Advertisements
Chapter 29 Reading RASHIN SANI Abokantaka Mai Gwada Ƙaddara by HAUWA A USMAN BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

RASHIN SANI Abokantaka Mai Gwada Ƙaddara by HAUWA A USMAN

Author :  HAUWA A USMAN Category :  Complete Novels

Chapter   29 / 38

84K to 87K   out of 111.2K words

d'aya tana period tayi wanka,
Hanash ko kullum sai ya zo ba fashi,
dan ya dage sai ya sakawa Khulud matsananciyar soyayyar shi a zuciyarta,
kasancewar babu Sanah babu mai d'ebewa Khulud kewa,
yasata fara kula Hanash,
tun tana shashshare har dai ta fara kula shi,
sai dai ko zancen yazo hirar dai d'aya ce ta Sanarta,
daga my Sanah kaza sai my Sanah kaza,
sosai Hanash ya rink'a d'ebewa Khulud kewa, yana bala'in kula da ita sosai,
saboda yadda ya nuna damuwa da kulawa a gareta,
musamman ma da bata da lafiya,
ko kuma da tace abu yake yi babu musu,
duk abinda zayyi ya faranta mata shi yake yi,
yana kuma gudun duk abinda zai b'ata mata rai,
sosai yake nuna mata so da soyayyarta a zahiri,
sannu a hankali soyayya mai k'arfi ta shiga tsakanin Hanash da Khulud,
suna yiwa junansu mugun so,
24hrs suna tare a waya, ko chart,
kasancewar Sanah da sassafe take fita school bata dawowa sai gaf da magrib,
idan kuma ta dawo bata da lokaci sosai datayi wanka taci abinci tayi sallah sai bacci ko karatu,
yasa kwata-kwata bata lura da abinda ke faruwa tsakanin Hanash da Khulud ba,
bata san komai ba,
ita kuma Khulud ba b'oye mata tayi ba,
dan bata samun lokaci ne yasa bata sanarda ita abinda ke faruwa ba,
sosai tsantsar soyayya mai k'arfi ta shiga tsakanin Hanash da Khulud,
fiye da tunanin mai karatu,
ta yadda babu abinda d'aya zayyi batare da d'ayan sa ni ba,
kullum kuma ko yaushe suna manne da juna a waya,
sunyi masifar bawa junansu mahimanci fiye da tunani.


Tun bayan faruwar wannan al'amarin babu wanda ya k'ara ganin wani tsakanin Sir Moli da Sanah,
sosai suka shiga wasan b'uya,
a gajiye lik'is Sanah ta koma gida yau ma,
Khulud na waya da Hanash taji shigowar Sanah tayi saurin mik'ewa,
had'i dayin cilli da wayar,
Sanah ta zube akan sofa,
had'i da cewa " wassh Allah na gaji da yawa,
cikin tausayawa Khulud tace sannu My Sanah,
Hanash dake ta faman hello hello,
jin shiru, ya jiyo muryar Sanah,
tsaki yayi had'e da kashe wayar,
Khulud ta rik'e hannun Sanah tace " muje kiyi wanka,
ba musu Sanah tabi Khulud zaunar da Sanah Khulud tayi a bakin bed,
kana ta shiga bathroom ta had'a mata ruwanka,
ta fito tace " my Sanah shiga kiyi wankan,
Sanah ta mik'e ta cire kayan jikinta ta d'aura towel,
ta shiga tayi wankan ta d'auro alwala,
kafin ta fito Khulud ta fiddo mata kaya marasa nauyi da pant ta aje mata akan bed,
Sanah ta fito ta zauna gaban mirror tana shafa lotion,
cikin matsananciyar gajiya,
Khulud tayi dariya tace " ko inzo na shafa maki man?


Ta fad'a cikin tsokana,
Sanah tayi dariya tace " dako kin taimaka da yawa,
mai kawai Sanah ta shafa ta zura doguwar rigar bacci,
ta saka pant kawai bata saka bra ba dan bata bacci da bra,
perfume's ta fesa,
kana ta fara k'ok'arin hawa bed,
Khulud ta kalle ta tace " abinci fa?


Naga kina k'ok'arin yin bacci,
Sanah tace " kai bar abincin nan kawai,
Khulud ta turo baki kana tace " Allah sai kinci kefa nake jira ki damo mu ci,
Sanah tayi murmushi tace " sorry jeki d'auko mana muci,
Khulud ta mik'e ta fita tana cewa " yauwa ko ke fa,
wayar Khulud dake gefe ta ringing,
Sanah bata kula wayar ba harta katse,
aka sake kira, nan ma bata yi picking ba,
sai da kira na 5 ya shigo kana ta mik'a hannunta daga inda take kwance ta lalubo wayar,
sunan ta kalla taga anyi saving da My Life,
cikin mamaki ta tace " my life kuma, waye kuma my life?


Ta tambayi kanta,
jin wayar na neman katsewa yasa ta saurin yin picking,
"hello my happiness ina ta kira shine ba'ayi picking ba,
yayi maganar zazzak'ar muryarsa,
gaban Sanah yayi muguwar fad'uwa,
a hankali ta zame wayar daga kunnenta ta k'ara kallan screen d'in,
taga tabbas ba wrong number bace,
tunda gashi anyi saving, cikin mamaki ta k'ara mayar da wayar kunnenta,
muryarta na rawa tace " bata nan,
jin muryarta ya sashi sakin tsoki had'i da kashe wayar,
wayar Sanah ta k'urawa ido cike da mamaki,
Khulud ta shigo d'auke da tray d'in abinci,
ganin yadda Sanah ta k'urawa wayar ido tanaR juyata,
ya sata zama kusa da ita,
" lafiya?

Khulud tace, cikin sanyin jiki Sanah tace " waye my life?

Murmushi Khulud tayi tace " he's my love,
"your love?

Sanah ta maimata cikin mamaki,
Khulud tace " eh!, ban baki labarinsa bane saboda baki zama,
da kin dawo kike kwanciya bacci,
Sanah tace " yanzu dama Khulud har akwai wani abu da zamu b'oyewa junanmu, har akwai abunda zamuyi batare da sanin juna ba?


Khulud tace " My Sanah baki zama fa,
Sanah tace " saboda bana zama shine ya hana ki fad'a min,
wannan ai ba dalili bane, tunda ba mutuwa nayi ba, ba kuma garin na bari ba,
cikin sanyin murya Khulud tace " I'm so sorry, ban san na hana ki bacci ne,
shiyasa kika ga ban sanar dake ba,
Sanah " ok yanzu ai ina jinki,
Khulud ta mik'e tsaye had'i da d'aga murya cikin farin ciki tace " I love him,
I really love him so much,
I love him more & more most my Sanah,
ke kad'ai nafi so a duniya sama da Hanash,
ganin yadda Khulud ke farin ciki yasa Sanah yin murmushi tace " who is he?

Khulud tace " Hanash Waseef,
Sanah tayi rolling sexy eye d'inta tace " taya za'ayi na sanshi,
description d'insa gaki man yadda zan gane,
Khulud tace " ai kin san shi ma,
Sanah tace " na sanshi, a ina?

Khulud tace " wannan wanda kukayi fad'a,
Sanah tace " wai wa?


Khulud tace " wanda ya watsa maki ruwan kwata har sau biyu,
ke kuma kika mare shi,
a firgice ta mik'e tana kallan Khulud had'i da ja baya..............


_Banyi editing ba, so nasan akwai typing errors_




MOMYN ZARAH

_*RASHIN SANI.......*_




*HAUWA A USMAN*
_JIDDARH_



```Wattpad:HauwaAUsmanjiddarh```



2⃣3⃣



Tace " wannan kike nufi?

Khulud tace " eh shi My Sanah,
Allah ina sanshi dayawa,
Sanah tayi shiru tana karantar yanayin Khulud,
taga yadda take cikin farin ciki,
tana murna da tsalle, take fad'in she love him so much,
Sanah tayi shiru tana tunanin yadda akayi yasan gidansu,
da yadda akayi har soyayyar su da Khulud tayi zurfi haka batare data sani ba,
Khulud ta fad'a jikin Sanah tace " nasan kema zaki soshi saboda nima ina sanshi,
shima yana sanki sosai,
ya manta da duk abunda ya faru tsananin ku a baya,
kullum bamu da wata hira sai taki,
ko ban yi mishi maganarki ba,
shi sai yayi man taki,
murmushin yak'e Sanah tayi, cikin sanyin jiki tace " wow! My Khulud gaskiya nayi murna,
da farin ciki da jin wannan labarin,
kice kun dad'e kuna shan love?


Ta fad'a tana kallanta,
Khulud tace " ba wani dad'ewa mukayi sosai ba,
da bani da lafiya ne ya nuna kulawarsa sosai akaina,
kuma shine yake d'ebe man kewarki,
taja hannun Sanah suka zauna a bakin gado,
kana Khulud ta shiga bata labarin mafarin soyayyarta da Hanash tun daga farko har k'arshe,
" kai amma abin ya burge ni,
Sanah ta fad'a tana b'oye damuwarta,
saboda yadda ta hango soyayyar shi a cikin kwayar idon Khulud,
tasan kuma muddin ta nunawa Khulud bata sanshi,
bata kuma kula shi, sai dai idan tayi mata haka bata yi mata adalci ba,
musamman ma data fahimci shima yana bala'in san Khulud d'in,
kuma yana kula da ita sosai,
dan haka bazata tab'a b'ata musu farin cikin su saboda wani banzan dalilinta ba,
ta kuma yiwa kanta alk'awarin daga yau har abada bazata k'ara k'insa ba,
saboda soyayyar da yake yiwa Uludinta,
da kuma yadda itama Khulud take sanshi,
ta kuma d'aukarwa ranta komai zayyi mata,
bazata tab'a ramawa ba, zaici arzikin soyayyar Khulud,
zata kuma ta danne komai a ranta,
ta kawar da komai, ta rink'a kula shi tana bashi girma da mutuncinsa,
saboda Khulud,
kuma koba komai, ai yana d'ebewa Khulud kewa,
yana kuma sanyata cikin farin ciki da walwala,
jin shiru yasa Khulud tab'a tace " My Sanah lafiya naji kinyi shiru?


Sanah tayi saurin k'ak'aro murmushi tana girgiza kanta tace " bakomai My Ulud,
kawai ina jin dad'i da farin ciki ne,
Khulud ta kalle ta k'ura mata ido na wani lokaci kana cikin sanyin murya,
tace " My Sanah ko baki san alak'a ta da Hanash ne?


Sanah ta zaro idonta,
tace " kai injiwa?

Khulud tace " My Sanah nafi kowa saninki,
nafi kowa sanin wacece ke,
nafi kowa halayenki da d'abi'unki,
dan girman Allah ki sanar dani gaskiyar abunda ke ranki gami da Hanash please,
Sanah ta kuma yin dariya tana rik'o hannun Khulud cikin nata,
tace " my Ulud ki kwantar da hankali,
babu abinda ke raina, kawai dai ina mamaki ne,
"mamakin me?

Khulud ta tambaye ta idanta na kanta,
Sanah tace " yadda akayi my Uludina ta fad'a tarkon love,
Khulud tayi dariya tace " kai my Sanah,
Allah nima ban san yadda akayi na fara ba,
haka nan kawai na ji ni.....
d'an shiru tayi,
Sanah tace " kika ji me?


Khulud ta turo bakinta,
tace " nima ban sani ba,
Sanah tace " a'a ina za'ayi haka ai dolanki ki fad'a man abinda kika ji,
Khulud ta lura akwai abinda Sanah ke k'ok'arin b'oyewa dan haka cikin sanyin jiki tace " my Sanah!
Sanah ta kalle ta,
taga Khulud ta k'ura mata ido,
rolling idanta Sanah tayi kana tace " me?


Khulud tace " please kin ban damar cigaba da kula da Hanash,
Sanah ta d'an yamutsa fuska tace " sai yanzu za'a nemi izinina bayan aikin gama ya gama,
Khulud tayi dariya tace " ni dai please ni yes or no?


Sanah tace " hmmmm sai bayan kin gama yanke hukuncin fad'awa a soyayyar sa?

Khulud tace " my Sanah ba mutum ne ke yanke hukuncin fad'awa a soyayya ba,
ita soyayyar ce take lokacin faruwar hakan,
shiru Sanah tayi tana san tuna inda ta tab'a jin irin wad'annan kalaman,
Khulud tace " nasan ba lalle ne yanzu ki fahimci hakan ba,
amma akwai lokacin da ke da kanki zaki fad'awa wasu,
Sanah ta shafa fuskar Khulud tace " karki damu kinji My Ulud,
nayi farin ciki sosai da jin wannan labarin,
Allah ya sanya alkhairi, Ubangiji yabar ku tare,
ya kuma albarci soyayyarku,
ya baku zuria ta gari,
Khulud ta amsa da Amin, idanta yana kan Sanah,
Khulud tace " Yayan su Zohal & Wajnah Waseef ne,
Sabah tace " kai haba?

Khulud tace " Allah da gaske uwarsu d'aya ubansu d'aya su uku ne kawai a wajen iyayensu,
Sanah tayi dariya kana tace " kin san me?

Khulud tayi saurin cewa " a'a,
Sanah tace " naga Sir Moli fa,
cikin zumud'i Khulud tace " kai a ina?

Sanah tace " a makarantar mu,
lecturer ne a department d'in mu,
Khulud tace " kuma ya gane ki?

Sanah tace " ya gane ni ko na gane shi?

" D'an rainin hankali,
Khulud tace " zaki fara ko?

Sanah tayi dariya kana ta shiga bawa Khulud labarin had'uwarta da Sir Moli tun daga farko har k'arshe,
amma ta kasa sanar da ita abinda ya shiga tsakaninsu,
karo na farko a rayuwarta data b'oyewa Khulud wani abu,
haka nan kawai taji bata san sanar da ita,
Khulud tayi dariya kana tace " kai wallahi drmarku na birgeni,
ashe an d'ora daga inda aka tsaya,
dama ina nan dana sha kallo wallahi,
Sanah ta tab'e baki, tace " rabu da rainin sense shi so yake ni na fara nuna na sanshi ko na gane shi,
yadda zai samu damar wulak'anta ni,
ya farfad'a man bak'ak'en maganganu san ranshi,
cikin dariya Khulud tace " durk'usawa wada ai ba gajiyawa bane,
my Sanah in kin nuna kin sanshi sai me,
wani abun ne zai ragu daga jikinki?


Sanah ta nuna kanta tana tab'e bakinta,
had'i da yin rolling sexy eye d'inta,
tace " ni na zan nuna na sanshi God forbid,
ta fad'a tana nuna kanta,
Khulud tayi dariya kana tace " Sir Moli witch kawai,
Sanah ta zaro ido had'i da mik'ewa tsaye tace " what! ni?

Khulud tace " eh mana in ba ke ba da wa!?

Sanah ta d'auki pillow tana bin Khulud,
Khulud tayi baya tana dariya tace " Sir Moli witch,
Sanah ta bita da gudu tana jefa mata pillows,
Khulud ta hau kan bed tana yiwa Sanah kwalo, had'i da tare pillows d'in,
wayar Khulud ta soma ringing,
Sanah tayi saurin d'aukar wayar tace " sake fad'a inba tsoro ba,
Allah yanzu na taro miki March,
Khulud ta rik'e kunnuwanta had'i da d'an girgiza kanta tace " I'm so sorry,
ban k'arawa, Sanah tayi dariya kana ta mik'e mata wayar,
da sauri ta amshi wayar had'i dayin picking,
" hello my life, ya kike?

"Lafiya lau, Alhamdulillah, an u,
yace " ina lafiya kamar yadda kike,
kin ci abinci?

"Eh, kai fa, murmushi yayi mai sauti har dimples d'insa suka lotsa kana yace " yanzu Mimmee ta gama bani,
Khulud tace " dear wai meyasa baka san cin abinci?

Dariya yayi yace " ni ma ban sani ba,
Mimmee dai tace haka nake tun ina Baby,
idan kika zo sai ki wakilci Mimmee ki rink'a baki ko?

Ya fad'a cikin shagwab'a,
fuskarta ta rufe kamar yana ganinta,
tace " hmmmm,
yace " Papu yace nayi miki magana kan zasu zo wajen Abbu,
tun last week na sanar dake amma kink'i cewa komai,
murmushi tayi kana tace " dama jira nake ayi approving d'in mu kuma anyi,
cike da mamaki yace " approving!?

Tace " yes!
Yace " waye zayyi approving d'in?

Tace " My Sanah mana,
ji yayi kamar ta watsa masa wuta,
amma sai ya kanne yace " to tayi yanzu?

Tace " eh tayi, dama ai na fad'a maka bata tab'a kin amincewa da abinda nake so,
Allah baka ga yadda taji dad'i tayi murna da farin ciki ba,
" shegiya karuwa 'yar iska ba,
ai dole ta yarda saboda tana tsoran kar na tuna mata asirin iskancin da take yi,
ya fad'a cikin ransa,
a fili kuma yace " masha Allah,
kana yace " yanzu if she's saying no ,
shikenan our true love has been cancel,
da sauri tace " wallahi capital latter YES!,
dan ban ko k'ara kallan inda kake balle nayi maka magana,
so put it your mind albarkacin My Sanah kaci,
ido Hanash ya runtse da k'arfi yana jin kamar zai mutu,
yana jin yadda zuciyarsa ke k'una had'i da tafasa,
in banda yana mugun san Khulud da tuni ya rabu da ita,
amma rabuwa da ita dai-dai yake da fitar numfashinsa,
daurewa yayi yace " ok any way,
yanzu yaushe su Papu zasu zo?

" Bari na nemi izini wajen my Sanah,
zayyi magana yaji ta kashe wayar,
wayar kawai Hanash yabi da kallo yana sak'e-sak'e da tunani a ransa,
Khulud ta juya ta kalli Sanah tace " my Sanah!
"na'am Sanah ta amsa,
Khulud tace " wai iyayen su Hanash ne zasu zo,
Sanah tayi saurin mik'ewa zaune tace " kai haba, yaushe?

" Ai shine nace bari na tambaye ki,
Sanah tace " ok bari naje na sanar da Mamu,
in yaso sai ta sanarwa da Abbu ko?

Khulud tace " ni dai a'a kunya nake ji,
Sanah tace " to mu sanar da Aunty Halan inyaso saita sanarwa da Yaya Ziyad shi sai ya sanarwa Abbu da Didi,
Khulud tace " ni dai kunya nake ji,
Sanah tace " to za'ayi idan ba'a sanar da su ba?

"Ko haka nan kawai zasu ga mutane da ka?

Khulud zatayi magana Sanah ta mik'e,
Khulud ma tayi saurin mik'ewa ,
Sanah zata fita Khulud ta rik'o tace " no,
Sanah ta fisge ta fita da gudu,
Khulud tayi saurin bin bayan ta,
da gudu suka yi parlor,
Abbu da Mamu na zaune suka gansu da gudu,
Abbu yace " lafiya!?

Sanah zatayi magana Khulud tayi saurin rufe mata baki,
tana yak'e tace " bakomai Abbu,
Sanah na k'ok'arin kwace bakinta ta d'aga hannunta alamar k'arya take,
Mamu tace " wai ku meye haka?

"Kun girma amma baku san kun girma ba,
kuna abu irin na yaran goye,
Sanah ta kwace bakinta tana hak'i,
Khulud na k'ok'arin sake rufe mata bakin tace " iyayen Hanash zasu zasu zo,
Khulud na jin Sanah ta fad'a ta saka kuka,
Abbu yace " to ikon Allah meye abin kuka kuma?

"Zonan kinji d'iyata ya fad'a yana mik'awa Khulud hunnu,,
ba musu Khulud ta nufi wajen Abbu ta zauna kusa da shi,
cikin rashin fahimta Mamu tace " waye Hanash?

Sanah tace " saurayin Khulud ne,
shine iyayensa suka ce suna san zuwa,
shine tace wai kar a gaya maku kunya take ji,
da gudu Khulud tayi bedroom d'insu cike da kunya,
cikin mamaki Abbu ya kalli Mamu yace " dama kin san da maganar ne?

Mamu tace " eh!
Abbu ya kalli Sanah yana murmushin jin dad'i cikin murna yace " zanyi magana da Didi,
sai na sanar daku ranar da zasu zo,
Sanah tace " tom, kana ta nufi bedroom,
ta iske Khulud, Khulud na ganinta mik'e tana dukan Sanah cikin wasa,
Sanah tayi dariya tace " wannan duk murnar ce, uhnnn amaryar Hanash,
Khulud ta kuma kaiwa Sanah duka,
wayar Khulud ta soma ringing,
Khulud tayi banza da wayar cike da murna Sanah tayi picking,
tace " hello!
jin muryarta yasa shi jin zafi har cikin ransa,
" hello ta kuma cewa,
sai da ya runtse idonsa kana yace " ina mai wayar?

Sanah bata d'auki wani abu ba,
tace " gata nan kusa dani,
a dak'ile yace " bata,
jikin Sanah a sanyaye ta mik'awa Khulud wayar tana yak'e,
cikin ranta kuma tana mamakinsa,
Khulud ta amshi wayar kana tayi masa bayanin komai,
guntun murmushi yayi kana yace " kiyi mata godiya,
Khulud tace " gata kayi mata da kanka,
yace " no ba sai kin bani ba,
kiyi mata kawai,
nima sallah zanyi,
shiru Khulud tayi batare data ce komai ba,
yace " I love you, good night,
bata bashi amsa ba,
ta kashe wayar,
kana ta tura masa text,

_Ka sani ban tab'a auren mutumin da baya san my Sanah baya kuma shiri da ita duk son danake yi masa,_
_wallahi koda sanka zai zama ajalina muddin baka san my Sànàh ko babu good understanding tsakaninku zan iya hak'ura da kai,_
_na barka har abada na kuma manta da kai da rayuwarka_
_so gwara ma ka sani ka kuma lura,_
_muddin kana so na kana kuma san aure na ka kasance da ni har rai da mutuwa to ka fara koyar yadda zakayi kà so Sanah ka kuma yi mu'amula da ita,_
_dan ko a ranar d'aurin auren mu Sanah ta nuna bata amince da kai bà wallahi sai na fasa,_


Murmushin takaci Hanash yayi bayan ya gama karanta text d'in,
yana jin inama zai iya rabuwa da Khulud da ya rabu da ita ya hutawa ransa da rayuwarsa,
sai dai bai iya rabuwa da ita a yadda yake jin mugun santa har cikin kwakwalwarshi,
text ya tura mata shima,

_I'm so sorry if I hurt you_
_ba da wata manufa nayi hakan ba, amma kiyi hak'uri please,_
_gobe zanzo na baku hak'uri ke da our Sanah, I love you so much_

Murmushi tayi kana tayi cilli da wayar ta kwanta.


Washe gari da wuri Sanah ta shirya kasancewar suna da lectures da Sir Moli 8:30am na safe,
tun da wannan abun ya faru Sanah ta shiga taka tsantsan dashi,
data ga suna da lectures dashi take sauri ta shiga class ta samu can baya lungu ta zauna,
a hankali Sanah ta shiga cikin class d'in tana takawa a hankali,
ta samu wajen a baya ta zauna tana jiran lokaci yayi ya shigo,
kan motarsa ya danno cikin makarantar,
a parking space yayi parking,
ya kai wajen 15 minutes kana ya zuro k'afarsa d'aya waje,
kai da kanin k'afar sanye cikin takalmin Nike,
kasan mamallakin k'afar yana cin

29 / 38