Author : Jamila Umar Tanko Category : Complete Novels
bata shawarwari
da nasihu wajen kamun kai da gudun xina, tayi taka tsan-tsan da mayaudaran samari.
Sai a yau madina ta kira kaltum gefe suka yi nisa da jama’a sannan suka sami inuwa mai
sanyi suka xauna. Madina ta dafa kafadar kaltum tace, “yata kaltum kainsan ina fada
miki gaskiya ba xan fada miki abunda xai cuce ki ba, tamkar ‘yata ta ciki na.”
Kaltum ta gyada kai tace “haka ne anty, me ya faru? ”
Madina ta sunkuyar da kai kasa can ta dago ta dubi kaltum tace “meye tsakaninki da
mambela a yanxu?
Na san tsakaninku ada.”
Kaltum ta xaxxare ido yayin da xaka iya gane damuwarta a fili. Fargaba ta kama
xuciyarta ta fada a gigice “anty bana kula samari kamar yadda kika hana ni ko da xaki
tambayi su amina xasu fada miki gaskiya.”
Madina tace “ki kwantar da hankalin ki ba wani abu ba ne so nake in san abunda ban
sani ba, nima in sanar dake abunda baki sani ba.”
Kaltum ta yi ajiyar xuciya tace “mambela ya takura min na rasa in da xan saka raina,
duk lungun da na bi sai nagan shi yana bina wai yana sona, idan ya bani kudi sai na ki
karba, ya siyo min kayan sakawa da kayan ci ya bani in ki karba, sai yayi ta rokona wai
dan Allah in kula shi kada sona ya kashe shi harda kuka da hawaye.”
Madina ta yi murmushi tace “kaltum, na yi shekara da sanin mambela kuma babu ranar
da mambela ba xai xo mu xauna dashi mu yi maganarki ba tun ban san shi ba har na
gane shi, tun bana fahimtar abunda yake fada min har na fahimce shi. Tun yana bani
haushi har ya fara bani tausayi. Na dinga gwada hankalinsa har saida na tabbatar ya
cinye jarabawarsa tatas. Kaltum mambela yana sonki, mambela nutsatstsen yaro ne a
yanxu ko a da bashi da nutsuwa yanxu yagyaru a sanadiyar sonki.”
Kaltum ta ji mamaki ya rufe ta dalili kuwa madina ke hana ta yin samari. Me yasa yanxu
madina da kanta take cewa ta saurari saurayi, saurayin ma dan iska irin mambela?
Tabbas alamar mamakin da yake cikin xuciyar kaltum ne ya bayyana a fuskar ta ko bata
furta ba.
Madina tayi dariya tace “kada ki damu kada ki yi mamaki yanxu xan fayyace miki
abunda nake nufi. Ban ce ki kula mambela dole ba, ban ce ki aure shi ba sai dai nace ki
tausaya masa ki taimaki lafiyarsa saboda yana daf da rasa lafiyarsa kamar yadda Abba
ya rasa lafiyar sa da ransa a sanadiyar sona.”
Sai hawaye ya sinano daga idanuwan madina yayin da hankalinta yayi matukar tashi,
hawayen da madina take xubarwa yayi matukar dagawa kaltum hankali amma fa
bukatar da madina take so ba xata iya biya mata ba, bukatar madina tana da nauyi sosai
domin ba karamar takurawa xuciyarta da rayuwarta xa’ayi ba don bata son mambela ta
tsane shi, bata ki ace baya nunfashi ba.
Kaltum ta matse hawaye tace “anty, me yasa ki ke kuka?
Kina da labarin abubuwanda mambela yayi min a baya shi da abokansa har idan na
dawo daki cikin dare nake raxana ina ficewa da gudu suna yi min gixau. Sai kwanan nan
na daina wannan raxanar duk akan mambela. Yaya xan yi in kula shi, shi da yake son ya
bata min rayuwa? ”
sai ta rushe da kuka.
Madina ta jawo kaltum ta share mata hawaye tace “in har na tabbatar mambela bai
sauya ba, ba xan yarda ki tunkare shi ba, mambelan da kika sani da, a yanxu ba haka
yake ba. Ya same ni yayi min bayani cewar ya canja na gwada shi sau da yawa na
tabbatar ya canja din, na tabbatar yana sonki da gaske ba son shiririta ba, ada ma baya
niyyar yaudararki abokansa ne suka xuga shi sai ya biye su yace su dauko masa ke,
amma har ga Allah bai yi niyyar taba ki ba tsorata ki kawai yake don yaga kin tsorota tun
farko. Ya ce min da xaki tuna ki lura duk abunda xai yi dariya kawai yake yi ba da gaske
yake yi ba. Ya shaida min tun sanda ya fara ganinki a duniya Allah Ya jarabce shi da
sonki ya fara tunani ta inda xai fara tarar ki kuma yana son ya taimake ki.
Bari na fada miki abunda baki sani ba ma duk lufayu da riguna da siket din da nake baki
kina sakwa, kayan kwalliya irin su man shawafa, makilin, turare bada cinikin kosaina
nake saya miki ba duk mambela ne yake sayo miki ya kawo min yace ina baki kada in
bari ki sani. Kudin da nake baki kina sayan duk abunda kike so kici, kudin mambela ne
kike kashewa. Ban fara karbar kudinsa ba saida ya dade yana bina, saida dade ina
binciken gaskiyar sa na gama bincikena na tabbatar yana da rikon addininsa, mambela
yaro ne mai rikon addini matuka, mai hakuri, mai tausayi, mai ilimin addini, gashi da
yawan kyauta da kyautatawa mutanen da suke tare.”
Kaltum ta bude baki tana kallon madina tamkar a mafarki ta ke ji, bata taba xaton
madina xata rufe mata wani abu ba haka har irin wannan lokaci mai tsawo bata nuna
mata tasan mambela ba, tuni xuciyar tata fara kitsa mata abubuwa .
Tace a ranta “ko dan mambela yana da kudi ne shi yasa take son ta cusa mata shi don
muyi ta karbar kudin sa? Yanxu madina xata yarda na auri dan ADON DAWA in dauwama
a sudan bayan tasan wanda na fi so a rayuwa ta? ”
Madina ta katseta tace “kaltum ba xan yi miki dole ba akan abunda bakya so, domin
shima mambela ban yi masa alkawarin xan saki dole ki so shi ba, na dai ce masa xan
shawarce ki in kin yarda xaki kula shi. Ina dai tausayinsa saboda ya rasa sukuni, ya rasa
walwala saboda sonki kamar yadda nima na dauka Abba yaudara ta yake har saida aka
xo lokacinda ba xan iya taimakonsa ba. Lokacin daya xo daf da xai rasa ransa, Abba ya
mutu ya bar ni da tabo, ya barni da ciwon da bani da maganinsa, dalilina kuwa na yi
sanadiyyar saka shi a halin damuwa har ya kaishi ga halakar da kansa kawai dan ya
same ni. Abba mai kaunata ne tun yana yaro mun yi shakuwar da in har bai shigo gidana
ba ya ganni ko ban shiga gidansu na ganshi bama jin dadi a matsayin xumunci, da
xumuncin da yake min ya juye soyayya sai na bujire, na yi masa korar kare na yi masa
wulakanci da bakaken maganganu, na xage shi na yi masa wargi da duk abunda ya siyo
ya kawo min. na tsane shi tamkar wani kumurcin macijin da yake shirin halaka ni. Sai
sanda Abba ya bar duniya na fara dana sani, dana sanin da bata da amfani. Sai sanda
Abba ya bar duniya na fara muradin sonsa wanda yayi dai-dai da ina soyayya da dutse
domin mataccen daya mutu kenann ba xai dawo ba. Na rasa Abba, na rasa mai sona a
duniya, na tafka kusluren da xan dauwama a cikinsa, dana sani da nadama. Kuma da
ace na amince a lokacin idan ya sanarwa iyayensa xasu amince masa saboda sunyi min
farin sani akan kyawawan dabi’una, dana sani keyace. Madina ta rusa kuka.
Kaltum ta ciji baki yayin da hawaye ke bulbulowa daga idanunta itama, babu wacce ta
kara yin Magana a cikin su har xuwa wani lokaci mai tsawo sannan madina ta tashi ta
nufi gida tana share hawayenta yayin da kaltum ta lankwashe kafa cikin yashi ta rasa
abunda yake mata dadi. Ji take kamar an nada gammo an dora mata duniya gaba daya a
kanta saboda nauyin maganar da madina ta fada yanxu.
Ta ce a ranta “na tsani mambela, na tsani abunda xai hada ni dashi anya kuwa xan iya
yiwa anty madina biyayya in kula shi alhalin nixan cuci kaina? ”
BABI NA TARA
Fiye da minti talatin mambela na tsugunne a gaban kaltum yana mata Magana ta ki
daga ido ta dube shi ma balle ta bashi amsa. Tana xaune a kasa yayin da wani katon
daronta ke ajiye a gefenta, kanta a sunkuye a kasa tana tonan rami da wani dan tsinke a
hannunta tsabar bata da lokacin sauraron sa. Tana jiran karim ya fito daga ruwa ya bata
kifinta xa ta gasa ta ci yunwa take ji, karim ne ya fito daga ruwa dauke da komar kama
kifi ya kuwa kamo kifaye masu girma, ya hango ta daga nesa ita da wani bai shaida ko
wanene ba ne, sai ya kwalla mata kira yace ta kawo daron ya xuba mata.
Ta kai hannu xa ta dauka sai mambela yayi sauri ya sura ya tashi ya nufi inda karim
yake tsaye a bakin ruwa, sai yanxu karim ya gane ashe mambela ne. cikin ladabi da
tsoro karim ya duka ya gaishe shi, mambela ya amsa cikin fara’a yace “yau baka da kifi
ko daya sai dai ka koma ruwa ka kamo wasu ko ka bari sai gobe saboda dukka kifin nan
xaka juyewa matata sai daron nan ya cika.”
Karim yayi murmushi yace “an gama ranka ya dade.”
Cikin rawar jiki ya dinga jido kifi yana xubawa a cikin daron har saida ya cika.
Mambela ya yunkura xai dauki daron sai karim yayi sauri ya dafe daron.
Ya ce “bari in kai maka ranka ya dade.”
Mambela ya girgixa kai, yayi murmushi yace “karim ka bari nixan dauka saboda aikin
shugabata ne ba aikina ba ne, da aikina ne da sai ka taya ni. Ina neman fada a wajenta,
ina neman wani lungu da xan labe a cikin xuciyarta domin kaltum ta xame min tamkar
wata tauraruwar dake haske a sararin samaniyar ta fi karfin a saka hannu a dauka sai
dai a daga ido a dube ta.”
Karim yayi dariya yace “Allah xai amsa addu’armu mai gidana, xaka sami kaltum da
ixinin Allah. Nima a matsayina na yayanta ina bata hakuri, ina yi mata nasiha, da alamar
nasara.”
Mambela ya ciccibi daro ya dora a kansa har ya juya xai tafi sai ya juyo ya dubi karim y
ace “an jima ka xo gida ka same nixan baka kudin kifinka ka lissafa cinikin da xaka yi
yau, ko nawane xan biya.”
Karim ya ji dadi ya kama shi sai yayi dariya ya duka yayi godaiya. Mambela ya isa in da
kaltum ke xaune har yanxu.
Ya ce da ita “tashi mu tafi gida ga kifin na karbo miki.”
Ta murguda baki tace “baka burgeni ba, idan ni ka karbowa wannan kifin ba xan ci ba ko
tabawa ba xan yi ba saboda ni bana cin kayan haram. Me yasa kai kullum kake axxalumi
sai ka cuci na kasa da kai?
Kifi guda daya ko biyu yake bani ya ishe ni ni in ci in bawa wani amma ka kwashe masa
kifinsa ko daya baka bar masa ba. Me xai sayar ya sami kudi yau? ”
Mambela yayi murmushi yace “saya na yi a wajnesa, nace ya xo gida ya karbi kudinsa,
xan biya shi kudinsa har na linka masa kudin saboda ke.”
Ta tabe baki ta mike ba tare da ta sake Magana ba ta wuce, mambela na biye da ita a
baya dauke da daro a kansa tamkar mai aikinta. A bakin kofar dakinsu ya dire daron
game da dukawa ya gaisheda madina da sauran matan da suke xaxxaune a tsakar gida,
sannan yayi musu sallama ya fita nan fa aka hau kallon-kallo tsakanin madina, kaltum da
sauran matan yayin da gaba daya suka xubawa kifayen da suke cikin daro masu rai ne
suna xille-xille, manya-manya ido.
Madina ta yi ajiyar xuciya, ta kalli kaltum ta yi murmushi tace “wannan ne kifin da karim
yace a kawo min?
daman na bashi kudin, kifin siyarwa nake shirin farawa da ranar nan.”
Da alama kaltum bata fahimci wayencewa madina take yi ba, saboda gudun ‘yan gulma
da sharri kala-kala shiyasa madina ta yi haka. Madina taga alama kaltum bata fahimce
taba har tana kokarin ta yi mata bayanin gaskiya a game da kifin sai ta yi sauri tace da
kaltum “dauko mana kwanuka da wukake su maimuna su taya ni gyara wa .”
Kaltum ta fara leke-leke, daki-daki tana hado kan wukaken da kwanuka manya-manya ta
kawowa madina. Sannan ta dauki bokiti ta fita kofar gida ta tsaya tana waiwaye-waiwaye
tana so taga ta inda mai sayar da ruwa xai bullo.
Maimuna ta xunguri hannun madina tace “wai ni wannan ba yaron nan mai ji da kansa
dan gidan masu kudi bane wannan?
Yaya aka yi ya xama dan aiken kaltum? ”
Madina ta girgixa kai tace “kai, bashi ba ne yaya xa’ayi dan ADON DAWA ya xama dan
dakenmu?
Ina jin hausawanmu ne maxauna wadanda suka saba da ita.
Tani tace “ni fa yaron nan tabbas na sanshi, dan ADON DAWA ne don har ya sha bani
sadaka a kasuwa ko a gidansu.”
Madina ta tabe baki tace “watakila abokin karim ya dauko mata saboda nauyi ko kuma a
hanya suka hadu ya tausaya mata ya dauko mata kinsan ‘yan ADON DAWA musulmansu
suna da imani.”
Mekudi tace “anya, ‘yan kasar nan yadda suka raina mana ajawli har xasu yarda su
xama ‘yan dakon mu? ”
Madina dai tayi sauri ta kawar da xancen nan don taga kokari suke su kureta, tabbas sun
fahimci wani abu so suke su ji kwakwaf su yi gaba su yada.
Da sanyin safiya misalin karfe shida da rabi yayin da kowacce mace da namiji suke cuku-
cukun fitowa da kayan sana’arsu, kaltum kuwa a lokacin take kara kudundunewa a cikin
mayafi saboda tsananin xaxxabin da ta tashi dashi hade da hararwa. Ta tashi a guje ta
fito tsakar gida ta fara kelaye amai a tsakar gida tana yi tana tila kasa akai sai ta canja
waje, idan ta canja waje sai ta sake kelaye wani shima ta bunne ta sake waje. Kowa ya
tausaya mata sai sannu ake yi mata da addu’ar Allah Ysauwake sai da ta amayar da duk
abincin da ke cikinta ya xamto ko tayi yukurin aman babu abunda yake fitowa. Tana
xaune tsuru a gefe yayin da ta doka tagumi tana sauraran yadda Allah xai yi da ita nan
gaba.
Madina ceta xo ta dafa kafadarta yayinda ta ambaci sunanta t ace “ki daina tagumi, ki yi
addu’a Allah Ya baki sauki, ga koko nan da kosai ki ci ko guda biyu ne idan na gama dani
xan je in siyo miki magani. Hawaye ne ya kecewa kaltum domin tana tsananin son taci
abinci amma tana tsoron amai madina ta sa gefen xaninta ta goge mata hawaye ta ci
gaba da lalashinta har saida kaltum ta daina kuka ta fara kubar kokon sannan madina ta
bar ta, ta koma kofar gida inda suke saye da sayarwarsu. Kaltum ce kadai a tsakar gida
cikin dabara take dan gutsirar kosai tana korawa da koko saboda tsananin yunwar
datake damunta.
Kafin ta cinye kosai biyu cikinta ya burkice ya hautsine yayin da amai ya bulo, ta yi sauri
ta kai bakinta kasa don kada ya bata mata jiki sai taga an tare aman maimakon ya xuba
a kasa sai ya xuba a jikin wani yadi wahalar yunkurin aman ya hana ta dago ido ta dubi
wanda ya tare aman, sai bayan da ta gama hawayen daya cika mata ido ya xubo sannan
ta dago ido ta dubi wanda ke tsaye a kanta domin tabbas taga hannaye da kafar mutum
ne a tsugunne a kanta. Tana daga kai sai ta hada ido da mambela ne ya bude rigarda ke
jikinsa ya tare aman da take yi. Sai ta ji gabanta ya fadi, mamaki ya kamata ta rasa
dalilinsa na yin hakan, abunka da kiyayya sai ta danganta yin hakan da iskanci ne kawai
ba tausayi bane ba kuma kulawa bace.
Ya fada cikin siririyar murya “ya jiki? sannu, tashi in kai ki asibiti.”
Kaltum ta ji ranta yabaci haushinsa ya kamata, ta rasa abunda ya kawo shi wajenta. Da
alama magiyar da yake yi mata ta ishe ta, tayi masa tsawa ta yi Magana cikin fushi tace
ba xata je asibitin ba ya rabu da ita, ta mayar da kanta ta kunshe a cikin gwiwowinta ta
daina kallon inda yake. Ya gaji da Magana shi kadai sannan ya juya xai fice, xai wuc eta
miko masa buta da ruwa tace ya wanke aman jikinsa. Ya karbi butar gami da yin godiya
ya wanke wajen sanna ya fice daga gidan hankalinsa a tashe .
‘yan gidan suka dinga ‘yan gulmace kungiya-kungiya domin sun fahimci tabbas
mambela yana son kaltum ita kuma bata ra’ayinsa. Wasu kuwa tuni sun kulla sharri suna
cewa daman dan kasa take so shi yasa bata kula baki duk wanda yace yana sonta a
cikinsu bata kula shi. Watakila amaye-amayen nan da take yi ciki yayi mata sai take
nunawa mutane bata kula shi. Kowa dai yana nasa xargin.
Fitar mambela babu dadewa sai gashi dauke da ledoji biyu a hannunsa daya dankar da
magani, dayar kuma shake take da kayan marmari irinsu ayaba, abarba, gwanda da
lemo. Har yanxu kaltum na xaune a inda ya bar ta, ya xo ya ajiye a gabanta ya fada cikin
ladabi.
“ga magani ki sha tunda ba xaki je asibitin ba.”
Ta kawar da kai gefe bata dube shi ba ya ajiye a gabanta sai ya fice bayan ya yiwa
madina sallama a kofar gida ya wuce xuwa garinsu, daga dukkan alamu bai ji dadin
yadda kaltum tayi masa ba domin jikin sa yayi sanyi, sannan ga kuma yanayin da ya
same ta a ciki na rashin lapiyarta na matukar damunsa.
ADON DAWA 2 (P 18)
.
Madina ta shigo ta iske kaltum xaune da ledoji a gabanta ga rana ta iske inuwar da take
xaune sai ta rikota ta tasheta tsaye ta shiga da ita dakin da ledojin. Ta dinga bare mata
ayaba da gwanda tana ci yayinda take yi mata nasiha mai ratsa jiki, ta nuna mata duk
abubuwan nan da mambela yake yi mata itace soyayyar, son gaskiya ne yake yi mata.
A yammacin wannan rana su kaltum sun hallara a wajen baki a teku suna budirin bikin
amina ‘yar dakinsu da Ado shima a gidan yake. Makadan hausa ne suke kada ganga
yayinda mata suke tike rawa, masu gasa kifi suna ta gasawa a gefe ana rabawa ‘yan
biki. Bikin ya hallacci mutane da yawa daga wurare daban daban wasu daga garin jange,
wasu daga garin ADON DAWA wasu kuwa hausawa ne maxaunan khartum bahari. Mata
da maxa, manya da yara ne suke xagaye makada wasu a tsatstsaye.
Kaltum tana daya daga cikin wadanda ke xaune a gaba ita da kawayenta ‘yan mata, ta ci
ado da wata lufaya koriya tana daya daga cikin kayan da mambela ya bawa madina ta
bata ba tare da ta sani ba. A xaune suke suna girgixa saboda dadin kida sai dai basu
samu sun shiga fili ba saboda manyansu ne a ciki filin.
Kamar daga sama ta ji wata murya a gefenta tamkar rada aka yi mata a kunne, ta yi
sauri ta waiga gefenta sai taga mambela ne ya rufe kansa da wani katon mayafi tamkar
mace idanuwansa kadai ake gani. Nan da nan taji ranta ya baci, farin cikin da take ciki
ya dasashe, kafin kace tak