Advertisements
Chapter 12 Reading Kanwar Matatah Book 1 Complete Hausa Novel BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Kanwar Matatah Book 1 Complete Hausa Novel

Author :  Takori Category :  Romantic Hausa Novels

Chapter   12 / 60

33K to 36K   out of 178.7K words

ciccibi zuma gumba garin daka tsumi turaran tsuguno miski da duk nau'in abubuwan da suke kankaro da martabar duk wata 'Ya mace! GARKUWAR MATA =?m?=?m? fatan mu shine mu bada gudumuwa domin samun zaman lafiya a zamantakewa, Muna garin Kano amma muna tura kayanmu kowane gari cikin farashi mai sauki da rahusa! kuma muna bada sari cikin girma da mutunci*
*GA*
*Kadan daga cikin abubuwan da muke sayarwa*
Rage tumbi=???
Nono=???
Sanyi=???
Karin kiba=???
girmar hips=???
Ni'ima=???
Sabulai=???
Humra=???
Turarukan wuta=???
Matsi=???
Miski=???
Dilka=???
Gangariyar Supplement din da zai mayar dake tauraruwar mace fatarki ta yi luwai kamar kina rayuwa a turai=?? ke dai 'Yar kada ki yi kasa guiwa cikin saukin farashi kalilan za ki kankaro da martabarki
GARKUWAR MATA=?m? Tana maraba da masu siyan daya da kuma masu bukatar sari
DOMIN NEMAN K'ARIN BAYANI
*08089965176*
*07084653262*


*_K'ANWAR MATATA ISN'T FREE, PAY #500 VIA THIS ACCOUNT NUMBER 0592412800 ZULFAU SAID GTBANK AND SEND YOUR EVIDENCE OF PAYMENT THROUGH THIS NUMBER 08128755583_*
[30/09, 7:11 PM] Rahamanatu: Sai da ya isa k'ofar gidan sannan ya d'auko wayarsa dake gefensa ya lalubo number Sarah da yayi saving da *_My endless bliss_* yayi dialing, ringing uku ya amsa kiran tare da fad'in, "Hello, Assalamu alaikum." Tab'e baki yayi kamar tana kallonsa tare da amsawa da, "Hi, wa'alaikissalam." Da sauri Sarah ta cire wayar daga kunne tana k'arewa special number d'insa kallo wanda ya k'are da 3 guda shidda a k'arshe. Turo baki tayi don sarai ta gane muryansa, gashi kuma tana tsoran yanke kiran don bata manta da deal d'in su na d'azu ba. "Wake magana!" "Bugun zuciyarki!" Kai tsaye ya bata amsa yana mai sakin murmushi. Sarah kuwa yana fad'in hakan zuciyar nata ta soma bugawa. Shuru tayi bata k'ara cewa komai ba. Sun d'au lokaci har na tsawon mintuna biyar babu wanda ya sake yin magana. _Khalil_ ya ciro wayar daga kunne, kamar yanda itama Sarah ta fiddo nata domin ganin is he still their. Sai taga yana reading kamar yanda shima ya gani daga can, mayar da wayar yayi kan kunnansa tare da fad'in, "Tun ba'a je ko ina ba, har kin fara karya dokar ko?" K'ara turo baki Sarah tayi daga can tare da fad'in, "To ni ai kai ne baka yi magana ba, kuma ni ban san mai zan ce ba." Gyara zama yayi cikin motar tare da fad'in, "Ki fito ina waje." Waro idanu Sarah tayi tare da fad'in, "Waje kuma? Ni dai......." Sai kuma tayi shuru bata k'arisa ba. "K'arisa maganarki mana, ke dai baza ki fito ba ko?" Kwanciya tayi rigingine tare da fad'in, "Ni dai Allahna yana sama yana kallo ba haka nayi niyyar cewa ba." D'age gira yayi kamar tana kallonsa tare da fad'in, "Au Allah d'in naki ne ke d'aya mai son kai. To idan ba tsoro ba ki fad'i abunda kika yi niyyar fad'i daga farko mana." Sai da ta juya idanuta sannan tace, "Ni dai so nake in ce maka, ni dai gaskiya.... Gaskiya, ummm-ummm...." Dariya ya saki tare da fad'in, "Kin ga k'aryar ma ta kasa fitowa. To bari na juya kawai kin ga kenan deal d'in mu ya rushe." Waro idanu Sarah tayi tare da mik'ewa da sauri tana fad'in, "Wallahi a'a, wallahi ni dai a'a ba haka nake nufi ba. Gani nan zuwa yanzu." Sosai ya saki dariyarsa tare da fad'in, "Matsoraciya, ana so ana kaiwa kasuwa." "To mai ake so d'in." Ta tambaya tana hararar wayar. " _Khalilullah_ mana." "Khalilo." Ta fad'i cikin zuciya har da Allah ya kiyaye. Bata san cewar a zahiri tayi maganar ba sai da taji yace, "Ni ne _Khalilo_ d'in?" "Na shiga uku na!" Ta fad'i jin ashe a bayyane tayi maganar. "Ki fito maman twins kar ki b'ata min lokacina." "Mene? Ni wallahi ba maman Twins bane. D'aya kawai zan haifa maka. Shima don babu yarda zanyi ne. Ai don dai zubar da ciki haramun ne, kuma tamkar kisan kai mutun yayi, da zubarwa zanyi wallahi." Fad'in Sarah. "Don Allah ki gwada! Da na baki tsan-tsan mamaki don kin san Allah sai na kuma yi maki real ciki kin haihu." Kuka Sarah ta saka tare da fad'in, "Kuma ba zan fito d'in ba. Mugu kawai!" "Dan Allah ban rok'eki ba, kar ki fito d'in cikin mintuna biyu rak." Yana gama fad'in haka ya katse wayar. "Kai Inna lillahi wa'inna ilaihir raju'un! Wannan wani irin jaraba ce haka? Ga duka ga tsinke jaka." Fad'in Sarah tare da share guntun hawayen da suka zubo mata ta nufi wardrobe ta d'auki Vail madaidaici ta yafa a kan riga da skirt d'in jikinta wanda ya amshi k'irar jikinta cif-cif. Babu ko hoda a fuska sai wani d'aure fuska take yi tare da fita waje ba tare da ta kalli y'an uwanta dake tsakar gidan ba. Babu mai shigar arziki a cikinsu. Marfu'a ma shayar da y'arta Fadwa take yi y'ar shekara d'aya da wata biyu. Ko kasheta za ayi baza ta iya nuna uban y'ar ba saboda yawan samarinta. Ga y'ar fara tas kyakkyawa kamar mahaifiyarta. Don duka Y'ay'an Lami kyawawa ne, duk da Lamin ita ma ba laifi tana da kyau, Sai dai ita bak'a ce, hasken Baba suka yo da kamannin fuskansa shiyasa gaba d'aya suke kama da juna sai dai wancen tafi wancen dogon hanci, ko kuma k'irar jiki. Wata kuma dimple gareta, wata kuma wushirya. Masu dimple d'in sune, Sarah, Na'ima da Hassana, masu wushirya kuma, Aina'u, Nuratu da Marfu'a, Lukman ne kawai ya d'auko Lami kaf, kamanni da hasken fata. Sai Aina'u da itama ba fara bace sosai kamar sauran y'an uwanta. Kuma ita tana da d'an jiki irin na mahaifiyarsu. Da kallo suka bi Sarah dukkan su, kuma babu wanda ya tambayeta ina zata je. Tura k'ofar gida tayi tare da fita ta coge a k'ofar gidan tana k'arewa motar da yake ciki kallo ta gefen ido tana mamaki shi motoci har nawa gare shi haka. Shima kuwa ta cikin tinted glass window d'in yake k'are ma halittar jikinta kallo yana mai jin wani irin matsanaicin kishi na taso mata. Domin gyalen dai bai da maraba da babu don babu abunda ya b'oye a jikinta. Ga shape d'inta da ya fito kamar zanata aka yi. Hannu ya kai ya d'auki glasses d'insa ya mak'ala a idanunsa tare da bud'e motar ya fito, luckily sai ga wasu almajirai su biyar zasu wuce, da hannu ya yafito tare da bud'e boat ya nuna masu abunda zasu kwashe su kai gidansu Sarah. Sarah na ganin uban kayan da ake fitowa dasu a cikin boat, back seat da kuma front seat ta bud'e ido tana mamaki don kamar za'a bud'e shago. Sai da aka gama kwashe kayan tsaf ya sallamesu sannan ya nufi wajenta don tuni ta bawa almajiran nan waje ta koma gefe. Fuskan nan b'utu-b'utu ya kalleta tare da zare glasses d'in fuskansa. Lokacin da Sarah ta d'ago ta saka idanunta cikin nasa, sai da gabanta ya fad'i ganin yanda launin idanunsa suka canza, duk lokacin da ta kalli idanunsa a wannan yanayin, tuno mata da ranar da aka samu cikin jikinta yake yi. "Ke har yanzu baki yi hankali ba ko Sarah!" Duk lokacin da ya furta sunanta, sai taji duk duniya babu wanda ya iya kira kamarsa. "To ni kuma mai nayi yanzu?" Ta fad'i tana mai turo baki. Ko kamun yayi wata magana, Lami ta turo k'ofar gidan tare da fad'in, "Sannu-sannu! Sannu da k'ok'ari yaron arziki! Wannan irin uban kaya haka? Kai an gode sosai. Ai irin ku ake so masu hannu a bud'e. Allah yayi maka albarka." Fad'in Lami tana washe baki. Sarah kuwa ji tayi kamar ta kwalla ihu tsabar takaici. Don Lami ta riga ta gama zubar mata da mutunci. Shi kuwa _Khalilullah_ ko kallonta bai yi, sai cewa kawai yayi, "Ameen." Yana kallon fuskan Sarah da ta gama b'ata masa rai. Juyawa Lami tayi ta koma ciki. Sarah kuwa sunkuyar da kai tayi tana jin hawaye na taruwa a idanunta. "Kar ki yarda wannan hawayen su zubo _Mine_, kar ki yarda su zubo don idan suka zubo nayi maki alk'awari sai na lashe su tsaf kuma a titin nan." Da kyar Sarah ta iya maida hawayenta suka koma, don ta san tabbas duk abunda _Khalil_ ya fad'a zai iya yin fiye da haka tun da dai yanzu haka cikinsa ne a jikinta. "Dan Allah kayi hak'uri da halin mahaifiyata." Mai makon yayi sharhi akan maganar da tayi, sai cewa yayi, "Sarah idan kina son zaman lafiya dani, kuma kina gudun abunda zai je ya dawo, to kar in kuma ganinki da irin d'an iskan gyalen nan. Wai ke baki san ba irinku bane suke saka gyale ba? Wallahi yawancin mata ku kuke ja ana yi maku fyad'e. Kin san cewa Allah yayi ku ma Sha Allah ta yanda ba kowani namiji zai iya had'iye miyansa akan ku ba, amma sai ku rik'a fitar da surar jikinku. Wasun ku ma har k'ari suke yi don kawai su burge samarin. To ni wallahi ban so, kuma ban so na sake ganin irin haka. Ki kiyaye ni _Mine_. "Wai wani _Mine_ sabida kinibibi. Ko ta ina na zama na shi oho!" Fad'in Sarah amma a zahiri sai cewa tayi, "Zan kiyaye daga yau in Sha Allah!" Politely ta fad'i maganar. Shi kuma _Khalil_ yace, "That's very good. Allah ya baki iko. Yanzu menene kike buk'ata?" "Turaren jikinka." Ta fad'i a cikin zuciya saboda yanda k'amshin yake fizgarta, don na yau ma yafi mata dad'i akan wanda ya saba sakawa. Amma a zahiri sai cewa tayi, "Babu komai. Ni babu abunda nake buk'ata. Abunda ka kawo yau ma yayi yawa." Harararta yayi tare da fad'in, "To ke na kawo mawa? Ni su Baba da mama da y'an uwanki da kuma babyna dake cikinki na kawo mawa. Akwai chocolate, wannan duka naki ne, au na baby na. D'an kai hannu cikinki ki fad'awa babyna daddynsa na gaishe sa." Ko kallonsa bata yi ba, balle tayi abunda yace, kuma dama shima ya san ba yi za tayi ba. Yana kallonta sosai, bini-bini zata shak'i iska ta lumshe idanu, ya karanci psychology, hakan ya fahimtar dashi abunda Sarah take shak'a. Murmushi yayi tare da fad'in, " _Mine_ akwai abunda kike so amma jik'imarki ta hana ki bud'e baki ki fad'a min ko?" Bud'e idanunta tayi a kansa tare da fad'in, "Ni babu abunda nake so. Kawai zuciyarka ce ta fad'a maka gaibu." Kallonta yayi na second hud'u sannan yace, "Ki rantse da girman Allah turaren jikina baya fizgar hankalinki har yake saka ki lumshe idanu." Mamaki ne ya kashe Sarah ganin ya d'ago jirginta. Sai ta diririce ta rasa mai zata ce sai kawai tayi shuru tana kallon k'asa. Komawa mota yayi, mintuna biyu sai gashi ya dawo da kwalin turaren *_Imperial Majesty_*, bakinsa kuma yana taunar masoyin nasa _Mastika gum_. "Wai kai baka gajiya da cin chewing gum ne?" Fad'in Sarah wacce bata ma san lokacin da tayi masa wannan tambayar ba. "Kin tuna wancen ranar haka kika ce min mai d'abi'u _KARUWAAA_?" Sai da ya,ja waa d'in yana dariya. Rufe fuska da hannunta Sarah tayi tare da fad'in, "To ai kai d'in ne ka cika cin chewing gum." "Shikenan kuma duk mai cin chewing gum ya zama karuwa ko? To ai gashi kin tunzurani kin saka nayi maki halin karuwan har gaki da tsaraba." Da gudu Sarah ta juya zata gudu ya rik'e hannunta tare da saka mata kwalin turaren a hannunta sannan yace "A sauka lafiya, a kuma gaishe min da Baba." Yana gama fad'in haka ya sakar mata hannu ita kuma ta shige cikin gida da sauri. Da gudu Lami ta rungumeta tare da zabga gud'ar da ya karad'e gidan, hatta Baba dake d'aki sai da ya toshe kunne yana fad'in, "A'uzu billahi minash shaid'anir rajim!" Lami kuwa sai ta hau yiwa Sarah kirari, "Yarinyar mai goshin arziki, yarinya mai k'irar matan manya! Gabanki fari bayanki fari k'al, d'awisu duk inda kika gitta sai an kalleki. Wuhuhuuuu ina gwanin wani ga nawa gwanar. Ni na san banyi asarar haihuwa ba wallahi. Kai jama'aa." Tana fad'in haka sai ta hau rawa da wak'a irin na matan zumunta, sai dai bata kiran sunan yesu almasihu sabida kar Y'ay'an su b'aro jirginta don duk da basu sallah, sai sun ga dama, baza suji dad'i ba idan suka fahimci ta koma addinin kiristanci wanda take ganin shine addinin gaskiya a gareta. Sarah kuwa sarai ta faminceta, a zuciyarta sai addu'ar shiriya take nemawa mahaifiyar tasu akan ta gane gaskiya ta natsu. Aina'u kuwa wani dogon tsaki tayi tare da fad'in, "A dai yi mu gani idan tusa zata hura wuta." A cikin zuciyarta. Sarah kuwa kaucewa tayi ta shige d'akinsu ta kwanta a kan gado tana tuno ranar data fara ganin _Ibarahim Khalilullah_ a rayuwarta. Tun da ta taso k'awa d'aya tal tilo take dashi a rayuwa, Muniba. Muniba na d'aya daga cikin mutanan da suka d'aura ta a kan hanyar madaidaiciya domin if not because of her she would have joined her siblings. Amma kasancewar Muniba ta taso gidan mutunci da tarbiya, don babanta shine limamin masallacin _Mai duguri road_, kuma an d'aura su akan ingantacciyar tarbiya. Makarantar bokonsu d'aya tun daga primary five har suka kammala secondary school, Muniba tayi k'ok'ari sosai wajen saita Sarah a kan hanya madaidaiciya, don farko itama ta soma d'auko rawan kai da y'an gidan. Irin su shigar banza, zagin d'an Adam duk tsufansa, rashin kunya da saurarsu. Muniba ita tayiwa Sarah registration na islamiyar da take zuwa *_MADARASATUL TATBIQUT TA'ALLIMUL ISLAMIYA_*, kuma makaranta ce da ba'a wasa ko kad'an. Kuma da ikon ubangiji sai da Sarah tayi sauka sai dai bata samu damar cigaba ba kamar yanda Muniba ta cigaba. Baba Nuhu sosai yaji dad'in haka, don ko a wancen lokacin, Sarah ita mai k'aunar mahaifinta, kuma tana jin maganarsa sab'anin Lami. Don ita b'ata tab'a sha'awar karuwanci ba kamar yanda sauran y'an uwanta suke yi. Burinta shine tayi aure ta zauna a d'akinta k'ark'ashin kulawar miji. Sai dai Baba Nuhu bai da k'arfi sosai wanda zai iya biyawa Sarah kud'i both islamiya da boko don lokacin ta kammala secondary school har ta yi jamb kuma ta samu admission a polytechnic na tudun wada, kuma Evening. Kuma registration kawai 63thousand ne. An buga an buga babu ta inda kud'in nan zasu fito, kuma Lami tayi rantsuwa da Allah kwandala baza ta biya mata ba, tunda ita bata taimaki kanta ba, babu yanda za'ayi ita ta taimaka mata. Haka Sarah tayi ta fad'i tashi har ta samu aiki wa wani babban restaurant wanda zasu rik'a biynata 20k duk wata. A kuma wannan lokacin wani babban yayan Muniba ya gansu tare da Sarah a bakin titi lokacin zata tafi restaurant inda take aiki, ita kuma Muniba zata tafi poly don ita ba evening lectures take yi ba. Ai kuwa yana dawo gida ya fad'awa mahaifinsu yaga Muniba da yarinyar gidan karuwai. Bayan ta dawo daga school aka mata dukan tsiya kuma ana zama mata jan layi akan idan ta ketara ta kuma had'uwa da Sarah kashinta ya bushe kuma baza ta k'ara zuwa makaranta ba sannan aure za ayi mata kamun ta jawo masu abun kunya kuma da ko wanene aka samu za ayi mata auren. Wannan shine dalilin rabuwarsu da Muniba. Ko a hanya basu k'ara had'uwa ba tun bayan da Muniban ta fad'a mata abunda mahaifanta suka yanke. Don ko a wannan lokacin Sarah bata daina saka k'ananun kaya ba shiyasa kowa yake mata kallon y'ar iska. A restaurant d'in nan ta soma ganin _Khalil_ yaje cin abinci. Shi kuma idan bai ci abinci a gida ba, babu inda yake zuwa yaci abinci hankalinsa a kwance kamar wannan restaurant d'in. Don abincin gargajiya suke yi kala-kala mai dad'i da tsafta. Sau uku ana aikenta kai masa menu, kuma duk taje sai sunyi fad'a don kallon y'ar iska yake mata, ita ma kuma kallon da take masa kenan don kullum da chewing gum a bakinsa, duk da kuwa ba k'as-k'as-k'as yake yi ba. Amma ganin duk lokacin da tazo kawo masa Menu wani harara take jifansa dashi tana magana k'asa-k'asa, shi kuma sarai yana jin ta sarai, don ce masa take yi karuwa. Shi duk wajen babu wacce ya tsana irinta, haka itama. Dad'inta ma sai ya kwashi watanni bai zo ba. Ta kwashi tsawon shekara biyu tana aiki a wajen har ta kammala diploma d'inta. Ranar da suka yi sign out, bak'ar skirt ta sanya iri straight d'in nan mai tsagu ta baya, sai fara k'al d'in shirt da mutane suka yi signing da maka ta ko'ina a jikin rigar gaba da baya. Kanta kuma tayi parking d'in gashinta a tsakiyar kai da yaci uban acuci maza na attachment, babu d'an kwali a kanta, sai wani siririn Chantilly Vail da ta yafa. K'arfe shidda ta tashi a aiki, bayan ta gyara jikinta ta kuma fesa turare sannan ta nufi wajen madam za tayi mata sallama don ita take bata kud'in motar komawa gida. "Aunty na gama zan wuce." "Yauwa Saratu, karb'i wannan hanyar wucewa gidanku ne, zaki kai wannan sak'on *Golden diamond hotel*, wani customer d'in mu ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ne ke son tuwon shinkafa miyar egushi. Kuma shi abinci idan ba na nan wajen ba, bai son na wani waje. Please ki tsaya ki kiyi delivery d'in wannan sai ki wuce gida. Ga kud'in transport." Ta k'arisa maganar tare da mik'a mata 1k da kuma ledan take away a ciki. Karb'a tayi tare da juyawa ta fita daga restaurant d'in. Zuciyarta d'aya ta nufi hotel d'in kasancewar har numbern d'akin aunty ta fad'a mata. Tana zuwa reception ta samu wani inyamuri tayi masa magana, duk a tunaninta shi zai karb'a ya kai masa abincin. Amma sai taga inyamurin ya daga waya ya kira can d'akin yayi magana da wanda zata kaiwa abincin. "Ok Sir!" Shine kawai abunda taji ya fad'a tare da yanke wayar sannan ya kalleta tare da fad'in, "Madam you can go in!" Da kamar za tayi musu, sai kuma ta nufi hanyar da zai sadata da matattakar da zai kaita room number d'in da yake ciki. Knocking tayi, daga ciki aka ce "Yes come in!" Tura k'ofar tayi tare da shiga

12 / 60