Author : Jamila Umar Tanko Category : Complete Novels
ta iso
inda kaltum ke tafiya ta dafa bayanta firgigit ta tsorata ta waigo da sauri sai taga
fatsumace sukayi murmushi alokaci guda fatsuma tace yaya jikin kalah, kin san fa tsoron
asibiti gareni shi yasa banbiku asibiti ba,
kaltum ta tabe baki tace bai kamaki bane dole dakinje,
fatsuma tace banda abunkima inake ina zuwa duba kalah duk irin muguntan da tayi miki
mezakije kiyi mata koda mutuwa tayi ma ina ruwanki?
kaltum tayi murmushin karfin hali tace muna yiwa Allah laipi muroke Shi Ya yafemana
meyasa bazan yafewa kalah ba?
yarta lami ta mutu meyasa bazan taimaketa ba tunda bata da kowa?
fatsuma ta tabe baki tace lallai kaltum dama haka kike da tausayi kamar lokacin
Sahabbai?
kaltum tayi daria, saboda na hadu da lalurar rashin lafiya nima Madina ta taimakeni
yayinda sauran suka gujeni shiyasa na kudiri niyyar taimakon duk wani mara lafiya
acikinmu tunda muna kasar da ba namu ba, babu iyaye babu dangi,
fatsuma tayi ajiyar zuciya tace gaskiyane yanzu ina zakije ?
Kaltum tace kasuwa zanje na nemo wa kalah abinci kafin magariba fatsuma ta yamutse
fuska tace mezaki sayar kisami kudi?
kaltum tace bara zanyi .
fatsuma ta dafe kirji tafada a bayyane cike da fargaba bara?
Bara fa kikace kaltum to Wallahi ba'a bara anan sai akamaki akaiki Chad ko maiduguri
ayar, nan ba bur sudan bace babban birninsu ne ba a wannan rashin hankali kame akeyi.
kaltum tayi kasake tana tunani to in banyi bara to mezanyi na sami kudi tunda sana'ar
tamu ta sassafene kawai muma sau daya samu muci abinci ko sau biyu saikuma wata
goben....
fatsuma ta katse tunaninta tace yanzu nan da ganni daga cen gidan nafito nasami sabon
aiki da yamma zandinga zuwa kuma kudi da abinci matar tace zata dinga bani kullum.
kaltum ta tambayeta cike da fara'a wanne
irin aikine ?
*fatsuma tayi murmushi tace gidan kunshi ne
da gyaran jiki (alewa da dilke )matane dankar suke taruwa ana bin layi ita kadaice don
haka aiki yayi mata yawa take neman masu tayata kamar masu yi mata aikin gida da
masu wanke wa mutane lalle da shafa mahallabiya nidai renon jaririyarta neke yi mata
yanzu ma aikena tayi insayo mata mahallabiya akasuwa zo muje ki rakani saimuje gidan
tare ki dinga tayani aiki idan kikaci sa'a kema saita daukeki aiki,
tafiya sukeyi fatsuma hira takeyiwa kaltum yayinda ita kuma addu'a kawai takeyi
azuciyarta tana fatan Allah Ya taimaketa matarnan tadauketa aiki asirinta yarufu ,
akusa da mai sayar da mahallabiya akwai masu sayarda madarar turare anan ne kaltum
tahadu da wani farin saurayi mesuna Abbas,
kallo daya ya wa kaltum yaji zuciyarsa taharba ta tsansar kaunanta ya dinga shisshige
mata yana tsoma baki acinkin cinkinsu ko kallo bai isheta ba domin ita duk abunnan da
akeyi hankalinta na gun aiki da tunanin halinda kalah ke ciki, saida Abbas
yamiko mata kwalbar turare sannan ma ta daga ido ta dubeshi ta sa hannu takarba
batare datasan manufarsaba ta manta ana godiya idan anwa mutum kyauta ta kada kai
tayi gaba fatsuma tace ta tsaya tana surutu dasu sannan can ta taho suka tafi a hanya
take shaidawa kaltum cewa Abbas ne ya tsaryar da ita yana tambayarta gidansu wai
kaltum yakeso,
kaltum ta tabe baki ta fada a yatsune au shine yabani turare ai danasan manufarsa da
bazan karba ba,
fatsuma ta zungureta tace ke wawuya ce ki so shi kawai yadinga zuwa zance yana kawo
mana kudi, abinci,sutura da kayan dadi,
kaltum tace Allah Ya sawake na so wannan.
fatsuma ta harareta tace yafiki kyau fa, balarabene fa kobaki kare masa kallo bane?
kaltum tace bai dameni bafa ya kyaleni,
haka dai suke tautauna harsuka isa gidan me kunshi katafaren tsakar gidane aka malale
da kafet hade da manyan fululluka mata birjik kowacce a kishingide an yarda mata
kunshi a laulausan fatarta da alama mai kunshin ta bunkasa domin matan manyane duk
a wajen daga dukkan alama motocinsu da direbobinsu a waje kofar gida suna jiran su,
kallonsu kawai kaltum keyi tana sha'awar baiwarda Allah Ya yi musu dama nice nasami
kwanciyan hankali da daula irin wannan, kaltum tafada azuciyarta dai-dai lokacinda ta
durgushe gabansu tana kwasar gaisuwa.
fatima wannan fa?
ina kika samo yar kyakyawan kawa itama yar
nigeria ne ko yar mali?
Inji Jawahir me kunshi.
fasuma tayi dariya tace kawatace kasarmu daya gidanmu daya kaltum sunan ta,
gaba daya suka zubawa kaltum ido sai ta sunkuyar da kanta kasa ta fada cikin
marainiyar murya hajiya kitaimake ni ki bani aiki mahaifiyata na asibiti akwance abinci
na
fito nemar mata,
sai hawaye ya kewa kaltum gaba daya suka tausaya mata harda masu tayata kuka,
kankace kwabo sunfara bude jaka ana zaro
sabbabin kudi ana mika mata sadaka tamike tana bi tana karba tana tarawa ta durkushe
a gabansu tayi godiya gami da kwawawan addu o I,
Jawahir takara mata da albishir da daga gobe tafara zuwa aiki ta dauketa aiki zata dinga
biyan ta,
kaltum tayi sauri ta dubi fatsuma farin ciki ya lullubeta su kayi dariya lokaci daya sannan
sukayi godiya tare,
kaltum tamike tsaye ta kara godiya tace zan koma asibiti wajenta gobe zan fara zuwa.
Jawahir tayi murmushi,
Ta ce Allah Ya kaimu kiyi mata sannu Allah ya sauka ke.
kaltum ta amsa da amin ta fice tana murna yayinda tafara kidaya kudinta metan wa
tamanin jine ma'ana dari biyu da tamanin saita kyalkwale da daria saboda farin ciki
tashiga tunanin abunda zata sayawa kalah wanda zataci tana tafe tana tunani saita
yanke shawara taje restourant ta sayo mata gasheshshiyar kazar da ake gasawa a inji
mai laushi da tiriri, marar lafiya zaiji dadin taunawa don haka kai tsaye ta wuce al-amana
resturant ta sayo wata dankwaleliyar kaza gashesshiya mai zafin gaske har tiriri takeyi
ta ashara jine tashiga super market ta cefano kayan shayi na hamsin wa ashirin jine fal
leda ta nupi asibiti ta ayyanawa a ranta cewar yan dakinsu na asibiti zasu sha mamaki
idan sukaga ta tilowa kalah wadannan kayan dadi a gaban ta kamar ba yanzu suka gama
mata wulakanci ba akan guntun sabulu saita yi murmushi ta gode wa Allah daya dubeta
Ya turo mata kudi nan mai dimbin yawa cikin dan kankani lokaci tsaka nin la'asar da
magrib, Allah Shine abun godiya kaltum ta fada abayyane tana shiga cikin get din asibiti
saita nufi dakin da kalah ke kwance ta duba igiyar data yi shanya saitaga an kwashe
zannuwan data shanya saita yi mamakin wayezai kwashe zannuwan nan bata tunani
sace wa aka yi tafi zaton
bushewa suka yi aka kaimusu kan gadon kalah,
tashiga dakin teburin ma'aikata ta duba da ke daf da kofar shiga har yanzu masifaffun
matan nan ne akan aiki ta dube su ta fada cikin gadara ina takardar maganin nan?
Kubani insayo sai taga sun turus da alama suna mamakin kalam kaltum,
can daya daga cikinsu tace kibarshi an bar matashi kyauta, kaltum ta wuce tana gyara
jibgegiyar ledar da ta shako da kayan dadi yayinda duk gadon da tazo giftawa marasa
lafiya da masu zaman jinyar su suka bita da kallo,
dadi yakama kaltum ta huce takaicin bakin cikin talaucin da ya addabesu , ita ma
yanzu zata jera kayan shayi akan lokarsu kamar yadda kowanne gado ake jerawa,
kallon ta suke ita ma tana baza ido tana dubansu duba irina ku kallah da kyau nice dai ta
dazu wacce ba ta da guntun sabulun wanki,
yanzu Allah Ya hore mata abunda yafi sabulunku,
dadi ne yayiwa kaltum yawa hartayi batan kai
tarasa gadonda kalah ke kwance kokuwa idone yayi mata yawa tafiya take hartakai
karshen dakin bataga gadon kalah ba saita juya ta kara tahowa tana baza ido dukka
bangarori hagu da dama saigata abakin kofar fita mamaki marar misaltuwa zaka iya gani
afuskarta ta fada abayyane ko ba dakin bane?
yayinda ta kara duban fuskokin yan dakin da ma'aikatan, hakika yan dakinne dan haka
daki ma shine babban abun tambaya ina gadon kalah?
Ina kalah ?
Shine kokarinda kaltum takeyi gashi babu wanda yace mata uffan
.ADON DAWA 23
.
TRUE LIFE STORY
.
masu son zaman kasarkuba dayawanmu
kaddarace muma badason ran mu ba dolece,
a bakin bandaki aka tsatstsaya ana kallon su kaltum yayinda mamaki ya rufe yan kallo
suna tambayar meyake faruwa ne meyakawo zancen zama akasar sudan?
kaltum ta wuce wajen fomfo batare da ta iya tsayawaba tabasu ansa ba Aisha ce ta
tsaya tana bayanin abunda yafaru, gaba daya suka bawa kaltum gaskiya suka bawa
ma'aikatan da yan dakin rashin gaskiya koba yan kasa bane ba ai musulmai ne,
wulakanci bashi da dadi kuma yan sudan nawa ne a nigeria sunacin arziki abun duniya
suke tarawa a Nigeria su dawo sudan suna zagawa,
akwai auratayyah asakaninsu dan haka
anzama daya,
aka cika bandaki ana bawa kaltum hakuri akanta karbi bokiti da omo tayi wanki taki
karba tace ai ta rantse indai bokitin yan dakinne bazatayi anfani dashiba
saida wata tabata sabulu sannan ta karba na
aishane bazata karba ba tunda tana dakin tana ganin wulakancin da akeyi mata bata
fitar da ita kunya ba sai daga baya zata biyota saboda kar yan dakin su tsaneta kome?
kaltum rigima da kyar ta karba sabulun ta wanke taje ta shanya igiyanda dake gaban
dakinsu tashigo dakin tana kallon kowa daya bayan daya jira takeyi ayi magana tayi
tsiwa babu mai iya hada ido da ita domin Aisha
takawo musu labarin abunda kaltum tafada abandaki
ta isa gadon kalah har yanxu shirkif take cikin barci, ta fada abayyane cikin harshen
larabci kalah zantafi cikin gari insamo miki abunda zakici nabar amana agurin ALLAH
domin Shi Ya halacci talaka Ya halacci me kudi ya halacci dan sudan ya halacci dan
Nigeria
sai kowacce tayi kiri-kiri tana duban kaltum sunsan magana ta yasar musu ta wuce kere-
kere ba mayafi kasancewar taraba mayafinta gida biyu ta rufa kalah
ma'aikatar daya ta dubi kaltum ta gyada kai
tace lalle yarinyarnan batada mutunci ashe.
kaltumta murguda baki ta fice yayinda suduka suka bita da kallo kaltum nashiga gidansu
matan gidan sukayo kanta suna tambayan yaya jikin kalah an sayi magungunan kuwa?
Wannan tambayan nasu ta bata mata rai don haka bata basu amsar tambayarsu ba ta
kada kai tayi daki,
buhun kayanta ta jawo ta bude ta daura wata lafayan tacire ta jikinta, yau zancen wanka
babushi tafice ko wacce taja bakinta tayi shiru babu wacce ta sake tambayarta komai
sunga ranta yabace kuma sunsan basu kyauta ba kallonta sukeyi harda lekenta akofar
gida su ga inda zata nufa asibiti ko
kasuwa,
hanyar kasuwa ta nufa don haka suka gaskata neman kudi zataje
nan suka dasa kujerar gulma cewa banda
yarinta ma meyasa kaltum zata damu kanta akan kalah, matarda ta cuceta takawota
Khartoum ta wulakantata ita da yarta , kaltum babu abunda basuyi mataba na wukanci
fatsumace ta hango kaltum ahanya yayinda tafito daga wani gida ta bullo da gudu ta iso
inda kaltum ke tafiya ta dafa bayanta firgigit ta tsorata ta waigo da sauri sai taga
fatsumace sukayi murmushi alokaci guda fatsuma tace yaya jikin kalah, kin san fa tsoron
asibiti gareni shi yasa banbiku asibiti ba,
kaltum ta tabe baki tace bai kamaki bane dole dakinje,
fatsuma tace banda abunkima inake ina zuwa duba kalah duk irin muguntan da tayi miki
mezakije kiyi mata koda mutuwa tayi ma ina ruwanki?
kaltum tayi murmushin karfin hali tace muna yiwa Allah laipi muroke Shi Ya yafemana
meyasa bazan yafewa kalah ba?
yarta lami ta mutu meyasa bazan taimaketa ba tunda bata da kowa?
fatsuma ta tabe baki tace lallai kaltum dama haka kike da tausayi kamar lokacin
Sahabbai?
kaltum tayi daria, saboda na hadu da lalurar rashin lafiya nima Madina ta taimakeni
yayinda sauran suka gujeni shiyasa na kudiri niyyar taimakon duk wani mara lafiya
acikinmu tunda muna kasar da ba namu ba, babu iyaye babu dangi,
fatsuma tayi ajiyar zuciya tace gaskiyane yanzu ina zakije ?
Kaltum tace kasuwa zanje na nemo wa kalah abinci kafin magariba fatsuma ta yamutse
fuska tace mezaki sayar kisami kudi?
kaltum tace bara zanyi .
fatsuma ta dafe kirji tafada a bayyane cike da fargaba bara?
Bara fa kikace kaltum to Wallahi ba'a bara anan sai akamaki akaiki Chad ko maiduguri
ayar, nan ba bur sudan bace babban birninsu ne ba a wannan rashin hankali kame akeyi.
kaltum tayi kasake tana tunani to in banyi bara to mezanyi na sami kudi tunda sana'ar
tamu ta sassafene kawai muma sau daya samu muci abinci ko sau biyu saikuma wata
goben....
fatsuma ta katse tunaninta tace yanzu nan da ganni daga cen gidan nafito nasami sabon
aiki da yamma zandinga zuwa kuma kudi da abinci matar tace zata dinga bani kullum.
kaltum ta tambayeta cike da fara'a wanne
irin aikine ?
*fatsuma tayi murmushi tace gidan kunshi ne
da gyaran jiki (alewa da dilke )matane dankar suke taruwa ana bin layi ita kadaice don
haka aiki yayi mata yawa take neman masu tayata kamar masu yi mata aikin gida da
masu wanke wa mutane lalle da shafa mahallabiya nidai renon jaririyarta neke yi mata
yanzu ma aikena tayi insayo mata mahallabiya akasuwa zo muje ki rakani saimuje gidan
tare ki dinga tayani aiki idan kikaci sa'a kema saita daukeki aiki,
tafiya sukeyi fatsuma hira takeyiwa kaltum yayinda ita kuma addu'a kawai takeyi
azuciyarta tana fatan Allah Ya taimaketa matarnan tadauketa aiki asirinta yarufu ,
akusa da mai sayar da mahallabiya akwai masu sayarda madarar turare anan ne kaltum
tahadu da wani farin saurayi mesuna Abbas,
kallo daya ya wa kaltum yaji zuciyarsa taharba ta tsansar kaunanta ya dinga shisshige
mata yana tsoma baki acinkin cinkinsu ko kallo bai isheta ba domin ita duk abunnan da
akeyi hankalinta na gun aiki da tunanin halinda kalah ke ciki, saida Abbas
yamiko mata kwalbar turare sannan ma ta daga ido ta dubeshi ta sa hannu takarba
batare datasan manufarsaba ta manta ana godiya idan anwa mutum kyauta ta kada kai
tayi gaba fatsuma tace ta tsaya tana surutu dasu sannan can ta taho suka tafi a hanya
take shaidawa kaltum cewa Abbas ne ya tsaryar da ita yana tambayarta gidansu wai
kaltum yakeso,
kaltum ta tabe baki ta fada a yatsune au shine yabani turare ai danasan manufarsa da
bazan karba ba,
fatsuma ta zungureta tace ke wawuya ce ki so shi kawai yadinga zuwa zance yana kawo
mana kudi, abinci,sutura da kayan dadi,
kaltum tace Allah Ya sawake na so wannan.
fatsuma ta harareta tace yafiki kyau fa, balarabene fa kobaki kare masa kallo bane?
kaltum tace bai dameni bafa ya kyaleni,
haka dai suke tautauna harsuka isa gidan me kunshi katafaren tsakar gidane aka malale
da kafet hade da manyan fululluka mata birjik kowacce a kishingide an yarda mata
kunshi a laulausan fatarta da alama mai kunshin ta bunkasa domin matan manyane duk
a wajen daga dukkan alama motocinsu da direbobinsu a waje kofar gida suna jiran su,
kallonsu kawai kaltum keyi tana sha'awar baiwarda Allah Ya yi musu dama nice nasami
kwanciyan hankali da daula irin wannan, kaltum tafada azuciyarta dai-dai lokacinda ta
durgushe gabansu tana kwasar gaisuwa.
fatima wannan fa?
ina kika samo yar kyakyawan kawa itama yar
nigeria ne ko yar mali?
Inji Jawahir me kunshi.
fasuma tayi dariya tace kawatace kasarmu daya gidanmu daya kaltum sunan ta,
gaba daya suka zubawa kaltum ido sai ta sunkuyar da kanta kasa ta fada cikin
marainiyar murya hajiya kitaimake ni ki bani aiki mahaifiyata na asibiti akwance abinci
na
fito nemar mata,
sai hawaye ya kewa kaltum gaba daya suka tausaya mata harda masu tayata kuka,
kankace kwabo sunfara bude jaka ana zaro
sabbabin kudi ana mika mata sadaka tamike tana bi tana karba tana tarawa ta durkushe
a gabansu tayi godiya gami da kwawawan addu o I,
Jawahir takara mata da albishir da daga gobe tafara zuwa aiki ta dauketa aiki zata dinga
biyan ta,
kaltum tayi sauri ta dubi fatsuma farin ciki ya lullubeta su kayi dariya lokaci daya sannan
sukayi godiya tare,
kaltum tamike tsaye ta kara godiya tace zan koma asibiti wajenta gobe zan fara zuwa.
Jawahir tayi murmushi,
Ta ce Allah Ya kaimu kiyi mata sannu Allah ya sauka ke.
kaltum ta amsa da amin ta fice tana murna yayinda tafara kidaya kudinta metan wa
tamanin jine ma'ana dari biyu da tamanin saita kyalkwale da daria saboda farin ciki
tashiga tunanin abunda zata sayawa kalah wanda zataci tana tafe tana tunani saita
yanke shawara taje restourant ta sayo mata gasheshshiyar kazar da ake gasawa a inji
mai laushi da tiriri, marar lafiya zaiji dadin taunawa don haka kai tsaye ta wuce al-amana
resturant ta sayo wata dankwaleliyar kaza gashesshiya mai zafin gaske har tiriri takeyi
ta ashara jine tashiga super market ta cefano kayan shayi na hamsin wa ashirin jine fal
leda ta nupi asibiti ta ayyanawa a ranta cewar yan dakinsu na asibiti zasu sha mamaki
idan sukaga ta tilowa kalah wadannan kayan dadi a gaban ta kamar ba yanzu suka gama
mata wulakanci ba akan guntun sabulu saita yi murmushi ta gode wa Allah daya dubeta
Ya turo mata kudi nan mai dimbin yawa cikin dan kankani lokaci tsaka nin la'asar da
magrib, Allah Shine abun godiya kaltum ta fada abayyane tana shiga cikin get din asibiti
saita nufi dakin da kalah ke kwance ta duba igiyar data yi shanya saitaga an kwashe
zannuwan data shanya saita yi mamakin wayezai kwashe zannuwan nan bata tunani
sace wa aka yi tafi zaton
bushewa suka yi aka kaimusu kan gadon kalah,
tashiga dakin teburin ma'aikata ta duba da ke daf da kofar shiga har yanzu masifaffun
matan nan ne akan aiki ta dube su ta fada cikin gadara ina takardar maganin nan?
Kubani insayo sai taga sun turus da alama suna mamakin kalam kaltum,
can daya daga cikinsu tace kibarshi an bar matashi kyauta, kaltum ta wuce tana gyara
jibgegiyar ledar da ta shako da kayan dadi yayinda duk gadon da tazo giftawa marasa
lafiya da masu zaman jinyar su suka bita da kallo,
dadi yakama kaltum ta huce takaicin bakin cikin talaucin da ya addabesu , ita ma
yanzu zata jera kayan shayi akan lokarsu kamar yadda kowanne gado ake jerawa,
kallon ta suke ita ma tana baza ido tana dubansu duba irina ku kallah da kyau nice dai ta
dazu wacce ba ta da guntun sabulun wanki,
yanzu Allah Ya hore mata abunda yafi sabulunku,
dadi ne yayiwa kaltum yawa hartayi batan kai
tarasa gadonda kalah ke kwance kokuwa idone yayi mata yawa tafiya take hartakai
karshen dakin bataga gadon kalah ba saita juya ta kara tahowa tana baza ido dukka
bangarori hagu da dama saigata abakin kofar fita mamaki marar misaltuwa zaka iya gani
afuskarta ta fada abayyane ko ba dakin bane?
yayinda ta kara duban fuskokin yan dakin da ma'aikatan, hakika yan dakinne dan haka
daki ma shine babban abun tambaya ina gadon kalah?
Ina kalah ?
Shine kokarinda kaltum takeyi gashi babu wanda yace mata uffan.
ADON DAWA 24
.
Babban abin tambaya shi ne, ina gadon kallah? Ina kallah ta ke? Shi ne kokarin da
kaltum take yi, ga shi babu wacce tace mata uffan, Kallonta suke tamkar a talabijin take
ba a zahiri ba. Ta koma ta dawo, se ta je kansu ta tsaya, tana musu duba irin na mamaki
da Al'ajabi. Can taetambaya, "don Allah ina mai gadon nan, kallah? "
Caraf ta ji an dafa bayanta, sai ta yi farat ta juya a tunanin ta kallah xata gani da kafarta
tana tafiya ko bsndaki ta shiga da kanta, juyawar ta, se ta ga masipappiyar ma'aikaciyar
jinyar nan ce, mamaki ya kama kaltum matuka ta bude baki tana dubanta.
Matar ta fada cikin marainiyar murya, "kaltum ki yi hakuri Allah Ya yiwa kalah rasuwa
dazu dagafitar ki,ko get baki kai ba. An leka da gudu ba a ganki ba.... "
Duk wannan dogon bayanin da matar