Author : Jamila Umar Tanko Category : Complete Novels
shiga ta kame direba yaja suka tafi, mamaki ya kama saurayin nan sai yaji ya fasa
zuwa unguwan ma gara ya dawo gida domin ya tsorata da yarinyan nan yar makaranta
tunda yake ko a hanya bai taba ganin mai kama da ita ba, yayi kwana ya juyo kofar
gidansu masu gadi sukayi sauri suka
bude masa get sai ya canja shawarar shiga gida sai yaji gara yabi bayan yarinyan nan
yaga daga ina take kuma me tazo nema a gidansu,?
saidai kash da yabi inda sukabi sai yaga wayam ko gabas ko yamma baiga ta inda sukabi
ba ya dawo gida cike da mamaki shi kadai da zuciyansa ba tare da yasan yanda zai
baiyana wa wani ba,
kaltum ma ta dawo gida cike da tsansar damuwa da nadamar meyasa bata bi shahida ta
shiga har gidan Tasi'u ba, ta bayyanawa 'yayyan shahida inda mahaifiyarsu take kuma
meyasa bata tsayar da dan saurayin nan ba, da alama dan gidan ne kanin Abba ta sanar
musu labarin da Madina ta bata akan hakikanin gaskiyar abunda ya faru cewar Madina
ba mayyh bace, ba ita ta kashe shiba kamar yanda suke zarginta, ta kuma fada musu
inda Madina take dakuma wahalarda take ciki sai ta tuna sojoji ne, daga sanda basu
gamsu da bayanintaba zasu iya afka mata da duka,
yini guda kaltum tayi cikin damuwa ko abinci takasa ci da zarar kuka yazo mata saita
shige bandaki tayi ta wanke fuska ta fito bataso kowa yagane abunda yake damunta
saboda babu wanda yataba tambayarta labarin sudan a cikin iyayenta.
da yamma makarantar islamiyyah take zuwa ita da kannenta dayake acikin unguwar
makarantar take da kafarsu suke tafiya yayinda direba ya ajiye mota ya tafi gidansa
aikinsa na ranar yakare indai ba oga Adnan bane ya aikesa cikin gari wajen yan uwansa
ba sai dai ko madam salaha ce ta aikeshi gidan kawayenta ko en uwanta itama.
tafiya tayi tafiya kaltum tayi shekara da dawowa daga sudan haka har ta gama aji hudu
tashiga aji biyar, ta sake gogewa ta waye saboda wayayyun kawayenda tayi a ajinsu
kusan duk abunda suke dashi tana dashi saidai inbata fadawa daddy ba zai saya babu
musu, kama daga sutura zuwa jaka da
takalmin makaranta masu tsada kayan kwalliya irin su hoda jan baki da sauransu,
aranar wata asabarce yan aji shida masu fita suke bikin fita (send up)amma da kayan
gida kowacce taje dan haka kaltum tasa dandashen leshinta ruwan zuma mai fulawa
koriya, anyi mata dinkin matsattse na riga da siket yayinda tahau kan wani dogon
takalmi (high hill) saita kara tsayi sosai, gyalenta kore ne ya shiga da adon leshin
yayinda jaka da takalminta suka zama ruwan zuma, ta dandasa wani farin gilashi a
fuskarta, yalo-yalon gashin kanta yazubo zuwa keyarta, tayi fari jawur da ita saikazata
idan kayi mata hausa bazata amsa ba, sun sha party anyi bayanai sannan akayi ciye-ciye
da tande-tande bayan an cashe sai aka watse.
direba najiranta a mota don haka tana fitowa tafada mota bayan ta gaisheshi cikin ladabi
sai ta shaidamasa unguwan yankaba takeso suje , tana fadar haka yasan inda take nufi
domin sun doshi shekara suna zuwa kofar Tasi'u su tsaya tayita leke-lekenta su tafi wani
lokacin ne idan sunga yarinyan nan shahida ta kirata tabata alewa su juya su dawo,
abun ya dade yana cinsa arai idan yayi alamar zai tambayeta saiya fasa domin kusan
kullum idan sukaje gidan a hanyar su ta dawowa kuka ta keyi shi yasa ma baya samun
damar tambayar ta, a yau kuwa ya sami damar jero mata dogayen tambayo yi a jejjere
saidai kash guntayen amsoshi take bashi ya dubeta ta madubi yayi murmushi yace kina
nufin wannan gida damuke zuwa bakya shiga?
kaltum ta gyada kai tace eh nan ne.
yayi murmushi yace yau dai zaki shiga ciki ko?
wannan karon ma gyada kai tayi tace eh zan shiga, Danladi ya fahimci kaltum bata son
tambayoyin nan don haka sai yayi shiru.
a inda ya saba ajiyeta anan suka tsaya wato karkashin wata katuwar bishiya dake kallon
kofar gidan Tasi'u, kaltum ta bude kofar mota amma bata fita ba, idonta ne cak akan
kofar gidan Tasi'u tana fatan kuma tana addu'ar Allah Ya fito mata da Shahida,
Allah mai karbar addu'a sai ga Shahida ta fito burum daga gida sanye da hijabi kuma
rataye da wata jaka mai kama da buhun sikari da alama makarantar islamiyyah zata tafi,
idon shahida akan motar su kaltum a inda idanuwansu ya kyallaro junansu sai su kayi wa
juna murmushi a lokaci guda.
kaltum ta daga mata hannu alamar kira babu
kokonto a zuciyar shahida saita tunkaro inda kaltum take zaune wato a cikin mota tana
isowa saita zube akasa ta kwashi gaisuwa, kaltum tayi caraf ta dagota tsaye yayinda
take rike da hannunta tana mai ambaton sunanta, shahida kin ini lfy?
ina zakijene da rana fatso-fatso?
shahida tayi dariya, islamiyya zan tafi.
kaltum ta tambaya cike damamaki islamiyyah da rana bada safe ko yamma ba?
shahida tace ina zuwa da safe duk ranar asabar da lahadi a taso mu shabiyun rana mu
koma tahfiz karfe biyu zuwa hudu na yamma sannan bayan magrib muje na dare.
kaltum ta gyada kai tace lallai ashe yanzu kinkusa saukewa ki zama malama kamar
mamarki?
shahida ta dubi kaltum cike da mamaki domin a iya saninta matan babanta dukkansu
biyu jahilaine, to wacce mamar ta take nufi?
ta rike hannun shahida tace kinci abincin rana ko?
shahida ta girgiza kai tace a'a ba a gama ba
shine na taho karna makara idan na dawo zanci.
kaltum tace haba dai ya za'a yi ki iya karatu cikinki da yunwa?
shigo mota kici cake da meat pie da lemo a wajen party aka bani, shahida tashiga bayan
mota kusa da kaltum ta zauna,
kaltum ta jawo ledoji dake ajiye a gefenta ta mika mata guda biyu kowanne akwai
dankwalan cake da meat pie ga lemon kwali da daurin cin-cin,
shahida ta tsinci kanta cikin farin ciki ta karba ta fara turawa daga yadda take cusawa
kasan tana tsananin jin yunwa.
.
Allah sarki, dan halak baya manta alkhairi, ko sharri aka masa sai ya saka da alkhairi, ku
dubi yadda kaltum ta sakawa Gg Ftt da alkhairi akan tsiyar da ta mata, haka ma kala,
Kuma ku duba yadda ta sakawa Madina da alkhairi akan erta da irin alkhairin da ta mata.
Da patan xamu ke lura da duk wata gaba na wannan littapin mai kyau domin mu dauka,
kuskuren cikin sa kuma mu nemi tsari wajen Allah da kiyayewa. Kamar yadda yau
kaltum tayi shigar ta bai dace ba, kamata yayi ko wace irin sutura ta sa ta dauko hijabi
ta daura akai ba gyale ba, yadda xai suturta ta a ko ina kuma a ko wannan biki
ADON DAWA 34
.
TRUE LIFE STORY
.
shahida ta tsinci kanta cikin farin ciki ta karba ta fara turawa, daga yadda take cusawa
kasan tana tsananin jin yunwa. dakuma marmarin abunda takeci don bata saba ci ba,
tausayinta ya kama kaltum saitaji kwalla ta cika mata ido tana tuna sanda Madina take
ciyar da ita asanda takejin yunwa, Allahu akbar, haka duniya take duk abunda ka shuka
shi zaka girba idan ka shuka alkhairi shi zaka girba idan ka shuka tsiya ita zaka girba ta
bibiyeka 'yaya da jikokin ka,
Madina ta taimakawa miskiniyar yarinya alokacinda take da iko da halin taimako yanzu
ga yarinyar tazo ta taimaki yar miskiniyar yarta ba tare da ta taba zaton ko amafarki
kaltum zata hadu da ire-iren zuri' arta ba,
kaltum kallon shahida kawai takeyi tamkar Madina take gani a idanuwanta sbd kamarsu
da sak hatta farcen yatsun hannunsu iri daya ne, maganarsu, kallonsu, dariyarsu duk iri
daya, kaunarta ta sake harde zuciyar kaltum kamar yadda takejin Madina a ranta,
shahida ta lura kallon yayi yawa saita fara takura tanajin kunya,
kaltum tayi sauri ta kawar da idanuwanta kasa, can ta dago ta dubi shahida tace ina
Mamar kine?
shahida ta kora lemon kwali tace tana gida.
kaltum ta girgiza kai tace ba sa'ada ba ina nufin mamarki data haifeki Madina.
shahida ta dago da sauri ta dubi kaltum yayinda ta tsaya cak daga abunda takeyi tajima
bata iya cewa komai ba sai ta fara magana cikin sanyin murya tace mamana Madina ta
bata an rasata.
da kaltum ta fara hawaye sai shahida ma ta fara kuka,
kaltum ta dafa kafadarta tace shahida daina kuka mamarki bata mutu ba tana raye
kuma bata bataba tana nan.
shahida ta zubawa kaltum ido tana mata duba irin na karyatawa,
kaltum ta sharce hawaye tace kinaso kiganta?
shahida ta girgiza kai tace nasan bazan taba ganinta ba don bazata sake zuwa ba har
abada,
kaltum ta gyara zama tace meyasa kika ce haka Shahida?
shahida ta sunkuyar da kai kasa tace ance mamana mayya ce ita ta cinye yaya Abba.
kaltum tayi caraf ta toshe mata baki tace karki sake fadar wannan maganar, kada kisake
fadawa kawayenki wannan maganar
sai ayi miki gori, sharri ce akeyiwa mamarki, Madina macece mai kirki ga hakuri Allah zai
wanketa in sha Allahu daga sharrin da akayi mata, kada ki fitar da rai zaki sake ganin
mahaifiyarki don haka kiyita addu'a Allah Ya dawo miki da mamarki kema ki zauna da
uwa kamar sauran kawayenki.
hawayene kadai yake kwaranya daga idanuwan shahida sai gyada kai kawai takeyi,
kukane yakecewa kaltum harsaida danladi yayi magana don tausayinsu don tun dazu
yana zaune agabar mota yana sauraron su yaji hawaye ya cika masa ido yace kaltum
yayakike kuka keda kike lallashinta ai saiki tayar mata da hankali idan taga kina kuka.
get din gidan general tukur aka bude wannan karon ma zukeken saurayin nan ne ta
ranan idanuwansa kiri-kiri akan kaltum da shahida kamar yadda suma suke duban sa har
ya wuce su, saiya dannan rivas ya dawo baya yazo dai dai inda suke ya zuge gilashin
wundon kasa ya kwalawa shahida kira a fusace,
shahida tahau karkarwa ta fito da sauri ta nufi wajensa sai kaltum taji ta tsorita ganin
yadda yake harararta saita rufo kofar mota da sauri tacewa danladi direba ya fizgi mota
su kara gaba don haka yakara tabbatarwa basuda gaskiya kuma bada alkhairi suke tafe
ba saiya tsorata musamman daya tambayin shahida tace bata santa ba, batasan
sunanta ba kuma gashi kullum sai ta zo ta kirata tana bata alewa ko biskit kuma tana
tambayarta ina mamarta Madina?
ANAN MUKA KAWO KARSHEN LITTAFI NA 3
ADON DAWA
LITTAFI NA HUDU
TRUE LIFE STORY
NA JAMILA UMAR TANKO (JUT)
PART 35
TARE DA SADIN MAA.
DAGA Al-Hada Hada Hausa Book stories
.
misalin karfe biyar na yammacin litinin kaltum yar makaranta sanye take da uniform na
makaranta harda jakar littatafanta agoye a bayanta tana tafe a bayan babur na adai-
daita sahu Keke napep, bata tsaya ako inaba sai a kofar gidan su shahida ta zaro kudi ta
biya mai napep yatafi,
ta kalli kofar gidan tsaf tana tunanin yanda zataga shahida, garin waige-waigenta ta
hango wannan zukeken saurayin zaune akan motar sa yana dubanta daga kofar gidansu
wato dan gidan general tukur daga yanda yake kallonta kasan akwai magana, bayan
duban mamaki da ganinta akwai duban dama ke nake nema babu mai kubutar dake
daga wajena yau saikin fadi abunda kike zuwanan kike nema,
bata tsorata ba saima ta harareshi ta kawar da kai gefe ta cigaba da tsayuwa akofarsu
shahida, ya tsaya kawai yana duban ikon Allah yayinda kansa yayi masa gingiringim yayi
sauri ya cire bakin gilashin da ya ragemasa ganinta sosai yayi sauri yayi kamar ya
kwallawa sojojin dasuke yi musu gadi kira su kamo masa yarinyan nan sai ya fasa ya
zura mata ido don yaga gudun ruwanta amma tabbas ya kudiri niyyan a yau dai bazai
bari yarinyannan ta subuce masa ba sai ya damketa yaji wacece ko waye ya aikota kuma
me take nema a wajen shahida.
tsawon mintina ashirin tana tsaye shi kuma bai daina kallon ta ba sai ga shahida da
kannenta sun taso daga islamiyya suna isowa wajensa suka duka suka gaishe da
makwabcinsu cikin ladabi ya amsa gami da cewa shahida ga bakuwarki can tana ta
jiranki tun dazu,
shahida ta dubi kofar gidansu domin can ya nuna nan da nan shahida ta isa inda kaltum
ke tsaye suka rike juna cike da murna,
kaltum ta rike hannun shahida tayi mata magana cikin sirri sai shahida ta waiwayo ta
kalli gidan general tukur gami da nunawa da hannu abun mamaki sai gani yayi sun
dunguma gidansu yana kallon kaltum duba na mamaki yayinda take masa duba na gani
kashe ni bana tsoro,
suka wuceshi kai tsaye suka tura katafaren get din gidan suka cusa kai basu dauki dogon
lokaci ba wajen amsa tambayoyin sojoji masu gadi kasancewar sunga kaltum da yar
gidan wato shahida shahida ce ke gaba yayinda kaltum ke biye da ita tana tafe tana
duban gidan yayi mata kyau kuma ya tsaru tunda farfajiyar daga farfagiyar gidan har
zuwa babban falon gidan, abunka da gidan yan boko komai an jere shi inda a inda ya
cancanta kasancewar babu kananan yara dazasu bata waje dan haka ko ina tsaf-tsaf
kamar an tande da harshe, babu kura ko datti ko da yake ba abun mamaki bane
kasancewar hadiman gidan suna da yawa mata da maza kowa da bangarenda yake
kulawa dashi.
a babban falo kaltum ta zauna yayinda shahida ta kutsa kai can ciki tana rada sallama
domin basu sami kowa a falonba kalle-kalle kawai kaltum keyi yayinda idanuwanta suka
dira wani rusheshen hoto enlargement amanne a jikin bango da alama dai hoton yan
gidan ne kakaf uwa da uba da ya yansu,
nan da nan kwakwalwarta ta fara tuno mata lbr da madina ta bata don bata manta da
sunayensu ba tace aranta ga general tukur da mummy hafsat ga babbar yarsu Surayya
ga yan autansu tagwaye hassan da hussaini daga nan kuma takasa tantance Abba da
mabiyinsa Anas saboda girmansu daya kamarsu daya kayan jikin su ma iri daya a hoton,
kuma irin wannan fuskar ta wuce a kofar gida don haka ba tantama kanin Abba ne, taci
gaba da jimamin mutuwar Abba a ranta yayinda hawaye ya cika mata ido a yayinda ta
ayyanowa Abba da Madina rayuwar aure domin sundace da juna kowannensu
kyakkyawane, Abba Allah Ya jikanka ka yafewa Madina itama bata kinka,
kaltum ta fada azuciyarta yayinda taci gaba da duban fuskar Abba da kaninsa
kasancewar ta rasa waye Abba a cikin su, shahida ne ta katse mata tunanin da ta keyi
tace wai ki shigo inji mummy hafsat tana falonta, kaltum taji zuciyarta ta harba sai yanzu
tafara fargaba, ta fara tunanin abunda zai je ya zo, kada fa haryanzu suna kufule da
Madina kuma ace suna nemanta su kama ta fushin da sukeyi da Madina ya shafeta gashi
ta shigo lungu ko duka ne kafin ta samu ta fito angama dirkarta, ga uwa uba sojoji masu
jajayen ido a bakin get sai yanda Allah Ya yi da ita yau kenan, ta fara jero salati a
zuciyarta na neman agaji daga rabbis samawati Ya taimaketa ta isar da sakon da ta
kudira a ranta ba don ta sami wani abu ba kuma badon ta burge kowa ba sai don ta
taimaki Madina ta wanketa daga zarginda akemata domin tunda ta dawo ta kasa samun
sukuni da kwanciyar hankali har saita fitar da abunnan aranta zata huta koda fadarshi
shine hanyar ajalinta,
shahida na gaba kaltum na biye da ita a baya har suka isa katafaren falo na alfarma a
inda idanuwanta ya hasko mata wata lafiyayyiyar mata mai kamala, yanda mummy
hafsat ke duban kaltum haka itama kaltum ke dubanta, dukansu mamaki ne fal a
idanuwan su,
kaltum bata zauna a kujerunda suke farko-farko ba har saida ta karasa gaban mummy
hafsat ta zube kasa ta kwashi gaisuwa cikin fara'a ta amsa tayi mata izinin ta tashi daga
kasa ta hau kan kujera saboda sanyin tiles,
kultum ta gyara zama ta girgiza kai tace nan ma ya isa mummy hafsat,
kiran sunan ta datayi shine ya kara mata mamaki kasancewar ko amafarki bata taba
ganin mai kama da kaltum ba balle tace yar gidan wane ne ba, ta gyara zama ta dubi
kaltum tayi murmushi cike da zumudi ta tambayeta yar makaranta yaya sunanki ?
Daga ina ?
Kaltum tayi murmushi ta amsa sunana kaltum daga nassarawa G R A nake ina
makaranta a crensent collage ajina shida, haryanzu dai bata amsa mata tambayanta ba
saima hargitsa mata tunani datayi mummy hafsat ta yatsuna fuska kadan tayi shiru can
tace ke yar gidan waye kenan?
kaltum tace yar gidan malam sale a gidan alh Adnan muke....
a fusace kyakkyawan saurayin nan ya turo kofa ya shigo damin dama labe yake ajikin
kofa yanaso yaji abunda kaltum ke tafe dashi sai yaji ta shiga shirme kuma daman bai
yarda da ita ba, ya daka mata tsawa mai firgitarwa har saida kaltum ta zabura ta dafe
kirji,
yace mummy kirabu da yarinyannan bata da gaskiya tunba yau ba take zuwa gidan nan
tana leke-leke ba, munafuka ce, ki barni da ita kawai in sa su Ashiru masu gadi suyita
gana mata azaba harsai ta fadi wanda ya turo ta a mota da take zuwa wani direba yake
kawota shine take amfani da shahida tana tambayanta sirrin gidan nan, yau kuma ta
shigo da kanta gashi nan tana kame-kame yau sai kin gwammace baki shigo gidan nan
ba.
yayinda yake kwanto belt din jikinsa mummy hafsat ta jawo kaltum jikinta ta daga hannu
wa dan nata ta dakatar dashi gami dayi masa gargadi kada ya sake yakaraso gabanta
balle yataba yarinyan nan da sunan duka, a tsaye yake rike da belt din sai tsuma yakeyi
don bacin rai yayinda kaltum ta rushe da kuka hakama shahida kukan takeyi sai
kakkarwa jikinsu yakeyi mummy hafsat tana rike da hannun kaltum tana durkushe
agabanta, tasa hannu ta share mata hawaye tace daina kuka fadamin meke tafe dake?
waye ya aikoki?
me kike nema?
kaltum ta share hawaye tace babu wanda ya turoni nina nemo gidan dakaina nazo..
ya sake kufula ya cije lebe yaji tamkar ya damko wuyan ta ya shake, mummy hafsat
harararsa takeyi alamar karya kariso, ta dago da kan kaltum sama tace yarinya kimin
bayani yanda zan fahimceki ban san ki ba amma kekin sanni har kina kiran sunana dasai
agida ake fada min balle ince a wajen aikina kika sanni ke yar sakandarine ko jami'a
bakije ba balle ince ke dalibatace, meke faruwa ne kaltum ?
Kaltum tayi ajiyar zuciya ta matse hawaye game da gyara zama ta sunkuyar dakanta
kasa ta fada cike da fargaba mai yawa don bata san abunda furucinnan nata zai
haifarba, farin ciki ko bakin ciki,
awajen Madina naji sunanki ita tabani lbrinki da kwatancen gidanki.
su dukka ukun suka maimaita a lokaci guda MADINA!!!
Zuciyoyinsu cike da mamaki shahida ta mike zunbur ta dafe kirji a inda aka hau kallon
kallon a tsakaninsu su hudun ba tare da wani ya kara iya cewa komai ba,
kaltum ta dubi kowannensu daya baya daya ta ce eh Madina mamar Abdul Malik Abdul
hakim da shahida tsohuwar matar Tasi'u itace ta bani labarin rayuwarta kakaf harma ta
sako zancen nan gidan general tukur da mummy hafsat tayimin dalla-dalla akan rasuwar
Abba, Madina ba itace silar hatsarin Abba ba, ba mayya bace bata taba sanin yadda ake
maita ba, Madina musulma ce mumina mai rikon addini wacce bata dauki rayuwar
duniya da zafi ba, ta fada ta maimaita irin tsananin son da takeyiwa Abba musamman
bayan ya mutu hawayenda,
kaltum ke fitarwa saida na mummy hafsat ya linka nata yayinda na shahida ya linka
nasu dukka,