Advertisements
Chapter 14 Reading TARKO Makircin Hassada by ZAINAB IDRIS MAKAWA BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

TARKO Makircin Hassada by ZAINAB IDRIS MAKAWA

Author :  ZAINAB IDRIS MAKAWA Category :  Complete Novels

Chapter   14 / 61

39K to 42K   out of 180.5K words

ALLAH-AL-MUHAYMIN,,,


Tuki yake a cikin natsuwa, da gwanin ta, sai dai hankalin shi na ga irin yadda zai tunkari mahaifan shi da zancen karin auren da yake son yi,
Musanman mahaifiyar shi mama Ladi wace yake gani tankar tama fi son matar shi Sadiya sama da shi,
Hannun shi ya daga guda ya shafo kyakyawan fuskan shi dashi tare da sauke ajiyan zuciya mai karfi,
Abubakar Buhari Birnin Kebbi kenan kyakyawan matashi mai,tashe ga kyau ga ilimi, ga Naira ,,,,
Daidai kofan gidan su inda malam tsoho kakan shi, da jama,ar sa suke zaune suka daukan karatun marance,
Duk wanda ke gurin a lokacin idon shi naga wanan kyakyawan bakar motar da ta tsaya a kofan gidan dattijon malamin,
Sannu a hankali ya bude motar inda ya sako kafar shi guda waje yana kokarin dauko wayoyin shi daga gaban motar,
Kafar shi kawai ya isawa wanda ke gurin ko waye zai fito a motar mai, ji da kansa ne,
Fitowar shi daga motar gaba daya yasa mutanen dake gurin gane cewa ai Abubakar ne, watau (mai sunan Malam),
Ai nsn take mutane suka gane cewa shi ne kusan gaba daya suka tashi zuwa mashi murnan da barka da zuwa,,,
Malam tsoho wanda ke daga zaune yana biya wa wani tsohon bafillace karatu,
Sai murmushi yake yi yana gyada kai don jin dadin ganin yadda jikan nashi ya koma a lokaci guda,
Direct daga gurin da masu taron shi suke, gurin tsohon ya nufa,
Takalman da ke a kafan shi yake kokarin cirewa don girmamawa,
Wanan ya,na daya daga cikin dabi,un duk, wani yaron gidan malam Manya,
Babba da karami dole ne idan zaka wuce ta gurin ka cire takalmin ka,
Cikin jin dadin ganin jikan nashi bai yarda tarbiyan gida ba,
Yake dan yake fararen hakoran shi wanda akasarin jikokin gida duk shi suka biyo, da fararen hakora, da kyau,
Abubakar kai ne tafe babu labatin zuwan ka a yau din,?
Murmushi yayi ya cewa kakan nashi nayi marmarin ganin ka ne malam shi yasa na taso don in duba ka,
Nan ya samu gefen tabarman da malam din yake, zaune,
Gaisawa sukayi a cikin girmamawa, inda malam yace ai sauri a shiga gida wurin maman Wadda a karbo ma Abubakar ruwa da fura,mai sanyi,
Ga mamakinbmalam tsoho sai ga Abubakar ya sha kusan rabin kufin furan da aka kawo mashi,
Wani sabon gaisawa suka kara shiga yi inda yake tambayan shi lafiyan mai dakin shi da kuma gurin aikin shi,,,

****** ****** ******
A can cikin gida kuwa labarin zuwan Abubakar ya iske mama Ladi wace duk ta kasa boye farin cikin ta afili,
Sai, rawan jiki ta,keyi tana cewa a yi sauri a aje a anso mata dan drinks ta bashi da kuma sakon abin miya wanda zata dafa mai abinci,
Duk da idan yazo daga ko wani sashe na gidan a na kawo mashi abinci, har izuwa ranan da ya tashi komawa,
Amma duk wanan bai sa mama Ladi ta daina dafa mai abinci da kanta,ba idan yazo,
Da sauri ta tura yaro gidan su Sadiya matar shi gurin Hajja don a sanar da ita,
Hajja tabawa yaron Naira hamsi wai ya sha Sweet da shi idan ya koma,
Yaro ya koma da murnan shi gida ya na, farin ciki,
Bai nuwa mama Ladi Naira hamsin din ba don yasan idan ya nuna mata zata iya cewa suraba shi da ita,
Sai bayan Sallah isha,i Abubakar ya shigo cikin gidan don ya gaisa da mahaifiyar shi da sauran, mutanen gidan,
Nan fa yai ido biyu da jerin kwanonin abincin da aka aiko mai da shi daga kowa shiya na gidan
A hankali ya samu gefen tabarman da aka shimfida mai,a tsakar dakin na mama,Ladi ya ksi zaune,
Cikin murna da farin cikin ganin dan nata take cewa,
Mai sunan malam kana tafe shine baka sanar da kowa cewa kana saman hanya ba,
Sai dai kawai mu ka gan ka kwatsam ba tsanmanin ka a yau din,
Murmushi yayi don yasan cewa duk a lokacin da mama ta ganshi tana cikin farin ciki da jin dadi,
Shima haka yana jin dadin kasan cewa mahaifiyar tashi sosai duk yasan cewa wasu daga cikin halaiyan mama tun suna yara baida dadi sam,
Tambayar shi mama tayi labarin matar shi Sadiya,
Tana cewa har yanzu dai shiru a gidan ka mai sunan malam ?
A hankali ya dago kai ya dube mahaifiyar wace ta tsura mashi ido don jin ansar da zai bata,,
Yadda ya kalli mama sai ya bata tausayi don ko bai yi magana ba tasan cewa ba wani ansa gamsasshe daga bakin shi,
Murmushi ya danyi tare da cewa mama har yanzu dai muna baran adduan ku ,
Akan Allah ya kawao muna mai albarka insha Allah,
Daga haka Abubakar yajawo daya daga cikin kulolin abincinbdake a gaban shi wanda yasan cewa,shi aka ajewa wanan abincin,
Mama dake gefe tace cikin sauri a,a aida ka dakata har a karasa abincin da nasa Samira ta dafa maka,,,
No, mama ki barshi kawai wanan din ma ai is Ok,
Kawai dai dama ina son cin abincin gida ne wanda nai missing dadewa,
Kai idon mama taga ko wani kulane yajawo sai idon ta ya sauka akan kulan da mama Saratu ta aiko mai dasu,,,
Kai, mai sunan malam ga kuloli da yawa masu dadi zakaci wanan ?
Yace cikin kai hannu ga kulan da ya bude din yana cewa,
Wanan din ma ai zai yi mama bari kawai inci, don bada yawa zanci ba,
Tuwon dawa, surfafe ne, da miyar karkashi danye, wanda yaji nama da man shanu,
Fuska mama ta daure don jin haushin daukan kulan sashen Baba buhari da yayi,
Daga sunan kadan zaici sai ga Abubakar ya buge fiye da rabin kulan abincin,
Ganin irin yadda ya kwashi wanan girkin da mama ke dauka mara dadi, agare ta,
Wanan girkin yaiwa Abubakar dadi sosai don rabo da yaci irin wanan girkin tun yana yawan zuwa gida hutu daga makaranta
Wayar shi ce tai kuka, wanda hakan ce ta da katar dashi daga cin abincin da yake yi,,
Yadaga don ganin mai kiran nashi a wanan lokacin da yake kwasan girki mai dadi,
Salawatu ce ke kiran shi a lokacin don haka ya dauki wayan a cikin murmusawa,
Mikewa yayi tare da kallon gurin da mama take zaune tana mai kallon kurulla,
Tun a gaban ta ya dauki, wayan sai dai a cikin harshen turanci yake magana,,
Don haka mama wace bataji may yake cewa ba sai bin bayan shi tayi da kallo kawai,
Amna dai gabanta ya fadi don hasashen da zuciyar ta yai mata akancewa Abubakar da wata mace yake zance, fa,
Idan ko hakane gaskiya za a dauko wani sabon zance ke nan agidan,
Don tasan cewa da yawa daga cikin yan uwanshi dama uban,nen su zasuyi farin ciki da wanan abin,,,,

****** ****** ******
Zaune take da tarin littatafai a gaban ta tana dubawa,
Kanta yana dan saye da farin gyale wanda ta dan yane fuskanta da shi,
Bitan littafan ta takeyi saboda , jarrabawan su da ke kara gabatowa,
Don haka tai matukar mai da hankalinta akan karatun ta yanzu,
Shigowan shi kenan gidan ya hango Meena zaune gurin da take bitan karatun ta,
Ya fi tsayin yan mintuna tsaye agurin yana kallon wanan yarinyar,
Ko kifta, idanuwansa ba ya yi farat daya yaji son ta da kaunar ta sun shige mai zuciya,
Kai tsaye yaji zuciyan shi na bashi shawaran ya tunkare ta don ya ji ita ko wacece,
Kamar kuma ya juya zuwa inda zashi bangaren yayan nashi sai ya ji sam bazai iya ba,
Sabosa haka gadan gadan ya cike da karfin zuciya ya nufi inda take,
Meen wace take duke ,
Zuciyan ta ya bata cewa tankar akwai wani mutum tsaye a kanta a lokacin,
Daidai wanan lokacin ne ta tsinkayi muryan shi yana mata sallama,
A dan firgice ta kara dagowa da sauri tana kallon shi
Daga gurin da yake a tsaye ya zura hannayen shi duk biyu acikin aljihun wandon shi,
Idon shi a cikin nata yake cewa kiyi hakkuri pls don naga kamar nadakatar dake daga karatun ki,,
Cikin maganar da yake yi ne ya tako izuwa gare ta,
Gap da inda take zaune ya karaso, inda har Meena zata iya dan jin hucin shi,
Mamakine kwarai ya kama Meenat din don haka ta kasa ko da wani kwakwaran motsi don fargaba,
Don dai ita asanin ta ga bakin dake zuwa gidan uncle din ta ba,
Ganin kamar ba zai iya dakatawa a inda yake ba yasa Meena tai saurin mikewa don barin gurin,
Muryan shi taji cikin wani irin yanayi yana cewa
Kiwa Allah da son manzon tsira ki dan bani minti biyu pls,
Cikin rintse ido da jin abinda bakon yace ta tsaya agurin da take,
Muryan shi takara ji a karo na biyu yana cewa don Allah a nan gidan kike da zama ne ?
Da sauri Meena ta dago kai ta dube shi ta ce, a hankali,
"Eh,
Ya kara gyara tsayin shi yace to amma ban sankiba beauty ?
Beauty kuma inji Meena ?
Cikin wani irin daga gira irin na mazauna kasan turai ya ce yes beauty, mana,
Kin ko gan ki kuwa, takar ke ce kika halitta kan ki,
A fusace Meena dake zaune tun shigowar shi ta mike tsaye,
Fuskan ta a daure tankar bata taba dariya ba a rayuwanta,
Rayuwan ta yai mata bakikirin a take idanuwan Meena suka kada, zuwa ja,
do yazuba mata still yana kallon irin yanayin da ta sauya atake,
Cikin dakewan murya Meena tace wani ne ya aiko ka ka tambaye ni, ko ?
Cikin murmushi yace mata kinga nayi kama da wanda za,a aiko ?
Kanta kawar gefe guda daniyar ta dan gezashi ta wuce abinta,
Gyalen kan tane ya dan silalo daga saman kanta zuwa kafadar ta,
A take gashin kan ta dake daure da wani ribbon ya baiyyana a fili
Wani iri ya na yi ya shiga cikin dan lokaci kadan,
Sai tsayawa ya yi yana mai kara kallon wanan yar matashiyàr budurwa da idon shi ya ga nan mai,
Ganin zata wuce ne ya iya bude bakin shi yace ,,,,,,
Iam ALI-ABBAS, MAHMUD, KA,OJE,
Cikin wani irin kallo Meena ke kallon shi don jin Mahmud din daya ambata,
Tasan cewa daga family din nasu yafito saboda su fulanin Ka,oje ne, ma,zauna sokoto,
Daga haka Meena ta dan gwauta shi ta wuce abin,ta
Kamshin turaren jikin ta da ta shafa, black s,s ya shaka,
A hankali ya dan lumshe, idon shi, don kamshin yai mai dadi so sai, har cikin ran shi,
Part din da take na Anty amarya can tanufa inda ta,samu babu kowa a,dakin nasu na yara,,
Sunan Ali,Abbas take nanatawa a zuciyan ta tankar mai mamakin sunan,
Hayaniya taji a falo hakan ne ya bata tabbacin cewa masu gidan sun dawo ke nan daga unguwar da suka fita,
Sai kuma ihun da taji duk ya gauraye falon da gidan alokaci guda,

Fitowa Meena tayi don tai masu sannu da zuwa da kuma ganin may sukewa ihu haka ?
Daidai gurin da ta tashi a nan wanan bakon yake zaune ga dan hankicin ta da tabari da sauran takardun ta a hannun shi,
Ido suka hada daga fitowan ta wanda hakan yai daidai da kai hankicin ta a hancin shi yana dan shaka tankar mai mura,
Wani irin shu,umin murmushi ya sauke mata a lokaci guda,
Wanda tai tankar bata fahince shi ba sai cewa tayi a kasalance mummy sannun ku da dawowa,
Mummy wace ke ta murnan ganin dan kanin nata a lokacin sun kaure da harshen fulanci,
Tankar ba shi ne dan gayen da zaka ce banda turanci bai iya komai ba abakin sa,
Mummy tace yawa, Meena sannu ko don Allah ki taimaka ki hadowa bakona drinks da abinci pls,
Hannu ya daga cikin muryan nan nashi maikama da sallo ya ce,
No ki barshi kawai ki bani cool water in dan sha pls, ?
A hankali Meena ta juya zuwa dauko mai ruwan sanyin da yace,
Don keta ruwa masu mugun sanyi har sun fara alamar kankara Meena ta dauko mai a cikin freezer su,
Tai hakane don taga iyakar turai da karyan sanyi,
Abin mamaki cikin rashin damu taga ya balle murfin goran ruwan,
Kai ya kafa ya fara kwankwada har saida ya kai karshen goran yan kankaru kawai suka rage a cikin goran,
Sannan ya aje goran a saman table din dake gaban shi, kusa da littafin Meenat din,,,,,
Ànty amarya ce ta fara mikewa don barin falon inda Meenatu ta mike don tabi bayan ta,
Wata yar sassanyar ajiyan zuciya taji Ali,Abbas ya sauke, sanan yace ina kuka samu wanan Beauty, Queen din a gidan ku,
Gurin da Meenatu take mummy ta dan kalla inda tace a cikin fulanci kar dai ka fara kace kana son ta don kasan diyan gwago Buriji, nan na jiran ka,
A take yanayin fuskan shi ya sake inda yake cewa, na fada maku, bana son wanan zancen sam,
Mummy tana dariya take ce mashi ai sai, dai yayi hakkuri kawai don duk family din su ba wanda bai san da zancen ba,
A dakin Anty amarya Meena ta samay ta tana cire dankunne a kunen ta,
A lokacin ta dan waigo tana kallon Meena tace kinga bakon turai ko ?
Brother din Asma,u ne a England ya ke zaune yana karatu bayan ya gama ya fara aiki a can,
Yanzu ya dawo nan Nigeria ne don gwaunati tana bukatan yai mata aiki,
Allah sarki inji Meena batare da tacewa uwar dakin nata komai ba,
Ta juya abin ta da nufin komawa dakin su da suke kwana,
Yar wayan ta Nokia wacce uncle din ta ya saya mata, don kiran mutanen gida,
Abdulhameed ne ya kirata a lokacin don haka sai bata karasa fita daga dakin ba ,
Nan ta tsaya a kofan dakin tana ansa wayan ce mata yayi ta fito gashi a waje don zai yi tafiya zuwa Lagos gurin saro kaya,
Komawa Meenan tayi dakin Anty a gaban mirror ta dan gyara fuskan ta sama sama,
A falo ta kara samun wa yan nan yan uwan junan watau mummy da brother din ta,
A cikin yanayin takun ta mai kama da na yanga, ta dan fito daga cikin gida don ta ratsa su, gurin da suke zaune a falon,
Sannu, kawai tai masu inda ta sa kai zuwa hanyar fita waje,,
Bayan ta, Ali, Abba's yabi da kallo inda ya kara ganin halittan ta da kyau, abin sai da yai touching din zuciyar shi,
Saboda irin yarinyar da yadade yana cigiyar samun irinta ke nan a kasar hausa,
Abdulhameed ta hango a yar farfajiyar gidan uncle din nata
Yana zaune a bayan motar , jikin shi saye da wasu kananan kaya, sai jacket da ya dora daga sama, wanda hakan ya nuna mata a cikin shirin tafiya yake
Hannun shi rike da keys din motar shi yana kadawa, a hankali,
A cikin irin takun nata ta karaso gurin da yake a kunyace
Tai masa sallama,
Wani irin kallon na can kasan ido yai mata yana mai sake murmushi a fuskan shi,
Sannu da zuwa, Dan uwa,
Hmm yar uwa sai kika gan ni yau a wanan lokacin kuma ko?
Murmushi Meenatu tadan sauke a daidai lokacin da ta dan kwanta kadan a bayan motan,
Kasan hakan ai daurowa ce da ban ganka a yanzu din ba, don nasan baku da lokaci a cikin irin time din nan,
Murmushi ya yi don jin abin da ta ce a lokacin don yasan cewa gaskiya ta fadi basu da time sam da rana sai dai da dare kawai,
Yace wlh kaya aka shigo muna dasu daga waje kuma wanan ne farkon shigowa dasu kasan,
Don hakane muke son zuwa mu kwaso su don mu samu su shiga da wuri,
A hankali tace Allah ya taimaka Allah ya bada sa,a da rabo na alheri,
Ameen ya Allah yar uwa,ta nagode kwarai da wanan addu,an da ki kai min ,
Amma insha Allah idan nadawo za mu shiga gurin hajiya ta don su gan ki,
Murmushi Meenat tayi gami da dafe bakin ta da sauri tadan dago kai ta kalle shi ida sukayi ido cikin ido,
Meenat tai saurin cewa rufa min asiri don Allah ai bazan iya zuwa gidan ku yanzu ba dan uwa na,
A, haba dai saboda may, ?
Meena, ta dan Allah mu ma bar wanan zancen kawai, don dai gaskiya ba zan iya zuwa ba,
Abdulhameed ya ji dadi har a cikin ran shi saboda irin wanan halin ya ke kara alfahari da Meena din ,

14 / 61