Author : Dana sani Amarya Category : Complete Novels
eye glasses ɗinta, safar hannu ta saka wanda hakan ya sanya cikar kamalarta fitowa.
Wayarta ta ɗauka tare da saka shi a cikin jakarta na companyn channel, tare da ɗaukar key ɗinsa ta nufi
hanyar falon cikin gidan.
Ita ma Salimah a shirye take cikin abaya, daga falon kuwa compound suka wuce tare da ɗaukan motarta
suka wuce gidan Nenehn.
Horn suka danna wanda atake mai gadi ya buɗe musu gate ɗin tare da shigar da motar nasu, compound
ɗin dake cike da motoci na alfarma.
Wani kalar farinciki ne ya ziyarceta ganin motar Abbhinta a compound ɗin, dan ta san duk inda ƙarfe
takwas yake a gidan yake musu idan za'a yi taron family.
Har kusan tuntuɓe ta yi tsabar farinciki, da ɗan gudunta ta iso cikin falon tare da faɗawa ajikin Ammi
dake zaune cikin cousins ɗinta da suke sa'anni.
Gidan acike ya ke da jama'a, su Rashanda ne da su Unaisah da Classy Reeda suka fito da ɗan gudunsu jin
muryar Liyanar a falon.
Umma Mansura ce ta fito hannunta riƙe da wani bowl dake cike da sararran rake ta fito daga cikin
kitchen ɗin falon jikinta sanye da wani less mai kyau da tsada.
Da ɗan sauri ta saki Ammi tare da faɗawa jikin Umma Mansurar da saura kaɗan raken dake hannunta su
ɓare.
Abbhi dake zaune ya na kallon ikon Allah ne ya ce ''Yau Daughter ni aka manta kenan.?"
Tsintar muryar Abbhi da ta yi ne ya sanyata saurin sakin Umma haɗe da rungume Abbhin, ta na mai
ƙyalƙyala dariya.......
''Ya Ubangijina ka basu daman share."
Allah ya yiwa fans ɗina masu sharing arziki fiye da Dangote ✨😤🌟
Ma ra sa share Allah ya kawo kuɗi na siyi mota na tada muku ƙura 😂😂
*THE REGRET*
PENDING AMARYA CE ✍️
JAJIRTATTU WRITERS ASSOCIATION
The Noble Writers Team.
**Pending Amarya 48**
What goes around comes around ⏮️⏩
Try to be a good father to your children not a cowed 🤍 🫧 🤧
Not edited 🌟💔🥹
****
Umma Mansura ce ta fito hannunta riƙe da wani bowl dake cike da sararran rake ta fito daga cikin
kitchen ɗin falon jikinta sanye da wani less mai kyau da tsada.
Da ɗan sauri ta saki Ammi tare da faɗawa jikin Umma Mansurar da saura kaɗan raken dake hannunta su
ɓare.
Abbhi dake zaune ya na kallon ikon Allah ne ya ce ''Yau Daughter ni aka manta kenan.?"
Tsintar muryar Abbhi da ta yi ne ya sanyata saurin sakin Umma haɗe da rungume Abbhin, ta na mai
ƙyalƙyala dariya.......
Da ɗan sauri ta saki Ammin tare da faɗawa jikin Umma Mansurar da saura kaɗan raken dake hannunta
su ɓare.
Abbhi dake zaune ya na kallon ikon Allah ne ya ce ''Yau Daughter ni aka manta kenan.?"
Tsintar muryar Abbhi da ta yi ne ya sanyata saurin sakin Umma haɗe da rungume Abbhin, ta na mai
ƙyalƙyalewa da dariya.
''I can see you guys are all happy seeing me here right beside you, na yi farincikin ganinku sosai, Aunties
and Mummies, da ma ya'n uwana, barkammu da haɗuwa da junanmu.''
''Ma shaa Allah daughter ya kike ya mai gidan.?" Umma Mansura ta faɗa tare da miƙa ma ta bowl ɗin
raken hannunta.
''Lafiya lau Umma, ina su Rashidat?, ko ba'a zo da su ba.?" Liya ta yi maganar tare da ɗaukan raken da
ke cikin bowl ɗin ta na mai fara sha.
''Daughter suna dakin ki ai, tun safiya suke jiran zuwan ki.'' in ji cewar Umma Mansura.
Tashi ta fara harraman yi da niyyar shiga cikin ɗakin, hannunta na riƙe da raken tare da cire veil ɗin
abayarta mai ɗan faɗi da ya lulluɓeta sosai ta na mai miƙawa Abbhinata.
Ɗakinta na gidan Nenehn ta nufa, har ta kai hannunta kan handle ɗin ƙofar ta ji muryar Ammi cikin
kunnenta.
''Liya, dawo nan ki zauna.'' Ammi ta faɗa ba tare da ta kalli mutanen dake wurin ba.
''Saboda mai?, haka kawai ba ƙawayenta ba ne , ke dai Salamatu ki rage baƙin halin nan na ki.''
Neneh da take saukowa da ita da Jiddah ta faɗi hakan, jikinta sanye da wasu ox blood color lifaya masu
kyaun gaske.
Gaishe da Neneh da Jiddah ya'n falon gabaɗaya suka yi, Liyana kam jikinta har mazari yake taje wajen
Jiddahn haɗe da ba sa side hug.
Murmusawa ya yi tare da shafa kanta ya na mai faɗin ''Ya Zahra na same ku lafiya.?"
Wani kalar frawn ɗin fuskarta ta yi tare da faɗin ''Allah ni Jiddah na yi fushi ma da kai.'' ta yi maganar a
shawgwaɓe kamar yadda ta saba yi ma sa.
Murmushi kawai ya yi tare da zama akan kujerar da take a matsayin na sa wanda ko da wasa Neneh ba
ta barin kowa ya zaunar ma ta.
Zame jikinta ta yi daga falon tare da shigewa ɗakin na ta wanda duk a idon Ammi da ta kasa magana
saboda ganin idanun Neneh kurr akanta.
Ƙarasa shigowa cikin ɗakin ta yi ta tarar da su Rashanda da su Ilham da sauran counsins ɗinsu gabaɗaya
suna ta hira, Yusrah na zaune daga gefen wajen book corner ɗin ɗakin ta na chatting da wayarta forming
boss lady.
Shigowarta ya sanya su wani kalar ihu haɗe da murna kowannensu na ta shouting ''Awwn.'', ''Mrs
HYDAR.''
Basar da su ta yi tare da faɗin ''Wai na fito rannan kuma ban ganku ba.?" Ta yi maganar ta na ƙoƙarin
amsar coke ɗin dake hannun Ilham.
Tsaki suka ja a tare, sannan Unaisah ta ce ''Ai ni na manta, da wallahi babu wadda za ta miki magana
acikin mu.'' ta yi maganar tare da harar Liya.
''Wallahi Yaya kin ɓata min rai, har yau idan na tuno kamar na yi kuka.'' Ilham ta yi maganar kamar ta
kwashe Liya da mari.
''Wannan kuma matsalar ku ce, ai sai ku bar masu aure su shana, haka kawai da daddaren Allah ku wani
kwaso jiki, wai za ku kwana.?"
Liyanar ta yi maganar tare da tashi da niyyar fita daga ɗakin.
Yusrah da tun ɗazu maganar Liya ke shigar ma ta kaine ta ajiye wayarta tare da juyowa ta na faɗin ''Toh
dan ubanki sai ki aurar da waya'nda ba suyi auren ba.''
All of them were shocked, dan su har ga Allah sun manta da wanzuwarta a ɗakin.
Classy Reeda ce ta ce ''I don't understand, wani ya yi mention ɗinta a nan ne?, ko akwai sa'anta anan.?"
Ta yi maganar tare da ajiye pillown da yake kan ƙafarta.
''The thing wonder me OOO." In ji cewar Rashidat.
''Yaya dan Allah don't respond to her, ki ƙyaleta dan Allah.'' Ilham ta yi maganar ganin Liyanar ta fara
ƙanƙance ido.
Tsaki Liya ta ja tare da faɗin ''Ni nafi ƙarfin nayi dake kema kin san sai dai na yi da Fatuh mai warin
hammata.''
Daga haka ta fice daga ɗakin tare da rufe musu ƙofar da ƙarfi.
''Kutumar......., wallahi sai gidan nan ya koma na yaƙi.'' Yusrah ɗin ta faɗa tare da ficewa ita ma daga
ɗakin.
Su ma gabaɗaya suka mara musu baya.
Afalon su Mama Fatuh har sun fito daga backyard daga dafa abincin da suke yi a traditional kitchen ɗin
gidan, yan aikin Neneh da Salimah da ta zame ta tafi can tun bayan zuwan su, suna ta rabon abincin da
ya ji crey fish.
Yusrah ce ta zo ta tsaya akanta cikin fushi tare da faɗin ''Mama ki taso mu tafi ba zan iya ɗaukan
wulaƙancin kowa a gidan nan ba.'' ta yi maganar hannunta riƙe da ƙugunta.
Umma Mansura ce da abin ya ɗaure ma ta kai ta ce ''Yusrah ban gane wulaƙanta ki ba ?, wa ya
wulaƙanta ki ɗin toh.?"
Ko kallonsu ba ta yi ba ta ci gaba da yiwa Mama Fatuhn magana.
Ammi ce ta kai dubanta wajen Liyana tare da faɗin ''Hope nothing happened a tsakanin ku.?"
''Ammi zagi na ta yi na rama.'' Liyana ta yi maganar tare da miƙewa daga kusa da Ammin.
''Yusrah ki yi haƙuri ma na ki koma ki zauna.'' Ammin ta yi maganar a sanyaye.
Tsaki Yusrah ta yi tare da faɗin ''Ki ajiye kirkin ki na banza da na wofi a gefe, watarana za ta miki amfani.''
Daga haka ta ja wani tsaki tare da barin wajen.
''Idan kun san wata ba ku san wata ba, Ikimat ki gaya ma ɗiyarki da ta kiyayi ƙasar shuri, ko da kuwa ta
na cin ko wani ƙasa ta zauna lafiya.'' Mama Fatuh ta yi maganar tare da ɗaukan jakarta.
''Yaya wallahi, ni ban san mai ya faru ba dan Allah ki yi haƙuri.'' Ammi ta yi maganar kamar za ta yi kuka.
''Wallahi Aunty kika ƙara ba ta haƙuri sai na kira Yaya na sanar da shi wannan maganar, tun da ke ba kida
hankali, ta ya ana ƙoƙarin kashe magana ya'rta na wa mutane rashin kunya kuma ta na maganar a kiyayi
ƙasar shuri, ita ma ta kiyaye sa, ubanwa rigimar ta kashe, ita ma kanta ta san Nabil ya ji wannan maganar
ba a nan kaɗai za'a tsaya ba, daga can ki yi can.'' Umma Mansura ta faɗi maganar zuciyarta a ɓace.
Juyowa Mama Fatuhn ta yi tare da faɗin ''Ai ni ban yi dake ba Mansura, da ƙanwata nake.''
''Sai ki gayawa Awwalu maƙera na garin maraɗi.'' Mama Mansura ta yi maganar tare da ɗauke kanta
gefe.
''Mansura za ki ci kaza - kazan ki, dan ubanki.'' inji cewar Mama Fatuh dake tsaye ta na huci.
''Idan kare ya na haushi ba'a tanka shi ai.''
Wani uban tsaki Mama Fatuhn ta ja haɗe da barin gidan.
''Umma ina su Abbhin suka je.?"
Liyana da tun ɗazu jikinta ya yi sanyi ta tambayi Umma Mansura.
''Daughter sun fita da Neneh da Jiddah taron Y'an Maiduguri.'' Mama Mansura ta ba ta amsan haka.
''Ilham zo ki raka ni gidansu Sultana.'' ta yi maganar ta na zira slippers ɗin da ta gani a palourn.
''Wace Sultanah da za ki kwashi jiki, ki tafi.?" Umma Mansura ta tambayeta tare da ƙafeta da idanuwa.
Cikin inda-inda ta ce ''Gidansu .........Ya Aliyu fa, nan maƙotan Neneh.'' ta yi maganar kamar za ta yi kuka.
Classy Reeda dake zaune kusa da Ammin ce ta ce ''Na biyo ku sisi.?"
Murmushi ta yi tare da faɗin ''Why not.''
Daga haka suka fice daga gidan.
><><><>><><><><>><><><>
Gidan tsaf yake a gyare masu aiki na ta haɗa hadan gyaran shi, ko ina na gidan tsit yake babu hayaniyya,
sai kukan fararen tsuntsaye dake tashi a gidan.
Direct part ɗin Mami suka nufa su ukun cikin shigarsu na abayoyi masu tsadar gaske.
Cikin siririyar muryarta ta yi sallama haɗe da shiga cikin luxury living room ɗin da ƙamshin turaren wuta
mai sanya nutsuwa ke tashi a parlourn.
Ƙarasa shigowa cikin parlourn suka yi Mami na zaune a tamkeken falon cikin wani holland atamfa da aka
ma ta ɗinki na alfarma da shi.
Sultan na daga gefenta kansa akan cinyar Mamin da take ma sa massaging kan na sa, wanda alamu sun
nuna kan nasa ciwo yake ma sa.
Ƙarasa shigowa ta yi ita da ya'n rakiyan na ta kanta a ƙasa har ta ƙaraso wajen da suke haɗe da
durƙusawa ta na mai gaishe da Mamin.
Amsa gaisuwar ta yi, tare da shafa kanta ta na mai sanya ma ta albarka haɗe da amsa gaisuwar su Ilham
ɗin da sai wani nannoƙewa take kamar sabuwar mayyar da ta lashe ɗan kishiyyarta.
''Daughter ya kaɗaici.?"
Murmushi kawai ta yi tare da faɗin ''Mami mai wankin ya miki ne.?" Ta yi maganar zuciyarta na ɗan
faɗuwa.
''Laah, daughter tun jiya da yamma bayan tafiyarki ya min wankin, and kin san da washing machine ne, ai
na gode sosai wallahi Allah ya yi albarka.''
''Amin Mami zamu wuce.''
''Noo wait yau ɗin nan na dafa miki favorite ɗin ki, ina ta jiranki ba ki zo ba, nake faɗawa Sultan zai kai
miki after noon, buh tun da kin zo is better ki tafi da shi.''
Kunya ne ya kamata, dan tun da Mami ta san zancan cikin jikinta, ta koma tarairayarta fiye da da.
Hannunta riƙe da wani tray haɗe da wasu plates aciki dake cike da kayan ciki, sai miyan iwedu da amala
wanda ya yi baƙi ƙirin.
Ji take kamar ta janyo hannun Mamin ta fara cin abincin, a hankali Mami ta sauke abincin tare da ajiye
ma ta shi a gabanta.
''Daughter aci daɗi lafiya, dan ke kaɗai na girka, and I hope you will like it.'' Mamin ta yi maganar tare da
amsar ruwa da lemon kankana daga hannun ya'r aikinta ta na mai dire musu shi.
''In shaa Allah Mami, kin san you're the best cooker ever." Liyama ta yi maganar a ɗan kunyace.
''Aunty Liyana ina wuni.'' Sultan ya faɗa ya na mai k'afeta da idanunsa masu firgita ta.
Ba ta amsa shi ba ta cigaba da cin abincinta.
Ƙarar buɗe ƙofar falon da aka yi shi ya ja attention ɗinsu gabaɗaya zuwa can wurin entrance ɗin. Amir ne
cikin shigarsa na kaftan sky blue da ta ma sa kyau sosai, ya ƙaraso falon haɗe da gaisar da Mamin,
kallonsa ta yi sosai tare da faɗin ''Son ya gida.?" ''Mami Alhamdulillah, daman Mami na ce mu ɗan gaisa
ne tun da hanya ya biyo da ni ta nan ɗin.'' ya yi maganar ya na ɗan daddanna wayar hannunsa ya na
kallon Liyana da ta kasa haɗa ido da shi.
''Mami ayi min package na shi na ƙoshi haka.'' ta yi maganar ta na mai marairaice face ɗinta.
Order ta bawa masu aikinta, Sultan kam silalewa ya yi ya bar parlourn, yayin da Amir ya duƙufa da
chatting ɗinsa, a take wayarsa ta fara ringing, ganin mai kiran na sa ne ya sanya shi tuntsirewa da dariya
a fili tare da ƙara kallon Liyanar.
Sai ta camerar wayarsa ya ƙara yi tare da zooming ɗin kyakkyawar fuskarta dan da ɗan tazara tsakaninsu
ya ƙara ɗaukan pictures ɗinta kusan uku a dai-dai time ɗin da ta ɗago idanunta ta kalli Amir ɗin, tare da
tura ma Hydar da ya addabe shi da kira tun first picture da ya tura ma sa.
Haka nan kawai ta ji da cewa Amir is up to something that will lead her to matsala ko akasin haka, hakan
ya sanya ta tashi tare da faɗin ''Mami sai da safe.'' ta yi maganar a sanyaye.
''Mabaruka, packaging box ya zama allura ne.?" Mamin ta faɗa da ɗan ƙarfi.
''Ga shi Maa.'' Mabaruka ta faɗa tare da miƙawa Mamin.
''Ina wanda na zuba a warmer da nace Sultan ya kai ma ta.?" Mamin ta tambaye su.
''See it here Maa.'' Agnes ta faɗa tare da ƙarasowa wajen da wani lunch box mai kyau a hannunta.
Miƙawa Ilham lunch box ɗin ta yi, shi kuma packaging box ta miƙawa Reedah.
Sannan suka fara harraman tafiyya, tsayar da su Mami ta yi tare da kawo musu wa ta leda dake cike da
turaruka.
''Amaryarmu har za ki tafi.?"
''Eh Yaya Amir, sai anjima.'' ''Okay dear.''
Daga haka suka fice daga gidan.
Tun a ƙofar gate ɗin suka fara dariya, Ilham na ta kwaikwayon Liya yadda take wani sissinne kai kamar
mayya.
Banza ta yi dasu tare da shiga cikin gidan Nenehn da har motarsu Abbhin na pake, alamun sun dawo
gidan.
<><><>><><><><>><><><>><
A kwance yake yau ɗin bayan ya dawo daga meeting ɗin da suka yi da ADAFAR VENTURES na Singapore
akan kayan da suke son a siyar musu da shi, laptop ɗinsa a kan cinyarsa sai wayarsa a hannunsa ya na
kallon wasu reels a Instagram. Sannan ya ga saƙon Amir alamun ya turo ma sa hoto.
A hankali ya ajiye laptop ɗinsa tare da shiga cikin message ɗin, zaune take ta na wasa da hannunta abinci
a gabanta, sai ɗayan kuma ta ɗan cuno baki alamun kamar wasu da portait ya lulluɓesu he can't say su
waye su.
Sai kuma ɗayan ta ɗago fuskarta ta zazzaro idanunta kamar wadda ta yiwa sarki ƙarya.
He just smiled, tare da ƙurawa pictures ɗin idanu, wanda suka ma sa kyau sosai.
Reply ya ma sa da faɗin ''For.???" Emojis ɗin dariya Amir ya turo ma sa tare da faɗin ''Ka dawo ka
kwashi gara my guy, ta dawo yadda kake so wallahi.''
Ganin message ɗin Amir ɗin ya sa wani kalar murmushi suɓuce ma sa tare da ma sa reply ɗin ''Really.?"
''Yeah.'' daga haka suka shiga wani hirar da ban.
Bayan sallar isha ma office ya koma ya duba wasu takardu tare da dawowa gida.
><><>><><><>><><><
Ko da suka shiga cikin falon da Mama Fatuh suka fara cin karo, suna zazzaune kamar ana sulhu.
Can dai suka saki jikinsu gaba ɗaya aka fara hira.
Ƙarfe goma na dare kowa ya watse, dan sai da suka ƙara wani faɗan da Yusrah, sannan ta kamo hanyar
gida ita da Salimah.
Bayan Salimah ta buɗe gate, shigar da motar ta yi tare da ajiye shi a muhallinsa.
Ko ina na gidan shiru, direct backyard ta nufa tare da kunna wutan solar sannan suka shiga cikin gidan,
da ko ina ya wadatu da haske.
Direct ɗakinta ta shige dan ba yunwa take ji ba, dan abincin gidan Mamin sosai ya yi ma ta rana.
Toilet ta shige tare da yin wanka ta fara shiryawa cikin kayan baccinta dan gobe ta na tunanin zuwa
ganin Doctor.
Wayarta ne ya fara ringing hakan ya sanyata ƙarasa k'ulle towel ɗin jikinta tare da ɗaga wani number
ƙasar waje da ba ta san code ɗinsa ba.
Har za ta ɗaga sannan wayar ta katse, in less than 5 seconds aka ƙara biyo kiran, a hankali ta ɗaga tare
da manna wayar akunnenta.
''Assalamu alaikum.'' ta faɗa a sanyaye, amma ba'a ba ta amsa ba, ''Hello.'' ta ƙara magana ta na mai
ɗauke wayar a kunnenta haɗe da mai da shi.
''With whose permission kike fita da mota, and da izinin wa kike fita, bayan school na yarje miki da kije?,
kin fara wasa da ni ko.!?" HYDAR ɗin ya faɗa a ɗan faɗace.
Wani kalar bugawa ƙirjinta ya yi jin muryar na sa a cikin kunnenta, sannan kuma a hankali ta ce ''I'm
sorry, Mami ce ba ta da lafiya, shiyasa nake fita, amma trust me wallahi babu inda nake zuwa bayan
nan.'' ta ƙarasa maganar a sanyaye.
''Shi kuma kwanar badawan gidan ƙanwar ubanki ne acan.?" Wani iri ta ji a ranta da kalar amsar da ya
bata, hakan ya sa ba ta amsa ma sa ba ta yi shiru.
''Ba magana nake miki ba?, kika min shiru.?" Ya yi maganar da ɗan zafi.
Cikin shashsheƙar kuka ta ce ''Yaya dan Allah ka yi haƙuri.'' ta yi maganar a sanyaye.
''Shut that your dirty mouth idan ina magana, ni sa'anki ne.?" Ya ƙara faɗa a tsawace.
Haushi faɗan da yake ma ta ya ba ta dan idan ta cigaba da sauraronsa za ta iya mayar ma sa da martani,
hakan ya sanya ta kashe wayar haɗe da cilli da shi akan gado ta na mai fashewa da kuka.
Cikin shashsheƙar kuka ta ce ''Mai nayi wa kowa ya tsane ni, ni Fatimatu, mai nayi?, ba ga uwar da ta
haifeni ba ba ga kowa ba, saboda zallar tsana da Neneh ta yi min ɗan bariki ta aura min, wanda ba ya
daraja Mahaifina, why me??, why now?, why not later?, ya Rabbi I'm still young for all this, wayyo Allah
na Aliyu zai min lahani, Allah ya ishewa mahaifina kalar cin mutuncin da kake yi ma sa, kai ma Billah sai
an