Advertisements
Chapter 24 Reading Kida A Ruwa Book 2 Complete Hausa Novel Hausa Novels
Advertisements

Kida A Ruwa Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Billyn Abdul Category :  Action Novels

Chapter   24 / 24

69K to 71K   out of 71K words

kansa. Fata kam tayi haske da kwanciya saboda zaman waje guda. Sai dai baza'ace akwai laushi na jin daɗi ba. Yanda yake kallonsa haka shima Dada ke kallon nasa, dan duk da ya rufe fuska a kallo ɗaya ya gane wanene, dan ko cikin rububi manta wannan halittar ta gabansa sai dai ɗimuwa a lokacin magagin mutuwa amma ba a cikin hayyaci ba.

         A karo na farko baƙon ya ɗan murmusa da ƙoƙarin danne abinda ke yunƙuro masa. Sai kuma ya kai hannu a hankali ya zare glasses ɗin idanunsa. A tare idanuwa nasu suka haɗu a cikin na juna. Imran ya kasa motsi. Haka shima Dadan bai motsa ba, dan kai tsaye zuciyarsa yake kallo a zahiri.

       Fin sakan talatin suna a haka kafin Dada ya saki wani ɗan murmushi da lumshe idanu ya buɗesu a lokaci guda, a hankali ya cigaba da takowa har inda Imran yake. Har yanzu nutsatstsiyar fuskar nan tasa da murmushin nan nashi na ƙasaita, ya motsa lips kamar mai son raɗa ya furta, “Ranka ya daɗe, soja… har yanzu baka daina kuka da ido ba?”.

       Kauda kai Daddy Imran yayi yana haɗiye hawayen da basu ƙaraso cikin idanunsa ba, amma da yake Zak-Shadow ɗin nasa Zak-Shadow ne shi har ya karantosu daga ƙirjinsa.

         Wata ƴar ƙaramar dariya Dada ya saki da kaiwa zaune, ƙafarsa ɗaya kan ɗaya hannayensa da yau babu handcuffs harɗe a ƙirjinsa ya sake faɗin, “Sit mana my Boss”.

      Yanzu kam shima murmushi Daddy Imran yayi, sai kuma ya gyara kujera ya zauna irin zaman Dadan suna kallon juna tamkar wani saurayi da budurwa.

      “Na yi missing naka sosai, Zak...” kalma mafi nauyi da girma dake riƙe da zuciyar Imran ta fito daga bakinsa. Sai kuma hawaye suka cika masa idanu.

       “Idan ka cigaba da wannan kukan, how many missions za ka gama?. Kalleni da ƙyau ina raye, kuma ina cikin ƙoshin lafiya mi kake buƙata bayan hakan daga UBANGIJI? Ko sai na tashi mun gwada ƙarfi ne?”.

      Dariya sosai Daddy Imran keyi cikin hawaye, dan ya fahimci yau raha Zak.. ɗinsa ke ji. Kai tsaye ya ce, “Kai dai ba zaka canza ba.”

         “Zama da kai ne Imran, kwana biyu sai nake jin matsanancin kewar ka. Ashe kana gab da ni ne shiyyasa.”

       “Duk randa muka zama a nesa da juna lallai ƙasa ta bizne idanun wani a cikinmu ne ko mu duka. Sai dai ni nafi fatan fara tafiya na barka dan nasan bazan iya ɗauka ba idan kai ne ka barni”.

     Idanu sosai Dada ya zuba masa. Dan haka shiru ya biyo baya, irin shirun nan mai cike da abubuwan da bazasu faɗu ba. Tsohon lokaci kafin Daddy Imran ya katse yanayin nasu ta hanyar miƙa masa briefcase daya shigo da ita.

       “New President Yusuf Tafida… ya buƙaci nazarin shari’arka tun daga farko har ƙarshe. Sai dai ba yau za mu faɗi komai ba. Amma daga yau ɗin game ya fara dawowa.”

     Cak numfashin Dada ya tsaya ba ƴan sakanni, ya kuma zuba ma Imran ido tamkar zai haɗiyo shi da su, “Sabon shugaban ƙasa, zai iya zama yana da alaƙar huɗɗa da waɗanda suka karyar da ni fa Imran, sai dai maybe shima bai sani ba.”

      “Miyasa kai wannan tunanin? Dama ce fa tazo mana daga UBANGIJI. Kafa san wanene Janar”.

         “Tabbas nasan Janar, sani na nagarta da mazantaka. Ba kuma bana farin ciki da damar bane, ina ganin kamar yazo da gaggawa ne, gaggawar da zasu iya kaishi ƙasa da ita a kaina, dan yazo musu da bazatar abinda ba shi suke hasashe ba a kansa. Dole ya zama mai zaɓi biyu a lokacin da ya bayyana musu ainahin fuskarsa a kaina. Saboda a tsarinsu babu wani shugaban ƙasa da zai kasance baya abota da su. Koda sun ɓoye masa waccan fuskar tasu a yanzu inada tabbacin zasu bayyana masa ita ya sansu ya san aikinsu. Matsalar kuma idan har yana son gaskiya, to sai ya tabbatar min da hakan da aikin shi. Ba da kalamai ba. Dan kar ya kasance na amince na fita ya zama yana cikinsu bazan ƙyalesa ba koda shine Abdul-rasheed Shehu Isa Kobi”.

       Daddy Imran ya fahimci hangen Dada, dan haka ya sauke numfashi mai nauyi yana jinjina kansa da faɗin, “Haysam na yarda da ku kai da Janar da Faro. In sha ALLAHU Janar bazai bamu kunya ba, yanda muka fara da shi zamu ƙare a tare koda sai bayan babu ran mu ne NASARA zata bayyana. Na tabbatar shima kamar mu ya ke, idan gaskiya tana gona, zai haƙo ƙasa ya nemota da kansa.”

      Dada yayi murmushin mai zafi fiye da bala’in da yake hangowa da ƙurar da zata tashi. “Shike nan Imran! ka gaya masa, idan yana neman gaskiya, kada ya zo da haske. Duk wanda yake neman ƙasar nan, sai dai ya biyo duhun dare. Ni zan fara jiranku daga yau. Ku dinga tuna kuma zan dawo da gudunmawata. Game on.... again.” yay furucin ƙarshe da wani salo yana kashema Imran ido ɗaya da yin alamar harba bindiga da yatsu biyu.

     Dariya Imran ya kece da ita, irin dariyar da shi kansa yasan ya jima baiyi ta ba. Kai koda kwatance baya kawota a zuciyarsa balle ma fuskarsa. Shima Dadan kallonsa yake yana wani shegen murmushi mai bayyana haƙwara, kai daka gansu kasan ƙara'in farin ciki ne na tsahon shekaru ke fidda kansa tun daga ƙasan zuciya har zuwa fuskokinsu. Sai dai Imran yasan minene ma'anar murmushi irin wannan a fuskar Zak-Shadow ɗinsa. Ya tabbatar zafin daya jure cikin wannan duhu na tsawon shekaru takwas da wata huɗu, sakamakon wannan murmushin idan ya fito ƙasa za ta sake girgiza......

<%><%><%><%>

        “Malam Almu maganar ciwo ai ta wuce wasa, kuma ta kori komai a rayuwa. Dan haka babu batun neman alfarma zuwa gida daga garemu. Ka shirya kawai abinka ga kuɗin mota. Wannan kuma sai kai amfani da shi wajen kaita asibiti, ALLAH ya bata lafiya yasa kaffara ne. Zaka wuce yau ne ko sai zuwa gobe? Dan muma zamuje airport ne ɗaukar Bilal yau zai dawo”.

       “Kai kai Masha ALLAH. Yau Alhaji Bilal zai dawo ashe? To bari na jira ya dawo tukkuna ai kamar zai fi”.

     Kai tsaye Mammah dake saurarensu ta ce  “A'a Malama Almu ban goya bayan haka ba, kaje dai tunda zaka dawo ai. Itama Innarka na buƙatar ka, kuma tana buƙatar a kaita asibiti. Ina ga ma idan kaga jikin babu daɗi sosai kawai ka ɗakkota zuwa goben ku taho nan a kaita asibiti zai fi”.

     Godiya maigadi yake jerama Mammah dasu Yaya Ja'afar har hawaye na cika masa idanu. Yana tausayi da mamakin alkairan bayin ALLAHn nan, shiyyasa a lokuta da dama idan ya tuna dalilinsa na zaman gidan nan tare da su sai yaji zuciyarsa na karaya akan ƙudirinsa. Haka ya miƙe yana shartar hawayen da shi kaɗai yasan dalilinsu ya fita...

      A gurguje maigadi ya shirya tare da damƙa gate a hannun sabon driver kamar yanda su Ja'afar suka ce masa. Ya wuce ya tafi yana ayyana wa a ransa ai bazai wuce jibi ba, idan har zuwa kwana uku bai dawo ba to bazai wuce safiyar kwana na huɗu ba in sha ALLAHU. Dan babu wani ciwo da Innarsa keyi kamar yanda ya faɗa, ogansa ne ya bashi umarnin zuwa ya sameshi da gaggawa a yau. Saboda shi Innarsa ma ta jima da rasuwa, a hannun kishiyar uwa ya tashi, azabar data bashi da wahala ta maida shi yanda yake a yau, sai dai a gidan Mammah sanin mutum cikakke sukai masa mai nagarta sakamakon ɓoye ainahin wanene shi da yayi a garesu....

   Tofa, wata sabuwa maigadi🤔🤐🏃🏼‍♀️.

   

÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷÷

     ★DUBAI★

    Duk yanda su Hajiya Hasiba suka so tafiya India bincike akan Adeel bai yiwu ba. Dan kuwa randa ta samesa da dabarun zuwa India business a ranar yace mata ya kammala shirin tafiyarsu. Ta jira har su dawo sai taje. Kota sanar masa business ɗin da kamfanin da zasuyi koma miye a kawo mata shi. Jin haka yasa ta saurin cewa ba damuwa suje ɗin kawai su dawo tayi nata uzirin daga bayan.

          Shirin nashi bai bata tsoro ba sai da ya tabbatar mata harda su Nabeeha za'a. Ta tambayesa ba'asi yace hankalinsa zaifi kwanciya idan tana acan tare da shi. Dan karma ya barta anan wani abu ya faru. Duk da kuwa yana da ƙarfin ikon sakawa a bibiyar masa ita duk inda ta shiga a cikin ƙasar. Amma baya buƙatar hakan, dan bayan abokinsa ɗaya jal babu wanda yasan yana bibiya ko son auren Nabeeha.

    Abinka da sai yanda akai da kai, dole suka hau shirin tahowa. Sai dai ran Nabeeha da Ismat fal farin ciki. Hakama Mamawo, dan koba komai itama akwai nata shirin data barma tata zuciyar game da Adeel ɗin, tana ganin kuma zuwansu ƙasar tasu ce zai iya cika cikin sauƙi saɓanin anan da wasu dalilai zasu iya hanata. Amima da Raihana ko basu so wannan tafiya ba. Dan harga ALLAH su daɗin zaman Dubai suke ji, har basa son tuna zuwa ƙasar haihuwarsu. Shiyyasa ma suke matuƙar jin haushin Nabeeha da taƙi bada haɗin kai bori ya hau. Dan wlhy da a cikinsu Adeel ya nuna yana son wata hohoho da wani labarin ake ba wannan ba ma..........✍️

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899*

*_Moniepoint MFB_*

*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_*

*_Telegram Number 09032345899_*

*_AREWABOOKS (Vvip)_*

*_Chapters & Audio_*

@BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276*

*_Access Bank_*

*_Bilkisa Ibrahim Musa_*

*_Kati MTN:- (500)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya:-_*

*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*

*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_*

*+234 805 568 7449*

*_Telegram Number👇_*

*+234 903 234 5899*

*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*

*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*

*_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._*

*_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_*

*_Akwai VIP Telegram 💃_*

*_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_*

*_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_*



_(2k)_

*9032345899*

*_Moniepoint MFB_*

*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (2k)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_*

*_Telegram Number 09032345899_*

*_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*.

_(1,500 CFA)_

*_+227 98 94 12 81_*

*_My NITA_*

*Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_AREWAPEN (Vvip)_*

*_Chapters & Audio_*

@BilynAbdull

*_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

24 / 24