Advertisements
Chapter 7 Reading adon dawa by Jamila Umar Tanko BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

adon dawa by Jamila Umar Tanko

Author :  Jamila Umar Tanko Category :  Complete Novels

Chapter   7 / 46

18K to 21K   out of 137K words

daya muke tasowa. Muna tashi daga
makaranta idan na shiga gida na ajiye jakar makaranta sai in karbi kudi a wajen
goggo fattu in tafi sarar kaya sannan in je in sayar.”
Madina tace “ban fahimce ki ba. Ke kadai din ne xaki iya xuwa ki sari kaya da
kanki? ”
Kaltum tace “ni nake xuwa in saro kaya, kar k ice tafiyar ba nisa, ko a mota tafiya
ce mai nisa daga masfala xuwa shara Mansur masallacin mai cixo. Sai na niki
tafiya kamar raina xai fita in saro kaya masu yawa sannan in doro kayan a kaina in
nufi harami in da xan baxa a bakin hanya ina sayarwa. Idan na sayar sai in koma
shara Mansur masallacin mai cixo in sake saro kaya in koma harami in sayar, har
sai dare yayi bayan sallar isha’I sannan nake komawa gida sai na tabbatar kudin
ya lunku sau biyu. Ma’ana idan riyad dari biyar ta bani sai ya xama riyad dubu
biyu, ranar da ban yi ciniki ba ne xan kai mata ruyad dubu daya da ‘yan kai.”....
.
Gida fa ya fara shiru, mai yasa aka rage

ADON DAWA 8
.
Madina tace “amma tana farin ciki da cinikin da kika yi mata bata kyarar ki ko? ”
Kaltum ta tabe baki ta ce “ko a lokacin xahma ma’ana lokacin da baki suke nan an
fi yin ciniki wato lokacin Umara da Hajji idan ta bani riyad dubu daya in yi sari,
daga safe xuwa dare sai nayi mata riyad dubu biyar xuwa dubu shida amma bata
godewa kuma se ta dake ni kullum.”
Madina tace “to cnikin nawa take so kiyi mata? ”
Kaltum t ace “duka na take yi kullum ba sai nayi laifi ba, ba kuma dan ban yi ciniki
ba. Yadda na lura doka ce wacce ta wajaba a kaina kullum sai ta xane ni ko da laifi
ko ba laifi. Daman ina dawowa take ce min in cire kayana a bakin kofar shigowa
daga ni sai dan wando, sannan in karaso gaban ta in durkusa, in mika mata cinikin
dana yi. Sai ta kirga ta soka a aljihunta sannan ta xaro wayar rediyo ta fara sharara
min a duk ilahirin jikina, laifin da take cewa nayi shine ban dawo da wuri ba ko
kuma sharar da nayi da wanke-wanken da nayi da asuba kafin in tafi makaranta
bai fita ba. In yi ta kuka da ihu ina mata magiya tayi hakuri ba xan sake ba. Har sai
hajja isra ta jiyo ta xo ta kwace ni sannan take kyaleni, amma tun sanda ta yiwa
hajja isra targade a yatsa garin kwata ta hajja isra ta daina saukowa ta kwace ni ki
san larabawa da tsoro. Sai dai ki ji tana cewa “fattu kiji tsoron Allah, ki kiyaye ranar
da hakkin yarinyar nan xai tabaye ki.” Amma goggo fattu bata ji, gobe ma xatayi
min wanda yafi na yau.”
Kaltum ta fashe da kuka, yayin da madina ma taji hawaye ba kakkautawa yana
xubo mata suka dauki lokaci mai tsawo babu wanda yake Magana don takaici. Can
kaltum ta ci gaba da Magana cikin kuka take cewa “bulalar roba irin ta jona rediyo
nan sai ta farfashe a bayana, yayin da karfen cikin wayar ke shiga cikin naman
jikina ya nutse, jinni yayi ta fita. Idan wayar ta fatattake ta kare sai ta bani kudi in
je in siyo wata a kanti da kaina, in kawo mata. Idan itama ta kare sai ta sake
aikena in siyo wata.”
Kaltum ta juyowa da madina bayanta, yayin data daga rigarta sai ga shatin bulala
xabga-xabga reras a jere a bayanta da wuyanta.
Madina ta shashshafa bayan yayin data gyada kai tace “kwarai kuwa wannan
tabon duka ne. Allah sai Ya kama matar nan da hakkin yarinyar karama wacce
bata jiba bata gani ba. Ta rabo ki da iyayenki ta xo ta axabtar da ke.”
Kaltum t ace “idan bayana ya farfashe yana jinni sai ta kaini bandaki ta daure
hannuna da wuyana da kafata a jikin famfo kamar yadda na gaya miki sani take in
cire kayana daga ni sai dan wando, sai ta dauko farin omo ta gurxa min a baya na
a wajen ciwon sai kaji ya dau xugi yana tafasa, yana kumfa sai ciwo ya kakkame,
sai jinin ya tsaya.”
Madina tace “ta daure ki a bandaki fa kika ce, kamar wata dabba?
Ko dabbace xatayi mata haka? ”
Kaltum t ace “na sha kwana a bandaki ina rawar sanyi har gari ya waye sannan ta
jibgo min abinci t ace sai na cinye. Shinkafa himilin guda da kaxa dankwaleliya
tace sai na cinye tas, inyi ta turawa badon ina jin dadin abincin ba saboda bana cin
abinci sosai na saba in yini ina talla baci basha don haka nama daina son cin
abincin kwata kwata.
Idan nace mata ya isheni sai ta kwada min mari tace sai na cinye duka, in yi ta ci
har wani lokacin in amayar da duk abunda na ci, sai ta sani in kwashe aman in
gauraya da abincin tace in cinye abincin da aman dole nake cakudawa in ci gaba
da ci.”
Madina ta tsartar da yawu gefe,
(NI KUMA DAN ANTY, HAR SE DA NA KOMA YIN AMAI , YANXU MA AKAN AMAN NAKE
OOOOOOOOO…….)
Ta dau dogon salati. Ta ce “kaltum kin sha wuya, kai wannan abu da me yayi
kama?
Ke kuwa me kika yiwa wannan tsohuwar take wahalar da ke haka da alama don
bata taba haihuwa bane take miki haka, da ta san xafin haihuwa da ta rage wani
abu duk muguntarta.”
(NI KUMA NA CE, “BA WANI DAMAN MUGUNTAR A JININTA YAKE, WASU BABU
HAIHUWA KUMA SUNA DA TAUSAYAWA DAN UWA. ALLAH MA YA TSARE MU DA IRIN
WANNAN RASHIN IMANI. AMEEN)
Kaltum ta matse hawayenta tace “duk unguwar sun san ina shan wahala duk da
basu san wata axabar da nake sha a cikin gida ba, amma suna ganin irin wahalar
da nake wajen daguwar tafiya in saro kaya sannan in je in sayar, in koma in sake
sarowa duk da kafa, saboda tsabar daukar kaya a kaina sai da kaina yayi tolo
gashin wajen ya kade ya gurguje saboda wahala.
Akwai wani yaro saurayi a makwabtanmu mai suna Anwar. Bakar fata ne amma
haifaffan Saudi ne yana tausaya min matuka y ace duk sanda xan je sari in je in
karbi kudin motar xuwa da na dawowa in daina tafiya da kafa. Haka kuwa aka yi
duk sanda na fito daga gida xan je in kwankwasa kofar gidansu ya fito ya bani riyal
biyu, riyal daya na xuwa daya na dawowa. Sai in je in shiga doguwar bus a kai ni
har kofar kantin sari, in saro kaya himili guda in sake hawa mota in tafi harami in
sayar. Abunka da yarinta idan na sayar xan sake komawa in saro wasu bana shiga
mota sai in tafi a kafata tunda Anwar bai bqni wanda xan sake komawa ba tsoro
kuma ya hana in dauka a kudinta, gani nake kamar xata gane.
Wata rana da axumi na fito daga gida karfe shida da rabi na safe, gari ma bai
karasa wayewa ba saboda akwai baki a garin don haka ana cin xahma. Anwar ya
bani kudin mota na tafi na hau doguwar mota mai beni hawa biyu, sama da kasa
don haka sai na samu lungu na shige a can sama.kan ka ce kwabo barci ya dauke
ni kasancewar axaune a bandaki na kwana, tsirara ga tsananin sanyi dan haka ban
samu nayi barci ba har asuba sannan ta kwance ni ta turoni sari ko karyawa banyi
ba, anyi mana hutu saboda axumi a lokacin.
Ina wannan barci har aka wuce dani inda xan sauka ban sani ba. Da barci yayi
barci saina sulale na mike a karkashin kujera na kwanta sosai na lulluba da
gyalena. Ban tashi farkawa ba said a wata mata ta tashe ni ta ce in tashi masu
mota dasu kai motar wajen parkin, sun gama aikin ranar. Sannan nayi firgigit na
biyo bayanta muka sakko tare da ita. Ina tafe ina laluba kudina a cikin jaka dana
daure a tsantsata, hakika kudina yana nan riyad dubu daya.
Ina fitowa sai na ganni a wata unguwa da ake kira shara sittin, sai ban damu ba
saboda tafiyar da xan yi xuwa sharu Mansur babu nisa sosai don haka na tabbatar
barci kadan nayi don ba’a wuce dani da yawa ba. Na duba sararin samaniya hakika
har yanxu rana bata futo ba yayin da na duba agogon dake daure a hannuna karfe
bakwai daidai. Sai farin ciki ya kama ni tunda na san karfe shida da rabi na fito
daga gida mintuna talatin kadai nayi a hanya. Na dinga tafiya ina sauri kamar xan
ci daka sai dai wani abu daya daure min kai sai naga du kana rufe kantina kuma
kowa na haramar tafiya masallaci ko’ina sai kiraye-kirayen sallah ake yi. Sai nake
ganin jama’a da dama suna cin dabino, wasu na shan shayi a cikin kantina ko a
cikin motocin su, gashi axumi ne kuma asuba ta wuce an gama sawur. Na tambayi
xuciyata me yasa suke karya axumin su?
Tambayoyi kala-kala na dinga yiwa kaina har na isa kantin sari. Mutum daya na
iske yana alwala a bakin kantin. Cikin harshen larabci ya amsa min y ace “ba’adis
salat”ma’ana, sai an idar da sallah xasu bude kantin. Na dube shi duba na rashin
fahimta n ace “ba kuyi sallar asuba da wuri ba ne? ”
ya yi dariya yace sallar magariba xa mu yi ba dai asuba ba. Ko dan bakya axumi
shi yasa baki damu a sha ruwa da wuri ba ko?
Sai gabana ya yanke ya fadi, nan da nan na rikice. Na ga wata mata ta xo wucewa
jikina yana karkarwa n ace mata “karfe nawa yanxu? ” ta duba agogon dake daure
a hannunta t ace “karfe bakwai.” Na tambaye ta “bakwai na safe ko bakwai na
dare? ” itama sai tayi dariya sannan t ace “bakwai na dare ne. ba ki ga ana shan
ruwa ba? ”
Sai na sulale na tsuguna ina ta salati, ina kuka hakika yau na shiga uku ban san
abunda xan je in gayawa goggo fattu ba, ga dare yayi gashi ban juya mata kudinta
ba. Ta yaya xan iya mayar da riyad dubu daya ya xam riyad dubu biyar ko dubu
shida, daga magaruba xuwa dayan dare? Sai da su kayi sallar isha’I aka yi asham
sannan suka bude kantina nan da nan na shiga na saro safar kala kala, da doxin
doxin din carbina. Na fito na shiga mota na nufi harami kuka kawai nake yi jikina
yana rawa, duk Alhajin da na gani sai in bishi, bakake da farar fata hawaye na
xuba ina cewa ku siya kaya na don Allah idan ban sayar ba duka na xa’ayi a gida.
Da yawa saisu tausaya min su saya ko basu yi niyya ba, wasu kuma saisu bani kudi
sadaka, wasu kuma su fisge rigarsu su wuce subar ni. Kan ka ce kwabo na siyar na
ruga da gudu na je na kara saro waqsu, na sake dawowa harami na sayar.
Akwai wasu kawayena ‘yan indiya da muka saba dasu a wajen talla, suma dasu ka
ga ina kuka sai suka tausaya min suka sarar min da kayansu dukka a yadda suka
saro na dora riba na sayar. A lokacin dasha dayan dare yayi jama’a sun fara tafiya
masaukinsu suna barin harami sai mu ma masu talla suka fara neman hanyar gida.
Ina tafe ina kirga kudin cinikin da na yi, saura kadan ya cika riyal dubu uku, sai na
dinga kuka ina addu’a yayin da hankalina ya kada yayi gida ina tunanin abunda
xan tarar don cinikin yau ba yawa. A titi na tunkaro wata mota wacce ta karkato xa
ta tsaya (parking) gwuiwata ce ta daki gaban mota. Kan kace kwabo kwabrina ya
fahse jinni yakece, na fasa ihu na daka tsalle gefe na tsuguna.
Hankalin direban ya tashi ya fito da gudu a gigice saboda yasan hukuncin kade
mutum a kasar, ko ba’a ji ciwo ba balle a ce har an ji ciwo har jinni yana xuba.
Larabci yake yi min, tambaya yake yana cewa wai me yasa nake tafiya kaina a
kasa, bana lura da motocin kan hanya duk da horn dinda yake yi amma ban jiba?
gashi nan na ja ya buge ni xan janyo masa wahala. Sai yaga ina ta bashi hakuri
burina in tafi in bar wajen ban damu da ciwon da na ji ba. ya kira ni na xo, sai ya
dunkulo kudi masu yawa ya bani yace in tafi chemist in sayi magani.
Na karba kudin ina murna, na wuce ina godiya sai na hada da kudin cinikina ya
xama riyad dubu biyar harda doriya. Nan fa na ji hankalina ya kwanta na tsaya a
fanfo na wanke jinin sannan na shiga gida. Na isketa a kufule tana jirana da
bulalarta a hannu, kallo daya tayi min na gane manufarta. Sai na fara cire abayata
na xama tik daga ni sai wando. Ina karkarwa na xo na durkusa na mika mata ciniki,
ta karba ta kirga. Sai ta Harare ni ta ce “ina kika je aka ganki a mota daxu da
magariba bayan ni ban baki kudin mota ba? ”
Sai na ji xuciyata ta harba tabbas wani ko wata sun ganni har an fada mata. Sai na
shiga dogon tunani ina neman hanyar da xan kare kaina. Ta daka min tsawa t ace
“Halima kawata ta ganki kina saukowa daga mota ina ki ka je? ”
Sai wata fasaha ta fado min nace askarawa ne suka kamani, suka tafi dani da kyar
suka sake ni suka sake ni. Ta fixgi kunnena ta murda da karfi t ace duk sanda na
sake na bari askari ya kara kamani to Nigeria xa’a mayar dani, ina xuwa Nigeria
kuma daga filin jirgi xa’a yanka ni saboda yankan kai ake yi a Nigeria. Sannan ta
kunnawa risho wuta yayi ja sosai sannan t ace in dauki risho din yana ci da wuta in
xo in wuce ta gabanta yayin da take shauda min bulala idan na bari risho din ya
fadi ko yayi karkacewa to dukan ya xube. “sai kaltum ta fashe da kuka mai
tsanani.
Madina ma kukan take, ta dafa kafadar kaltum tana lallashinta tana bata baki.
Tsawon lokaci kaltum bata daina kuka ba, saida kyar ta ci gaba da Magana. Ta ci
gaba da cewa “tun ina kukan idan tana dukana har na daina kuka, tun ina ihu har
na daina ihu, wannan abu kuwa yana bata haushi matuka ta fi so ta dake ni in yi
kuka da hawaye sannan ta ji dadi don haka take dukana kamar xata fitar min da
rai ni kuwa bana iya kukan.
Da wahala ta yi wahala sai nake fita in da Askarawa suke kame don su kamani
amma basa kamani, sai daga baya na gane ashe basa kama masu talla sai masu
bara don haka ina ganinsu sai in wurgar da kayan tallar nayi wuf na fada cikin
masu bara. Naci sa’a kuwa rannan aka kamani aka kaimu sijin wato kurkukun da
ake ajiye wa'anda aka kama ma’ana wa’anda basu da takardar ixinin xama.”
Madina tace “yaya rayuwar kita kasance a sin?
Kuma yaya goggo fattu ta yi data ji an kama ki? ”
Kaltum t ace “ai babu wanda ya san an kamani sai dai idan ta ji shiru ban dawo ba
ta shiga tunani, musamman idan ta ji labarin an yi kame a harami. Bata cika
damuwa ba saboda tasan riga kafin da ta yi min, ta riga ta tsorata ni da xuwa
Nigeria . tace idan na yarda aka kawo ni Nigeria yanka ni xa’a yi a filin girgi, ni
kuwa na yarda na dauka da gaske take yankan ake yi din. Su kuma askarawa baxa
su yarda su kai yaro kasarsu ba shi kadai sai an hada da iyayensa. Don haka saisu
tambayemu muna da iyaye a nan Saudi ya? Sai mu ce a’a saboda idan muka ce
eh, to xa’a aka mu gaba a kaimu wajen iyayen namu.
To a haka da suka gaji da tambayar iyayen mu muka ce babu suka fitar da mu
suka kaimu harami, amman ranar jikina se da ya gaya min, domin irin abunda ta
saba min na cin xali, shi ta min. sauran da muke siya da siyrwa da su ba’a dukansu
ko basu sayar da kayan su duka ba, basa damuwa saisu mayar gida gobe su xo su
sayar amma banda ni, yi nake kamar raina xe fita sai na siyar ninkin baninki du da
haka kuma ban tsira ba. Kaltum ta rushe da kuka.
Madina ta girgixa kai yayin data kurawa kaltum ido tana duban ta xuciyarta cike da
tausayi akan tausayin da take ke ji a da. Can kaltum ta dago da luhu luhun
idanuwanta ta kalli madina idanuwansu yayi musu jajawur ta ci gaba da cewa “da
wuya tayi wuya shekara ta xagayo na fara wayo ina tunanin mafita sai naga babu
wata mafita wacce ta wuce in koma sijin in xauna shine kadai salamata. Saboda a
sijin akwai bangaren yara xalla a inda ake bamu duk wani abun dadi da ko a
gidanmu ba ma ci. Shinkafa da dakwaleliyar kaji ga taliya, macaroni, lemo iri iri,
nono (laban), madara, xuma da gurasa, kankana, da sauransu.
Watarana na ji labarin ana kame a wata unguwa tuni na xubar da kayan talla na
nufi wajen, na sami fili na xauna ina bara. Da nayi sa’a sai suka gano ni suka kuwa
xo cafke ni suka yi, suka tafi da ni sijin. Na shafe wata biyu cif a sijin, ina walwalata
tare da sauran yara har akayi karamar sallah muna can, suka bamu kayan sallah
kala bibbiyu.”
Madina tace “atamfa ko leshi? ”
Kaltum ta yi dariya t ace “larabawa ai basa saka atamfa ko leshi, dogayen riguna
ne da dankwalayen su sai riga da siket ko wandaduna jeans wanda xamu saka
daga ciki sannan mu dora da abaya daga sama, muci, mu sha, mu yi wasa, babu
duka, babu xagi, sai dai muna leka wata ‘yar huda muna ganin bangaren karuwai
da aka kamo su ake duka.”
Madina t ace “kullum sai ayi ta xane su? ”
Kaltum t ace “a’a, duk sanda aka kama karuwa sai a sakata a wani daki wanda aka
sakale bulala sako sako, bulalen an jona su da na’urar lantarki. Ana saka karuwa
sai a fito a barta a ciki sannan a kunna na’urar, makunnar na waje. Kan ka ce kobo
bulalen nan sun hau aikinsu na duka ciki da waje, duk tsallanta haka ko kwanciya
tayi sai dukan ya sameta, abunka da na’ura mai kwakwalwa daga sanda bulala
tamanin ta cika sai injin ya mutu da kansa ma’ana bulala tamanin hukuncin xina,
ana kiran dakin XANXANA.”
(YA ALLAH KA TSARE MU DAGA AIKATA TA, DA MU DA EN UWAN MU MUSULMAI
BAKI DAYA AMEEN.)
Madina ta yi tagumi t ace “ikon Allah, kaji kasar da ake shari’a ake hukunta masu
xina ba kamar kasarmu ba Nigeria wanda a wani bangaren ma xina ta xama
fassion. Yaya ake yi da karuwa, idan an gama dukan ta? Nasan mafi yawancin su
‘yan Nigeria ne ko? ”
Kaltum ta girgixa kai t ace “cikin ikon Allah kuwa ban taba ganin an kamo bakake
ba, sai irin kananan mutanen

7 / 46