin haka wa gari ya waya ?

"Kanka ka cutar zuciyarsa ta bashi amsa da hakan ..
"Tabbass haka ne zan cuci kaina da d'ana, idan na rasashi wa zai zame min gurbinsa a wannan duniya?
Ya sake jefawa zuciyarsa wata tambayar yana duban iyayen al'ameen d'aya byn daya .
"Muwaddat ba diyar cikina bace amman ina jinta tmkr ni ne na kawota duniya ,sai duk da haka, ai gurbin ido ba Ido bane, idan na rasa d'ana, rayuwarta zata cigaba yi agidan mijinta , domin kiyayyar mace na wani d'an lokaci ne, baya tabbata muddin rai ,gara tun wuri nasan abun yi akan lamarin tun kafin abubuwa sugama rinca'be min .

sanyayyiyar ajiyar zuciya ya sauke da karfin gaske lokacin da yaji iyayen al'ameen suna sake furta wata goma cif suke son a saka ranar auren ,shi kuwa inshallahu kafin lokacin zai tabbatarwa kansa muwaddat ta zamo mallakin bunayya ne da yarda Allah ,ba mallakin ala'meen ba , koda kuwa hakan zai zamo sanadiyar 'batawarsa da ummi zai gwamaci haka amman tabbas zai bawa d'ansa farinciki .......
haka dai taron ya watse batare da abi ya wani saki jikinsa ba, baki na barin gidan ya d'auki wayarsa ya Kira alhaji Muhammad ya zayyane masa komai daya faru , cike da matsanancin mamaki dady ya dinga saurararsa har sanda ya dasa aya kana ya furzar da wani numfashi mai zai fi a ransa yace "kenan ala'meen haka zai yi masa ?
"da fari ya saka shi ya zamo k'aramin mutun a gurin iyayen litafa ,yanzu Kuma yana shirin rukujewa masa burinsa akan muwaddat ,amman babu komai zai saka masa ido yaga iya gudun ruwansa.......

********
A ranar da aka sa ranar auren muwaddat, haka nan bunayya ya yini da zazzabi mai tsanani, zuciyarsa ta dinga tsinkewa tana harbawa ,duk motsin da yayi sai gabansa ya fad'i, gabad'aya zuciyarsa tayi masa nauyi da kunci, zafi kashi da kashi yake ji acikin zuciyarsa..
Gashi daman tun daya shigo kasar cikin damuwa yake hakan ya rasa sukuni , ramar da yayi tayi yawa sosai har ta fito fili, haka fuskarsa ta bayyana dukkan damuwar dake zuciyarsa .

suna zaune a gurin shakatawa shi da abokansa, gabad'ayansu suna tsananin tausayin halin da suke ganinsa ciki , suka zabga tagumi kowane daga cikinsu ya kasa magana.

Nabeel ne yayi karfin halin magana yace" m.a ya dace ka cire wannan damuwar aranka tunda kazo kasar nan baka bar zuciyarka ta huta ba,kullun cikin tunani kake,ka shafe damuwar dake cikin zuciyarka, domin suna nuni ne da yadda ka yiwa rayuwarka kyakkyawar fahimta.


saboda a yanayi na matsayinka da wayewarka da gantanka da isarka, da wahala ace kana irin wannan tunani. domin su wad'an nan abubuwa guda uku daka mallaka kyau kudi ilimi suna sa mutun yayi kowani irin girman kai suke sa mutun,mutun ya dinga jin kansa ishashen da babu wanda ya isa sai shi,shi ke sa mutun ya dinga jin babu abinda ya isa yazo ya dameshi saboda isarsa da takama ..

saboda haka ina mai jan hankalinka tunanin da kakeyi a wannan lokacin yayi yawa , ka bar zuciyarka ta hutu ka yarda da kowani rin kaddara samu ko rashi..
M. A yayi tsit kansa na kasa ,ya kasa cewa komai har sai da Nabeel yayi shiru sannan ya d'ago kai ya numfasa.

Nabeel gabad'aya naji zantuttuka ,kuma zanyi amfani dashi, ina son ku ta yani da addua duk kwanaki nan bana jin dadin zuciyata da gangar jikina, ji nake tamkar ana zarar raina, jikina na bani akwai abinda yake faruwa gida,ko Kuma yake Shirin faruwa da rayuwata , nayi waya gida kowa na lafiya ban sani ba ko boye min suke ..
"to kayi addu'a mana shine mafuta inji cewar nabeel, "Inshaallahu duk zamu tayaka da addua amman ka saki ranka plz..

***********
tun daga lokacin da aka tsaida magana mai karfi tsakanin al'ameen da muwaddat shikenan al'ameen ya maida lagos tamkar ilori da ogbomosho duk weekend din duniya a lagos take yi masa, ta bangaren muwaddat babu yabo babu fallasa ta kan d'an sakar masa fuska ,shi kansa al'ameen idan akace masa muwaddat bata sonshi a halin yanzu zaice karya ne , saboda irin kulawar da take bashi idan tazo.....

wasa wasa bunaya ya kasa samun natsuwar zuciya duk da suna waya da chatting da muwaddat kmr yadda suka saba amman duk sanda ya runtsa idanunsa sai ya kasa bacci, gashi dai kowa ta bangarensa lafiya lau yake, dan babu wanda basa waya dashi har muwaddat bai ga wata al'amun akwai wani damuwa attare daita ba yafi tunanin dai damuwar iya kansa kawai ta tsaya kullun damuwarsa na sake karuwa ya rasa mai ke damunsa da rayuwarsa gabad'aya .

Haka nan ta bangaren faiza taki barinsa ya huta, kullun zata kirasahi a kalla sau goma , sai dai duk nacinta haka zata gaji ta hakura dan daidai rana d'aya bunayya bai yi tunanin d'aukar kiranta ba, dan bai San me take nufi dashi ba ,bayan ya fito ya bayyana mata abinda ke cikin ranshi .
Ta bangaren faiza kuwa babu abinda ke dawainiya daita sai zallar shaukinsa da farincikinki burinta ya kusan cika tunda Yaya al'ameen zai zamo miji ga muwaddat tasan tabbas bunayya zai zamo mallakinta ,ta d'auki tamarar zatayi komai idan dai zai zamo miji gareta ...

Haka nan yau cikin bacci ya mike a matukar zumbure yana mai dafe daidai saitin zuciyarsa dake bugawa da karfi, nan fa gumi ya rufeshi ta koina ajikinsa, ahankali "yashiga furta kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun.. .

cikin haka kiran faiza yashigo wayarsa yana dubawa yaga itace Yaja dogon tsarki tare da furta another matsala kawai......
ya ajiye wayar yana gyara kwanciyarsa ,ita kuwa jin tayi kira ya kai sau goma sha bai da niyyar d'auka kamar koda yaushe yasa taji ranta ya 'baci , ta dinga jin tamkar ana diga mata dalma ne akan zuciyarta ,take zuciyarta ta harzuka tasoma tunanin abinda zata masa wanda tasan babu makawa zai nemita domin Karin bayani .

Shiru yayi kawai yana tunanin matakin da zai d'auka akanta yaji shigowar sako da kmr bazai duba ba sai dai yayi tunanin ko muwaddat ce,dan haka ya lalu'bo wayarsa sakon da idanunsa suka ci karo dashi ne yasa shi tashi zaune da sauri yana sake dafe daidai saitin zuciyarsa dake harbawa har wannan lokacin , da karfi ya furta "what..?
"When ?

Kana ya tsurawa sako ido yana sake karantawa yana sake maimaita kalmar Inna lillahi wa Inna lillahi raji'un ga abinda sakon ya kunsa"

_slm a lokacin danake rubuto maka wannan sakon ina cikin matsananci farinciki da annashuwa ,ina maka albishir da kaima zaka rasa cikar burinka daka girma dashi, yadda bazan sameka ba, haka kaima ba zaka samu damar cika burinka, domin kuwa yau kimanin wata daya kenan da aka saka ranar auren aunty muwaddat da yaya al'ameen har ma da sadaki atsakani, wannan abu yayi min dadi ni faiza za'ayi to zero_

cikin wani irin tashi hankali ya zabura ya mike yana sakin qara tare da cewa "ba dai muwaddat dina ba, muwaddat tawa ce ni kad'ai ,duk runtse duk wuya babu wanda ya isa ya aureta sai ni...
nan take jikinsa ya shiga rawa ,yasoma k'ok'arin kiran faiza tana kallo wayar na ruri ta saki wani shu"umin murmushi "ai nasan zaka kirani ,ni kuwa bazan d'auki kiranka ba ,kai ma kaji abinda mutane sukeji ,tana kallo wayar na cigaba da k'ara amman taki d'auka daga karshe ma ta kashe wayar gabad'aya tana dariyar mugunta .

Gajiyayi yasoma neman layin muwaddat domin jin gskyr lamari amman shiru bata d'auka ba, gashi dai wayar tana ringing , hankalinsa yayi mugu mugun tashi yasoma ganin double, ya dafe goshinsa da hannuwansa duka yashiga bin bagon d'akin ,can ya saki k'ara mai sauti sai ga abokansa guda biyu sun shigo d'akin a matukar razane sukayo kansa suna tambayarsa "lafiya M. A me yasameka?

yayi shiru kawai yana dubansu d'aya bayan daya tmkr wani zautacce,ya dungule hannunsa d'aya ya naushi iska Yana furta " imposble .....wani ya aure muwaddat bani ba, ya wucesu cikin sauri ya k'arasa gaban wardrobe dinsa ya bud'e saboda ya rasa me ya kamata ya fara yi ,akwatin kayansa ya janyo yashiga zuba kaya yana kiran waya "

sai lokaci suka fahimci abinda yasa ya fita haiyacinsa , suka matso kusa dashi suna tambayarsa "yanzu ina zaka haka da kake k'ok'arin had'a kaya?

"Nigeria ya basu amsa atakaice ....."plz M. A.. ..
"don't dont say anything to me dan ba fahimtarku zanyi ba, sai sai.. .. yayi shiru tare da cilla da wayar bai gama jin mai ake fad'a masa acikin wayar ba .......

"haba M. A kayi hakuri mana kasanyawa zuciyarka natsuwa ,karka tafi cikin wannan tashin hankali ,Dan girman Allah ka bari zuwa ..."NO bazan bari ba sadik yayi maganar yana d'aga murya ,Ni zata yiwa wannan wulakacin saboda taga ina sonta ?

"wallahi sai na bar kasar nan, kuma a yau idan ba haka ba zan haukacemuku ,zan na tashi hankali kowa yau a gidan dan haka kusan yadda zan bar kasar nan .....
sai sai na ....ya kasa k'arasawa ya dunkule hannunsa ya bangon d'akin yana furzar da numfashi mai zafi ..
Sadik ya rungume shi ajikinsa "plz m.a kayi hakuri zamu San yadda za'ayi ka bar kasar but at least kasanyawa zuciyarka natsuwa.. numfashi kawai yake ja Yana saukewa tamkar mai cutar asma yana girgiza kai ..shi kawai yasan halin tashin hankali dayake ciki .

nabeel najin yadda sadik ke fama dashi gurin bashi hakuri amman yaki ,yasa ya d'auki wayarsa dake yashe da har lokacin ba'a katse Kiran ba ,cigabasa wayar ,inda yake tambayar "ko akwai jirgi mai zuwa nigeria ayau din ?
daga can bangaren aka bashi amsa da akwai amman sai gobe karfe shida zai tashi na safe. "okay ka mana booking ya fad'a atakaice cikin tashi hankali ,sannan ya dawo ga bunayya ya tsura masa Ido Yana kallonsa ,duk ya wani firgice , gabad'aya ya rasa wani irin so bunayya yake wa muwaddat ,tun haduwarsu yasan da zaman muwaddat ,itace macen data hana mata dayawa samun gurbi acikin zuciyarsa ,duk macen daza tace tana son shi sai ya kusheta yace "muwaddat dinsa tafita kaza , ranar dai babu wanda ya runtsa acikinsu , Allah Allah suka dinga yi gari ya waye ya bar kasar..

Washegari tun asubar fari ya bar kasar london zuwa Nigeria ..

mmn sudais


MUWADDAT



~NA~

*AYSHA A BAGUDO*

~DEDICATED TO~
_AUNTY SALAMATU AYYUBA_
_(UMMIN KADUNA )_


warning!!!

don't read this novel if you know you are not married... ❌❌❌coz this book contains only for mature people , if you read it, is for your own risk ......


WATTPAD @HAUESH

bismillahirrahmanirrahim

page 37


...tun da muwaddat taji sautin muryarsa yana furta kalmar "abi ummi ku daina wahalar da kanku ciki na ne.. ... zuciyarta ta tsaya cak ta daina aiki na wunci gadi....
kafin daga baya zuciyarta ta soma bugawa da karfin gaske,maganarsa ba'a iya kunnenta kad'ai suka samu nasarar tsayawa ba har ma da gangar jikinta da koina take jin saukar furucinsa tamkar saukar aradu ....



yi tayi kmr ta kwasa da gudu ta bar parlour'n domin tsira daga wannan taskon tashin hankalin data tsinci kanta mai tattare da abun kunya , amman babu halin aikata hakan sakamakon gabobi Jikinta da take jin tamkar ba'a gangar Jikinta suke ba , ahankali jikinta ya sake d'aukar rawa kamar mazari, hawayen idanunta suka tsananta gangarowa bisa kuncinta , da kyar ta juyo inda ummi da abi wad'an da sukayi mutuwar zaune agurin suka dawo tamkar matattu suna duban bunayya ,mamaki ne ko kuwa dimuwa ce tasa me su alokacin, ita dai bata sani ba, dan tashin hankalin da take ciki ya ninka nasu.....

Cikin tsananin matsanancin tashin ahankali bakinta ya cigaba da maimaita kalmar inna lillahi wa inna ilaihi rajiun jikinta na wani irin kyarma .

wannan kalmar da muwaddat ke maimaitawa a fili itace ta dawo da ummi da abi cikin hankalinsu suka shiga kallon ita kanta muwaddat din, kallo kuma irin na tsantsar mamaki da al'ajabi da tashin hankalin.
"da gaske ne abinda kunnuwansu suka ji ya fito daga bakin tilo d'ansu ko kuwa karya ne ?

ummi ta tsaida kallonta akan bunayya sosai tana son ya karyata mata abinda taji ya fito daga cikin bakinsa cewar karyar ne ba gaskiya bane....
amman sai taga yayi shiru yaki cewa komai illa wayarsa daya rike gam kmr za'a kwace daga hannunsa , yayinda a bad'ini kuwa ba za iya misalta kalar tashin hankali da shi kansa yake ciki ba...


da kyar ummi ta had'iye abinda taji ya tsaya mata a makoshi ta kira sunansa cikin wata irin murya wacce bai ta'ba sanin umminsa dashi ba "bunayya ......
cikin jikin muwaddat kai kayi shi ko kuwa kunnawanmu ne suka jiyo mana sa'banin haka?

A sukwane ya d'ago kansa ahankali zuciyarsa na wani irin bugawa da karfin gaske ya tsurawa umminsa da hawaye suka gagara tsayawa akwarnin idanunta ido yana kallonta , kafin daga baya ya d'an lumshe tsumammun idanunsa ya bud'esu fesss akanta ya janyo numfashi da kyar ya fitar hankali, sannan yace "eh ummi cikina ne kuma ina son abuna plz ku bar min shi......
" inna lillahi wa inna ilaihi rajiun shi yayi nasarar katsewa bunayya hanzarinsa.

"cikinka ne kuma kana son abunka ,abar maka shi bunayya?
Ummi ta furta haka tana kuka ,ya d'aga mata kai ala'mun eh, ai ko ta sake rushewa da wani sabon kuka.....

kuka ummi take sosai tamkar ranta zai fita tana dafe da kirjinta da take jin tamkar zuciyarta zatayo waje.

"wace irin bakar rana ce yau gareni ?

"Meke Shirin faruwa da rayuwata data ahlina ?

"Ya Allah kasa zantuttukan bunayya su kasance cikin mafarki nake jiyo su ?


"Allah Allah kasa karya ne ,karka nuna wannan bakar ranar acikin rayuwata "me zancewa duniya ........ ?
"Me duniya zata fad'a akaina ?
"Idan wannan abu ya kasance gaskiya ya ..ya ..ta kasa k'arasa zancen zucin da take sai ta kama haki tana fidda numfashi sama sama ......

shi kuwa abi gabad'aya kasa magana yayi yana cigaba da kallon bunayya cike da matsanancin mamakin karfin hali irin nasa "wato dai sune suke masa kallon yaro k'arami wanda bai isa aure ba,a she shi

43 / 53