Advertisements
Chapter 2 Reading TARKO Makircin Hassada by ZAINAB IDRIS MAKAWA BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

TARKO Makircin Hassada by ZAINAB IDRIS MAKAWA

Author :  ZAINAB IDRIS MAKAWA Category :  Complete Novels

Chapter   2 / 61

3K to 6K   out of 180.5K words

ango,
Sai dai rashin samun wadattacen lokaci da ango bai yi ba yasa bukin ya dan rage armashi,
Amma duk da hakan ba laifi, don, yan uwa da abokan arziki sun nuna farin cikkin su da wanan bukin gida ya cika sosai a ranan,
Bayan buki da kwana biyu ango da amarya suka kama hanyar Lagos can inda Abubakar yake, aikin sa yake kuma zaune,,
Sai dai da amarya zata bar gidan ma haifiyan ta uwar nata taba wani ruwa tare da yin hayaki, a cewar ta na neman tsari ne, da samun sa,an daki,
Gidane ma daidaici suke a ciki, acikin rufin asiri da wadata,
Zama sukeyi na,rufawa juna, asiri da mutun tawa a tsakanin su,
Sai dai matsala daya shine Sadiya bata da kuzarin aiki, sam, don haka bata damu da wai dafa abinci ba,,
Zata iya kai wani lokaci tana barcin abinta ba tare da ta dafa ko mai taci ba,,
Gyaran gida kusan weekend take yin shi don ita sam kazanta bai damay taba,
Don a gida neman kudi ne kawai a gaban su shine tun safe za,ai tayi batare da an yi wani girki ko gyaran gida ba ,
Saukin al,amarin babu yan uwan Abubakar da suke ziyaran su a lokacin,
Wanan shine, shimfidar labari da zan bayar,,,,


Mama ladi, ce zaune a tare da aminiyar ta, suna dan tataunawa,
Mama, Ladi ta marairai ce kai tana fadawa aminiyar ta, da muwar ta,
Sai da Hajja ta gama sauraron maganar da Aminiyar ta tazo mata da shi,,,
Hajja ta ce tau,Ladi yanzu yarda da mutum abin tsoro ne,
Da sauri Hajja ta dago kai cikin nuna mamakin da jin abinda Hajja tace,
Cikin mamaki tace Hajja ashe yanzu har akwai wani abinda zaki ji shakkun gaya min a tsakanin mu,
Ba hakana ba,ne Ladi abin ne bai son yawan surutu kuma,siri ne mai girma a tsakani,
Kinga ke nan ba zanso har wani yaji wanan zancen ba gaskiya,
Kara matsowa Ladi tayi kusa da Hajja don ganewan da tayi cewa, maganan da zasu yi, mai, muhin mancine sosai
Hajja tace wa Ladi, ki bari zuwa jibi in,Allah ya kai mu akwai inda zan kai ki,
Da murna ladi tabar gidan don farin cikin ta kusa samun mafita,
Buhari yana a majalissan malam mahaifin shi ya hango, dawowan maidakin nashi acikin zafin rana,
Cikin rayuwan shi yake masifa da ita yana fadan rashin zaman gida irin na Ladi,
Amma tana iso gurin da suke sai cewa tayi a gaishe ku,
Yan kadan ne suka karba mata, da ingwaiyya Ladi ke dawo,?
Ta ansa da fadar Awo, Allah ya maisan da ni lafiya,
Daga haka ta,shigewan ta ciki, inda malam da dan shi buhari, takaicin ya hana,su cewa kala,

Acikin gida ma, haka mata suka dinga gaida Ladi da dawo,
Idan sunce mata Aho, yaya,
Ita ko sai cewa takeyi ingwaiyya, agaishe ku, dai,,,
Tas, ta samu shiyan ta don Meena ta gyara mata shi tas,,
Amma halin kiyayya irin na Ladi sai cewa tayi wai Meenat, bata zuba mata ruwa a randar kasar ta ba,
Tun daga inda take take, kwadawa yarinyar kira,
A gigice Meenat tafito tana kokarin daura dan kwalin atamfar dake kan ta,
Cikin masifa take cewa wa kike son ya cika radan ruwan da naga baki debo ruwa ke, zuba min ba?
Meenat ta bude baki da niyar tayi magana amma kuma sai kawai ta kasa saboda idon ta da ya kawo ruwa,
Salati Ladi tasa a lokaci guda tana tafa hannayen ta, cikin mamaki,
Meena ko uwar ki ta hana ki min dan aikin da kike tayani ne kuma,
Cikin mamaki Meenat tadaga kai ta dan kali Ladi don jin cewan da tayi wai aikin da tasha dan ka dan ne,,,
Hakan ya ne yasa Meenat jin wani irin gululu a zuciyan,
Ita dai gaskiya ta gaji da wanan kawaicin da ina ke sa tanayi wa mama Ladi
Wace kuma duk cin mutum cin ta a kan sune yake karewa ko yau she,
Saboda mugun tsanar da mama,Ladi takewa mahaifiyar abin har ya shafi diyan ta,
Wanda hakan ba karamin batawa Meenat rayuwa yakeyi ba,
Don haka azuciyar ta sha alwashin cewa daga yau zata san abin yi
akan mama, Ladi,,,,,,,,
Wacce duk wanan aikin da ta sha tun safe bata gani ba, sai ko karin cima uwar ta fuska takeyi,,,,,,


ZEE MAKAWA YELWA
,🕸🕸TARKO🕸🕸
🕸🕸🕸🕸🕸🕸
3⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA
YAURI


Bayan yan bayanin da malamin su yai masu amma ita mama Ladi, ba wai ta fahinci abinda yake nufi bane,
Wani kwalla mai marfi wanda ita mama Ladi din take gani a cikin jeran dakin Hajja tasan shi,
Shine malamin ya rufe da wani bakin kyalle yace su dauka zuwa gida ,
Amma kada su bude sai bayan kwana arba,in cif sanan ta bude,
Daga wananranan da zata bude kwallan duk kukan abinda taji aciki shine zata dinga yankawa,
Dajin an ambaci yanka gaban mama Ladi ya yanke ya fadi ras,
Saboda jin an abaci yanka acikin al,amarin, don dai ita dai a iya sanin ta yanka wani abune na mushirikanci,,,
Tana son tambaya amma Hajja ta tattare da godiya gurin malamin,
Haka suka biyo hanya hajja nata koda malam da aikin shi
Tana kuma yiwa mama Ladi barka da samun wanan abin acikin sauki,

Da yake dare ne mama Ladi bata samu wani matsala ba gurin shiga da kwallan gida,
Can ta samu karkashin gadon ta tatura shi ta boye batare da ta bude ba kamar yadda malam ya umurce ta dayi,
Sai dai tun ranan tasa yarq suka debo mata duwatsu, ta boye.
A kullun tana kidayawa guda guda tana jefawa don gudun mantuwa,,
Sai dai duk abinda take yi sam mama Ladi bata yarda tayi nisa da dakin ta ,
Don gudun kada kaddara ya kai wani gurin kwallah ya bude ya bata mata tsari,,
Wanan kafa kafan da takeyi yasa mutanen gidan gane cewa mama ladi tana acikkin wani yanayi a yan kwanakin nan,

Rana akeyi yau kamar kullun don yanayin garin ke nan da yawan zafin rana,
Daga makarantar boko suke tafe kowacen su sauri takeyi tasamu ta isa gida,
Makarantar jeka,ka dawo ta yan mata dake Badariya suke zuwa watau Salamatu Husaini,
Dake cikin tsohon makarantar Abdullahi Fodio,
Isar su gida acikin gajiya yasa,su kowace ta nufi sashen su,
Meenat na isa, ta samu ta cire takalmin sadal din dake a kafan ta tun a waje ta fara cire hijab din ta,
Saboda bata,son shiga dakin su da kayan makaranta ajikin ta,
Acewan ta, rigar yakan yi warin jemage ne dake makarantan su,
Daga ita sai unders din ta tashige daki inda ta dauro zani zuwa wurin wanka,,
Wani yaro ne cikin masu daukan karatu, yake ce mata wai mama Ladi tana kiran ta,
Kamar bata ji shi ba har zata wuce yaron dan aiken mama ladin,
Saboda wani irin mugun haushi da taji a cikin ranta mutum yadawo ko sallah bai yi ba za,a fara sashi aiki, ke nan,
Muryan mahaifiyarta ce taji tana cewa cikin irin sanyin maganar ta,
Dake fa ake magana yar mama, kin yi kamar bakiji shi ba,
Baki gaba Meenat tace, mama kofa sallah banyi banci abinci ba,
Kai mahaifiyar ta takada kawai don takaici, bazaki je kiji ko may take kiranki akai ba,
Muryan Baba Samaila ne sukaji, a bayan su yana cewa ,
Yanzu fa naga shigowar su daga makaranta bata ko ci abinci baza ki ce yarinya ta je don dole,
Ko ta tafi can wani abinci Ladi zata bata, halan, ?
A,a malam wai gani nayi dama kada yaya tace kuma ba,a tura ta ba,
Anki tura din ,
Ba tana da yara a dakin taba wai taje ma na duk abinda Amina kayi mata tasu suyi mata,
Walle na gaji da,wagga irin bakar dabi,a
Yaro ya dawo ma baida hutu shin,?
Duk yadda akayi haka dan aiken mama Ladi ya zayyana mata zancen,
Inda ba bata lokaci ta nufi sashin na Baba samaila,
Agaida may "ya shin,
Ni ta,zaka gwada ma haihuwa shin?
Au ashe ke haihu Ladi an?
Banga alama ba tunda banga kina gwada masu rashin mutunci kaman wadda kika wa sauran diyan mutane ba,?
O Lailai Samaila yanzu akan "ya ka ta fari ka,kak fada shi, ?
Tai ka jika ta kasha tunda kumya bai i,shi ijjiyanka ba,
Banduk jikata amma yanzu kam da dawon ta da makaranta ko abinci da sallah ba ta yi ba
Kika zuwa kice wai atai zuwa yi maki aikin wahala,
Mamaki sosai ya kama mama Ladi ganin cewa yau wai itace ke magana ana mayar mata da ansa,
Don ita a tunanen ta,duk ta shanye mutanen gidan gabadayan su,
Shiyasa take taka kowa yadda taso,
Abinda bata sani ba shine duk gidan kawici ake mata akan mijin ta baba Buhari,
Dattijon kirki mai mutunci da zumunci da sanin ya kamata,
"Dan kowa agidan tankar nashi yake dauka bai banbanta tsakani sam,,
Wanan dalili ya sa dadewa baba samaila yake wa mama Ladi halar ci akan "yar shi Amina wace mutanen gidan dana shiya suke cewa Meenat,,,,
Juyawa mama Ladi tayi da suraitai abakin ta, zuwa sashen su,
Yar da suka dawo tare da su Meenat daga makaranta,
Tana zaune saman kofar dakin su tana juya shinkafa da miyan manja da nama,
Gefe guda cup ne wanda ta debo, fura mai sanyi aciki ga goran dake dauke da ruwan sanyi,
Tambayar mama takeyi akan yaya akayi don jira takeyi mama ta taso Meena a gaba tazo ta ci mata mutunci,
Ke rufen min baki kin ke ji ya,
Gani da tayi cewa rayuwar mahaifiyar ta ya baci sosai yasa ta ja bakin ta tai shiru,,
Sai dai tanayi tana dan daga kai tana duban hanya shigowa ko zata ga Meenata shigo, sashen nasu,

Daga inda malam yake zaune yaga fitowan Meenat, da wuri zuwa cikin daukan karatu,
Malam yai mamaki kwarai don ganin cewa yau jikan nashi ta fito daukan karatu dawuri ba tare da ta makara ba,
Duk da suna da manyan dakuma wa yanda suka dan dara,su amma hakan bai hana wanan yariyar cinma manyasu ba , ga karatu,
Hakan ke kara,sa kakan nasu najin ta ajikin shi sosai,
Gashi kuma bawai wani dadi mahaifanta ke ji acikin gidan ba,
Hakan ko ya samu asaline na rashin dan uwan haihuwa da shi baba samailan baida acikin gidan,
Gwago hafsi ce kuma tayi aure ita a garin Kalgo bako a cikin gari ba sai in ta shigo gari,,
Baba samaila ba karamin jurumi bane don har aikin soja yatafi, amma bai wani dadeba ya bari saboda mahaifin shi da bayason wanan aikin,
Yanzu mota ya saye yana shiga kauyu ka yana dauko itace da sauran kayayyaki yana shigowa dasu gari,,,,
Amina yau yaya ankayi kin kafito da,wuri ko uwar taki bata nan ne,
Malam ke tambayar ta acikin wasan jika da kaka da yakan mata wani lokaci,
Murmushi tayi tadan noke kan ta acikin hijabin ta ba tare da tabashi ansa ba,
Sai can tace baba na yace min intahowa na makaranta,
Wai daga yau ya yanke aikin nan, da nika zuwa yi wa mama kullun, don kada a wuce ni ga karatu,,
Murmushi malam yayi kawai don yadade da sanin cewa wata rana hakan zai faru,
Don dai irin yadda mama take nuwa bai dace ba sam saboda babu adalci acikin tafiyan,

Baba Buhari ne ya shigo gida dauke da buta a hannun shi, da alamar ruwa yake so acikin butar,
Gurin randar ruwa ya nufa daniyar diban ruwa, don ya zuba a butar,
Muryan mama Ladi ce ta bayan shi take cewa yau kan ai mai diya ya hana diya tai diban ruwa,
Yau samaila ya gwada min baida kunya don ko nauyi bai ji ya kalli ijjiya ta yaka ce wa wai diya tai tadawo ko hutawa batayi zan damay ta da bakin kira,
Sororo yayi tsaye da buta a hannun shi yana sauraren ta,
Saida ya tabbatar tagama ya nunata da hannun shi dake dauke da mudar radan ruwan yace,
Ke, Ladi ke Ladi, Walle kiji tsoron Allah, daga dai yau Samaila yai magana kan Amina kikacewa wai ya gwada,maki rashin kunya, yai fada kan "ya tai ta fari,
Walle Ladi an,kiji tsoron Allah ga al,amarinki,
Duk yadda mutanen ga ka kauda kan su ga al,amarin diyar su, bai,ishe keep ba, sai keyi masu kazafi
To, to ta ka shigan ma dan uwaka ke nan ko don ba yau ba nasan bakason abinda Yarinya taka min,
Dauri ai sai ka hwada min in sani ko,
To ai yanzu ke sani ko ?
To katai zuwa inda zaka samu ruwan zuba ma butan ka tunda bata taho ta debo muna ba,
Wanan maganan shi ne sanadin daina duk wani wahala da meenat keyiwa mama Ladi,
Sai kuma kiyayya abin ya koma masu sosai don sam daga mahaifin da matar har yaran su ba shiri tsakanin su da sahen mama Ladi
Dan dama dama gurin ita kishiyar mama din baraka wace babu ruwan ta da zancen su,

A gajiye yadawo daga gurin aiki, tare da ledoji manya a hannayen shi,
Da kyat ya samu ya shigo gidan nashi don nauyin kayan da ya dauko,
A falo take zaune daga ita sai yar shimi a jikin ta sai littafin dake hannun ta tana karan tawa kanta babu hula ko dan kwali,
Da sallama ya shigo gidan,
Ita ma Sadiya sau guda ta daga kai ta kalle shi takawar izuwa abinda takeyi,
Batare da ta kara daga kai ko ta mike ta taya shi karban kayan ba tace mai sannu da dawo,
Umhumm ya ce mata cikin rashin sakin fuska ko walwala,,
Kayan ya aje a gaban ta saman tebur ya wuce direct gurin fridge,
Goran ruwa mai sanyi yafito dashi daga cikin fridge din,
Kai ya kafa har sai da ya shanye ruwan, sanan ya cilla goran ta bayan shi,
Shi da kan shi yadawo gurin kayan da ya,aje yafara fitar da su guda guda,
Duk hakan baisa ta aje littafin ba ta dube shi saima kara mike kafa da tayi tana kadawa,
Sadiya, Abubakar ya kira sunan ta acikin nuna son ta maida hankalinta zuwa gare shi,
Littafin ta aza saman cinyan ta tadan dawo da diban ta gare shi,
Hankali ta ga ba daya ya koma gare shi, don son jin may zaice, mata,
Da farko kayan siturun da ya,sayo mata,su ya fara turawa gaban ta
Dago kai tayi tana son jin karin bayani daga bakin maigidan nata,
Wanan kayan naki ne ki dinga amfani dasu, pls, sai kuma wa yan nan kayan
Ya nuna mata kayan leda kayan abincine ki kai su duk inda ya dace a aje ko wani daga cikin su,
Daga haka Abubakar ya mike zuwa dakin kwanan su don yadan watsa ruwa ajikin shi,

Abubakar bai fitoba sai gab da sallah magrib don ahi mutum ne mai son yin sallah a cikin jam,i kamar yadda sunna yai ko yi,,,,,
A gurin da ya bar kayan a gurin ya samay su kamar yadda ya barsu, dazun,
Mamaki sosai ya kamashi don shi a iya sanin shi agida idan mahaifan su ,sun shigo da kaya
Tun daga nesa mace zata zo cikin ladabi takarbi leda ko kayan, akai su inda ya dace,
Amma shi sai gashi yau , ya sayowa matar shi abu anma ta nuna mai halin ko in kula, da su,
Agurin da ya barsu a gurin ya samay su kamar dazun,
Shim ko don bata san kudin da ya kashe bane akan sayayyan da ta wulakanta,
Wata zuciya tace, mai kawai rashin da,a da tarbiyan kwarai ne bata samu ba,
Sai bayan ya je sallah ne ya dawo, ya kwashi kayan abinci zuwa inda ya dace akai ko, wani,,,
Daga wanan ranan ne, ya sa wa rayuwan shi hakkuri akan duk wani al,amari na zaman takewan wasu,
Abubakar mutum ne mai kwazo agurin aikin shi don shi dama irin mutanen nan talent ne,
Sosai Yai fice gurin manyan ma,aikatan su wanda hakan yasa yana halar ta seminar kala kala akasan har kasa shen, waje,
Don haka kudi ke shigo mai ta hanyoyi da dama daga gurin aikin,,,,,,

ZEEE MAKAWA YELWA
🕸🕸🕸TARKO🕸🕸🕸
🕸🕸🕸🕸🕸🕸🕸
4⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

2 / 61