Author : Dana sani Amarya Category : Complete Novels
gidan ba tare da kowannensu ya ďauki Abu
makamancin trolly ba.
Direct Airport suka nufa ba su wani jima ba suka shige private jet ďin Abbhu Wanda bai koma Nigeria ba.
AFTER SEVEN HOURS
KARFE uku na rana jet ďinsu ya dira a Aminu Kano babban filin jirgin da ke birnin jihar mu ta dabo.
Amir na tsaye ya na jiransu a jikin motar sa ķirar Tesla model S black color.
Idanunsa na kan jet din da ya dira a wajen, cikin minutes ķalilan suka fito daga cikin jet ďin, shi ne a gaba
sai Liya da kuma Marwa dake last ďin fitowa, he was very surprised da ganin jarirai a hannunsu. Amma
da ya tuno da Liyana da ciki ta bar ķasar sam sai ya cire mamakin hakan daga zuciyarsa.
Hydar ne ya ķaraso wajen da yake tare da sakar masa ranķwashi dan tuntuni yake masa magana amma
sam yaķi basa amsa.
“Oouch Man, kai a rayuwarka idan ba ka yi mugunta ba ba ka Jin daďi ne?.”
Amir ya yi maganar tare da ya mutse face ďinsa.
“Shut up jare, ķanwata za ka aura you better start to dey practice yadda za ka ďinga min biyayya if not i
will sue you to court.” Hydar ya faďa tare da buďewa Liya bayan motar.
Ita ma Marwa zagayawa ta yi ďayan b’angaren tare da zama a bayan kujerar.
Shi ma Hydar gaban motar ya nufa sannan direct suka ďauki hanyar gidan Neneh.
To their surprise sai suka tarar da gidan a cike sosai da family cars na Maiduguri.
“Malam dallah wa yace ka kawo mu gidan nan, kai mu gidanmu mai son ganinmu ya zo ya same mu.”
Hydar ya faďa a fusace.
“Wa fushinka zai bawa tsoro?, sai dai matar taka dai.” Amir ya faďa tare da zare mukullin motar.
“Bani pink jet ďina dallah idan ya so kayi ta soki burutsunka, ďan rainin hankali kawai.” in ji cewar Amir
ďin tare da amsar Aida daga hannunsa.
Tsaki Hydar ya ja ya na mai faďin “ Ai na zaci ba ka gan su ba ko makantar naka ya motsa.”
Amir bai tanka masa ba ya shige cikin living room ďin Nenehn da ake ta rairai waķoķi na larabawa.
A hankali suka shiga takawa ita da Marwa har suka shigo cikin falon gidan inda ya haďa mutane da yawa
cikinsu har da Abbhu da Abbhi da Ammi da Mami da ma su Rashanda da Umma Mansura.
Ily na zaune daga can wani corner ta na chatting.
Gidan gaba ďaya ya hargitse saboda murnan ganin jarirai har uku.
Aliyu kam tun da ya ga ba ta shi ake ba ya tattara shi da Amir suka wuce can garden ďin gidan Mami.
Ganin ita ma babu mai bi ta kanta ne ya sanyata shigewa ďakinta tare da fara rage kayan jikinta. Wanka
ta yi sannan ta sanya kayan Ily a jikinta.
“Yaya Liya ba ki da kirki wallahi tun da kika zo nake ta miki magana ko kula ni kin ķi yi.” Ily da shigowarta
kenan ta faďa tare da zama a kan kujerar dake ďakin nata.
Shiru Liyana ta mata tare da ci gaba da abin da take yi.
“Liya magana fa nake mik…” ba ta ķarasa ba Liya ta sauke ta da wasu maruka zafafa guda uku.
Sannan ta cigaba da rayuwarta.
“Mai na miki.?” Ily ta faďa tare da dafe ķuncinta ķwalla na zuba a idanunta.
“Ni za ki ciwa amana Ily?, yanzu Sultan za ki aura?, mai yasa za ki min haka, ni ba ma wannan ba, saboda
ni maķiyar ki ce har ni za ki b’oyewa aurenki sai a wajensu Rashidat nake Jin maganar aurenki, yanzu da
ban auri yayansa ba, da ci min amana za ku ďin ga yi ta bayan idona kenan, toh na gode.” Liya ta faďa
tare da share ķwallarta.
“Wannan Wace kaliyar magana kike yi haka Yaya, yanzu na fasa aurensa kike nufi?, miye aibunsa?.”
Ily ta faďa a sanyaye.
A fusace Liya ta ďago kanta da niyar ba ta amsa amma ido huďun da ta yi da Aliyu ya sanyata saurin
haďiye zancan da yake bakinta.
Cikin takunsa na ķasaita ya tako har inda suke tsaye tare da faďin “ Which Sultan are you talking
about?.” Ya faďa da kakkausar murya.
“Magana muke a kan bikin Ilham Ya Aliih.” Liya ta faďa tare da yin murmushin yaķe.
“Ba next week bane ba auren?, ai next tomorrow za a fara events na ji kamar Ana faďa.”
“Yeah, that’s what we’re discussing.” Ily ta faďa da sauri.
“Okay, keep it up.” daga haka ya fice daga gidan.
Ya na fita Neneh ta shigo.
“Ilham sai kuma kika ji labarin jikar Bob Marley , ķanwar Naira Marley ta haifi ya’n uku ko?.” Nenehn ta
faďa tare da fara shafa wa Ily wani ruwan turare a jiki.
“Babu ruwana Neneh.”
“Toh wake tsoron ta mutu balle ta yi rai, gobe za a kawo lefenki da safe, zan aurar da ýar gata ba ayawo
ba.” Neneh ta faďa tare da tab’e bakinta.
“Wallahi Neneh idan kika b’ata min rai za ki ga rashin mutumcin da zan miki, ba sanyi nayi ba, wallahi
gwara ki tattala tsufanki ko na maida Abbhina da Umma Mansura marayun dole, soo respect yourself.”
Ta na faďan haka ta fice daga ďakin.
Ko da ta fita su Rashidat da Reedah na ta ďawainiyya da jariran dan Unaisah sai gobe za ta zo.
Zama tayi acikinsu ta na hira, ganin tara saura 15 minutes ya sanyata sanya slippers ďinta tare da ďaukan
wayarta domin zuwa garden dan wannan lokaci ne da iska mai ďadi ke fita a garden ďin.
Tsaye suke a jikin bushiyar wani Guava, hannunsa ďaya na dafe da trunk ďin bushiyar.
ba ta wayi su waye su ba sai da taji muryar Marwa na faďin “Ya Alih ni mutuwata ita ce kaďai ma fi alheri
agareni, idan nace zan yi auren wallahi bani da mutumci a idon Wanda zai aureni.” Ta faďa tare da
fashewa da kuka.
“Yanzu Marwa aurenki kike so nayi ko mai?, kema dai kin san ba na raayin auren mata biyu, kuma na
Riga na yiwa Liyana alķawarin ba zan mata kishiya ba.” Hydar ya yi maganar a sanyaye.
“ No God forbid, ba zan ma shiga farin cikin kowa ba.” Ta ķarashe maganar tare da goge hawayenta.
Jin an dafa kafaďarsa ne ya sanya sa juyowa a ďan firgice.
“Marwa has gone through alot, Allah ya maka arziķi daidai gwargwado, wanda zaka iya tufatar da mata
ma fiye da ďari, and ni na ya’r je maka da ka aureta In dai har za ta zauna lafiya da ni, bani da matsala, ni
dai Kar ta shiga sabgata shi ne matsalata, wuce ka taho mu tafi.” Ta faďa a ďan tsiwace tare da jan
hannunsa suka bar Marwar a tsaye.
“Uban mai ya kai ka wajenta.” Ta faďa a faďace Bayan sun bar wajen.
“Malama respect yourself uwa kike yanzu, ki ajiye childish behavior din nan naki.” Hydar ya faďa tare da
wuceta ya fice daga gidan Nenehn gaba ďaya.
Tsaki taja tare da shigewa gidan Nenehn da ta tarar da Alya na ta tsala kuka.
Sai da ta dallah ma yarinyar harara sannan ta fara ba ta nonon.
Bayan ta gama ma dakinta ta shige tare da kwanciyyarta.
Har ta fara bacci ta ji ana kai hannu kan kumatunta.
A hankali ta dago da kanta tare da ķafe manyan idanunta akan kyakkyawan fuskar mahaifinta.
“Woooh Abbhi!.” Ta faďa a ďan tsorace tare da tashi ta na mai jinginar da bayanta ajikin fuskar gadon.
“Babyn Abbhi kin manta da Abbhi right?.” Ya faďa tare da zama a kusa da ita, haďe da janyota jikinsa.
“Noo,ta ya zan manta da soyayyata, I missed you Abbhi.” Ta faďa tare da marairaice idanunta ta na mai
ķara manna jikinta a jikinsa kamar mage.
“Abbhina alot has happened da bana nan ko?, wait gist me! Gist me.” Ta ķarashe maganar tare da gyara
zamanta sosai a jikinsa.
Shafa kanta ya fara yi a hankali sannan ya ce “Noo, Ke ki fara bani labari akan honeymoon dinki then sai
na baki nawa.”
“Promise?.”
“I never failed you, you know?.”
“Yeah, haka nè Abbhi, first mun je Zurich the place was very nice, sannan muka biya China then that his
stupid Cousin ruined everything.”
Ta ķarashe maganar kamar za ta yi kuka.
“Mai ta yi ?.”
“Abubuwa da yawa wallahi Abbhi, ex dinsa ce kuma har yau wai yana sonta, Abbhi na bar sa ya aureta a
daura auren da na Ily ko kar na amince?.”
“That wasn’t our agreement tsakaninmu da iyayensa kafin muka bashi ke, idan Banda mamanki waye
mai kishiya a Family ďinmu?, ko kin taba ganin na siya miki Abu kala daya dake da Maimunatou?, sooo
duk wani Abu da zaa ce ku biyu da wata ke da shi I dislike it dan haka babu zancen wata kishiya.” Abbhi
ya fada tare kokarin tashi daga dakin.
“Buh Abbhi.”
Tare numfashinta Abbhin ya yi da faďin “ kar na sake Jin kalar wannan maganar a bakin ki, is that clear?.”
“ Okay Abbhi.”
Fita ya yi daga dakin ita ma ta koma ta kwanta tare da kunna datar wayarta dan yaran na wajen Ammi da
Neneh.
Wani message nè ya shigo anyi save number da “My Favorite Headache 😒
🦋😒 💖.”
Bude message ďin ta yi ta fara karantawa a hankali “Ke ma kin san an wuce time din da zan yi sa in sa
dake, come outside naga wannan kyakkyawar fuskar naki mai cike farinciki, and wear something sexy
we’re going out.”
Murmushi ta yi mai kyau sannan ta masa rply da faďin “A Ina zan bar yaran.”
😒
“Mai ye amfani wannan fitinanniyyar tsohuwar.?”
“Watch your tongue she’s my Grandma 😒.”
“Sooo what , malama ki fito I’m starving.”
“Na taho maka da abinci nè?.”
😌
“yunwanki nake ji ai ba na abinci ba, just hurry up before i kick the bucket.”
“Ina off abi you don forget say i born pikin.”😌
“Come out jare kullum a nan kika fi ķwarin pidgin make I no change am for you ooooo.”
Emoji din dariya kawai ta tura masa sannan ta tashi ta ķara shiga wanka tare da canza pad da kuma wasu
abubuwan.
Wani lingerie dress ta saka tare da ďora wani dogon himar a kai, dan har yanzu kwai kayanta a gidan
Neneh, sannan ta fito daga cikin falon da ya rage daga Ammi sai Neneh da wasu danginsu na Maiduguri.
“Ke Sirikar Kyari Ina za ki da daren Allah, yayin da halittun Allah ke bacci.” In ji cewar Neneh dake riķe da
Aida.
“Ina ruwanki wai da ni?.” Ta faďa tare da murguda mata baki sannan ta fara kokarin tafiya a hankali.
“Ba da ke ake bane?.”
Ammi ta faďa a zafafe
“Ke ko da ki bar tijararriyyar ta ci gaba da abin da ta saba.” Neneh ta faďa tare da cuno baki.
Sai da ta harari Neneh sannan ta ce “Daman Ammi Papan yaran nan nè zan kaiwa saķo.” Ta yi maganar a
sanyaye.
“Ahhh, kaji sabon kwartanci, toh aikam babu inda za ki, ya latsi bulus na shekaran jiya da na jiya ya jira
kuma sai kin yi arba’in.” Neneh ta faďa tare dallawa Liya Harara.
“Na miki maganane?.” Inji cewa Liya.
“Malama wuce ki shige ciki.” Ammi ta faďa tare da amsan abin da wata cousin dinta ke mika mata…..
Ga update din yau 😂😌
The Regret ❤️
Not Edited 🚫👎
Pending Amarya ce ❤️
https://whatsapp.com/channel/0029VbAyucH7j6g0IDCpPi2V
Faridatool Noor 🦋
JAW 🦋
Surah Al-Hadid (57:4)
“And He is with you wherever you are.”
Let’s Dive in ✌️
Bismillahir Rahmanir Rahim ❤️
Pending amarya 63………………..
“Ke ko da ki bar tijararriyyar ta ci gaba da abin da ta saba.” Neneh ta faďa tare da cuno baki.
Sai da ta harari Neneh sannan ta ce “Daman Ammi Papan yaran nan nè zan kaiwa saķo.” Ta yi maganar a
sanyaye.
“Ahhh, kaji sabon kwartanci, toh aikam babu inda za ki ya latsi bulus na shekaran jiya da na jiya ya jira
kuma sai kin yi arba’in.” Neneh ta faďa tare dallawa Liya Harara.
“Na miki maganane?.” Inji cewar Liya.
“Malama wuce ki shige ciki.” Ammi ta faďa tare da amsan abin da wata cousin dinta ke mika mata.
Kamar ta rushe da kuka, jiki a sub’ule ta wuce ta shiga ďakinsu ba dan ranta ya so ba.
ko da ta shiga ďakin wayarta kawai ta ďauka ta tura masa saķon ba za ta samu damar fitowa ba.
Cikin seconds 30 ta ga reply dinsa.
“Dama na san za’a rina, an gama komai kema gobe zaa kawo naki lefen na sunan Yaran nan, and I need
to discuss something important with you, Please.”
Murmushi ta yi sosai sannan ta masa reply da “Ba Lallai fa na fito ba yanzu, ance ba zaka kara ganina ba
sai nan da 40 days 😂.”
“Which 40 days you’re kidding me right?.”
“Wallahi I’m serious, toh mai kake son fada min let’s discuss anan din.”
“Wallahi Fatima maganar nan ba na waya bane, ki san yadda za ki yi ki fito.”
“They won’t let me out manaaaa 😫😂.”
“Ta ya kike fita before?.”
“Ta sanadin Abbhina mana 😒.”
“Then Ina mijinki I command you ki fito ko ranki ya bace ko ta sanadin waye.”
“ka ji ķarfin hali kuma🙄.”
Ganin har an yi minti biyar da tura masa message ďin ķarshen bai mata rply bane ya sanyata maida hijab
ďinta ta na mai tunanin hanyar da zata fita.
Ta na cikin wannan tunanin su Ilham suka shigo hannunsu riķe da ledoji na kayan maķulashe.
“Yaya kin ga na siyo miki favorite drink ďinki.” Ily ta faďa hoping yayarta za ta mata magana.
“Wai wannan kuma mai aka mata take ta hawa kamar yeast daga ganin mutane kuma sai ki wani ďaure
fuska?.” In ji cewar Reedah dake cire earrings ďinta a bakin madubi.
“Bari mu gayyato ma ta Yusrah ta ďan ci mata mutumci za ta dawo daidai.” Rashanda ta faďa tare da
kyalkyalcewa da dariya.
“Wannnan kuma matsalar ku ce, wani ya fada min ya zan fita daga gidan nan na sami Hydar abeg.”
Liyana ta faďa a sanyaye.
“Eleven fa ta yi mai zaku yi?.” In ji cewar Reedah.
“Ka ji ya’r iska?, Ina ruwanki da abin da zamu yi?.” Liya ta faďa a fusace.
“Allah ya baki hakuri, ku taho mu fita a sace I think babu Wanda zai gane ki a cikinmu.” Reedah ta fada
tare da gyara zaman gyalenta da bata cire ba.
Daga haka su duka hudun suka fice daga ďakin, sun ci saa kam domin babu kowa a living room ďin.
Komawa suka yi gaba ďayansu suka barta ita ta ķarasa fita daga falon.
karo ta kusan ci da shi, dan har ya gaji da jiranta ya nufo cikin gidan da kansa.
Da sauri ya fizgota jikinsa tare da nufar garden din gidan da ita.
Kujerun dake wajen na hutawa ya nufa da ita tare da zama kanta a kan kafaďarsa.
“Ya Alih.”
“What’s wrong?.”
“Ka ce zamu yi magana, kuma kayi shiru, bacci nake ji.” Ta yi maganar a hankali dan haka kawai zuciyarta
Ke dukan uku uku.
janyeta ya yi daga jikinsa, Sannan ya karkato da ita suna masu fuskantar junansu.
“Fatima.” Ya kirata da kakkausar murya
“Naam.” Ta amsa a sanyaye tare da ďago kanta.
“Fatimah Kar kiyi tunanin na ci zarafin ki ko kuma wani abu da zai sanya ki Jin kaman ba kiyi min yadda
ya dace ba, let me go straight to the point, please Fatima ki amince na auri Marwa dan saboda future
ďinsu Alynerh, yanzu abubuwa da dama na judging dina akan wannan abun da muka aikata cikin rashin
sani.” Ya yi maganar tare ďurķusawa a kan gwiwowinsa.
“You called it rashin sani, in dai addinin da nake yi kake yi na tabbatar da cewa tun da ka shiga 10 to 15
years ka san hukuncin Zina da kuma haramtata da akayi, toh daman tun da can ba sona kake ba, go on,
marry her idan hakan ne zai sanya ka farinciki.” Ta ķarashe maganar hawaye na zuba a idanunta.
“Wallahi Ke nake so a yanzu, I’ve feelings for her buh naki ya danne.” Ya faďa tare da matso da fuskarsa
gabb da nata.
“Oh really, by the time da zaka haďa jiki da ita kuma nata zai danne nawa ko?, Aliyyu kayi duk abin da ya
dace, lokacinka ne, sai yadda kayi da shi.” Ta faďa tare da ķoķarin tashi daga wajan.
Jawo ta ya yi tare da ķoķarin haďe bakinsu waje ďaya, wani fitila mai hasken gaske ne ya dallo su wanda
hakan ya sanya shi saurin hankaďeta tare da tashi dan ya san ba zai wuce Neneh ba ce.
“Aahhh lallai, yanzu har nan kuke iskancin naku kenan?, dole gobe Usama ya samo min masu welder su
samin ķofa a wajen nan.” Ta ķarashe maganar tare da ķara dalle fuskokinsu da fitilar.
“Daďinta dai auren sunnah ne a tsakaninmu.” Aliyu ya faďa tare da bin ta kusa da ita ya na kokarin
wuceta.
Sai da ta sakar masa duka a baya sannan ya wuce ya na dalleta da harara duk da duhun dake wajen.
“Uhhhmm, Karina uwar soyayya kya shiga ciki kiyi wa Salamatu bayani, dan ni dai kalar wannan da safe
ake yin sa.”
“Ko da rana ake yi mai ruwanki?, sa ido.”
“Borin kunya ne kuma wannan, ki shigo ciki shine magana.” Neneh na faďin haka ta bar wajen.
Sai da ta raka Nenehn da harara sannan ta tattare hijab ďinta, ta nufi building ďin gidan.
Ammi na falo a tsaye ana ta faďin ina Liyana ta shiga saboda yaran ke ta kuka, an tambayi su Rashida
suma sun ce basu ganta ba.
“Ai sai da na bincikota, ta na can ta bajesu Lantana da Talatu a barbaje, toh ni dai Allah shi kyauta ace
yarinya bata Jin magana, ta girma bata san ta girma ba, a zamaninmu idan muka haihu sai mu kusan
shafe shekaru biyar ba mu ga mijinmu ba, kuma mu zauna lafiya.” Nenehn ta faďa tare da yin upstairs
dinta.
Hawaye na zuba a idanunta ta karasa shigowa cikin gidan da Ammi Ke tsaye da Alynerh a hannu ta na
jiran shigowarta.
“Wai Fatimah mai sa ba kya Jin magana ne a rayuwarki, yaran da suke naki ba na riķo ba ki basu Nono sai
ya zama bala’i?.” Ammi ta yi maganar ta