Author : HAUWA A USMAN Category : Complete Novels
yake hutawa.
Khulud na kitchen tare da Hanash tana girki yana taya ta,
ya motsa jikinta ya rungume ta baya yace " Allah yasa nan da 8 months mu samu baby,
ido ta zaro tace " 8 months kuma?
Yace " eh! man, ai nasan zuwa yanzu na saka kwai na,
ya fad'a yana shafa cikinta,
dariya tayi tace " da wuri haka?
" To me zamu jira!?
Tace " wai meyasa kai kullum baka da wata magana sai ta haihuwa da yara,
kab'arsa ya d'ora bisa kafard'arta yace " wallahi Khulud bani da burin daya wuce naga yara na a duniya,
ina mugun san yara da yawa Allah,
kinga ma Jadda kullum bata da wata magana sai ta samun yara,
kullum tambayarta matarta nada ciki,
murmushi tayi kana tace " Allah ya bamu masu albarka ya amsa da " Amin,
girgikin ta gama ta zuba a food flask,
ta juyo ta kalle shi tace " to ga na my Papu,
dariya yayi yace " shiyasa kullum babu bashi da wata magana sai taki,
dariya tayi tace " ai haka ake so,
to mu gama cin abincin sai mu kai musu ko?
Cikin zumud'i tace " da ni zakaje,
"eh! yace , yana fita da abincin,
sai da suka gama kintsawa kana sukayi gidan Mimmee,
part d'in Jaddah suka fara shiga saboda kar tayi musu k'orafi,
zaune suka iske ta a parlor,
tana ganinsu ta mik'e idanta nakan cikin Khulud,
tayi murmushi tace " mai ciki da kanki, meyakun kiyi mana waya mu muzo?
Dariya Khulud tayi tana sunne kanta,
Jadda tayi murmushi tace " kin ganni nan harna fara siyan kayan haihuwa ta fad'a jawo wata leda,
bud'ewa ledar tayi ta shiga ciro kayan jarirai kala-kala,
Hanash yayi dariya yace " kai Jadda wannan ai har kin fimu zamud'in haihuwar,
tana dariya tace " ai dole d'an Hanash guda,
ai duk ranar da aka haife yaron nan zaiga gata,
ji nake kamar na jawo watannin haihuwar,
murmushi sukayi kana sukayi mata sallama,
suka shiga part d'in Mimmee,
babu kowa a parlor'n, dan haka Hanash yayi sallama da k'arfi,
Papu ya fito daga gyms room,
yana murmushi cike da so da jin dad'in ganinsu,
dan harga Allah Papu yana mugun san Khulud,
yana jinta har cikin ransa, yana jin babu abinda bazai iya yi mata ba,
kullum cikin tambayarta abinda take so yake,
amma amsar d'aya ce babu,
har jiran ranar dazata nemi wani abu daga gare shi,
har k'asa suka durk'usa dukkansu suka gaidashi,
ya amsa cikin fara'a,
Hanash yace " Mimmee fa?
Papu yace " sun tafi kasuwa dasu Wajnah,
Hanash yace " dama 'yar gaban goshinka ce tayi maka girki,
Papu yayi murmushi yace " masha Allah, a zubo min naci,
Khulud ta mik'e ta shiga kitchen ta d'auko plate da serving spoon ta zuba masa sakwara da miyar agushi data gashi dajin dry dish da sukunbiya had'i da ganda,
Papu yace " kai masha Allah gaskiya nagode sosai,
Papu ya zage yaci abincin sosai ya k'oshi,
ganin har yamma su Mimmee basu dawowa yasa su Hanash tafiya.
Su Khulud na tafiya kiran Sanah ya shigo,
da sauri tayi picking amma batayi mata magana ba,
Sanah tace " hello my Ulud!
Khulud tayi mata banza,
Sanah tace " kiyi hak'uri idan laifi nayi,
still Khulud batayi mata magana ba,
Sanah tace " kiyi man magana please,
fashewa da kuka Khulud tayi wanda yasa Hanash saurin yin parking,
yace " lafiya my wife,
bata kalle shi ba, tace " haba my Sanah ace har shiga wata na biyu amma baki zo kin ganni ba,
d'an tsoki Hanash yaja jin dailin kukanta kana yaja motar,
Sanah tace " kiyi hak'uri gobe zan zo na yinar miki kinji my Ulud,
cikin murna Khulud tace " Allah da gaske goben zaki zo?
Sanah tace " Allah nayi miki alk'awarin zanzo na yini ma,
cikin zumud'i Khulud tace " me zan dafa miki?
Sanah tace " no karki bawa kanki wahala,
ki bari idan nazo sai mu girka tare Khulud tace " OK badamuwa,
har suka isa gida Sanah da Khulud na waya.
Washe gari da wuri Sanah ta shirya,
driver ne ya kaita a k'ofar gidan ta sauka ta shiga cikin gidan,
tsaye ta ganshe sanye da jallabiya,
da gani yasan da zuwan nata ita yake jira,
"sannu da zuwa mayya makwawaciya,
uwar naci da jaraba,
an kore ki an kore amma dan tsabar jaraba da naci kin dage sai kin zo,
wannan wanne irin naci da jaraba ce,
bata kula shi ba, ta rab'e ta gefensa zata wuce,
da k'arfi Hanash yasa hannunsa ya fisgo ta ya dawo da ita baya,
kana yace " ke! ni sa'an uban ki ne da ina yi maki magana zaki wuce?
" Ko gidan da kike k'ok'arin shiga gidan uwarki ne?
Idanuwan Sanah sukayi jajir saboda tsabar ruwan bala'i,
amma ba damar yin magana,
ga abun gudu sai da ba gurin zuwa,
a cikin kwayar idanta ya hango tsantsar b'acin rai da ruwan masifar dake cinta,
murmushi yayi yace " oh! na manta da tantiriyar fitsararriya mara kunya nake magana,
idanta ta runtse a hankali, sannan ta bud'e had'i da had'iye abinda take ji ,
ta zagaye shi zata wuce,
da k'arfi ya kuma jawo ta had'i da kifa gigitaccen mari,
kana ya hankad'a baya ta fad'i k'asa,
nunata yayi da yatsa yace " wallahi kika kuma k'ok'arin shiga cikin gidan nan sai nayi miki jahilin bugu dan ubanki,
shegiya kamar gidan ubanta ko da gadanta cikin gidan,
still batayi mishi magana ba ta mik'e ta kakkab'a jikinta,
ta kalle shi ido cikin ido tace " kaci darajar masu daraja,
kaje kaci albarkacin alk'awarin daya yiwa Khulud,
kuma duk d'an halak cikekken mutum baya karya alk'awari,
k'ara d'auke ta yayi da mari,
sai da ta kifa saboda k'arfin marin,
kana yace " lalle 'iskanci da rashin kunyarki sun rik'a in banda haka kizo har cikin gida na ki nemi gaya mana magana,
to bari kiji matuk'ar san da kikewa Khulud gaskiya ne,
matuk'ar kina san farin ciki da walwalarta su d'ore kiyi nesa da ita da gidanta,
zatayi magana yasa hannunsa ya rik'o hannunta ya soma janta a da k'arfi har tana fad'uwa yana fizgota
sai da ya kaita har waje kana yacewa mai gadi " duk ranar daka k'ara barin wannan ta shigo a bakin aikinka,
Ita kuwa Khulud na parlor zaune tana zaman jiran Sanah,
haka kawai taji gabanta na fad'uwa,
a hankali ta mik'e ta shiga bedroom wajen Hanash,
ganin baya nan yasa ta lek'awa bathroom nan ba baya nan,
a hankali ta juya zata fito,
karaf idanta ya sauka akan Hanash dake tsaye bakin get yana zazzaga ruwan bala'i,
a kamar mutun ta hango a durk'ushe a gabansa,
a hankali ta k'ara lek'awa dan taga wanda ke durk'ushen amma bata gane ba,
bata wani damu data gani ba, dan haka tayi komawarta parlor ta zauna,
d'an tsoki taja had'i da kallan agogo,
a hankali tace " kodai my Sanah bazata zo ba?
Ta tambayi kanta,
baki ta tab'e kana tace " Hanash ko shida wa oho!
yake ta bambami,
gabanta ne yayi muguwar fad'uwa tunowa da tayi Sanah,
da sauri ta mik'e ta koma bedroom d'insa ta kuma l'ek'awa ta window,
ganin still bata ganin wanda ke durk'ushen yasa juyawa ta fita da gudu ta nufi harabar gidan...................
*Alhamdulillah wata ya tsaya, inai mana fatan muyi azumin Ramadan lfy, Allah kuma ya amsa mana ibadunmu*
MOMYN ZARAH
_*RASHIN SANI.......*_
*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_
```Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh```
_DIDECATED TO_
*MY AUNTY AYSHA ALIYU GARKUWA*
(```GARKUWAR MARUBUTA```)
~MY UWAR ROOM~
2⃣8⃣
Khulud ba ko takalmi ta k'arasa harabar gidan,
shi kuma dai-dai lokacin ya juyo yana niyyar shiga cikin gidan,
a tsakiyar compound suka had'u,
kallanta yayi kana yace " lafiya?
" Lafiya ta bashi amsa tana hangawa bayansa,
bayan nasa shima ya juya ya kalla kana ya mayar da idansa kanta,
yace " me kike dubawa?
" My Sanah ta bashi amsa,
" oh!, yace yana rik'o hannunta,
da nufin shigar da ita cikin gidan,
k'in binsa tayi ta tsaya cak, tana kallansa a marairaice,
yace " me kuma?
" Ina My Sanah ta tambaye shi,
wata muguwar fad'uwa gabansa yayi,
amma ya dake kamar babu komai yace " kamar ya?
Tace " bada ita na ganku yanzu kuna magana ba?
Murmushi yayi had'i da sungumarta cak,
yayi cikin gidan da ita, cikin sanyin murya tace " please my Sanah!,
murmushi ya kuma yi yace " oh! wannan duk d'okin ganin our Sanah ne?
Zata kuma yin magana yayi saurin had'e bakinsu,
yana cewa muje na gaisa da baby na,
dan nasan idan our Sanah tazo ba'a da lokaci na,
ya fad'a yana tura k'ofar bedroom da k'afarsa,
dole tasa Khulud yin shiru amma badan taso ba,
dan gaba d'aya hankalinta yana kan Sanahrta,
kwantar da ita yayi a kan bed yana cigaba da shan bakinta,
had'i da shafa jikinta, a hankali ya rabata da kayan jikinta,
kana ya kashe arna, Hanash bai wani samu yadda yake so ba,
dan Khulud bata sakar mishi jikinta yadda ya kamata ba,
bata kuma taimaka mishi wajen bashi hakk'in nasa ba,
dan kwata-kwata bata cikin hankali da nutsuwarta,
dama ko ba yanzu ba,
yana fuskantar irin wannan matsalar daga wajen Khulud,
dan kwata-kwata bata da wayewa a wajen sex,
kwanciya takeyi kamar ruwa sai dai shi ya sarrafa ta,
amma even romance Khulud bata iya yi mishi,
farko-farko ya d'auka kunya da rashin sanin, da kuma rashin sabo da abun ne ke damunta,
amma yanzu gashi kusan 3 months da auren su,
amma still bata san komai ba,
gashi shi ba abokanai ba balle ya kaita wajen matan su suyi mata bayani,
kuma shi kunyarta yake ji bai iya yi mata bayani da kansa,
dan gani yake kamar cin fuska da wulak'anci ne,
shi yadda ake fad'ar ana mugun jin dad'in sex shi bai wani ji,
dan wani lokacin ma sai yayi da gaske yake yin releasing,
tun abun bai damunshi har abun ya fara damunshi sosai,
wani lokacin koda yana cikin buk'ata hak'ura yake yi,
dan bai san shan wahala a banza,
bayan komai ya lafa tsakanin Hanash da Khulud ya jawo ta jikinsa ya rungume ta tsam a k'irjinsa.
Yana shafa kanta, deep down kuma yana sak'e-sak'e a ransa,
yana jin inama zai iya fitowa ya fad'a mata gaskiyar abinda ke ranshi,
sun kai 15 minutes a haka kana ta mik'e ta shiga bathroom,
tayi wankan tsarki ta shirya,
wayarta ta d'auka da nufin kiran number Sanah,
Hanash yayi saurin cewa " my love yunwa nake ji bani abinci naci,
ido ta zaro waje tace " yanzu fa kaci abincin,
yayi kyakkyawan murmushinsa kana yace " bakiga uban aikin danayi yanzu ba?
" Ai dole naji yunwa tunda kin zuk'e abincin dana ci,
bata kuma cewa komai ba saboda kunyar abinda ya fad'a,
ta juya da sauri ta nufi kitchen,
tana fita yayi saurin d'aukar wayarta ya sanya number Sanah a black list,
bata jima da fita ba ta dawo d'auke da tray,
sai da yaci abincin sosai kana ya shiga wanka.
Sai da Sanah ta tsaya a bakin get d'in da Hanash ya hankad'o ta,
taci uban kukanta sosai, kana ta share hawayenta,
ta mik'e ta nufi bakin titi,
tana tafe hawayen bak'in ciki na sake zubo mata,
Allah ya taimake ta tun kafin ta k'arasa bakin titin ta samu mai napep,
da sauri ta tsaida shi ta shiga ta zauna,
sai da ta zauna kana ta fad'a masa inda zai kaita,
sai da ta tsaya a bakin get d'in shiga gidan su,
ta saita kanta kana ta shiga, dan bata san kowa ya fuskanci abinda ke faruwa tsakaninta da Hanash,
bata tsaya shiga part d'in Halan ba tayi shigewarta part d'in Mamu kai tsaye,
a parlor ta iske Mamu tana jera abinci a dinning,
kallo d'aya Mamu tayi mata ta fuskanci da akwai matsala,
da sauri Mamu ta nufe ta tana cewa " ke lafiyarki?
Murmushin k'arfin hali Sanah ta k'ak'aro kana tace " meye Mamu?
Mamu ta kalle ta cike da mamaki tace " ban gane me ba?
" Bayan ga fuskarki nan da idanki sun nuna kinyi kuka,
rolling sexy eyes d'inta tayi kana tace " kuka kuma Mamu?
Mamu tace " ke ban san rainin hankali,
zanci ubanki wallahi, ni kike san yiwa yawo da hankali dan gidan ku?
Sanah ta zumb'uro baki kana tace " ni fa babu komai Mamu,
Mamu tace " wai tsaya ma, ba gidan Khulud kika tafi ba?
Sanah tace " ni kuma?
Ta fad'a tana zaro idanta waje,
" ni bance zani gidan Khulud ba,
Mamu tace " kan uba!, ke ni kike san maidawa mahaukaciya ko me?
" Idan ba gidan Khulud kika ce zaki ba, gidan ubanki kika ce zaki?
Sanah tace " a'a ni test naje nayi,
Mamu tace " oh! ni Allah na, Ubangiji ya kawo mu wannan lokacin,
yanzu Sanah ni zaki yiwa yawo da hankali dan ubanki yanzu kina nufin har kinje BUK,
kinyi test kin dawo ko me kike nufi?
Ta fad'a tana kallan Sanah a k'ufule,
Sanah tace " kai Mamu dan Allah kiyi hak'uri ki kwantar da hankalinki mana,
cikin fad'a Mamu tace " a gidan ubanki zan kwantar da hankalin nawa,
kin fita kin kuma dawo min gida kina kuka,
sannan kina neman raina man hankali,
amma ina zuwa,
ta fad'a tana nufar inda ta ajeye wayarta,
ta d'auka had'i dayin dialing number Khulud,
da sauri Sanah ta k'arasa inda Mamu ke tsaye fuskarta d'auke da tsoro tace " me zakiyi Mamu?
Mamu bata kula ta ba,
ta maida hankalinta ga abinda take yi,
Khulud na zaune kusa da Hanash taji wayarta na ringing,
bai wani damu ba saboda ya san ya saka number Sanah a black list,
da sauri Khulud tayi picking ganin number Mamu,
cikin girmamawa Khulud ta gaida Mamu,
Mamu ta amsa kana tace " Khulud ba gidanki Sanah tazo yanzu ba?
Sanah najin Khulud Mamu ta kira tayi saurin zaro ido,
Khulud tayi shiru ta rasa amsar da zata bayar,
a hankali tace " lafiya Mamu?
Mamu tace " 30 minutes back tayi man sallama tace " ta tafi gidanki,
amma yanzu ta dawo cikin damuwa kuma da gani taci uban kuka sosai,
ido Sanah tayi rolling,
itako Khulud idanta ta zaro tana yiwa Hanash kallan zargi،
kana ta cewa Mamu bani Sanahr,
Mamu tace " kamar ya na baki Sanah?
" Karku had'u kuyi min yawo da hankali,
tambayarki nayi dan haka ki bani amsa,
cikin sanyin murya Khulud tace " eh nan tazo,
Mamu tace " meya faru da har tayi kuka?
Khulud tayi shiru na d'an wani lokaci kana tace " wai cikinta ke ciwo,
Mamu tayi tsaki kana tace " Allah ya shiryeku,
cikin sanyin Khulud tace " Mamu bani ita please,
Mamu tace " ai kina da phone number ta ki kira ta mana,
Khulud zata kuma yin magana Mamu ta kashe wayarta,
bata k'ara bi takansu ba ta cigaba da subgoginta,
cikin sanyin jiki Khulud tabi wayar da kallo na wani d'an lokaci,
kana ta k'urawa Hanash ido tana karantar yanayinsa,
" me!?
Yace, yana kallanta, yayinda gabansa ke fad'uwa,
idanta na kansa tace " me kayiwa My Sanah?
Da sauri ya mik'e zaune kana yace " kamar ya menayi mata?
Idan Khulud na kansa still tana karantarsa tace " please me kayi mata?
" Wani abun tace nayi mata?
Ido ta kafe shi dashi batare data kuma cewa komai ba, shima shirun yayi bai ce komai ba,
wayarta ta d'auka,
tayi dialing number Sanah amma sai taji not reachable,
bata kawo komai a ranta ba ta aje wayar,
itama Sanah nacan na faman neman layin Khulud amma busy yake nuna mata.
Tunda Sir Moli ya lura matuk'ar ya keb'e da Sanah yana loosing control,
yasa shi yin nesa sosai da ita,
ya gujewa duk wani abu da zai keb'anta shi da ita,
dan shi kansa yana mugun mamakin kansa,
ya rasa meyasa yake shiga wani yanayi idan yana tare da ita,
ya rasa meyasa yake mance kansa idan yana tare da ita,
shi dai yasan a iya tsayin rayuwarsa bai tab'a kusantar zina ba,
ya zauna da turawa, larabawa, indiya da sauran jinsunan duniya,
amma bai tab'a tsintar kansa da irin haka ba,
sai akanta,
sosai ya dage da yin azumin nafila da istigfari,
saboda neman tsira dan gani yake kamar ya aikata babban laifi.
Yauma bayan sun gama attending lectures,
bata fito ba sai gab da magariba,
ganin yanayin garin na damuna ga kuma dare na neman kawo kai,
yasa Sanah yin sauri sosai,
tun daga nesa ya hangota,
yayinda dashi ke zaune cikin motarsa k'irar ferrari,
yana driving,
idansa ya lumshe lokacin dayazo zai wuce ta dai-dai ita,
yana san taimaka mata ya d'auke ta,
amma baijin zai iya yin haka,
dan gudu da kaucewa duk abinda zai kai shi ga keb'ewa da ita,
balle har a samu sab'anin da zai iya kawo shigar wani abun a tsakaninsu,
motar Sanah tabi da kallo had'i da tab'a bakinta tace " kai dai ka sani.
Hanash kwance akan k'ayataccen royal bed d'insa,
ya fad'a duniyar tunani,
idan da abunda yafi damunsa yanzu a duniya bai wuce na rashin gamsuwa da jin dad'in sex da bayayi ba,
saboda kwata-kwata baya samun ishashshiyar gamsuwa,
ba wai dad'i ko ruwan ni'ima ne Khulud bata dashi ba,
tana da ni'ima sosai kamar me,
dan ruwan ni'imarta har mamaki yake bashi wani lokacin idan yaga yadda take b'ulb'ulo da ruwa daga k'asanta,
shi abinda ke damunsa
kwata-kwata bata iya sex ba,
bama tasan yadda zata yi sex d'in ba,
ga rashin samun had'in kanta wajen sex,
da rashin taya shi, kwata-kwata bata iya komai ba,
ba kuma tasan komai,
shi kad'ai yake kid'ansa yake rawarsa,
ko romance bata iya ba, gashi bata iya sex styles and irin kukan kissa da nuna irin tana enjoying sosai ba,
sai dai ta kwanta kawai kamar ruwa,
shi zayyi komai ya sauka,
wannan abun yana matuk'ar damunsa,
dan tun abin baya damunsa yanzu har abun yazo ya zame mishi babban matsala,
dan wasu lokutan ma yana bala'in jin haushinta,
dan ji yake kamar ya rufe ta da duka,
ita ko irin shigewa jikin miji, da nanik'ar miji batayi,
ko irin zama akan cinyarsa batayi,
kwata-kwata ba romantic girl bace,
shi kuma gashi so hot romantic,
yana bala'in san irin rayuwa da soyayyar turawa,
yana san koyaushe ya kasance matarsa tana nanik'e dashi,
yana bala'in san mace mai san jiki,
da iya love, & romancing,
sosai yake cikin damuwa, ya rasa ta inda zai b'ullo mata,
ya rasa ta hanyar da zai bi yayi mata bayani,
yana tsaka da tunaninsa ta shigo,
zama tayi a bakin bed d'in fuskarta d'auke da murmushi tace " breakfast is ready Sir,
idanshi na kanta yace " ji babu ko d'an sexy abu balle romantic,
babu even kiss, just breakfast is ready,
ya fad'a cikin ransa,
a fili kuma yayi mata guntun murmushi,
kana ya mik'e ya shiga bathroom batare dayace mata komai ba,
mik'ewa tayi ta fita ta koma parlor,
yana jin fitarta ya tab'e baki had'i da cewa " even wanka da miji bazata iya ba,
dan duk wad'annan abubuwa babu yadda bayyi ya koya mata ba amma tak'i ta d'auka,
sai da yayi wanka ya shirya kana ya fita parlor'n,
a parlor ya same ta zaune, tana ganinshi tayi saurin mik'ewa tana murmushi,
shima murmushin yayi mata kana suka zauna a dinning table,
serving d'inshi farfesun kayan ciki da soyayyar doya da miyar kwai tayi,
sama-sama ya d'an tsakuri abincin ya mik'e,
da sauri ta kalle shi ta kalli abincin tace " wai kana nufin har kayi me?
Murmushi yayi mata yace " Alhamdulillah na k'oshi,
bata kuma yin magana ba ta mik'e rik'e da brief case d'insa,
" ba ko tarairayar miji, ko irin ta saka ni gaba tana yi man shagwab'a tana tarairayata akan dole sai naci abincin babu,
ina cewa nak'o shi shikenan, bayan tasan ba iya abinda na saba ci kenan ba,
ya fad'a cikin ranshi,
har bakin mota Khulud ta raka