Author : HAUWA A USMAN Category : Complete Novels
kiyi ta maimaita innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
cikin sanyin jiki Sanah tace " to, amma wallahi sosai gaba na ke fad'uwa fa,
Khulud ta dafa ta had'i cewa " karki damu kinji my Sanah?
"In sha Allah babu abinda zai faru,
kuma ma baga ni ba, tayi maganar tana dariya,
kai Sanah ta d'aga mata cikin sanyin jiki batare datace komai ba,
suna isa clubs d'in su Sanah ta koma gefe ta zauna tare da rafka tagumi hannu bibbiyu,
hango ta Khulud tayi, a zaune a hankali ta nufe ta had'i da durk'usawa a gabanta tasa hannunta ta zame tagumin da Sanah tayi,
tace " my Sanah meke damunki ne?
"Nima ban sani ba haka nan nake ji na wani iri,
tayi maganar kamar zatayi kuka,
Khulud tace " in Allah ya yarda babu abinda zai faru sai alkhairi,
karki damu kinji my Sanah?
"To Sanah tace, Khulud ta rik'o hannunta tace " to taso muje muyi fara wasan ko,
Sanah tace " a'a ban jin zan iya buga ball d'innan,
ido Khulud ta zaro had'i cewa " tab! kema kin san baki isa ba,
Allah sai kinyi kinji ma na rantse,
salan a cinye mu yau, Sanah ta d'aga kai ta kalli Khulud tace " kiyi hak'uri amma yau banyin ball,
baki Khulud ta zumb'uro had'i da zama a gefen Sanah tana tab'a baki zatayi kuka,
Sanah tace " ke meye kuma na kuka?
Khulud tace " Allah idan baki san nayi kuka to ki taso muje muyi ball,
idan ba haka ba yau na kwana ina kuka,
Sanah tayi dariya tana kamo hannun Khulud tace " shikenan tashi muje mu fara,
dariya Khulud tayi tace " thank you so much my Sanah,
sosai wasa ya d'auki zafi, sai buga ball suke yi,
har lokacin babu 'yan b'angaren da suka ci,
ganin haka ya zuciya Sanah dan haka ball d'in na shigowa hannunta, ta bugata da k'arfi,
da hannu 'yar d'aya b'angaren ta tare ball d'in dan haka akayi musu fanaret,
duk suka tsaya cak aka saka Sanah ta sake buga ball d'in.
_Wayyo tsautsayi da k'addara_
*RASHIN SANI* yasa Sanah buga ball d'in da iyakacin k'arfinta,
bisa tsautsayi sai ball d'in ta daki Khulud sosai a ciki,
garin Sanah ta juya ta kuma yiwa Khulud k'afa a cikin ta,
Khulud ta k'urawa Sanah ido tana daga tsaye tace " my Sana....
Bata k'arasa ba ta zube k'asa,
a kid'ime Sanah ta nufi Khulud da gudu tana kiran sunanta da k'arfi Khulud!!!!
saboda tsabar rud'ewa yasa Sanah mantawa ta kuma taka cikin Khulud da takalmin 'yan ball akan ruwan cikin ta,
tsananin azaba ne yasa Khulud sakin mahaukaciyar k'ara,
kana idanuwanta suka kakkafe numfashinta ya d'auke cak,
da k'arfi Sanah ta shiga jijigata tana kiran sunanta da k'arfi cikin matsanannacin kuka,
ganin bata motsi yasa Halan tafiya staffroom da gudu ta kira Malamai,
da gudu su Sir Moli suka k'araso a kid'ime Moli ya kalli Khulud,
yaga kwata-kwata bata numfashi,
da sauri ya sunkuya kusa da ita yana tab'a k'irjinta, gami da kunnensa a hancinta,
jin yayi shiru yasa Sanah sakin mahaukacin kuka ta rirrik'e shi kamar zararariya tace " meya same ta?
Rik'e hannunta yayi yana kallan Sir Jeeb tare da girgiza masa kai yace " bata numfashi ina ganin kamar fa ta mut..........
Bai k'arasa ba yaji Sanah ta fad'o jikinsa,
bata numfashi idanuwanta sun kakkafe............
MOMYN ZARAH
_*RASHIN SANI.......*_
*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_
```Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh```
1⃣2⃣
A gigitacce Sir Moli ya mik'e rik'e da Sanah a hannunsa,
yana jijjiga ta had'i da kiran sunanta da k'arfi,
Sanah! Sanah!! Sanah!!!,
duk ya rud'e ya fita hayyacinsa,
jikinsa sai kerrrrma yake, yana rungume da ita, ya nufi fanfo da gudu,
duk Malamai da students dake wajen tsayawa sukayi kallan ikon Allah,
kanta ya tara a bakin fanfon yana jijjigata,
while yana cigaba da kiran sunnata da k'arfi,
ajiyar zuciya ta sauke da k'arfi ta bud'e idanta a hankali,
shima ajiyar zuciyar ya sauke had'i da runtse idansa,
da sauri Sanah ta mik'e daga jikin Sir Moli,
dakyar tace " ina my Ulud?
Sai lokacin hankalin Sir Moli ya koma ga Khulud,
da sauri ya mik'e daga durk'ushen dayake,
ya nufi inda Khulud ke kwance ya sungume ta yayi sick bay da ita,
Sanah da Halan suka bi bayansa suna cigaba da kuka,
da sauri aka kwantar da ita akan patient bed,
school doctor d'in su ya fara dubata,
Sir Jeeb da sauri ya fita yayi dialing number Abbu,
dayake kowacce students akwai number parent ko guardians d'inta,
bugu d'aya Abbu yayi picking ganin VP Roni ke kiransa,
hankalin Sir Jeeb a tashe yace " Assalamu Alaikum,,,
"Amin wa'alaikassalam Abbu ya amsa,
bayan sun gama gaisawa, Sir Jeeb yace " Sir please kuzo makarantar yanzu,
gaban Abbu yayi muguwar fad'uwa,
a hankali yace " innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
lafiya dai ko?
Abbu ya tambaya a k'agauce, VP yace " lafiya, amma ba lau ba,
a kid'eme Abbu yace " meya faru?
"Khulud Rawan ce ba lafiya,
da sauri Abbu ya mik'e yana cewa " meke damunta?
"Wallahi bamu sani ba amma doctor yana duba ta,
"ok to gamu nan, Abbu ya fad'a yana fita,
hankali tashe ya kira Didi,
" hello Dide yace,
cikin rawar murya Abbu yace " ka shirya yanzu zamu je Roni,
a firgice Didi yace " lafiya, meke faruwa?
Abbu yace " wallahi nima ban sani ba,
yanzu Vice Principal d'in su ya kira ni,
yace Khulud bata da lafiya, tsaki Didi yayi yana komawa kan sofa ya zauna,
" yanzu dan Khulud bata da lafiya sai mun kwasa rid'i-rid'i har mu biyu munje?
Yayi maganar cikin dauriya yana danne abinda yake ji,
Abbu yace " please karka yi min irin halin naka nako in kula,
ya za'ayi akira daga makaranta a sanar damu 'yar mu bata da lafiya amma ko a jikinka,
Didi yace " to ai kai ne da wata magana,
saboda bamu da aikin yi sai mu tafi Roni har mu biyu dan Khulud bata da lafiya,
kai ma da zaka ji tani da bazaka je ba,
Abbu yace " idan ban je ba waye zaije?
Didi yayi shiru, Abbu yace " ai bama ni kad'ai zani ba,
" kai da wa zaka je?
" Ina ruwanka tunda kai dai baka zuwa shikenan,
Abbu ya kashe wayarsa yana mamakin kara da kawaici irinna Rawan,
Didi ko yana jin Hamraz ya kashe waya,
ya kwantar da kansa akan sofa had'i da runtse idansa,
dan Allah ya sani yana mugun san Khulud,
duk cikin yaransa babu kamarta,
yafi santa fiye da kowa, kawai dai yana kara da kawaici ne saboda tsakaninsu da Hamraz, kuma Hamraz yana iyakar bakin k'ok'arin sa wajen tsayawa iyalin su akan komai,
ko kayan abinci da school fees kafin shi ya biya sau d'aya,
Hamraz ya biya sau goma, haka ma a b'angaren cefane, da kula da iyayen su komai Hamraz keyi bai jiransa,
saboda akwai so, k'auna, sabo da matsananciyar shak'uwa a tsakanin su,
tun suna yara suka taso da san junun su,
kamar yadda suka ga Ganez da Danish na san junan su har yau har gobe.
Juju dake kitchen tana girkin abinci,
ta fito da sauri,yadda taga yanayin Didi ya canja ne ya tabbatar mata ba lafiya,
a hankali tace " lafiya Dide?
Shiru yayi bayyi magana ba,
komawa tayi kitchen ta rage wutar girkinta sosai,
kana ta dawo, ta zauna a kusa dashi,
cikin sanyin jiki ta dafa kafad'arshi,
tace " lafiya, meke faruwa?
Ta kuma tambayarshi a karo na biyu,
ganin bashi da niyyar yin magana ne,
yasa ta tausasa muryata k'asa-k'asa tace,
koma me ke damunka kayi addu'a,
sai Allah ya sausauta maka shi,
ya kuma yi maka maganin matsala da damuwarka,
ko kayi ta maimaita,
innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
tana kaiwa nan ta mik'e cikin sanyin jiki zata bar wajen,
tausayinta ne ya kama shi, dan haka yayi saurin rik'o hannunta,
yace " Khulud ce bata da lafiya,
yanzu Abbu ke sanar dani Vice Principal d'in su ya kira shi,
" meke damunta?
Ta tambaye shi,
" ban sani ba, dan ni ko tambayar Abbun ma ban tsaya yi ba,
shiru tayi had'i da k'ura masa ido,
kana tace " Allah ya sauke, Ubangiji ya bata lafiya,
"Amin yace yana kallan kwayar idanta,
murmushi tayi masa kana tace " kasan dai yanzu ba 'yar mu bace,
sai dai muyiwa Abbu da Mamu jaje,
dan nasan yanzu haka ma suna cikin tension,
tayi maganar tana dariya,
danta kwantarwa da Didi hankalinsa,
dariya yayi shima kana yace " kamar ko kin sani,
ke kinji yadda Abbun ya kira ni a kid'ime wai in shirya zamu Roni,
dariya tayi, zatayi magana sai kuma tayi shiru,
cikin alamun jimami tace " Sanah fa?
Dide yace " me?
Tace " Allah sarki 'yata Sanah,
Allah kad'ai yasan cikin mawuyacin halin datake ciki yanzu,
cikin jimamin shima Dide yace " wallahi kuwa,
nasan yanzu tana can cikin tashin hankali da kuka,
ni nama fi jin tausayin Sanar akan Khulud,
murmushi Juju tayi ta mik'e tace " bari na dubo abinci,
Mamu dake tsaye bakin k'ofa,
ta share hawayenta, ta juya ta koma part d'in su.
Abbu na kashe waya ya kira Ziyad, Zafran ya sanar da su,
batare da wani b'ata lokaci ba,
suka d'au hanyan Roni, Ziyad na driving,
Zafran na gefensa, Abbu yana baya,
sai da suka hau hanya sannan Abbu ya kira Mamu ya sanar da ita,
sosai hankalinta yayi masifar tashi,
ta nuna masa kamar bata sani ba.
A makaranta ana ta faman k'ok'arin maido da numfashin Khulud,
amma kwata-kwata babu alamar dawowarsa,
wata irin gigitacciyar k'ara Sanah ta saka,
had'i da fasa kuka ta fad'a jikin Khulud ta rungume ta tana ihuuun kuka,
" please my Ulud ki tashi, kinyi man alk'awarin duk abinda nasaki zakiyi,
idan kuma na hana ki zaki bari,
dan Allah ki tashi, wallahi idan kika mutu nima mutuwa zanyi,
bazan tab'a rayuwa cikin farin ciki da walwala ba,
matuk'ar baki tare dani,
a hankali tasa hannu tana marin kuncin Khulud a hankali,
tana cewa " ki tashi kince bazaki ta tab'a rabuwa dani ba,
kince tare zamu girma muyi aure,
dan Allah ki tashi my Ulud,
nayi miki alk'awarin bazan tab'a barinki cikin k'unci da matsalar rayuwa ba,
nayi miki alk'awarin bazan tab'a barinki cikin damuwa da masifa ba,
nayi miki alk'awarin zan zame miki garkuwa daga dukkan matsalolinki,
zan zame miki maganin dukkan damuwa da k'uncinki,
dan Allah ki tashi ta k'arasa maganar cikin rikitaccen kuka tana d'ora kanta akan k'irjin Khulud,
duk wanda yaga yadda Sanah ke kuka tana magana tana jijjiga Khulud abin sai ya bashi tausayi komai rashin imanin mutum,
sai yaji zuciyarsa ta karyae,
Halan na gefe na aikin kuka,
Sir Jeeb zaune kan sofa ya zuba musu ido cike da tausayin Sanah.
A hankali Sir Moli ya d'ago pure red eyes d'insa ya kalli Doctor yace " wai ya ake ciki ne har yanzu shiru?
Doctor yace " hmmm gaskiya ciwon babba ne dan ko numfashi batayi,
Sanah ta k'ara sakin rikitaccen kuka,
Sir Moli yace " kamar ya?
" gaskiya koma me ke damun yarinyar babban ciwo ne,
Sir Jeeb yace " wai har yanzu baka gano ciwon ba?
" Eh, ban san takaimaiman abinda ke damunta ba,
ni fa ina ganin mutuwa zatay........
gigitacciyar k'arar da Sanah ta kwalla ce ta hana Doctor k'arasa abin da yayi niyyar fad'a,
a gigice ta mik'e tsaye had'i da d'ora hannu aka tana rikitaccen kuka mai ban tausayi,
" a'a wallahi na tabbatar Khulud bazata tab'a mutuwa ta barni ba,
ko ita kanta mutuwar zataji kunyar d'aukar Khulud a gaban ido na,
kuma koda mutuwar ce da gaske tazo nasan Khulud zatayi iya k'ok'arin ta na ganin bata tafi na barni ni kad'ai ba,
tayi maganar a matuk'ar rud'e,
gaba d'aya ta fita hayyacinta, ta kid'ime ta fita fit daga hayyaci da nutsuwarta,
jikinta sai rawa da kerrrrma yake,
ganin yadda ta rud'e ne yasa Sir Moli dakawa Doctor tsawa " kai baka da hankali ne, baka san aikin ba ne?
Yayi maganar a tsawace, da sauri Doctor da Sir Jeeb suka kalle shi cike da mamaki,
da saurinsa ya rik'e Sanah ya sunya hannu a hankali yana goge mata hawayenta,
cikin sanyin murya yace " kiyi hak'uri Khulud bazata mutu ta barki ba kinji?
Kai ta d'aga masa, " ki rink'a yi mata add'u, ki dai na kuka, tunda kinga bata san kukan ko?
Ta kuma d'aga masa kanta a hankali,
" magana zakiyi kinji ban san nodding kai,
da sauri tace " na dai na, ban k'arawa,
ya shafa kanta yace " yawwa good girl,
cikin sanyin murya ta kuma cewa " bazata mutu ba ko?
Tayi maganar hawaye na gangaro mata,
cike da tausayinta ya d'aga kai,
" ka tabbatar zata tashi?
Ta kuma tambayarsa,
" in sha Allah, ya bata amsa,
bazato yaji ta fad'a jikinsa tana cewa " thank you so much Sir,
tayi maganar tana k'ara shegewa jikinsa,
murmushi yayi yana k'ok'arin zame jikinsa daga nata,
da sauri ta k'ara matseshi, tana cewa " I will never forget you in my life,
yayi murmushi kana yace " are sure?
" Yes , tace tana cigaba da kukanta,
a hankali ya zame jikinsa, duk da tana k'ok'arin k'ara shigewa jikin nasa,
ya mik'e yana kallan Sir Jeeb,,
da mamaki ya gama kashe shi a tsaye,
ba Sir Jeeb kad'ai ba, duk wanda ke wajen yana cike da tsantsar mamaki da al'ajabi,
ya lura sarai da reactions d'in su amma ya basar, ya tamke face yace,
" ka kira gidan nasu kuwa?
"Eh na kira su tun d'azu ma,
Sir Moli ya kuma cewa " tun yaushe ka kira su?
" Tun wajen 2 hours back, yaci ace sun iso ma,
yayi maganar yana duba agogon hannunsa,
" ka k'ara kiran su please, asan abinyi tun da wuri,
"ok yace yana ciro wayarsa daga aljihu,
yana k'ok'arin kiran su, kiran Abbu ya shigo,
da sauri Sir Jeeb ya d'aga,
Abbu yace " gamu mun k'araso muna bakin get,
kana ina?
Da sauri Sir Jeeb yace " gani nan zuwa,
ya kashe wayar yana kallan Sir Moli,
yace " sun k'araso fa, Sanah dake zaune bakin gadon da Khulud ke kwance ta d'ora kanta saman chest d'inta,
ta k'ara runtse idanta hawaye na zubowa.
Da sauri Sir Jeeb ya fita ya tari su Abbu,
hannu Sir Jeeb ya mik'awa Abbu had'i da d'an risinawa,
"Assalamu Alaikum, sir Jeeb yace,
fuskar Abbu d'auke da murmushi ya amsa,
Sir Jeeb yace " muje office,
"Ok cewar Abbu yayi gaba,
Ziyad da Zafran na bin su a baya,
zama Abbu yayi a kan kujerar dake fuskantar Sir Jeeb,
ajiyar zuciyar ya sauke kana yace " please Sir kuyi hak'uri bamu san meya faru ba,
muna staffroom Halan ta zo ta kira mu,
saboda yadda hankalin mu yake a tashe bamu tsaya tambayar abinda ya faru ba,
Abbu yace meya same ta?
" Har yanzu Doctor yana kanta,
ba'a gano takaimaiman abinda ke damunta ba,
"tana ina yanzu?
Mik'ewa Sir Jeeb yayi yace " muje,
duk suka mik'e suka bi bayansa,
da sallama Abbu ya shiga cikin sick bay,
duk Malaman dake wajen suka amsa,
ganin yadda idanuwan Khulud yayi fari fat,
babu alamar bak'in kwayar ido,
ga idan ya kakkafe
yayi masifar d'agawa su Abbu hankali,
da sauri suka nife ta, Abbu na cewa " Subhanallah,
hannun sa na rawa ya d'ago Khulud yana jijjiga ta had'i da kiran sunanta,
Ziyad da Zafran kasa motasawa suka yi daga inda suke tsaye,
zuciyar su ta karye sosai,
sun shiga rud'u da tashin hankali,
Abbu ya d'ago ya kalli Doctor da idanuwansa da suka gama zama yin jajir,
muryarsa na creaking yace " please Doctor meke damunta?
"Nayi iyakar bakin k'ok'arina wajen gano abinda ke damunta amma na kasa,
Doctor ya fad'a cikin sanyin murya,
a hankali Abbu yasa hannu ya d'ago kan Sanah dake ta kuka kamar ranta zai fita,
d'agowa tayi ta kalle shi had'i da k'ara fashewa da rikitaccen kuka,
tace " Abbu na kashe my Ulud da kai na,
ni da kai na buga ball, na kuma naushe ta a cikinta, sannan na taka ta da takarmin 'yan ball a cikinta,
dan Allah ka bata hak'uri kace mata tashi ban k'arawa,,
*_RASHIN SANI_* ne yasa ni yin hakan,
wallahi Allah Abbu ban sani ba na buge ta na kuma taka ta,
ni da kai na yiwa kai ma illa,
ni da kai na, na kashe my Ulud,
ni da kai na, na illata rayuwa ta da zuciya ta,
bazan tab'a yafewa kai na ba,
bazan tab'a sake tsintar kai na cikin farin ciki da walwala ba,
bazan tab'a sake dariya da murmushi ba, har na mutu,
duk wani abu na jin dad'in duniya da walwala na haramtawa kai na har abada,
ko aure bazan tab'a yi ba Abbu,
ta d'ago hannunta da k'afarta tana yi musu wani irin kallo,
kana tace " bazan tab'a yafe muku ba,
mutuk'ar my Ulud ta mutu sai na azabtar daku,
sai na azabtar da kai na rayuwa ta,
azabtarwa mai rad'ad'i, ta k'arasa maganar cikin matsanancin kuka,
mai cin rai.
Kanta Abbu ya shafa, kwalla na taruwa a idansa,
kana yace " ba laifinki bane Sanah,
da sauri ta d'ago kanta ta kalle shi,
tace " Abbu laifin waye idan ba laifi ba?
"Wallahi Abbu ni da kai na, na buge ta na kuma taka ta, a kan ruwan cikinta,
tayi maganar kamar zararriya,
" k'addara ce tasa faruwar hakan,
karki d'orawa kanki laifiin kinji Sanah?
Zata yi magana Abbu yayi saurin mik'ewa had'i da sungumar Khulud,
da sauri su Ziyad da sukayi mutuwar tsaye suka tare shi,
jikin Zafran na rawa ya karb'i Khulud daga hannun Abbu,
jikin Sanah na rawa ta mik'e tabi bayan su,
saboda sauri har tana tuntub'e,
cike da tsantsar tausayinta Sir Moli ya bita da kallo har suka fita,
kishingid'a yayi akan sofa had'i da lumshe idanuwansa,,
kafin su fito har Halan tasa Juniors sun fito musu da kayan su kaf,
babu abinda ta bari, ko tsinke,
Ziyad ya bud'e