Advertisements
Chapter 5 Reading TARKO Makircin Hassada by ZAINAB IDRIS MAKAWA BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

TARKO Makircin Hassada by ZAINAB IDRIS MAKAWA

Author :  ZAINAB IDRIS MAKAWA Category :  Complete Novels

Chapter   5 / 61

12K to 15K   out of 180.5K words

Baba Buhari yai matukar tashi, a take idon shi ya fara silalo da hawaye,
Nan take gaba dayan su suka shiga karanto addu,o,i iri iri don neman tsari a gurin ubangiji mu,
Sannu a hankali ya koma barcin da yake yi sai dai wanan karon numfashin shi yana sauka,a hankali ba kamar farko ba,
Ganin ya samu barci kuma alamar da yar sauki a zancen
Yasa malam yasa Baba Buhari ya debo mai garwashin wuta a waje,
Cikin sauri baba ya nufi gurin samo garwashin, wutan da aka umurce shi,
Wani dan kulli malam y bude ya debo hayaki aciki,
Nan aka zuba duk da barci yakeyi amm sai da ya dinga sake atishawa, mai karfi har sau biyu,
Malam manya da Baba Buhari dake gefe suka, sauke ajiya zuciya a hankali,
Sai a lokacin malam ya juyo inda Baba Buhari yake a tsaye, ya ce,
Ya samu sauki insha Allah, amma idan ya farka a bashi wanan ruwan ya sha,
Har malam ya taka kamar zai bar dakin sai kuma ya juyo, inda Baba Buhari yake a tsaye
Yanayin fuskan malam yasa gaban Baba Buhari ya yanke ya fadi,
Malam yace,cikin wani irin yana yi wanan zancen yazama siri a tsakani ku da dan uwanka har matar ka,
Cikin karfin hali Baba Buhari ya,ansa da kada kai gami da cewa to, a fili,
Daga haka malam yabar shiya cikin sauri batare da ya kara furta wani abu,ba,,,,,,

Mama Ladi wace tin safe ta kasa zaune ta kasa tsaye don maigidan nata bai ce mata kalla ba akan wanan mumunan halitan da suka dauka a dakin ta, wada za aiy da dodon kwallah a takaice,,,
Ga sako tun da rana da Hajja ta damay ta da,shi wai tazo malam na San,inna na son ganin su,
Wanan aiken ya kara tayar mata da hankali sosai don tana tsan,manin ko, dodon kwallah ya koma gurin shi ne,
Amma ta san yau duk abinda zai faru sai dai ya faru don dai ba ta da wani kafa da hae zata samu fita zuwa Anguwa,
Don a yinin ranan ba abinda takeyi sai rokon ubangiji Allah sauki,,,

Ba karamin kidemawa mama Ladi tayi ba, don ganin irin aiken da Abubakar dan ta wanda suke kira da mai sunan malam, ya yi ba,
Hakalinta ya tashi kwarai duk da tana cikin tashin hankalin dama,
Sam bata taba tunanen cewa yana da irin wanan arzikin ba,
Sai gashi zuwan Wada gurin shi yai ma kowa aike da ya tayae mata da hankali,
Mama bata san lokacin da ta manta wancen zabcen Dodon kwallah nata ba,
Sai ta hau sake maganganu kawai tana cewa wai anfara zuwa gurin dan ta yawon maula batare da sanin ta ba,
Sai kuma cewa da takeyi ita bazata yarda a mallake mata "da ba har ya dinga abu batare da shawaranta ba,
Hakan yasa tun tana yi ba wanda ya tanka mata har saida Baba,Buhari ya taka har kofan nata duk da haushin ta da yake ji,
Daga labulen dakin yayi ya ce mata cikin fada, Ji mana Ladi,
Kin dai san cewa dama ina da,ke a raina ko? Ba wai na manta da zancen bane,,
Don a,sanadinki ga dan uwana can a kwance tun jiya,
Don haka ki san zaman ki a gidan nan tun yanzu don ba, zan yarda ki zubar muna da darajan gida ba a cikin shiya,,,
Tunda Baba Buhari ya fara magana sai mama ladi tai tsit don ta hango zancen gaskiya ya ke a idon shi,,,,
Ganin bazata tanka masa ba yau ya sa shi kumtawa da karfi alamar zaki sani,,,
Can cikin gida kuwa sai murna da farin cikine ya mamaye kowa don ba lungun gidan da,ba aiwa alheri ba,
Abinka da babban gida kafin wani lokaci labari ya karade cewa mama Ladi batai farin ciki ba da,wanan baiwan da Allah yai mata,a dakin ta,
Don dai ka haifi da yana wa mutane alheri wani abu ne na musan man,,,,

Yau kimanin sati uku ke nan da komawan Baba Wada gida daga Lagos,
Zama tsakanin Abubakar da matar shi ana dai yi ne kawai don kowa ma miskilin kanshine, ba mijin ba ba matar ba,
Babu wani abinda ke burge shi daga halaiyan Sadiya din,
Duk ta kowani gefe Sadiya bata da gurin da za,a yaba mata akai,
Don haka, yau tun wayewar gari Abubakar ke son yiwa Sadiya magana akan ta je gurin gyaran kai ko kitso,
Sai dai kuma yana dan shakkan yi mata zan cen don baya son ta fassara mai zancen shi,
Don inhar son samu ne itace da kanta ya kamata ta san kanta yana bukatan gyara,
Gashi kuma agaskiya dole ne yau ya daure ya fada mata ta gyara kan nata,
Sai da ya dauko goran ruwa a fridge ya dawo inda ya ke zaune da farko,
Muryan shi Sadiya taji yana cewa Ni kan dai Sadiya nace yau ya kamata ki shirya in kai gurin gyaran kai ko kamar yadda naga mata suna yi,,
Abinda Abubakar ya fahinta shine tunda ya fara magana
Sadiya tai yi kicin kincin da fuskan ta alamar maganar bai mata dai ba,
Sai cewa tayi gaskiya ni ban son fita ban san kowa ba a gari
Ai,kuma gashi, nakan iya kamawa na gyara da kauna,
Murmushi yayi irin na takaici yace Sadiya ke nan
In banda abinki ta yaya mutum zaiwa kan shi gyara kamar yadda wani zai mai yayi kyau,
Kara bata rai tayi alamar yanzu bata yarda da zancen zuwa gurin gyara ba,
Daga karshe sai cewa tayi ni banga rashin kyaun wanan din da nake lalabawa kaina ba,
Galala ya yi ya saki baki yana kallonta don kuwa tagama bashi mamaki,,,,


ZEEE MAKAWA YELWA
🕸🕸🕸TARKO🕸🕸🕸
🕸🕸🕸🕸🕸🕸
7⃣

ZAINAB IDRIS MAKAWA

IYYAKA NA,ABBUDDU WA,IYAKA,NAS,TA,INN,

SADAUKARWA
Sadaaukar da wanan pages din a kullun gare ku yan family mu na ALIYU HARZAMI KANO

FATAN, ALHERI GARE KU MAKARANTA WANAN NOVEL DIN MAI FADAKARWA,


A kan wata katuwar shifidaddiyar tabar suke zaune, a sashen malam,
Kallo guda zakaiwa Baba Samaila kagane cewa yai ciwo mai karfi a cikin yan kwanakin nan,
Duk wanda yaga irin yadda aka shimfida wanan tabarman yau in dai har a gidan kake ba wani abin mamaki ba,
Don duk wata maga tasamu mai muhinmanci za,ayita haka ake shimfida,
Sai har matan sashen na malam dole a lokacin subar sashen har zuwa lokacin da za,a gama zancen,
Zaune suke da alamar suna jiran wanine a lokacin,
Mama Ladi ce tafe cikin tsoro da fargaba take tafiya don jin da tayi cewa malam ne yau da kan shi ke kiranta,
Wasu zannuwa masu ruwan zuma da yan adon flowers kore da ja ne a jikin ta,
Ta daura guda da dan kwalin shi da riga sauran sanda biyu kuma ta yafa a jikin ta har zuwa kai,
Azaton mama ladi tunda taji shiru har kwana kusan goma ta dauka zancen ya wuce ne,
Amma kiran da malam yai mata yau ya sa ta jin nauyi da fargaba don bata san ko may zai faru ba,
Wani iri tsuki Baba Buhari ya ja tunda ta tunkaro gurin,
Cikin tsawa ya ce mata ke dai san ke mu ka zaman jira tun dazun shina ki ka wagga tahiya,
Malam Manya ne cikin murya irin ta manya ya ce mashi koni, "an, bita sannu, tunda ta taho,,,
Can gefe guda,mama Ladi ta samu ta zauna ta gaida malam a hankali,
Addu,a akafara bude taron dashi,, tare da neman wa zurian su gamawa lafiya, da fatan alheri ga ko wani musulmi,,,,

Gyaran murya malam din yayi wanda ya kara dawo da hankali kowa zuwa gare shi, don sauraren abin da zaice,
Malam ya fara da kiran sunan mama Ladi, da cewa,
Ladi,
Mama ta ansa kai a sunkuya da cewa naam Baba,
Wanan zaman da ki ka ga mun,yi don ki muka yi shi badon komai ba sai don, mu tatauna mu ji yaya ankayi haka ya hwaru,?
Shirune ya biyo baya tankar babu wani mahaluki a gurin zaune,
Ganin baza tai magana ba yasa Baba Buhari cewa cikin bacin rai ko ni an malam bari dai in yanke alakata ga wagga bakin irin ,
Yar nema mugguyar shiya,
Dibo wadda kinka mayar min da dan uwa saboda bakin kwadan ki,
Mi kin ka rasa duniya ? da,,,,,,,
Malam ne ya katse Baba Buhari cikin daga hannu tare da kiran sunan shi da karfi,
Wanda hakan yasa baba saurin yin shiru don bin umurnin mahaifin shi,,,
Malam ya ce Ladi an, magana zakiyi don musan ta ida zamu bullo ma,wagga zancen,
Don ba karamar magana ta, ba ke ga aikina ta sihiri,
Ko yaushe yana iya dawo wa,
Gaban mama Ladi ne ya fadi ras don jin cewa wanan dodon kwallah zai iya dawo wa ko wani lokaci,
Zama ta dan gyara tare da kara dukar da kan ta a kasa inda tafara cewa,,,
Malam, walle sherin shedan na da kuma Hajja ,,,
Gani ni, nayi ina zaman banza bani sana,a shina na tai inda Hajja, ni ce ta taimaka min,
Walle bata fada min cewa sihirina za,a yi min ba sai dai bayan kwana biyu ta aiko min cewa in aiko da, kwalin, Lipton shayi guda uku,
Sai na saye na aika mata dashi takara aikowa tace in dan bayar da ko nawa gare ni,,
Sai na aika mata da dari biyar, bayan kwana hudu ta aiko cewa ranan laraba mai zuwa in taho da kwallah akwai inda zamuna
Sainace mata banda kwallah mai dan kyawo tace min in bari tana dubawa cikin nata,,
Sai kuma ta kasa karasa maganan tai shiru tare da dukar da kai,
Muryan malam ce da ya jefo mata tanbaya yasa ta saurin dago kai,
Wane malamina ko in ce boka kun ka tai wuri nai ?
Nan ma shiru mama Ladi tayi saida Baba Buhari ya daka mata tsawa,
Cikin dan i,iniya tace malam na San,Inna munkatai wuri nai
Wa, akacewa hakana inji malam ke tambaya tace shina can kasan yar mayan ka shike da zama,
Salati sukayi gaba dayan su yadda akayi tun daga shiyan sarakuna ace mace ta tashi har mayan ka,,,
Malam ya ce Ladi baki kyauta ba gaskiya, ke manta da gidan da kika aure na,,
A ce yau macen da ke gidan ga na, ta tai gurin Boka don dai rashin tawakkali,
Ladi rashin tauhidi na har ya kai,ki ga wagga harkan,
Yau idan kaga mutum na sha,ani nai iyakan ka dashi ijjiya,
Amma tambaya ba shi shuka ma alheri ga wagga zamani da muke ciki,
Ke de ga halin da dan uwan mijinki ya shiga ciki sanadiyar wagga abin,
Sai a lokacin mama ladi ta daga kai ta dan kalli Baba Samaila wanda ya ramay ya wani zabge a lokaci guda,
Nan da nan hankali mama Ladi yai matukar tashi ,,
Tai matukar kidimewa don ganin irin yadda Baba Samaila ya koma a lokaci guda,
Sai kawai ta shiga rusa kuka wi,wi tana cewa malam don Allah a yafe mata tayi kuskure, bazata sake ba insha Allah,
Malam ya ce, yanzu da zaran zancen ga yai girma duk gari ji zasuyi a dauka cewa tana MAITA,
Don ke ga Allah ya taimake ki da ace kin fara da bashi kazan da yaka so da shikenan ke bi hanya,
Don wata,rana har mutun zaicewa ki bashi jinin shi yasha, ke ko idon ki ya rufe kin iya sihiri
Baba Samaila dake zaune jingine da bango yace ai,duk zafin neman bai kawo samu,
Kawai mutum ya hakkura ga duk yanayin da ya tsunci kan, shi, don yanzu badon Allah ya gyara ba da, ba,a san iya inda wanan abin zai tsaya ba,,
Cikin muryan kuka mama Ladi kewa ku ya fe min don Allah
Malam yace Allah dai ya yafe muna baki dayan mu,,
Kuma wanan zancen ina son ya tsaya dai dai iya mu kada inji shi ga wani nan gaba,
Hakan yaiwa mama dadi so,sai don malam ya kashe wutan zancen,,,
Haka rayuwa ta kasance da ci gaba a gidan malam ,
Yanzu tsakanin mama Ladi da Hajja sai yar nisa da nisa don babu irin mugun shakuwar nan ta da,
Ita ko Hajja ko a jikin ta don arzikin ta,sai gaba gaba ya ke yi a koda yaushe,,,,

Rashin zuwan Abubakar gida akai akai ya fara da mun malam, Manya yanzu,
Don a iya ka sanin tun lokacin da mai,sunan nashi yai aure har izuwa yanzu baizo gida ya kai sau uku ba,
Gashi yanzu tasan ma,shekara, biyu da rabi da auren shi,
Abu guda ne shine duk wani dan uwa ya je zai aiko masu da sako mai yawa a kawo masu,
Ita ma fanin Sadiya matar shi haka ne,ko da yake mahaifiyar ta ba wai ta wani damuwa tayi da rashin zuwan yar nata gida ta yi ba,,,,
Kuma yadda yan gidan su, Abubakar suka damu da rashin samun karuwan ma,auratan,
Ita Hajja a nata bangare hakan bai wai damay ta ba sam,,
Idan anyi magana cewa har yanzu dai sadiya bata haihu ba sai tace lokacine bai yi ba,
Ita ko, bangaren mama Ladi ko in ce gidan su Abubakar rashin samun haihuwan shi na da mun su,
Tun dai malam Manya wanda kance abokina dai har yanzu shiru ba labari,
Bukin Sallah babba na bana Allah ya nufi Abubakar zuwa gida tare da mai,dakin shi watau sadiya,
Daga shi har ita kallo guda za kai masu kasan cewa akwai kwanciyan hankali da wadata atare da su,
Don hasken shi ya fito sosai gashi ya dan kara jiki da girma, gwanin ban sha,awa,
Wanan zuwan da Abubakar yayi ya kara tayar wa malam manya hankali irin yadda yake jin labarin, jikan nashi abin yafi da nan so sai,,
Gashi harda motar kanshi yazo lafiyya ga kuma tsaraba mai yawa,
Sai,dai duk yawan wanan tsaraban da yazo da su a kofan dakin mahaifiyar shi, mama ladi a ka labta su,,
Wanda shi Abubakar sam bai so haka ba yaso ne ace akai su can kofan dakin malam,
Tun da malam ne wanda ya tashe shi tun yana yaro sai ko sauran iyayyen su maza musan,man Baba Samaila,,,
Wanda tun baiyi aure ba duk abinda ya samo sai yace na Abubakar din shine ,

Mutanen gidane ke ta turuwan zuwa sashen Baba Buhari gurin gaida bakin Lagos da sukai saukan dare,,
Don ba,a samu ganin su da dare ba sai yau da safe don haka ake ta zuwa, ganin su,,,
Girman da yaran gidan nasu yayi yasa shi mamaki matuka don bai yi tsanmanin cewa sun,kai haka ba,
Kusan duk wanda ya shigo indai dan gidane da tsaraban shi,
Amma kuma sai wanda mama taso aba ma abin kwarai,
Duk wanan rabon da akeyi babu dan shiyan Baba Samaila ko mutum guda da ya shigo sashen, har zuwa yanzu,
Daidai shigowan ,Saratu matar Baba Samaila da iyalinta
Abubakar wanda ba ma,abuci magana bane tun farko, daga shi har matar shi,,,
Yana zaune, gefe guda yana wasa da wayan da ke a hannun shi,
Wanda alokacin kusan a hannun shi yan gidan suka fara ganin wayan Mobile,
A cikin natsuwa suka gaishe shi kamar kowa tare da masu yaya hanya,
Ya amsa cikin dan sake fuska kadan, da cewa mama, mun samay ku lafiya,?
Da ga haka bai kara cewa komai ba ita ma dai mama saratu juyawa tayi zuwa kofan waje da yaran ta,
Shiko Abubakar sai kokarin duba kaya yake yi wanda zai basu,
A daidai kofa duk wanda ke gurin a lokacin zai iyajin abinda uwa da Dan takeyi a dakin,
Haba mama inji Abubakar ya ce yan uwanane fa na ji ko duka tsaraban zan basu ai sunci shi a guri,na,
Kai ne dai ka dauke su a haka ni ko diyan shaibu, ban yarda da wanan ba balle diyan, Samaila masu daukan kai kaman wata tsiya,
Murmushi kawai mama Saratu tayi a lokacin don jin abinda mama ladi ke fadawa dan ta, akan su,
Haba mama kibar fadin haka don ni baba Samaila baida maraina a gurina,
Kaine kasan may yai maka ni dai ban yarda ka dauki cikin wa yan nan leshin kaba su sai dai wancan na gefe da na cire ma,
Suna hada ido da kishiyan mama Ladi sai wa mama saratu signal da ido ta wuce kawai,
Isan su sashen su yayi daidai da lokacin da sakon Abubakar ya iso gare su,
A lokaci guda mama saratu da yaranta Meenat da Awal

5 / 61