Author : ummu maryam Category : Complete Novels
yarubawa"
"please garin Yoruba na da yawa..wanne daga ciki?"
"Gaskiya bansan sunan garinba..."
"Dan Allah kasan gidan wani danuwan su?" Mutumin girgiza mashi kai yayi, nan Salem
yaji kafanshi bata daukan shi, Dan durkusawa yayi wajen for more than five minutes
sannan ya mike ahankali ya koma waje tare da shiga cikin jet dinshi ya bar wajen,
"I regret falling in love with you.." Yafa cikin zuciyanshi
[10/8, 12:06 AM] Fadila S. Takko: ❤
ZAKISAN KONI WAYE
❤
®zuwairat(ummu maryam).
3⃣7⃣
Wajen karfe one suka isa yola,har lokacin hawaye bai bar zubowa tawaba, nadaman
abinda ya fidota kawai take, wani makeken gida suka shiga sukayi parking, waya taji
sunayi
"Mun iso..." Shuru yayi for a moment sannan yace
"OK ma" fita sukayi suka bude mata, kin fitowa tayi, daya mai bakin fuska ya
fixgota, ya rike mata hannu
"Dan Allah kar kuyimin komai.. Narokeku...ni kadaice wurin mamina... Please kuyi
hakuri.." Ta dinga fada cikin muryan ta Mara fita don kuka, cikin wani katon falo
suka wulla ta sannan suma suka shigo, falon ta fara kallo, gabanta ne yayi mugun
faduwa data ga makeken hoton Salem, sanye yake da red fitted suit hannunshi cikin
aljihunshi.. Fuskanshi kaman da models, kara kara juyawa tayi ta ga wani yana tsaye
bayan wata beautiful mata da wani cool looking man, nan tasan gidansu Salem aka
kawota, sabon kuka tafarayi, sun fi minti ashirin da zuwa sannan Umma ta fito,
tafiyanta na kasaita tamkar ka tabata jini ya fito, tawa daga kumburarrun
idanuwanta tayi ta kalleta, gani tayi da ita da Salem kaman an tsaga kara, tsawo
kawai zai nuna mata, da sauri tawa tayi kneeling down kanta kasa hawaye na zuba
tana fargaban abinda zai faru, Umma tsayawa tayi tana kallon tawa, mamaki ne kwance
kan fuskanta don atunaninta wata gingimemeyin Yoruba zata gani, sannan kuma Sam
babu alaman yarbancin jikin ta, kallon fuskanta tayi taga she is beyond wonderful.
"Please sit" ta fadawa tawa, Ahankali tawa ta girgiza kanta, gaidata tayi dukda
muryan ta bata fita,amsawa tayi tana kara mamaki don Sam hausanta babu alaman yare
cikin shi..kallon guys din tayi
"Are sure she's the one?"
"Yes ma..daga gidanshi muka daukota" daya daga cikin guys din ya amsa mata, kallon
yanda tawa take shessheka tayi
"Kunyi mata wani abune?" Ta sake tambayan su, da sauri suka girgiza mata kai.
"Excuse us" ta fada masu, da sauri suka fita, kallon tawa tayi
"Come closer" ta umarceta, tawa bata mike ba tayi rarrafa zuwa gabanta, Umma kura
mata ido tayi ta rasa abinda zata ce mata, Ahankali tace
"What is your name?" Cikin shessheka tace
"Tawakaltu Lukman"
"Wace yare ce ke?"
"Yoruba" ta amsa mata Ahankali,
"Koma ki zauna muyi wata magana" tawa kara girgiza mata kai tayi,
"Bari insa akawo maki abinci kafin muyi magana" tawa still girgiza kai tayi, Umma
tsaya kallon ta tayi sai taga sam yarinyan ba irin yarinya marasa jin maganan nan
bane...cikin zuciyanta sai tafara nadama daukota dayawa akayi,
"You can't let your only son marry Yoruba" wata zuciya ta fada mata,
"Kinsan Salem Yusuf sulaiman?" Umma ta tambayeta, Ahankali tawa ta gyada mata kai
"Meke tsakanin Ku?" Ta sake tambayan ta, shuru tawa tayi bata ce komaiba, Umma
tacigaba dacewa
"Nice mahaifiyan Salem...kuma banason ki dauka cewa don inci maki mutunci yasa nasa
adauko Mani ke...me kikeyi gidan ?" Gaban tawa faduwa ya farayi,still bata ce
komaiba
"Zina kukeyi?" Da sauri tawa ta girgiza mata kai sabon hawaye na zubo mata,
"Then me ya mace kamanki takeyi gidan namiji mara aure?.." Tawa bata ce komaiba sai
goge hawayenta take, Ahankali Umma tacigaba dacewa
" anyway.. Kome ke tsakanin Ku inason ta tsinke from this moment... Badan baki
yimin ba..Aa..saidon aladan mu da naku ba daya bane ...but if you want...you can
name your price... From 1m to 20m zan iya baki indai kin yimin alkawarin zaki rabu
da Salem" tawa girgiza kanta tayi tafara cewa
"Please I don't want anything.. I want to go to my mami...kuma bazan kara kula
Salem ba" tafada cikin muryan ta Mara fita, Umma duk sai taji haushin kanta
"Please kar ki kirani da muguwar mace...am just a woman that loves her son.."
Ahankali tawa tace
"You are not ma..." Umma Dan murmushi tayi, tawa kuma goge hawayenta tayi,
"Yanzu ina baki shawaran kar ki Kara zuwa gidan saurayi..baa haka a aladanmu" Umma
ta fada mata, Ahankali tawa tace
"First love wallahi bansan gidanshi bane..." Umma dadin sunan taji.. Don babu mai
kiranta hakasai Salem
"Hope babu abinda yayi maki" da sauri tawa ta girgiza mata kai
"Ki gayamin in yayi maki wani abu.. Am he's mother..I know how to deal with him"
"Baiyi min komaiba "
"That's good to hear..hope baki ji haushin abinda na fada maki ba?"
"No ma" ta amsa mata Ahankali
"Tashi daga kneeling kici abinci sai insa a maida ki gida" bata tashi daga kan
gwuiwowinta tace
"Thanks ma..na koshi"
"To shikenan.. Yanzu are we friends?" Da sauri tawa ta daga mata kai
"Then ki bani number ki..sai mu dinga gaisawa time to time" Ahankali tawa taba
labarin yanda guys din suka yarda mata waya, mikewa Umma tayi ta shiga bedroom
dinta, baa dadeba ta fito dauke da wani waya gionee m6 amma ba sabuwa ba, sai wata
Leda mai dauke da kudi, tana zuwa ta mika mata wayan, kememe tawa taki mika hannu
"Ikon Allah.. Ki amsa mana" girgiza kai tayi
"To..kina fushi kan maganan danayi maki kenan"
"Aa..nagode" ledan ta mikewa tawa
"Gashi ki sayi duk abinda kike so.." Shima tawa girgiza mata kai tayi
"Gaskiya we are not friends.. Ya zaayi kiyi refusing dina..to amsa" ta kara mika
mata wayan, Ahankali tawa ta amsa
"Thanks ma" Umma kara miko mata kudin tayi amma taki amsa, duk magiyan da Umma tayi
bata amshi kudin ba
"Shikenan.. Amma ki huta zuwa yanma sai a tafi dake gida" kanta kasa tace
"Zan tafi yanzu"
"To shikenan.. Bari insa driver na ya maidaki gida" girgiza mata kai tayi
"Kawai su kaini park" Umma sawa tayi aka dauketa tana tunanin anya ta kyauta abinda
tayi..don yarinyan ta kwanta mata
"She's Yoruba" tafada cikin ranta.
Tawa mancewa tayi bata dauki bag dinta daga cikin motan guys din da suka kawotaba,
wani hummer ya kaita park. Kuka kawai take in ta tuna daga yanzu babu ita ba
Salem.ji take kaman yau yafi kowane rana bakin ciki da muni a rayuwanta,.Ana
sauketa ta duba taga babu bag dinta, wani shagon da ake saida waya ta shiga ta
mika masu wayan da Umma ta bata, abanza suka sai wayan a 18k, bata tsaya ciniki
dasuba ta amshi kudin, cikin shagon ta amshi wayan ta kira mami tayi mata karya
cewa motan su ta lalace sannan kuma an dauke mata waya a park.
Cikin park ta shiga ta hau motan Ilorin , duk Wanda ya ganta yasan bata cikin
hayyacinta.
❤
Tun cikin kauye ake tambayan hinde abinda ya faru cos kuka take kaman anyi mata
albishir da jahannama, bata cewa kowa kala ba ta isa gidan ameera, da kuka ta iso
Wanda hakan yayi sanadiyan mikewa ameera dake kudundune cikin zaninta,
"Wayyo sun kashe ni " tafada tana kuka
"Inna meyasameki?" Yarta ta tambayeta, hinde zama tayi nan kasa
"Zinarin da ameera ta bani aka amshe../" bata idaba ameera dake tsaye bakin kofa ta
saki ashar
"Wallahi kinyi kadan...kawai ki kawo min zinari na..don wallahi sai ya sayi
dukkanku.." Tafada tana rike kugunta
"Wallahi Aisha..wasune suka amshe..."
"Tell that to the birds..sai kin biyani kayana...kawai daga nace Dan saki da ku
shine zaki cuceni?.. Aikam ban yarda sai kin biyani..." Hinde bata ce komai ba
tacigaba da kuka
"Ki fidomin kayana..barauniya..." Gaskiya ki bar zaganmin uwar..." Inji diyar
hinde, tafa hannu ameera tayi sannan ta nuna diyar
"Look at this creepy zombie.. Har kin isa kiyi magana inda nake magana?..ki gayawa
barauniyan nan ta bani kayana..in ba hakaba in na fita daga gidan nan...sai na
kulle duk zuriyanku..banza karamar bazawara..." Yarinya tsaka taja ta mikar da
uwarta, aikam da sauri ameera ta karasa inda suke ta rike hinde da hannu daya
sannan ta mika mata dayan hannunta
"Yanzu mikomin zinari na..." Bata karasa ba aka bude gate majed yashigo, ko
kallonshi batayiba tacigaba da girgiza hinde tana cewa
"Ki bani yanzu ba sai gobe ba..." hinde sai kuka take ita kuma banzan diyarta sai
kokarin kwace hinde take,
"Meke faruwa nan?" Majed ya tambayesu, cikin kuka hinde ta gaya mashi, ameera kam
ko kallo bai isheta ba ,nace ko kin mance abinda ya taba yi maki
"Dalla malama ki saketa..."
"Ka biyamin zinari na mana..."
"Baki sakinta?..." Yafada yana karasowa inda suke, ameera na ganin ya karaso wajen
su tayi saurin sakin hinde, Hinde najinta free ta bar gidan da gudu diyarta ta bi
bayanta, ameera nuna majed tayi da dan yatsa
"Ban manta abinda ka yimin ba..kuma when the time is right zan rama..."" Tsaki ya
ja zai shiga ciki ya dauki abinda akace ya dauko wayanshi yafara ringing, nan Abdul
ke fada mashi tawa ta gudu, da sauri majed yaje ya dauki CCTV recorder ya kara
gaba.
❤
Salem ya dawo abuja duk Ahankali shi tace, baisan ta inda zai fara Neman ta
ba...baisan wane garin Yoruba zai fara zuwa ba, kaman ya hadiye zuciya ya mutu
yakeji don zuciyanshi baki wulik take, yana sauka daga jet ya nufi inda ya sauke
ameera, dakunan yadinga dubawa daya bayan daya kilan Allah yasa ya ganta ciki,
amma nothing. Gaban wani kujera ya zauna ya hada kai da gwaiwa, gani yake in zai
ganta yanzu babu abinda zai hanashi cin uwarta for playing with his heart
"Tawa..you can't run from me...Nigeria is too small for you to run.. Wallahi sonki
bazai hanani maganinki ba..." Ya fadawa kanshi.
Around 2pm su Abdul suka dawo amma babu courage din da zasu shiga ciki, tsakar
gidan Salem ya fito yana kale2, ajiyan zuciya kawai yake, baisan ana guduwa daga
mutum don yawan arzikin shi ba. Tun safe baisha ko ruwaba, tap da bawa flowaer ruwa
yaje yayi alwallah sannan ta ya fita waje don zuwa masjid, nan yaga su Abdul tsaye
waje, ko kallonsu bai yiba ya wuce su, kan hanyan da zaibi ya hangi wani abu kaman
waya tarwase a kasa, Ahankali ya karasa wajen, yana zuwa ya tsaya yana kallon
wayan, nan take yaga kaman wayan tawa, Dan dukawa yayi ya dauki wayan yaga confirm
wayan tawa ne, juyawa yayi yaga CCTV na kallon wurin, daukan sim card din yayi ya
saka cikin aljihunshi ya kara gaba.
Yana dawowa yaje dakin da wasu mutane uku ke duba mai shiga da fita suke, yana
shiga CCTV monitor takwas nagani, yana shiga yace
"I want to see what happened since in the morning"
[10/8, 12:06 AM] Fadila S. Takko: ❤
ZAKISAN KONI WAYE
❤
®zuwairat (ummu maryam)
3⃣8⃣
Kan daya daga cikin kujeran wajen Salem ya zauna, fara maido recording din baya
sukayi, Salem kurawa monitor din ido yayi, ana zuwa inda tawa ta fita, da farko ya
saidasu, fara playing dinta akayi, har inda gate ya wulla ta saida ya gani,
idanuwanshi cikowa yayi da kwalla, kallon su yayi
"Kuna ina wannan lokacin?" Ya tambayesu
"Sir muna masjid cos 5:20am ne" daya ya amsa mashi, cigaba da playing yayi har inda
tawa ta fita tana kallon gidan tana goge hawaye, kan Wanda ke waje ya maida kanshi
, nan yaga sannan wasu suka saida tawa..da sauri Salem ya mike tsaye, gani yayi
suna yi mata magana kuma the next minute suka fara nuna mata bindiga, hannu Salem
ya dora bisa kai, yana kallo suka tafi daita.. Komawa yayi kasa ya fashe da kuka
kaman Dan yaro, don gani yake tamkar an kashe ta, dayan daga cikin guys din yadan
dafa mashi kafada, da karfi Salem ya tureshi sannan ya mike tsaye,
"Kuna ina sanda aka dauketa!" Yafada da karfi, dukkan su shuru sukayi suna kallon
juna
"I said kuna ina!?..." Still shuru sukayi.. Ahankali Salem ya fara cewa
"What have I done to deserve this From you guys... Na baku free food.. Free
shelter...the best cloth...and you can't do your job...saboda in wani ya gaji ya
huta sai wani ya hau aiki, shiyasa na dauki Ku uku aiki..amma hakan bai da
amfani... Nasan you guys are incompetent.. All of you are fired!!!" Ya fada sannan
ya fice daga dakin yana kuka...yasan in ba Umma ba babu wacce zatasan yana abj
balle ayi kidnapping tawa..
"Umma..why..." Kuka ne yaci karfinshi, kasa ya zauna gaban jet yana kuka kaman
yaro, pilot ne yazo ya dinga rarrashin shi, saida yayi mai isanshi sannan ya mike
ya kalli pilot din
"Call me those fools outside" yafada cikin husky voice, da sauri pilot ya kirawo su
Abdul, cikin jet ya shiga da sauri su Abdul suka yi parking motan su suka shiga
cikin jet sannan pilot ya kalleshi
"Sir ina zamu?"
"Yola" yafada yana kafa speck a fuskanshi.
Around 3:45pm suka isa yola, personal house dinshi suka sauka sannan suka dau motan
sukayi family home, agaban masjid dake gidansu sukayi sallah sannan Salem yayi
trekking zuwa gidansu, yana daf da shiga gidan yadan juya aikam sai ya hangi bag
din tawa cikin flowers din kofan gidansu, da sauri ya karasa wurin ya dauki bag din
ya bude gani yayi har kudinta na cikin bag din...wani sabon kuka yafarayi
"What did Umma do to you...you caused it..why do you have to run from me?.....is it
a crime to love you?..." Kan ya dora da bangon gate dinsu yana kuka, yafi minti
goma wurin sannan ya shiga ciki. Already guards suna jiranshi, yana zuwa yav kalle
su
"Don't let anybody into this falo..except Abba.. Kun gane?" Yafada yana nuna masu
side din Umma
"Yes sir" suka amsa mashi sannan yashiga ciki.
Afalo ya tardata tana zaune ita kadai tayi tagumi, ko tunanin me take? Oho.
Takalmin kafanshi ya cire, ya karasa inda take, kwantawa yayi kasa flat tare da
rike kafan Umma, sai lokacin Umma tasan da mutum cikin falon, kuka sosai Salem ya
farayi
"Umma na rokeki da sunan Allah.. Ki bani yar mutane in maida masu..." Umma kallon
mamaki tafara yi mashi
"Kai ..kana haukane?.." Kai ya fara daga mata
"Umma am mad in love with tawa..kin dauketa..please tell me where she is..." Umma
kokarin kwace kafanta tayi amma Salem yakara rike ankle dinta kaman his life
depends on it..
"Umma please tell me inda kika kai tawa...nasan baki sonta amma bansan you can go
this length ba..." Kuka ya dingayi har da shessheka.. Umma tsaya kallon ikon rabbi
tayi..
"Son..please free my leg.." Girgiza kai yayi
"No Umma.. Na rokeki..kifadamim inda kika kai Tawakaltu.. Menayi?..meye
laifina?..is it my fault that I feel in love with the wrong person?... Ba laifi na
bane...bani na sa zuciya ta ta kamu da son wacce baki soba... Umma please tell me
inda kika sa aka kai taw..." Kuka yaci karfinshi , yana kuka yana tari.. Gashi tun
safe ko ruwa baishaba, tari yacigaba dayi sosai kaman ranshi zai fita, shafa mashi
kai Umma tafarayi, da sauri ya kauda kanshi yacigaba da tare, saida ya gama
yacigaba dacewa
"Ki fadamin..please..." Wani tarin yafarayi, nan fa hankalin Umma yafara tashi,
kokarin cire kafanta tayi amma Salem bai saki kafanba
"Son please sit up...you are hurting yourself.."
"Umma you don't care if I die...inda kinasona zakiso abinda nake so..." Tari
yacigaba dayi kaman ranshi zaifita,,
"Son please ka tashi..." $ kara girgiza mata kai yayi, yacigaba da tari, saida
tarin ya lafa yacigaba da kuka tare dacewa
"Wallahi Umma.. Bantaba tunanin zan kamu da son yarinya hakaba...but I can't help
it...nidai ..." Coughing yacigaba dayi ahankali Umma tace
"Ita ta fada maka nayi mata wani abu?..."
"Ai hired guys dinki yarda mata waya sukayi...Umma why...tunda bakin son tawa na
hakura daita..amma please tell me where she is.." Yafada cikin kuka, kokarin mikewa
tayi amma yanda Salem ya rike mata kafa ya hanata tashi
"Ka sakarmin kafa kafin in bata maka rai..."
"Wallahi ki kashe ni...hakan zai fimin sauki..." Umma kwalawa guards dinta kira
tayi suzo su dauke Salem daga dakin amma suna zuwa bakin kofan guards din Salem
suka hanasu shiga,..duk yanda sukaso wucewa basu samu hanya ba, sunfi minti ashirin
ahaka, Umma gani tayi da gaske Salem yake, gashi sai tari yake babu sassautawa, duk
yanda Umma taso lallashin sa abun yaci tura, datace ya sakar mata kafa sai yace
"Please tell me where you took tawa.." Magiya Umma tafarayi sosai amma yaki
sakinta, Sam bata son Abba yasan abinda ke faruwa don dukda yana da saukin kai baya
tolerating nonsense, Salem kuka yake sosai Umma tarasa yanda zatayi dashi, abu
kaman wasa har hour daya tayi Salem yaki sakar mata kafa wai dole saita fada mashi
inda ta kai tawa. Ana cikin haka Abba ya dawo, tundaga nesa taga guards din Salem
dana Umma tsaye suna kallon juna, kallon Mara dadi, ana parking mota Abba ya fito
ya nufo wurin,
"Meke faruwa nan?" Ya tambaya yana kallon each and everyone, daya daga cikin guard
din Umma yace
"Sir..Hajiya keta kiran mu amma sun hanamu shiga" Abba kallo guards din Salem yayi
"Meye haka?"
"Sir we are following orders" inji majed, Abba bai kara cewa komai ba ya shiga
ciki, nan fa gaban Haj yafara disco ,Abba kallon Salem dake kwance kasa yana kuka,
"Me ke faruwa nan?" Ya tambaya yana kallon su, Salem baice komaiba yacigaba da
kuka shi ita kuma Hajiya shuru tayi
"Baku jina ne?"
"Abba ka fadawa Umma tabani tawa..."
"What are you talking about?" Abba ya tambayeshi, cikin kuka ya fada mashi abinda
ya faru
"Subhanallahi.. Hajiya is he saying the truth?" Umma shuru tayi, alaman bata da
gaskiya, Abba dukawa yayi
"Son stand up..." Da sauri ya girgiza mashi kai
Abba ka fada mata ta gayamin inda ta kai Tawakaltu.. " Abba kallon Umma yayi
"Wai ina kika kai yarinyan mutane?" Ahankali Umma tafara cewa
"Son kayi hakuri... Babu abinda nayi mata...I just beg her to stay away from you..
And she promised..." Kuka sosai Salem yafarayi
"Umma why..." Tari yafarayi sosai yana nishi sama2, da sauri Abba ya dagashi, aikam
sai jini hancinshi..kuka Umma tafara
"Wallahi nayi nadama...tun yarinyan na nan nafara nadaman abinda nayi.." Abba dirty
look yayi mata sannan ya rike Salem
"Muje part dina in baka first aid kafin in kira doctor.." Ahankali Salem ya girgiza
mashi kai
"No Abba.. Allah yasa wannan yazama ajalina..." Tafiya yafarayi, ko tsakiyan dakin
bai kaiba ya fadi kasa, da gudu Abba da Umma suka karasa wajenshi, acikin tension
Abba ya kira doctor, Umma kwalawa guards kira tayi tana kuka, gabaki dayan su suka
shigo dakin, duk ahankali su tashi yayi especially personal guards dinshi. Daukan
shi su Abdul sukayi,
"Follow me!" Dad ya umarcesu, da sauri Abba ya fita suka bi bayan shi.
Wani part my dauke da hospital equipment aka kaishe, Salem bude ido yayi yaga
mutane triple, maidasu yayi rufe tare da dafa kanshi.
Bayan minti ashirin doc yazo, bai bata lokaci ba ya sa mashi drip.
❤❤
Yau ya komawa ameera sabo cos yau ita kadai ta wuni, gashi da musassara ta wuni ga
ciwon kai dana Mara, duk abin duniya ya isheta, bakin gate taje tayi knocking,
" meye?" Suka tambayeta, cikin kuka tace
"Dan Allah Ku kiramin hinde.." Banza sukayi daita,
"Kunji Dan Allah.. Bani da lafiya ne..."
"Kar ki kara aikanmu...darajanki daya da baki da lafiya.. Bari musa akira maki ita"
daya daga cikin su ya fada sannan ya kira wani ya aikeshi ya kira hinde.
Bayan kaman minti ashirin sai ga hinde ta shigo gidan , gani tayi ameera durkushe
kasa tana kuka hannunta kan maranta
"Lafiya?" Ta tambayeta tana karasowa wajen ta, cikin kuka tace
"Cikina...wayyo..menses zanyi..."
"Meye messes" tafada tana dagata tsaye
"Alada zanyi..." Tafada tana kuka tana yarfa hannuwa,
"Daman haka yake yi maki?" Kai kawai ameera ta daga mata,
"Sannu" hinde ta dinga yimata, ta maidata daki sannan ta dora mata ruwan ,