Advertisements
Chapter 4 Reading Kida A Ruwa Book 2 Complete Hausa Novel Hausa Novels
Advertisements

Kida A Ruwa Book 2 Complete Hausa Novel

Author :  Billyn Abdul Category :  Action Novels

Chapter   4 / 24

9K to 12K   out of 71K words

ga ruwa nan, ka kuma tashi muje muci abinci”.

    Imran ya ɗan sake murmusawa yana shafa kai, cike da girmamawa ya ce, “Sir zan sha ruwan dai, abinci kuwa amin afuwa kada madam tayi fushi nabar nata”.

      Ƙaramar dariya Genaral yayi duk da kuwa shima ba mutum ne mai yawan fara'a ba. Cike da dattako ya ce, “Gaskiya bazan so ɗiyata kam tai fushi ba. Amma duk da haka sai kaci, dan na saka an shirya maka ne na musamman”.

    Babu yanda Imran ya iya dole ya haƙura suka hau teburin cin abincin da aka cika da kayan daɗi. Sai da suka fara cin abincin cikin nutsuwa falon shiru janar ya katse shirun da faɗin, “Ina fatan babu wata damuwa tare da Haysam? Yana cikin ƙoshin kafiya?”.

       Sai da Imran ya haɗiye abincin bakinsa sannan ya jinjina kansa, sai dai fuskarsa ta janza zuwa damuwa. “Alhamdullih Sir. Babu wata bayananniyar damuwa ta zahiri. Dama kuma mun san bayan killacewa babu abinda zai yarda ya ɗauka ga wani na ƙasƙanci in dai Haysam ne. Dan har yanzu JININ MAZA na'a kan FARCE”.

      Sosai Janar yay murmurshi mai faɗi. Ya ɗauki ruwa yana tsiyayawa a kofin gilashi. “Wato Imran da ƙasar nan tasan asarar da tayi na killace Haysam na kwana ɗaya kawai data jima da yima kanta da kanta ALLAH ya isa. Balle ma ace na tsawon shekaru uku da wasu watanni. Irinsu Haysam a ƙasa tamkar hasken diamond ne a tsakiyar sahara. Amma ban san miyasa ba, maimakon aga haskensu anfi kallon wahalar ɗakkosu da gujewa zafin saharar ne da yawanta..”

        “Sir bazasu fahimta ba, irinku ƙalilanne ke fahimta saboda zukata masu ƙyau da ALLAH ya baku. Amma wlhy a tsayin rayuwata ban taɓa cin karo da mutum mai tsananin kishin ƙasa da son cigabanta ba irin Haysam. Mutum ne shi mara tsoro, mai tsayawa akan gaskiyarsa koda kuwa ace zata ƙona shi. Sannan yana so da sauri, shiyyasa yake komai da sauri. Amma na rasa miya tare musu?”........✍️

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899*

*_Moniepoint MFB_*

*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_*

*_Telegram Number 09032345899_*

*_AREWABOOKS (Vvip)_*

*_Chapters & Audio_*

@BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276*

*_Access Bank_*

*_Bilkisa Ibrahim Musa_*

*_Kati MTN:- (500)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya:-_*

*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*

*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_*

*+234 805 568 7449*

*_Telegram Number👇_*

*+234 903 234 5899*

*_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_*

*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*

*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*

*_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._*

*_Akwai VVIP AREWAPEN kenan 💃_*

*_Akwai VIP Telegram 💃_*

*_(Ƴan WhatsApp ku haƙura kawai ƴan ta'addar bati sunfi yawa a cikinku gaskiya tsoron rashin m ɗinku nake 😂🤣)_*

*_Telegram Audio 2k ne kacal ba tsada 💃. Sai kusaka ta wannan account ɗin👇_*



_(2k)_

*9032345899*

*_Moniepoint MFB_*

*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (2k)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_*

*_Telegram Number 09032345899_*

*_Ƴan NIGER🇳🇪 kuma bazamu barku a baya ba in sha ALLAHU zaku biya (Telegram vip 1,500 CFA) domin littafin KIƊA A RUWA..... na ji Audio-vocal. Sai ki biya tanan👇_*.

_(1,500 CFA)_

*_+227 98 94 12 81_*

*_My NITA_*

*Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 1,500 CFA vip telegram

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_AREWAPEN (Vvip)_*

*_Chapters & Audio_*

@BilynAbdull

*_Ƴan WhatsApp kuzo muyi shawara idan zaku iya amana ayi harkar nan daku 😂, dan bana son a barku a baya duk da dai bakwa ji, ba raga min zakuyi ba na sani duk da ƙaunar da nake muku 🤣😂._*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_ALLAH ka gafartama iyayenmu 😭🙏_*

*_Typing📲_*

*_💦KIƊA A RUWA...!!💦_*

*_Bilyn Abdull ce 🤙🏻_*

*_بِسْمِ اللَّهِ الرَّحْمَٰنِ الرَّحِيم_*

_Da sũnan Allah, Mai rahama, Mai jin ƙai._

*_GENERAL FICTION_*

_Wannan labari ƙirƙirarre ne. Sunaye, wurare, da abubuwan da suka faru duk ƙirƙira ne, ba su da alaƙa da gaskiya ko wani, koda Bilyn Abdull ce 😂._

*_BOOK 2_*

_Chapter 5_

__________________

*_MS TOFA GALLERY_*

Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/D1ZOZr50SfwCQUbhMB0eVC CEO Maryam Tofa 07010346400 inshaAllah zakiyi dariya kayanmu nada sauki da inganci kedai kiyi joining group din don ganewa idonki kaya masu kyau da aminci. Akwai GHT Supplements masu inganci.Allah yasa damu da alkhairi.

__________________

*_TELEGRAM GROUP_*

https://t.me/+erpSeN2ssqgwYTdk

*_WHATSAPP CHANNEL_*

https://whatsapp.com/channel/0029VbBMI7RLY6d9zU893c1F

*_TIKTOK_*

https://vt.tiktok.com/ZSDkPqMm1/

*_INSTAGRAM_*

https://www.instagram.com/invites/contact/?i=fc2g6shv1k6u&utm_content=p17zzzv

______________________

.........“Bai tare musu komai ba, gaskiyarsa da rashin tsoro yasa suka kasance su a tsoracen. Sannan an tasirantar da siyasa ne a cikin al'amarin a yanzu.”

          “Shima abinda ya gaya min kenan, da nace masa zaluncine yasa suka rufemu. Yace ba zalunci bane siyasa ce kawai”.

     “Ƙwarai da gaske maganarsa gaskiya ce, wasan ya canja daga yanda ya fara ya koma siyasa saboda an janyo hankalin wasu masu zuciyar kwaɗayi a cikinsu da kuɗi, sannan duk masu son ayi gaskiya an daƙilesu. Kaga dai sunyi duk yanda zasuyi sun hana wasu a cikin adalan shugabanin komawa tenure ɗinsu ta biyu, sun ƙalama ministoci da yawa sharrin da sai da suka bar ƙasar. Yanzu sun ɗora wanda suke so akai gashi har sun shiga shekara ta uku akan mulki, sun samu damar yin yanda suke so. Duk da lafawar hare-haren nan dakaga an samu akwai manufar da suke son cimmawa ne kawai, sannan sun sami abinda suke so wato cigaba da haƙar ma'adanai.”

        “ALLAH zai mana maganinsu Sir”.

     “In sha ALLAHU Imran, sai dai muma dolene mu tashi tsaye sannan ne zamu samu taimakon UBANGIJI. Dan tabbas in dai ba wani motsi mai girma mukai ba akwai babbar matsala da zata iya faruwa anan gaba. Ciki kuwa harda halaka Haysam dana samu tabbacin suna shirin yi.”

     Cikin matsanancin tashin hankali Imran ke kallon General. Shima sai ya jinjina masa kan nasa. “In sha ALLAHU bazasu samu dama ba. Shiyasa ma na yanke wani hukunci. Wanda ta hanyarsa ne kawai naga mafita a fitowar Haysam daga prison”.

        Imran ya ture plate ɗin abincinsa gefe, cikin bugun zuciya da rawar murya ya ce, “Sir wane irin hukunci ne wannan? Wlhy komai wahalarsa da haɗarinsa zan kasance tare dakai muyi domin kuɓutar da Haysam, dan raina fansa akan Haysam Abdul-rasheed Shehu”.

           Cikin jinjina kai da sauke ajiyar zuciya General ya ce, “In sha ALLAHU wannan abotar taku sai kunci moriyarta mai tsaho a duniya sannan ku kasance a aljanna tare. Imran a yanzu kaf hanyoyin fitar da Haysam na bisu amma duk an rufe su ta hanyar makirci da ƙarfin ikon masu mulki. Dan haka nai nazari nima da gane hanya ɗaya muma ta rage mana. Wato irin hanyar da sukabi suka rufe kaf ƙofofin muma dole ne mubi tanan mu buɗe ƙofifin. Dan tabbas Haysam shine ƙashin bayan karya waɗan nan mutanen da shirye-shiryen su. Badan wasu bazasu iya bane, badan babu kamar Haysam bane, badan babu masu irin gaskiyarsa da jarumtarsa bane. Akwaisu da yawa cikin matasan sojojinmu dama sa'anninku ɗin, kai harma wanda suka fishi duk za'a samu. Kawai Haysam shine ya fara musu illa, yay musu sani na haƙiƙa, sannan yake firgitasu da basu tsoro tunda har suka tattara duk karfinsu wajen son ganin sun danne shi. Dan haka ina son shi daya fara wannan aikin ya ƙarasa shi dan su san ZAKARAN DA ALLAH YA NUFA DA CARA...... Sannan da gaske shi ɗin KIƊA A RUWA NE MAI TADA HANKALIN SU. Dan haka Imran zan shiga SIYASA..”

         “SIYASA! Sir?!”.

    “Ƙwarai kuwa Imran SIYASA. Dan yanzu haka na fara shiga jikinsu, har wasu a cikinsu sun ɗorani a shawarar fitowa ɗan majalisan tarayya. Na kuma yarda na amince musu, sannan zan musu duk yanda suke so dan babbar kujerar mai gaba ɗaya nake hari nan da shekaru huɗu masu zagayowa bayan an gama tenure mai zuwa bayan wannan”.

       “Turƙashi”. Cewar Imran yana zuba tagumi da hannu biyu. Murmurshi Genaral yayi mai faɗi, cike da dattako ya ce, “Yaƙin namu ne mu duka. Wannan shine hikimata ta cewa kada ka ajiye aikinka. Dan a yanzu haka kaima suna shirye-shiryen ƙara maka girma. Acewarsu zasu fara jan ra'ayinka dan zafafa zuciyar Haysam da ɗarsa masa cewar baka tare da shi. Su kuma samu sirrikansa....”

      “ALLAH ya kiyaye, bana buƙatar ƙarin girmansu....”

    Ƙaramar dariya Genaral yayi, cikin katse Imran ya ce, “Kwantar min da hankalinka mazan fama. A yanzu da bamu da zaɓin daya wuce maida kammu sakarkaru. Ta haka ne kawai zamu kamo bakin zaren, mu kuma tantance su waye ainahin munafukan. Su waye masu gaskiyar? Sannan mu cimma burin mu kuma. Amma na baka dama kaje kai tunani mai zurfi. Sannan zan sake shiga da fita dan ka sake ganawa da Haysam a karo na biyu, ka nema shawara a wajensa kuma. Imran idan wani zai iya gane zuciyar Haysam daga cikin duhun prison, kai ne. Ka koma. This time, ka saurare shi da idon zuciya, ka kuma gaya masa shirin mu da manufar mu. Na tabbatar zai bamu goyon baya shima.”

     

     Wannan maganar ta General Yusuf ita ta kulle ma Imran baki tun jiya. Haka kuma ya cigaba da yawo da ita tsakanin safiya zuwa marece na kowane rana. Har ALLAH yasa a karo na biyu ya sake samun damar ziyartar Zak-Shadow a karo na biyu bisa tsayawar Janar ɗin......

<<•>><<•>>•<<>>

       A PRISON GATE...

      Ranar ta yi zafi sosai kasancewar ya tareta ne a lokacin zafin nata. Domin kuwa ƙarfe ɗaya ne a lokacin. Dan daga massalaci ma ya wuce special Military Corrections Facility.... ɗin. Wani nauyi ya lulluɓe zuciyar Imran tun daga lokacin da ya taka ƙasa ya ƙarasa gaɓar ƙofar babban prison ɗin. A karo na biyu cikin satittika biyu yana zuwa wurin da rabin zuciyarsa ke tsare.

      Ya shigar da sunansa kamar zuwan farko, aka tabbatar da izinin shigarsa bisa doka. Daga haka aka rakashi zuwa ɗakin ganawar kamar na wancan lokacin. Wurin nan buɗaɗɗe da babu shamakin gilashi a tsakaninsu kamar saura, kujera biyu, teburi a tsakiya. Cikin mintuna kaɗan aka kawo Dada. Hannayensa daure da handcuffs, fuskarsa ɗin nan a ɗaure kamar yanda kowa ya santa, sai dai a yanzu babu zafafawa kuma ba murmushi. Amma idanunsa sun kasa ɓoye gajiyar shekaru uku da wahalar ƙuncin rashin aikin daya zamewa jiki da zuciya sabo.

       Imran ya zuba masa ido batare da yace komai ba. Shi ma Dada bai yi magana ba har sai yada ya zauna. Sai wani ɗan shiru mai zurfi ya cika ɗakin. A hankali Dada ya zubama Imran ɗin juyayyun idanunsa, kamar yanda shima Imran ɗin ke kallonsa.

     “Ni karka cinye ni”.

   Dada ya faɗa yana hararar Imran. Murmurshi Imran yayi a karo na farko. Shima sai ya furta, “Da zaka haɗiyun ma ai da na huta. Kaga sai mu fice abinmu batare da kowa yaji ya gani ba mu koma gida kaga yanda Mammah ta ƙara ƙyawu. Nimrah da Ruƙayya dasu Asma'u da Khalifanka suka girma. Ma'aruff da Ja'afar suka zama magidanta harda ƙyawawan yara masu kama da kai da duk suka ci sunanka da sunana. Ammar da Bilal suka sake girma. Mu'azz ma ya fara zama ɗan saurayi. Ummi da Momy da Mimi sun sake haihuwa, Biebah ta sake zama budurwa ƴar jami'a. Nabeeha na cikin kewa da son ganinka.”

      Wani sassanyan murmushi Dada yayi yana mai girgiza kansa da sake tsatstsare Imran ɗin da idanunsa. “Shike nan ka faɗa kaji daɗi, ALLAH ya albarkaci rayuwarsu gaba ɗaya. Ya sanya farin ciki da kwanciyar hankali a ciki. Ina fatan Mammah bata da wata damuwa?”.

          Shima cikin murmurshi Imran ya ce, “Alhamdullahi Mammah na cikin ƙoshin lafiya. Duk da dai an shiga ruɗani a farkon ƙaddarar, amma zuwa yanzu zuciya ta amsa da hannu biyu kuma ALLAH ya saka nustuwa da farin ciki. Sai dai addu'a ba'a gajiya ba. Dan kwanan nan ma suka dawo daga Umrah su dukansu dan har Nimrah da Ruƙayya ba'a bari ba. Kasan yanzu sune autocin Mammah, suna zuba shagwaɓar su yanda suke so da rashin ji. Dan a wata biyu kawai da tawa dawowar an gayyaceni makarantarsu karo na huɗu kenan akan rashin jin su. Mammah kuma da anyi magana ta tare ko ina ta hana ai musu faɗa. Koda yake suma su Ja'afar ɗin babu mai son musu faɗan, sai Hafsa ce ma ke ɗan lallasasu idan sunje gidan shiyaysa basa son zuwa can su kwana”.

        A mamakin Imran murmushi mai faɗi Dada yayi a yanzu fiye dana farko har haƙoransa na bayyana. Ya ɗan taɓe baki da faɗin, “Ai nasan za'a rina. Dan tun a ranar farko na fahimci kam hali yazo ɗaya. Shike nan dai Mammah ta cika min burina na ƙwace Ruƙayya.”

      Imran ya ɗan murmusa shima da faɗin, “Ta cika maka kam ita da Nimrah, dan Nimrah ta taka rawar gani wajen janye hankalinta da ƙyau”.

       “ALLAH ya raya su”.

Ya faɗa a taƙaice.

   Imran ya lumshe ido, muryarsa a raunane ya ce, “Amin ya rabbi. Gani na dawo Zak.... Ina bukatar ka bani dama dan fahimtar abin da bakace ba a ranar farko.”

        Dada ya ja dogon numfashi. Ya jingina da kujera kamar mai yaki da wani abu a zuciya. “Babu abin da zan iya faɗa da baki ba tare da ya cutar dani ko ya cutar da ku ba”.

     Imran ya jinjina kai. “Na fahimta, amma ka sani nazo jin duk abinda zaka iya rubutawa… Sannan a wannan gaɓar faɗar tafi amfani, dan nima ina tafe da muhimmiyar magana. Idan ba yau ba, yaushe?”

        “Haka ne”. Cewar Dada yana zaro wasu murɗaɗɗun takardu daga ƙarƙashin rigarsa ta prison. Kai tsaye ya miƙa takardar ga Imran kamar yana mika zuciyarsa. “Ka sakata a jikinka dan nasan bazasu bari ka fita da ita ba. Na rubuta wannan cikin shekaru uku. Babu kuma wanda ya kamata ya gani sai kai.”

      Hannu Imran ya miƙa masa shima, bai karɓa nan take ba saboda nauyin da kalmar “Sai kai” ta yi masa. Idanun Dada suna cike da gajiya amma akwai hasken wanda ya tsaya tsayin daka, wanda bai fasa ba, baya jin kuma zai fasa ɗin koda na daƙiƙa guda ne, duk da cin zarafi, yaƙi, da shekaru uku na shiru sukazo masa da shi. Ba wanda suka killacesa anan yake kallo ba ƘASAR da masu tasowa a GOBEN ƘASAR kawai yake hange da kallo. Shiyyasa ya yarda zai sadaukar wajen ginawa tare da duk mai zuciya irin tasa, domin ƴaƴa da jikoki su amfana a bayan rayuwarsu.

       Imran ya karɓi takardar cikin sauke ajiyar numfashi. Kallonta yake cike da nauyi saboda sirrikan dake cikinta. Yana buɗewa ya ga layuka marasa yawa amma masu nauyi:

Sunaye. Abubuwan da suka faru. Kurakurai. Shakku. Hujjoji.

Da kalma guda ta ƙarshe. Sai kawai ya nannaɗeta kamar yanda ya bashi ya ɗaga rigarsa ya sakata a cikin ɗammararsa ta soja.

       Imran ya haɗiye wani abu mai zafi da ya tsaya masa a makoshi. Cikin ɗacin murya ya ce, “Zak… me kake so mu fara? Ina kake so mu fara kalla ko tunkara?”.

     Dada ya ɗaga kai ya kalle shi kai tsaye. Wannan kallo Imran bai taba mantawa da shi ba tun lokacin da suka yi fice-ficen yaki tare. Muryar jarumta ta shiga kunensa da izza da tabbacin MAZAN SUNA NAN A MAZANSU NA FAMA. GWARAZA KUMA BARADAI Masu tsayayyar zuciya da tsayayyar KALAMA..........✍️

_Zaku sameshi a waɗan nan manhajar guda uku in sha ALLAHU._

*_NIGER🇳🇪- (500 CFA) (Telegram vip 1000 CFA)_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_My NITA_*

*_Zaku iya kuma tura katin Airtel na ƙasar NIGER shima 500 CFA ko vip telegram 1000 CFA_*

_Shaidar biya👇_

*_Whatsapp number_*

*_+227 98 94 12 81_*

*_TELEGRAM VIP 1000 (1K)_*

*9032345899*

*_Moniepoint MFB_*

*_BILKISU MUSA IBRAHIM_*

*_KATI MTN (1k)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya: 👇_*

*_Telegram Number 09032345899_*

*_AREWABOOKS (Vvip)_*

*_Chapters & Audio_*

@BilynAbdull

*_WHATSAPP (500)_*

*1487616276*

*_Access Bank_*

*_Bilkisa Ibrahim Musa_*

*_Kati MTN:- (500)_*

*_09032345899_*

*_Shaidar biya:-_*

*_Whatsapp Number +234 805 568 7449_*

*_MASU SON A TALLATA MUSU KAYANSU SUMA_*

*_WhatsApp Number 👇_*

*+234 805 568 7449*

*_Telegram Number👇_*

*+234 903 234 5899*

*_ASSALAMU ALAIKUM MUTANE NA MASU ALBARKA_*

*_Maza ku matso MASOYAN Bilyn Abdull da IDANU suka hana karatun novels...._*

*_Tofa Bilyn ku ta samo muku hanya mai sauƙi da kina aiki, ko kina kwance kina hutawa, ko kina inda baki son yawan surutu earpiece ɗinki kawai zaki maƙala a kunne ko Bluetooth kisha sauraren littafin KIƊA A RUWA.... Cikin sauƙi.... 💃_*

*_Kar dai na cika ku da zance. Zamu fara saida littafin KIƊA A RUWA.... Na saurare (Audio) kenan akan farashi mai sauƙi da rahusa._*

*_Akwai VVIP AREWAPEN

4 / 24