Advertisements
Chapter 32 Reading RASHIN SANI Abokantaka Mai Gwada Ƙaddara by HAUWA A USMAN BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

RASHIN SANI Abokantaka Mai Gwada Ƙaddara by HAUWA A USMAN

Author :  HAUWA A USMAN Category :  Complete Novels

Chapter   32 / 38

93K to 96K   out of 111.2K words

ni ma ita nake nema,
rabo na da ita nakai 1hr,
Aarib yana k'ok'arin yin magana Sanah ta fito cikin arniyar kwalliya,
sanye take cikin riga da skirt na material lace,
yayi masifar yi mata kyau,
d'inkin yayi d'assss a jikin ta,
fuskarta tasha make up,
da sauri Aarib ya mik'e had'i da zuba mata ido,
cikin ransa yace " love of rest of my life,
a hankali Sir Moli ya d'aga kansa ya kalle shi,
dan yaji abinda Aarib yace,
tana murmushi ta k'araso ta zauna kusa da Khulud,
Khulud tayi murmushi tace " kinyi kyau sosai my Sanah,
Aarib yace " ai dama ita mai kyau ce ko ba make up,
Sir Moli ya tab'e bakinsa had'i da kansa gefe,
Sanah tayi murmushi tace " da gaske Yaya?

Aarib yayi dariya yace " kina da kyau sosai ma,
gaki da manyan ido farare tass,
masu d'aukar hankali, ga dimple both side, then wushirya da farare hak'ora a jere,
ga dogon bak'in gashi har gadon baya,
ga........
d'an tari Sir Moli yayi dan kwata-kwata ba san hirar yake yi ba,
Sanah tayi murmushi tace " thank Yaya,
karaf idan Khulud ya sauka akan pant & bra d'in Sanah,
ido ta zaro had'i da kallan Sanah,
da ido Sanah tayi mata alama da meye?

Itama Khulud da ido ta nuna mata pant & bra d'in,
ido Sanah ta zaro had'i da satar kallan Aarib da Sir Moli,
wanda duk abinda suke yi yana kallansu,
Sanah tayi yak'e kana ta sanya k'afa zata ture su,
Khulud ta zaro ido had'i da girgiza mata kai,
Sanah ta cije hak'ora had'i da zaro ido,
ta motsa lips d'inta ta yadda babu wanda zai gane abinda tace,
tace " ya kike san ayi to?

Khulud tace " kina tab'awa zasu gani,
Aarib yace " me?

Dan ya ji abinda Khulud d'in ta fad'a,
da sauri sukayi murmushin yak'e kana sukace bakomai,
Sanah ta kuma cije hak'oranta alamar kin gani ko?

Khulud tace " me?

Aarib yace " a ina?

Suka kuma yin yak'e had'i da cewa " bakomai,
Sanah tayi rolling sexy eye d'inta tace " ki kwashe,
ta fad'a yadda babu wanda zai ji ta,
da k'arfi Khulud tace " tabb! ni?

Aarib ya kalle su tare cikin alamar tambaya,
Sir Moli yana sane da duk abinda suke yi basarwa kawai yayi had'i da kauda kansa gefe,
ganin yadda duk sukayi tsuru-tsuru yasa Sir Moli yin murmushin gefen baki kana ya mik'e,
da sauri Aarib ma ya mik'e Sanah na ganin sun mik'e tayi saurin sa k'afa ta tura su k'ark'ashin sofa,
ajiyar zuciya suka sauke a tare,
kana suma suka mik'e,
hannu Sir Moli ya mik'awa Aarib sukayi musabaha kana yace " zan tafi,
Aarib yayi dariya yace " ok mun gode sosai,
kana ya kalli su Khulud yace " my Sanah ku raka shi,
Sanah turo baki kana tace " Yaya shifa ba yaro bane,
ai yasan hanya,
Khulud tace " Sanah!
Sanah ta kalleta kana tayi gaba,
Aryan yayi murmushi kana ya fita,
Khulud tabi bayansa,
suka jera da Sanah suka bi bayansa,
sun kusa isa bakin motarsa Halan ta kira Khulud,
Khulud ta kalle shi tace " Sir mun gode sosai,
Allah ya nuna mana naka,
Allah ya maida kai gida lafiya,
murmushi yayi mata kana yace " amin,
Khulud ta juya zata tafi Sanah na k'ok'arin bin bayanta,
Khulud tace " kije ki raka shi mana,
Sanah ta turo baki tace " ni dai a'a,
Khulud ta k'ura mata ido had'i da cewa " Sanah!
Sanah ta kuma turo baki kana tabi bayansa,
yana sane da tana biye dashi amma bai ko juya ba,
ya shiga motarsa ya fige ta, kamar zai taka ta,
tabi motar da harara kana ta ja tsoki ta juya ta koma cikin gida,
Hanash na tsaye yana kallan duk abinda suke yi,
yaja tsoki kana yace " dan daraba ba'a iya hak'uri na yau kad'ai,
sai an zo har gida anyi, iskancin ma yanzu ya wuce ayi a makaranta.


Bayan sallar la'asur Malamar addini tazo tayi wa'azi akan zamantewar
aure,
tayi musu nasiha sosai mai ratsa jiki da jijiya,
sosai nasihar ta shiga jikin duk wanda ya halarci wajen,
tun daga wajen wa'azin Sanah da Khulud ke ta faman kuka kamar ransu zai fita,
dama mutane sun san za'ayi haka,
dan kowa yasan rabuwar Khulud da Sanah akwai ganin ikon Allah,
d'akinsu suka shiga suka rufe suna ta faman cin uban kuka,
ana yin sallar Magrib Abbu ya aiko a kira masa Khulud da Sanah,
babban parlor'n gidan Halan ta shiga dasu,
India suka iske kowa da kowa harda kakanninsu ciki,
fad'a aka yiwa Khulud sosai kan zamantakewar aure,
kusan kowa sai da yayi mata fad'a,
inda zuciyar kowa ke cike da tsantsar tausayin su,
musamman ma Sanah,
Abbu ya kalli su Mamu yace " a fad'awa mutane babu kai amarya,
sunna zanyi ni da kaina zan kai 'yata,
daga ni sai Mamu, Halan da Sanah,
duk mai san zuwa yaje daga baya,
Didi yayi murmushi yace " wama zaije?

"Uba da kansa zai kai 'ya d'akin miji?

Abbu yayi murmushi yace" eh sunna zamu raya,
kana ya kalli Halan yace " kuje ku shirya nan da 10 minutes zamu tafi,
Khulud da Sanah najin haka suka k'ara fashewa da sabon kuka,
Halan ta mik'e rik'e dasu ta fita,
basu fi 10 minutes d'inba suka fito rik'e da juna gam,
suna ta kuka, har suka sanya zuciyar mutane karyewa,
motar Abbu suka shiga, Sanah da Halan suka saka Khulud a tsakiyarsu,
Abbu da Mamu na gaba,
tunda suka shiga cikin motar baka jiyo komai sai sautin kukan su,
sun rirrik'e juna kamar za'a raba su har abada,
a harabar gidan Khulud Abbu yayi parking suka fito,
Abbu da kansa ya rik'e hannun Khulud ya shigar da ita cikin gidan,
da suka zo shiga main cikin gidan Abbu ya tsaya a bakin k'ofar shiga,
ya shiga biya mata addu'a Khulud na maimaitawa kana yace " ki shiga da k'afar dama,
bismillah tayi kana ta shiga da right leg d'inta,
zama Abbu da Mamu sukayi akan sofa,
yayinda Khulud, Sanah da Halan ke zaune akan Italian carpet,
addu'o'i Abbu ya kuma yi kana ya sake yi mata fad'a sosai,
sai da ya gama ya kalli su Halan yace " ku tashi muje,
Mamu da Halan suka mik'e amma banda Sanah,
Khulud ta rirrik'e ta gam suna cigaba da kuka,
Abbu ya kalli Sanah cike da tausayawa yace " tashi mu tafi,
cikin muryar kuka Sanah tace " Abbu zan tsaya saboda siyan baki,
tunda bamu da wasu k'awaye dole ni zan jira,
shiru Abbu yayi kana yace " ok tom,
har ya kai bakin k'ofa ya juyo yace " karki sake ki kwana,
dan wallahi idan kika kwana sai ranki ya b'aci,
yayi commanding d'inta,
cikin muryar kuka ta amsa da " tom,
kana su Abbu suka fita,
shiru kawai Abbu yayi yana driving amma a k'ark'ashin zuciyarsa yana mugun tausayawa Sanah,
while itama Mamu da Halan tunanin da suke yi kenan har suka isa gida.


Su Abbu na fita Sanah ta kalli Khulud cikin muryar kuka tace " yanzu shikenan bazamu k'ara kwana tare ba,
bazamu kuma cin abinci, muyi wasa tare ba?

Khulud tace " meyasa?

Ta fad'a still crying,
Sanah tace " gashi kuwa aure ya raba mu,
daga yau ni kad'ai zan rink'a kwana,
ni kad'ai zan rink'a yin komai a rayuwata,
Khulud tace " mutuwa nayi?

Sanah tace " ai ko baki mutu ba aure ya raba mu,
shikenan munyi nesa da juna,
ta fad'a cikin matsanancin kuka,
Khulud tace " dan Allah my Sanah ki daina kukan,
ta fad'a itama tana kukan,
Sanah tace " dole nayi kuka,
daga yau zan kasance komai nawa ni kad'ai,
gwara ke kina da mijinki ma, zai rink'a d'ebe maki kewa ta,
amma ni babu kowa,
Khulud tace " duk duniya babu mai d'ebe min kewarki my Sanah,
you still alone in my heart baki da kishiya a zuciya ta, har yau har gobe ke kad'aice,
murmushi Sanah tayi tana gogewa Khulud hawaye tace " thank you so much,
Khulud tace " nayi miki alk'awarin har abada babu abinda zai raba mu koya shiga tsakanin mu,
Sanah tace " ni ma nayi miki alk'awarin bazan tab'a barinki kiyi kuka ba,
Khulud tayi dariya tana goge mata hawaye,
Hanash bai shigo gidan ba sai around 9:00pm na dare,
dan yayi tsammanin 'yan kawo amarya ne suka kawo ta,
shi kad'ai ya shigo kasancewar shima ba wasu abokai ne dashi ba,
rik'e da ledoji,
fuskarsa d'auke da murmushi,
ganin Sanah yasa shi yin turus,
kana ya k'ak'aro murmushin dole,
yace " ana nan ana ta faman kukan ko?

"Ni dai a taimaka man kar ayi ciwon kai,
Khulud ta d'ago red eye d'inta ta kalle shi,
ganin ya shigo shi kad'ai yasa Sanah cewa " Ango ina 'yan siyan bakin?

Murmushi yayi kana yace " bana da abokanai ai,
tana mik'ewa tsaye tana goge fuskarta tace " aiko na tsaya ne saboda kar 'yan siyan baki su zo su iske babu kowa,
yace " ok shikenan sai ki kwana anan,
Sanah ta zaro ido tace " in kwana a ina?

Abbu yace " kar in sake in kwana,
Hanash ya d'anyi shiru kana yace " Ok shikenan muje na maidake gida,
Khulud najin ance za'a mayar da Sanah gida ta k'ara fashewa da matsanancin kuka,
jikinsa ya jawota ya rungume ta yasa harshe yana lashe mata hawayen,
babu wani jin kunyar Sanah na tsaye,
cike da mamaki Sanah ta kawar da kanta gefe,
Khulud tayi saurin kwace jikinta,
ta ruga ta rungume Sanah gam,
sai dakyar Hanash ya sa Khulud ta saki Sanah,
dukkan su suna ta faman kuka kamar zasu mutu,
da gudu Sanah ta fita daga parlor'n tana cigaba da kuka,
a harabar gidan ta tsaya had'i da jingina jikin motarsa,
a hankali ya tako wajen cikin takunsa na izza,
ya zuba mata ido,
yace " do you think zan d'aukeki a motata ne?

Ya fad'a yana yi mata wani irin kallo mai cike da kyama,
" so idan ma kina tunanin hakan ki daina,
dan ban tab'a d'aukar mazinaciya fasik'a cikin motata,
wallahi kin ban mamaki duk irin tarbiyyar gidanku,
da halin mutumci da kirkinsu ke kin fita zakka,
saboda tsabar ke kwararriyar karuwa ce,
duk iskanci da kike yi cikin makaranta bai isheki ba,
sai kin kawo k'ato har cikin gidan ubanki,
ranar d'aurin aurin 'yar uwarki,
haba ashe shiyasa baki da kunya kwata-kwata,
nayi mamakin yadda kika iya d'aga hannu kika mari cikekken namiji kamata,
a kan titi a cikin bainar jama'a,
ina 'yar mutumci zata iya irinka,
ai dama idan kaga haka sai rikakk'un karuwai,
banza 'yar iska kawai, wallahi dana d'aukeki a motata gwara a sace gaba d'aya motocin dana mallaka,
kuma baki kwanar min a cikin gida tunda ba gidan ubanki bane,
sai kira shi abokin fasik'ancin naki ya maidaki gida,
kinga kun sake samun wata damar kuna iya yin abunku cikin mota,
ya k'arasa maganar yana kallanta,
cike da kyama,
" innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
dama kallan da Hanash yake yi mata kenan?

Ta fad'a cikin ranta,
wato kallan karuwa, mazinaciya, fasik'a yake mata,
a hankali ta shiga tunani,
tabbasa ya ganta da Sir Moli har sau uku,
na farko ya ganta kwance kan table a office d'insa,
babu d'an kwali, ya kuma d'age mata riga,
na biyu ya gansu cikin wani yanayi,
har Sir Moli na shan bakinta,
kuma tana sanye da kayansa,
na uku ya ganta d'aure da towel a gabansa,
tabbas dole yayi zargin wani abun,
tunda su ba ma'asumai bane,
dole yayi tunanin akwai wani abu tsakaninsu,
tunda shima d'an Adam ne kamar kowa,
yana da zuciya kamar ta kowa mai sak'a alkhairi da sharri,
dole zayyi musu mummunan zato,
tunda shi ba daban yake da kowa ba,
saboda ko ita ce ta kanshi da mace kamar yadda ya ganta da Sir Moli dole tayi masa mugun kallo,
kuma ko shi Sir Moli ya ganta da wani kamar yadda Hanash ya ganta dole zayyi zargi,
musamman ma har sau uku,
d'aya daga ciki kuma yana shan bakinta,
kuma su ba waliyyay bane,
sai lokacin wasu abubuwa da dama suka shiga dawo mata cikin kanta,
ashe dayace wad'anda suke yin haramtacciyar soyayya ma basu b'oyewa ko jin kunya da ita yake?

Ashe saboda wannan dalilin ne ya rungume Khulud a gabanta,
innalillahi wa'inna ilaihirraji'un,
ta fad'a had'i da rutse idanta, dan tasan bata da bakin wanke kanta,
tasan duk duniya duk wanta ya ganta haka dole yayi tunanin wani abu,
tasan ko Mamu da Abbu da suka haife ta ,
suka fi kowa sanin halinta da ciwonta,
suka ganta kamar yadda Hanash ya ganta dole suyi zargin akwai wani abu,
" tab! tace a ranta,
tana jin zafin abun,
tana jin tuk'ok'in bak'in ciki a zuciyarta,
" ya Salam! ta kuma fad'a
idanta ta runtse hawayen bak'in ciki da takaici na zubo mata,
a hankali ta bud'e idanta ta ganshi still yana tsaye hard'e da hannuwa yana kallanta,
hawayenta ta goge ta kalle shi ido cikin ido tarrr,
had'i da nuna shi da yatsa,
cikin rashin tsoro da tsiwa ta bud'e baki zatayi magana,
alk'awarin datayiwa Khulud ta tuna,
" _nayi miki alk'awarin daga yau har abada duk abinda zai yi man ban kuma ramawa,_
a hankali ta sauke hannunta data nuna shi da shi,
kana ta juya zata tafi,
murmushi Hanash yayi mai sauti kana yace " iskanci da fitsarar naki da kika saba zaki kuma yi man,
batare data jiyo ko tayi magana ba,
ta fice daga gidan,
murmushin jin dad'i yayi kana ya juya ya koma cikin gidan.


A parlor ya iske Khulud kamar yadda ya barta tana ta faman kuka,
a hankali ya zauna kusa da ita had'i da jawo ta jikinsa ya rungume,
cikin muryar kuka tace " My Sanah! fa?

Ya gane abinda take nufi dan haka yace " nasa driver ya maida ta gida,
shiru tayi tana jin gabanta na fad'uwa,
haka nan taji tsoro da fargaba sun shigeta,
cikin nutsuwa Hanash ya mik'e ya shiga kitchen ya d'auko plate da cup,
a hankali ya jawo ledojin daya jigo dasu,
ya bud'e su,
ya kalle ta yace " my queen me zaki ci?

Cikin kuka tace " my Sanah!

Shiru yayi had'i da k'ura mata ido yana nazarin yanayinta,
a cikin idanuwanta ya hango rashin yarda,
da kuma rashin kwanciyar hankali k'arara,
wato idan ya fahimta jikinta ya bata akwai wani abu,
mamakin tsananin soyayyar dake tsakanin su yake,
murmushi yayi kana yace " me?

Shiru tayi batare data amsa ba,
a hankali ya kuma jawo ta jikinsa,
ya manne ta da k'irjinsa ya shiga lallashinsa,
sosai Hanash ya lallashi Khulud kana ya bata abinci taci kad'an,
sai fresh milk data d'an sha,
mik'ewa yayi da ita a hannunsa ya nufi bathroom,
ganin ya nufi bathroom yasa Khulud fara mutsu-mutsun sakkowa daga jikinsa,
k'in ajeta yayi sai da ya kaita har cikin bathroom d'in,
kana ya dire ta cikin tub bath,
yana yi mata wani irin kallo yace " wanka zamuyi,
cikin tsoro Khulud ta zaro ido waje tace " kai da wa?

Yayi murmushi kana yace " with my wife,
murmushi tayi tace " ok tom,
ta fad'a tana k'ok'arin fitowa,
dariya yayi mai sauti kana ya mayar da ita cikin tub bath d'in,
Khulud ta kwab'e fuska tana san soma kuka,
tace " please ka barni nayi,
yana dariya yace " wannan duk tsoron mijin ne haka?

Kuka ta soma yi cike da shagwab'a,
yayi dariya yace " sorry bari na fita,
kiyi wanka ki d'auro alwala,
ya fad'a yana fita,
direct bedroom d'insa ya shiga ya shiga wanka,
ya fito ya shafa lotion & body spray kana ya fesa perfumes kala-kala,
ya shirya cikin arnan kayan bacci ya nufi bedroom d'inta,
itama tuni tayi wankan ta d'auro alwala,
ta shirya cikin kayan bacci so slink,
doguwar rigar har k'asa,
ta shafa turaruruka da body spray kala-kala,
ta d'auki k'amshi ta ko'ina,
ta zura hijab har k'asa,
tana gama shiryawa ya shigo,
bakin gado ya zauna yasata ta shinfid'a musu prayer mat,
ya ja su Sallah bayan sun idar ya dafa kanta ya shiga kwararo addu'o'i kamar yadda sunnah ta koyar.


Suna idarwa ta fara hamma,
ya kalle ta yace " bacci ko?

Kanta ta d'aga masa tace " eh!
"ok yace kana ya mik'e ya d'auke ta cak ya nufi kan bed da ita,
kwantar da ita yayi kana shima ya kwanta ya jawo ta
jikinsa,
yana shigewa jikinta mata kamar wani k'aramin yaro,
a hankali ya sanya hannunsa yana shafa jikinta,
cikin wayo ya fara k'ok'arin cire rigar jikinta,
da sauri ta rik'e masa hannu,
duk ilahirin jikinta kerrrma yake yana tsuma,
yadda kasan ana kad'a mata gangi,
cikin wani irin salo yakai bakinsa saitin kunnenta,
muryarsa na rawa yace " please ki bari muraya daren yau,
ya k'arasa maganar yana hura masa iska cikin kunnenta,
da sauri ta runtse idanta, while jikinta na cigaba da rawa,
bakinsa da nata ya had'e ya shiga tsotsar bakinta,
yayinda hannunsa ke yawo a jikinta yana shafa ko'ina,
a hankali Hanash yayi sama da hannunsa zuwa k'irjinta,
ya shiga wasa da k'irjinsa,
still bakinshi na cikin nata,
a hankali ya zame rigar jikinta ya mayar da ita naked,
kana shima ya cire kayan jikinsa,
duk abinda yake yi bakinsu manne,
cikin nutsuwa ya gangaro da bakinsa zuwa k'irjinta,
had'i da cusa hannunsa cikin gashin kanta,
yayinda d'aya hannun keta faman shafa ta,
ganin gaba d'aya ya rud'e ya gama fita daga hayyacinsa,
duk ilahirin jikinsa kerrrma yake,
yanayinsa da kamanninsa sun sauya,
yasa Khulud k'ara rud'ewa tsoronta ya k'ara k'aruwa,
taga kamar ba Hanash d'inta ba,
cikin muryar kuka tace " no please,
muryarsa na rawa yace " dan Allah,
still bai bar abinda yake yi ba,
sai da yayi romancing d'inta sosai,
ya tsotse tass in an out kana,
a hankali ya burkitata,
ya hawaye kanta,
ya fara k'ok'arin neman hanyar shiga,
azaba tasa Khulud fashewa sa matsanancin kuka tana tureshi da iya k'arfinta amma ina,
ya sakar mata gaba d'aya nauyinsa,
a hankali ya bita harya samu k'ofar shiga,
Hanash jinshi a duniyar dabai tab'a ziyara ba,
yasa shi zagewa iya k'arfinsa yana kashe arna,
bai sarara mata mata ba, sai da ya samu nutsuwa,
kana ya d'agata ya koma gefe,
had'i da jawota jikinsa ya rungume ta tsam,
itako sai ajiyar zuciya take saukewa cikin wahala.


Kasancewar unguwar su Hanash unguwar manyace,
layukan duk kusan iri d'aya ne,
yasa Sanah kid'imewa ta kasa gane takamaiman hanyar fita bakin titi,
tafiya kawai take tana waige-waige cike da tsoro da fargaba,
gashi dare yayi sosai, dan yanzu 11:00pm na dare,
awa biyu kenan tana ta tafiya tana neman abun hawa,
amma ta rasa, tunda ta fito ko mota d'aya bata gani ba,
ga Sanah ba saba tafiyar k'afa tayi ba,
ga dare yayi sosai, duk ta rud'e tsoro ya cika ta fall,
tana tafe tana kuka,
da zarar ta shiga wannan layin sai taga kamar ta koma baya,
haka idan ta kuma shiga wani layin sai taga kamar ta kuma komawa baya,
haka taitayi tana bulayi ita kad'ai cikin unguwar,
kowanne gida rufe,
sai faman haushin karnuka da take jiyowa daga cikin makamakan gidajen,
sauk'inta d'aya dayake unguwar manyan mutane ce,,
ko'ina a haskake yake da wuta,
babu duhu kwata-kwata,
wajen so silent,
k'arar motar taji tazo wucewa shuuuuuu,
d'agowar da zatayi hasken motar ya dalle mata ido,
ta yadda bata iya ganin komai,
kafin ta ankara sai taga motar tsaye a gabanta,
a tsorace Sanah ta d'ago kanta fuskarta cike da hawaye,
fuskar tayi jajir, a kid'ime ta mik'e tayi baya da aguje,
ta fara gudu iya k'arfinta,
a hankali matuk'an motar suka bi bayanta da motar cikin wani irin gudu,
da gudu aka sha gabanta da motar,
ganin da gaske gudu take yasa matuk'in motar fitowa،
da sauri ya rufe mata bakinta,
had'i da d'aukarta cak ya dannata cikin motar ya rufe....................




MOMYN ZARAH

_*RASHIN SANI.......*_




*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_



```Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh```



2⃣6⃣



Da k'arfi ya rufe motar kana ya zagaya ya shiga mazaunin driver,
da k'arfi Sanah ta shiga dukan glass d'in motar tana ihuuun kuka,
had'i da neman ceto,
" Keeh! ni ne,
taji muryarsa ta daki dodan kunnenta,
ajiyar zyciya ta sauke da k'arfi kana

32 / 38