Advertisements
Chapter 22 Reading KIRAN RABO BOOK1 CMPLT BY NANA HALEEMA BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

KIRAN RABO BOOK1 CMPLT BY NANA HALEEMA

Author :  NANA HALEEMA Category :  Complete Novels

Chapter   22 / 28

63K to 66K   out of 83.2K words

hannu
Nayla ta ce, "Twiny."

Nayla ta kalle ta dan ta san daman sai ta tambaye ta, in akwai wanda ya san halinta
a gidan su to Jidda ce. Jidda ta ce, "Twiny kin san dai ban yarda da abinda ki ka
cewa Abiy ba ko? Ai ba yau kika sana mafarkin Umma ba, Meyasa baki taɓa shiga
damuwa ba sai a wannan lokacin?." Nayla ta sunkuyar da kai bata ce komai ba. Jidda
ta ce, "Twiny ki faɗa min damuwar ki don Allah."

Nayla ta fashe da kuka ta rungume Jidda tana kuka sosai. Jidda ta riƙe ta tana
shafa bayanta a hankali dan ta san ƴar uwarta ta tana da babbar damuwa. Sai da ta
bari ta gama kukan sannan ta ɗago tagoge idanun ta ta ce, "mu je mall mu dawo." A
haka suka tafi dukka su babu mai walwala a tare dashi, sun jima sosai duk da basu
yi wata siyayya ba, sai dan kawai kasuwar da nisa inda suke.

Ɗakin su ita da Jidda ne kawai sai matar Yaya Anty Halisa dan Jidda babu mijinta
suka zo. Da suka dawo Anty Halisa bata nan hakan ya saka Jidda cire mayafi ta zauna
kusa da Nayla. Kallon ta tayi sosai ta ce, "Faɗa min damuwarki." Nayla tayi ajiyar
zuciya ta ce, "Twiny wani ne." Jidda ta ce, "me wanin ya yi miki?." Tayi shiru bata
ce komai ba. Jidda ta ce, "kin faɗa soyayya ko?."

Nayla ta kalle ta sai hawaye ya sakko mata, Jidda ta riƙe hannunta ta ce, "tun a
Kaduna naga yanayinki ya yi min kama da wacce ta fara soyayya, kuma na tabbatar a
Kano ki ka yi gamo da ƙaddararki. Waye shi? Ya san kina sonsa?."
Kai ta girgiza tana kuka ta ce, "ban san sonsa nake yi ba Twiny, da na san zan fara
sonsa da ban je Kano ba, da na yi zamana tare da Mama da Abiy a gida, wallahi da
bazan je ba." Jidda ta ce, "ƙaddarar kenan ai. Kuma ita soyayya ai ba kai make
sakawa kanka ita ba, Allah ne, kuma yin kanta take yi a zuciyar ɗan adam."

Nayla kuka take yi sosai tana cewa, "ban san ya zanyi ba, kullum cikin kewar
ganinsa nake, kullum cikin son jin muryarsa nake amma ko number wayar sa bani da
ita Twiny. Meyasa soyayya zata yi min haka? Meyasa zan fara son wanda bani da
tabbaci akan zai so ni?. Twiny ko kallo ban ishe shi ba, hasalima maganar minti
ɗaya bata taɓa haɗa mu dashi."

Jidda cikin sanyi ta ce, "Waye shi?." Ɗagowa tayi daga jikin Jidda ta ce, "Ki yi
haƙuri Twinny, zan faɗa miki amma ba yanzu ba." Jidda ta ce, "kina addu'a?."
"Ina yi sosai."
"Ki sake dagewa kina faɗawa Allah damuwarki, in ba alkhairi bane Allah ya cire shi
daga rayuwarki, in kuma alkhairi ne Allah ya daidai ku."

Da jajayen idanun ta ce, "gwara na yi addu'ar Allah ya cire min shi ɗin, dan ko
yana sona bana tunanin Abiy zai amince."
"Me zai hana ya amince?." Nayla ta girgiza kai tana aiyana dan bata san waye bane
shiyasa take faɗar haka.

Jidda ta ce, "yanzu dai tashi mu je mu shiga mataf ki sake faɗawa Allah damuwarki,
zama bai kama mu ba ai Twiny." Nayla ta miƙe tsaye Jidda ma ta miƙe sai Nayla ta
ce, "yau ban ji kina waya da Baby ba." Jidda tayi murmushi ta ce, "yana can Kano
yana neman gida, ya dage sai unguwa ɗaya yake so kuma gidan sai wanda ya yi masa
wai ai kuɗinsa ne, siya zai yi ba haya ba." Nayla tayi dariya ta shiga tayi alwala
Jidda ma tayi suka fita zuwa masallaci.

A ɓangaren Abiy bayan fitar su Nayla kowa ya fita ya zama daga shi sai Mama
ya yi shiru bai ce komai ba. Mama cikin ƙarfin hali ta ce, "ka yarda da abinda
Nayla ta ce maka?."

Abiy ya kalle ta ya ce, "koda abinda ta faɗa yana damunta to tabbas akwai wani abun
da yake damunta bayan wannan." Mama tayi murmushi ta ce, "ka fahimta kenan, nima na
ga haka a tare da ita sosai."
"Amma me kike gani yana damunta?."
"To in na faɗa sai ka ce ba haka ba, gwara nayi shiru kawai." Abiy ya ce, "kina
nufin Hajja?."

Kafin Mama tayi magana ya ce, "kinga mu bar zancen nan, domin bazan amince son
zaman Kano ne ya mayar da Mamana haka ba. Akwai dai abinda yake damunta amma ba
wannan ba." Mama ta yi shiru kawai bata ce komai ba amma ya zama dole ya nemo
damuwar Nayla ko dan ta san meye in zata amfane ta tayi amfani da ita.


••••••••

Narma gabaɗaya ta susuce soyayya tayi mata mugun kamun da bata yi tunani ba, ta
koma wani iri ko yaushe cikin tunani take da faɗuwar gaba. Yanzu gashi in ta kira
Omar ɗin ma baya ɗauka, gabaɗaya sai ta sake shiga damuwa ta yi wani iri kamar ba
ita ba.

Iyayenta duk sun lura da yanayin ta ranar Mum tayi nufin sake tambayarta. Ɗakin ta
ta shiga ta same ta tayi tagumi ta zauna a gefen ta ta ce, "Narma." Narma ta kalli
Mum ta ce, "faɗa min abinda yake damun ki kika zama haka." Narma ta ce, "Mum nima
ban sani ba, amma Ina sonsa sosai Mum, Ina ji in ban aure shi ba zan iya mutuwa."
Mum ta riƙe fuskar ta tace, "Waye shi? A Ina yake?."
Narma ta ce, "A Kano yake, kuma yanzu na samu labarin baya jin daɗi Ina so naje na
duba shi Mum." Mum ta bita da kallo mamaki ta ce, "anya shima yana sonki kuwa?."
"Yana sona sosai Mum, yana sona. Tunda Dad baya nan gobe da safe zan je Kano zuwa
jibi sai na dawo kin ji Mum?." Mum ta bita da kallo cikin tausayin yanayin da take
ciki ta ce, "is okay, sai Najwa ta rakaki."

"No Mum bana so kowa ya ganshi mamaki nake so na baku, ni kaɗai zan je." Mum ta ce,
"shikenan dai. Amma jibi zaki dawo da safe, kuma ban amince da wannan Tiger ɗin
matsayin driver ba. Ki kira drivern Kano su zo su ɗauke ki ki gama abinda zaki yi
ki dawo kin gane?." Jin abinda Mum ta ce sai gabanta ya faɗi, amma da yake an barta
zuwa Kano bata damu ba ta amince da hakan.

"Kar ki damu Daughter, zaki auri wanda ki ke so kin ji?." Kai ta ɗaga cikin farin
ciki Mum tayi hugging ɗinta tana rarrashi kafin ta fita barta. Narma tana fita ta
tashi ta kalli kanta a madubi tana so ta gane itace ko kuwa ba ita bace, domin ta
san ta canja, halayya ta da kamanninta duk sun canja saboda Omar. Mamaki take yi
wai daman zata iya fara soyayya da wanda bai ma san tana yi ba? Soyayyar ma kuma da
mutum irin Omar. Itace fa Narma da maza suke so ta yi musu replying message balle
kuma ta yi magana dasu, amma ga Omar ya haukata ta lokaci ɗaya ta fita daga
hankalin ta.


Ajiyar zuciya ta yi ta lumshe ido tayi tana sake buɗe ido a bayyane ta ce, "Faruk
gani nan zuwa."

Washe gari.

Jirgin ƙarfe takwas ta hau dan haka da wuri ta shiga kano, tana fitowa taga Yahya
wanda ya san da zuwan ta tun a daren jiyaa. Gida aka kai ta daƙyar ta iya haƙura
aka yi sallar azahar ta hau mota ta nufi gidan Didi kai tsaye. Sai da taje ƙofar
gidan sannan ta kira Omar a waya.

A lokacin yana kwance a ɗaki abubuwa sun yi masa yawa, ya kasa gane abinda ya
damunsa gabaɗaya wani irin yanayi ya damu zuciyar shi da gangar jikinsa.

Kiran ta ya shigo wayarsa ya kalli wayar, bai yi saving ba amma ya gama haddace
ƙarshen number ta ko dan kiransa da take yawan yi a kwanakin nan ne bai sani ba.
Kai ya dafe bai ɗauka ba yana kallo har ta katse, wani kiran ya sake shigowa kamar
bazai ɗauka ba sai ya ɗauka.

Narma da ta fara kuka yana ɗauka ta ce, "Faruk Ina ƙofar gidan ku." Da hanzari ya
miƙe zaune ya ce, " ki ka ce?."
"Uhum, Ina ƙofar gidan ku."
"Me kika zo yi gidan mu?."
"Ina kiran ka baka ɗauka shiyasa nazo." Kasa magana ya yi ya tashi ya fita ya kuwa
hango motar ta a ajjiye a gefe, ganin sa sai ta buɗe motar ta fito.

Kallon ta ya yi itama shi take kallo ta ɗauki wayar hannunta sake kiransa ya ɗauka
ta ce, "na ƙaraso ko zaka zo mota mu yi magana?." Omar yace, "meyasa kika zo?."
Narma tayi murmushi kawai bata ce komai ba. Da yake yana kallon ta tana kallonsa
sai ya ce, "ki koma gida zan zo."
"Na san ba zuwa zaka yi ba" ta faɗa tana yanke wayar ta nufo gidan, yana kallon ta
tana tahowa zuciyar sa cike da tsoro da kuma tsantsar mamakin zuwan ta gare shi.

Sai da ta shigo gidan sannan ta zuba masa ido tana kallon sa ko kofta ido bata yi.
Numfashi ta sauke ta kawar da kai gefe tana jin haushin zuciyarta da ta saka ta
fara son wannan mutum mai shegen shariya da nuna ko in kula kamar sa.

Narma ta kalli gidan ta ce, "Sister fa?."
"Bata nan" ya bata amsa babu ɓata lokaci dan ya ƙagu ya ji abinda tazo dashi. Tayi
shiru bata ce komai ba, hakan ya saka ya ce, "Ina jinki, me ya kawo ki Kano har
kika zo nan?. Kar ki ɓata min lokaci ki faɗi abinda yake ranki."

"Babu abinda ya kawo ni Kano, na zo Kano saboda kai kuma saboda kai zan koma."
Narma ta gyara tsayuwa tana kallonsa ta ce, "ban san me zan ce maka ba, ban iya
ɓoye-ɓoye ba haka zalika ban san wani abu tsoro ba indai a kan abinda yake zuciyata
ne. Abinda na sani kawai Ina sonka Faruk! Ina sonka so na Aure!."

*Book 1 free ne*
*Book 2&3 paid ne, akan naira 500 kacal*
*VIP group 1k*
*VIP2 on ArewaBooks.*
*domin biyan kudi ka tuntubi wannan number via WhatsApp*
wa.me/2349030398006
Dm to subscribe yours.

Nana Haleema❤️

*KIRAN RABO.*
#Fitattubiyar2025

©️*Nana Haleema.*

Wattpad@Nanahaleema
Arewabooks@nanahaleema11.

*Book 1*
*P 20.*


Wani irin dumm Omar yaji a zuciyarsa, ya zubawa fuskarta ido yana kallo ba cikin
mamakin da ya gama ɗaure masa jiki. Ya kasa motsi sai kallon idanunta da yake yi
kamar yadda take kallon sa. Narma tayi murmushi tare da hawaye ta ce, "kayi mamaki
ko?." Sai ta girgiza kai ta ce, "nima kwana nake Ina mamaki, kwana nake Ina
tambayar kaina Narma ta ya hakan ya faru. Kullum tambayar kaina nake yi Narma
meyasa ki ka shiga wannan rayuwar, meyasa ki ka fara son wanda bai damu dake ba. Da
wannan tunani nake kwana nake tashi tunda na bar garin nan har yau da nake tsaye a
gabanka."


Narma ta ce, "Ina sonka, Ina sonka!. Ban san me zan ce maka ka yarda ba amma abinda
nake ji a raina kawai Ina so nayi rayuwa da kai a matsayin mijina, ban damu da
abinda zai biyo baya ba, ina so na rayuwa da kai daga nan har a tashi duniya. Ban
damu da abinda kowa zai ce ba, kawai Ina so na dinga duba gefena na ganka a tare
dani ko yaushe, ban damu da kowa ba, ban damu da komai ba. Da zuciyata kawai na
damu, abinda yake cikinta kuma soyayyar ka ce, Ina son ka!" Ta faɗa tana kallon sa
kamar yadda yake kallon ta.

Kai ta girgiza tace, "ba wasa nake yi ba wallahi, zan iya aurenka na zauna da kai a
ko wanne yanayi. Please Faruk! ka amince dani as your life partner, wallahi ina
sonka!" Abinda take faɗa kenan kamar zata zubar da hawaye. Bai yi zato ba, bai yi
tsammani ba, ya tafi duniyar tunani kawai yaji ta kwanta a jikinsa ta rungume shi
sosai tana kuka.

"Innalillahi!" Ya furta a bayyana yana riƙe hannayenta ya janye ta daga jikinsa ya
ce, "Narma!." Kallon sa tayi karo na farko da ya kira sunan ta, bata ɗauka ya san
sunanta ma tunda bata taɓa ji ya faɗa ba sai yanzu. Hasalima bashi da sunan da yake
faɗa mata tunda ba magana yake yi mata ba.
Ganin irin kallon da yake mata ya yi kama da na fushi da fusata sai jikinta ya yi
sanyi. A kausahe Omar ya ce, "Ki bar wannan abin da kike yi, Ko da wasa kar ki sake
kuskuren cewa zaki riƙe ni, bana son wannna shirmen kin fahimta!?" Ya faɗa a fusace
yana nuna ta da yatsa. Kai ta girgiza ta ce, "I'm sorry!."

Omar ya ce, "Sannan ki koma gida, ki bar cikin gidan nan yanzu. Abinda ki ke so
baza ki same shi daga gare ni ba." Narma ta narke fuska ta ce, "Kana nufin baza ka
iya sona ba?." Ya ɗaga mata kai alamun eh kana ya ce, "in ma wasan kwaikwayo kika
shirya ki dakatar dashi bazai yi tasiri a kaina ba. Kar ki sake zuwa cikin gidan
nan ba tare da kin sanar dani ba, bana so na sake ganinki, ki fita daga gidan nan
kafin na nuna miki asalin waye ni."

Kallon sa kawai Narma take yi jin yana ambatar wasan kwaikwayo, yanzu kenan
soyayyar da take yi amsa ce ya ɗauka wasan kwaikwayo ko bayyana masa ɗin da tayi ne
ya zama wasan kwaikwayo?.

Narma murya na cracking ta ce, "Wallahi Ina sonka, wallahi i'm ready to marry you.
Ban damu da abinda zai biyo baya ba indai zan samu cikar burina na amince zan zauna
da kai a ko wannan yanayi."

Kuka take yi mara sauti duk sai ta sake dagula masa lissafi, shi bai san da wacce
makama zai ɗauki maganarta ba dan shi gani yake kamar akwai abinda ta shirya
shiyasa ta zo masa da wannan maganar. In ba haka ba kai tsaye tazo ta furta tana
son shi kamar ba mace ba? Macen ma irin ta mai aji da kuɗi da mulki na siyasa? Ta
ya zai amince da wannan tatsuniyar mai kama da wasan yara?. Kuma shi wata mace bata
taɓa kallon sa ta furta masa wannan kalma ba, bai taɓa tsayawa da wata mace na
adadin mintinan da yake tsaye da Narma ba. Shifa Didi kawai ya sani, itace komai na
sa, Bai taɓa alaƙantuwa da ko wacce mace ba in ba ita ba. Shiyasa yake jin kansa
uncomfortable saboda ita ce mace ta biyu a rayuwarsa da ya samu kusanci da ita, da
ita ya taɓa haɗa jiki, da ita ya taɓa tsayawa suna doguwar magana, da ita ya fara
zama waje ɗaya shida mace, itace ta fara furta masa kalmar so a rayuwarsa. Jin
kansa yake yi yayi nauyi, nauyi yake a zuciyarsa dan yanayin ya zama baƙo a gare
shi.

Da wannan tunanin ya ce, "kina ji.....!" Baya tayi tana kuka kamar wacce ta rasa
hankalinta ta ce, "ba wasa nake maka ba, ba ƙarya nake maka ba, ba yaudararka nake
ba, ba plan na shirya maka ba. Wallahi Ina sonka da gaske ba da wasa nake ba. Dama
ana cire zuciya da na cire zuciyata na nuna maka abinda nake ji a kan ka. From the
moment i saw you in our house fell in love with you, saboda zuciyata bugawa ta
dinga yi da na ganka, na ɗauka kwarjini kayi min a lokacin, amma a yanzu na fahimci
sonka nake yi. I'm not joking about my feeling, it's not a game or drama or
whatever you think about it. I truly love you" ta haɗe hannayenta waje ɗaya ta ce,
"Please believe me" ta faɗa tana zubewa a wajan tana kuka sosai.

Kama ƙugu Omar ya yi yana kallon ta, wai shi Omar wata mace take ɗuke a gabansa
take kuka da sunan tana sonsa. Ya kasa banbance yanayin da yake ciki, tausayinta
yake ji ko haushi take bashi shi kam bai sani ba. Bugawar zuciyarsa yake ji na
tausayinta ne ko na meye dai shima ba sani ba.

Ba ya so Didi ta dawo ta tarar da ita a wannan yanayi, hakan ya ya buɗe baki zai yi
magana amma ya kasa. Shi bai san ya ake rarrashin mace ba har ta daina kuka, bai
taɓa ganin kukan mace a gaban idanun kamar haka ba sai a wannan lokacin, bai san ta
ya zai fara ba kwata-kwata. Ya sake kallon ta ya ce, "ki bar kuka ki tashi daga
wajan nan."

Bata daina kukan ba amma ta miƙe tsaye ya ce, "na ce ki bar yi min kuka bana so!"
Ya faɗa cikin tsawa kaɗan wacce ta sakata haɗɗiye kukan nata. Ya kalle ta ya ce,
"Yanzu ki je gida zan zo zamu yi magana anjima."
A sanyaye ta ce, "ka tabbatar zaka zo?." Ya ɗaga mata kai alamun eh. Ta kalle shi
ta ce, "in ma baka zo ba zan dawo, Ina so naji amsar ka akan abinda na faɗa maka.
Bazan koma Abuja ba sai na ji amsar ka." Bai ce komai ba sai cize bakinsa da ya yi,
ya kalli fuskarta ya ga ta koma ja sannan da gaske ta ɗan rame kaɗan.

Wuce shi tazo yi ta sake kallon shi ya ce, "Faruk ka kawar da duk tunanin da ka ke
yi a kaina, da gaske nake Ina sonka." Kulle ido ya yi ya buɗe sai yaga ta bar wajan
da alama ta fita. Ƙarasowa ya yi ya ganta ta fita a guje ta ƙarasa mota ta shiga ta
ja motar da ƙarfin gaske.

"Wai ni za a yaudara" ya faɗa a bayyane bayan motar ta fice daga layin. Sai kuma
kalamanta suka dinga dawo masa cikin kansa ya kulle ido ya ce, "ni dai ba sonta
nake yi ba, kawai na kasa mantawa da tunanin ta ne. Wannan film ɗin da tazo ta
shirya kuma duk zai ƙare."


"Kai kuma kai da wa ka ke magana kai kaɗai?"Didi ta faɗa tana shigowa gidan.

Da sauri ya buɗe ido ya kalle ta ya daidaita nutsuwarsa kana ya ce, "kin dawo?."
"Eh na dawo" ta bashi amsa tana wucewa bata ce masa komai ba. Daɗi yaji da ta bata
tarar da Narma ba da bai san me zai ce mata ba.

Bai shiga inda take ba ya koma ɗaki yana tunani kala-kala akan abubuwan da suka
faru wanda yake kallon sa kamar a mafarki, tsaki ya yi kawai cikin tunanin da ya
rasa wanne zai kama ya yi.

Didi bata sake ganin sa ba sai bayan sallar magriba ya shigo cikin gidan. Duk da
yadda yaso ɓoye abinda yake ransa sai da Didi ta fahimta. Ta kalle shi sosai ta ce,
"lafiya ka ke kuwa?." Ya girgiza kai ya ce, "lafiya lau." Bata ce komai ba ya zauna
yana kallon ta yana ji kamar ya faɗa mata yaji me zata ce, amma kuma yana ji kamar
ba sai ya faɗa mata ba yaudara ce kawai ake so a shirya masa.

Didi ganin yana kallon ta kuma bai yi magana ba sai ta ce, "ya dai?." Ya yi ajiyar
zuciya ya ce, "Didi a misali namiji kamar ni wacce irin mace ce zata iya cewa tana
sonsa?." Didi da mamaki ta

22 / 28