Advertisements
Chapter 6 Reading ZAKISAN KONI WAYE by ummu maryam BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

ZAKISAN KONI WAYE by ummu maryam

Author :  ummu maryam Category :  Complete Novels

Chapter   6 / 44

15K to 18K   out of 130.5K words

dashi sai in maido maka..." Shuru kB yayi kaman mai tunanin wani
Abu sannan yace
"To alh Amman million 2 zaka bada..kasan in ba kaiba babu Wanda zan yarda inyiwa
wannan alfarman..." Ba musu dad ameera ya amince.

Wacegari tun gari bai wayeba dad ya tafi wurin da kB ke saida exotic car a sharada.
Yana nan zaune har karfe tara kafin yaranshi su bude wajen, suna budewa kB yasa
yaranahi suka karbi jeep din dad sannan suka bashi wani dunkullen jaguar, da
agreement din cewan dad zai kawo million 2 inzai dawo.

KB ya taimaka mashi sukayi activating navigation din motan, cikin kankanin lokaci
ya nuna mashi address din Salem, babu bata lokaci dad ya hau motan ya fara tahowa,
yana tafiya motan na nuna mashi inda zaibi har ya iso wani makeken gida, horn yayi,
mai gadin gidan ya dan bude, rufewa yayi yashiga cikin gidan , falo ya tarda Abdul
nan ya fada ga wani mutum chan waje yanason shigowa, Abdul mikewa yayi yaje side
din Salem, a lokacin Salem na zaune yana waya da first love dinshi , Salem dan
kauda wayan yayi
"Alh Abdul ya akayi?"
"Sir wani mutum ne yake son shigowa..da alaman wurinka yazo..." Salem yasan alh
umar ne don babu Wanda yasan address dinshi
"Go and tell him...bani da lokaci yanzu..." Yana kaiwa nan ya cigaba da waya da
ummanshi.
Abdul komawa yayi ya fadawa maigadi sakon shikuma mai gadi ya fadawa dad ameera
"Ai kam ba inda zani...zan jirashi har sai ya sami time din" ya fada cikin ranshi.

Salem kam bai fitaba kuma baisa aka kiramashi dad ameera ba, har lokacin sallan
zuhr sannan ya fita, shida Abdul, dad ameera na ganin an bude gate ya fito daga
cikin mota da sauri ya nufeshi da sauri shima Abdul ya tare oganshi, Salem na daga
kai ya ganeshi bata fuska yayi kaman baitaba dariyaba, cikin girmamawa dad ameera
yace
"Good after noon s...."
"Who are you?" Salem ya watsa mashi tambaya batare da ya amsa gaisuwanshiba. Dan
runtsunawa dad ameera yayi kafin yace
"Sir nine umar adam ..."
"And so?"
"Sir kaikace inzo..."
"Katafi gobe ka dawo am busy..." yana kaiwa nan ya juya ya barshi nan tsaye. Jikin
ba kwari dad ameera ya juya yabar wurin, Salem dan juyawa yayi yaga yanda jikinshi
yayi sanyi
"Don't give up...cos yanzu na fara treating dinku" ya fada ciki ranshi.

Haka dad ameera yaje ya biya million biyu bai samu biyan bukata ba.
Wacegari ma ya koma Amman da motan shi kasancewan ya riga yasan gidan, kaman jiya
ma Salem cewa yayi bashi da time ya tafi gobe ya dawo.
Atakaice saida dad ameera yayi sati daya yana zuwa sannan Salem ya bashi daman
shiga falo, yafi hour uku zaune kafin Salem yafito, fuskanshi Sam babu walwala.
Zama yayi ya dora kafa daya kan daya yana kadasu ahankali
"What can I do for you.. Don yan kwana kin nan ka hanani sakewa.." Ahankali dad
ameera ya dan rutsuna sannan yace
"Sir..aikina..."
"Please mister man...bani da time..talk fast" yafada babu alaman wasa amuryanshi
"Sir ban yi komai ba kuma an aikomin da emails wai anyi firing dina...."
"Bakayi komaiba...kana kirana mara adalci kenan..."
"No sir ba abinda nak...." Salem ya kara katseshi dacewa
"Yes mana...you are telling me ban san aikinaba tunda bakayi komaiba na
koreka...anyway nazo garin nan kuma na duba ayyukanka sam batayiba...sannan
abubuwan daya kamata abawa local hospitals kyauta saida masu akeyi..." Dasauri dad
ameera yace
"Sir ba haka bane...."
"Mr umar are you by any means calling me a liar?..." Da sauri dad ameera ta girgiza
kai
"No sir...am sorry.."
"Sorry for your self" yafada yana daria cikin ranshi don yanda mutumin ya zama abin
tausayi cikin dan kankanin lokaci
"As I was saying before you interrupted... In na gayawa Bill Gates abinda akeyi
azone dinka INA tabbatar maka da komai naka zaa amshe..." Da sauri dad ameera ya
runtsuna
"Sir ka rufamin asiri kaman yanda Allah ya rufa maka asiri.."
"Zan rufa maka asiri on one condition..." Da sauri dad ameera ya kara cewa
"Anything sir..." Salem balance yayi kan sofa sannan ya fara cewa
"Na san kasani bani da mata...kuma daga ganinka kana kama da mutanen arziki..so
inason acikin family dinka koma yanuwanka ka nema min yarinyan da zsan aura batare
da bata lokaciba...and dana so auren yarka saidai bansan ko kanada yarinyan data
isa aureba" tunda yafara magana dad ameera ke murnan cikin zuciyanshi.. Imagine ace
sir Salem surukinshi ne
"Sir ina da yarinyan data isa aure mana.."
"Really?.." Yafada yana tunanin
"Nasan zaayi hakan" dad ameera yacigaba dacewa
"Yes sir..na baka ita...kuma bana bukatan sisinka..." Cikin ranshi yace
"Daman bani da niyyan kashe sisina kan lalatacciyan yarka..." Dariya karfin hali
Salem yayi kafin yace
"That's wonderful of you...Amman wani hanzari ba guduba...bata da Wanda take
so?...kar a samu matsala"
"Babu kowai..yanzu yaushe kake bukatan akawo maka mata?" Shuru Salem yayi for a
moment sannan yace
"Zan gaya maka..ka amshi number ta wajen guard dina sai ka kirani"
"OK sir" dad ameera har ya mike sai kuma juyowa
"Sir yanzu ina iya komawa bakin aikina?"
"I will let you know" ya amsa mashi atakaice. Dad ameera fita yayi ranshi fal don
anashi tunanin ko da bashi da aikinyi ba zaiyi talaushiba muddin yana da Salem
amatsayin surukinshi. Sai Allah Allah yake yaje gida ya bawa angel dinshi labarin.

Yana fita Salem ya kira agent dinshi, bayan sun gaisa Salem ya fara cewa
"Inason ka samomin fili a kauyen abuja.."
"Karami ko babba?"
"Girmanta yayi 100by100 sannan kasa afara ginashi right away...sannan ka tabbatar
fence din yayi tsawo kaman na prison... Kuma ayi ginin ciki da pure kasa no
cement.."
"Sir no cement kuma?"
"Are you deaf?...nace banda cement ko kadan..."
"OK sir...daki nawa?" Shuru Salem yayi kaman bai tunani sannan yace
"Daki biyu sai very small kitchen sannan bathroom da toilet waje daya"
"Alright sir" mutumin yafada sannan Salem ya katse wayanshi.
Dariya ya farayi yancewa
"This is going to be marvelous..."

[10/8, 12:06 AM] Fadila S. Takko: ❤
*ZAKISAN KONI WAYE
* 💙💚💛💜💛
®zuwairat(ummu maryam)

1⃣5⃣

Dad ameera sauri yake don ya isa gida, yana shiga gidan ko parking kirki baiyiba ya
shiga ciki.

Direct dakin mom ya shiga, mom juyowa tayi ta kalleshi kafin tace
"Alh lafia? Ko yauma baka samu ganin shi ba?" Hulan kanshi ya cire yana cewa
"Hajiya.. Ameera ta tayi goshi..." Mom na jin ya kira sunan ameera ta dan bata
fuska kaman ba ita ta haifetaba.
"Me akayi kuma?" Dad cire babban riganshi yayi yana cewa
" ameera ta tayi goshi wallahi... Saidai yan bakincik su mutu" dan tabe baki mom
tayi
"Wai me yafaru?"
"Ai naga kin bata fuska daga kiran sunan ameera.. To albishirinki"
"Ni ka gayamin abinda ke faruwa" zama dad yayi kusa da mom tare da dora hannunshi
kan kafadan mom sannan ya fara cewa
" sir Salem yace yanason ameera da aure kuma na bashi..." Zumbur ta mike
"Haba alh..yace yanasonta ko ka kaimashi tallanta...kuma yarinyan da ba ganin kowa
da gashin arziki zaka bawa shugabanku gaba daya ta jawo mana zagi?" Ta danyi shuru
ta hadiyi wani abu sannan ta cigaba dacewa
"Gaskiya alh ka sake shawara.." Shima mikewa yayi
"Daman nasan haka zakice...wallahi da ba gabana kika haifeta ba da sai ince bake
kika haifetaba...to aure anyi angama...cewa yayi zai kirani..yana kirana yau zansa
a daura masu aure a tafi da ita gidan Hutu...ban taba ganin inda uwa take bakin
ciki da karuwan yarta ba sai a kanki...rubbish" mom baki ta tabe kafin tace
"Ni ina ruwana...daman tsutsun daya ja ruwa kanshi yake karewa....ayi lafiya" dad
baice mata komai ba ya fice, direct dakin ameera ya tafi ,nan ya zaiyana mata yanda
sukayi da Salem, dad bata gamaba tayi daka tsalle ta fada jikin dad dinta, shima
rungumeta yayi.

Bayan dad yafita, kwantawa ameera tayi kan gado tana cewa
"Daman haka Allah yake biyawa bawanshi bukata? Daman duk abinda mutum ke in har
kasa abun cikin ranka zaka samu?.. Imagine me as Salem wife , imagine me as surukin
former President... Woowww" tafada da karfi tana tsalle kan gado, wayanta ta dauka
tafara dailing number zeenat.



Bangaren Salem kam hankalishi kwance don yanzu kwana uku da maganan shi da dad
ameera, gini kam ana chan anayinta abinka da mai naira har an gama fence din kuma
da aka turowa Salem hoton cewa yayi yayi kadan akara tsawon fence din, wani irin
dogon fence mai kama da tower akayi sannan aka fara ginin ciki, shima har sunkai
tsakiya aka turawa Salem hoton, shima cewa yayi dakunan sunyi girma a ragesu.

Yau yana kwance murmushi ne kwance a fuskanshi.. Kona meye oho, wayan shi ya dauka
yasa Abdul ya kira Makeup artist dinshi.

Around 5pm suka bar gidan, suna zuwa daidai inda ameera ta mareshi ya fara kallon
wurin kawai sai ya hangi kaman yarinyan data siya mashi cotton wool lokacin da yake
nasal bleeding, kallon Abdul yayi kafin yace
"Alh wancan kaman yarinyan data siyamin auduga ko..." Shima Abdul kallon wurin yayi
"Yes sir..itace kuma kaman abun hawa take jira...kilan ta tashi daga wurin aiki"
Salem rage gudun abun hwanshi yayi yana cewa
"Wane aiki take?" Abdul murmushi yayi
"Sir bakaji sanda madam din datakewa aiki tana zaginta wai ta kashe mata kudi har
da cewa saita biyata..." Shuru Salem yayi kaman mai tunanin wani abu sannan yace
"Sam banjiba ai yarinyan nan tana marina wuta ya daike min Amman naga sanda ta sayi
auduga ta baka...Amman baka gayamin aikn datake ba" suna zuwa daidai inda take
Abdul nacewa
"Inajin abinci suke saidawa don naji matan nacewa tawuce ta bawa mutane abinci"
Salem tsaida taxi yayi inda take, tawa na ganin taxi ya tsaya sai tadanyi baya
kadan, Salem dan fiddo kanshi yayi ita kuma ta kura mashi ido tana tunanin ina
nasan wannan mutum, Salem zai bude baki yayi magana ta fara cewa
"Lah...Ashe kaine..ina wuni"
"Lafia lau...kinyi tunanin na mutune?" Dan murmushi tayi Wanda ya bayyana one side
dimple dinta
"Aa..kawai banyi tunanin kai bane"
"To naji..zo in baki lift"
"Aa nagode..." Kura mata ido yayi for a moment kafin yace
"I insist.. Ko kina tsoron kar..." Dan daria tayi ya dan saci kallon hakoranta
"Meye na tsoro.. Kawai dai nagode.." Shima Salem Dan daria yayi itama tawa tadan
kalleshi tayi saurin kauda kanta
"Please ki shigo in ajiyeki" kallon Abdul tayi kafin tace
"wannan passenger da ka dauko fa..kar mu shiga hakkinshi..." Abdul murmushi yayi
"Kar ki damu ni abokinshi ne..." Tawa Dan tsayawa ta yi kaman batason shiga kuma da
ka ganta da akwai Dan alaman tsoro tare daita, kara daga kai tayi ta kallesu suka
hada ido da Salem, cikin ranshi cewa yayi
"Wannan yarinyan da akwai manyan idanuwa kaman na mage" ahankali ta bude bayan
motan tashiga , tana shiga ta dan kwantar da kanta bayan seat da alaman gajiye
take, Salem juyawa yayi ya kalleta
"Hajiya ina zaa kaiki?"
"Oh sorry...tukuntawa zaa kaini"
"Babu nisa ma" inji Abdul, Salem fara tuki yayi, yana cikin tafiya yadan saci
kallon ta ta mirror yaga sai lumshe ido take ahankali, cigaba da kallonta yayi
har ya mance da tuki yake, saida ya kusa bige wani sannan yadawo hankalinshi, bai
dade ba yakara kallon ta wannan karin itama ta daga kanta sukayi ido hudu dashi,
murmushi yasakar mata kafin yace
"Nagode da taimakonki fa..."
"Haba ba komai...Amman kabani mamaki..." Daga kanshi yayi ya kalleta
"Da nayi me?" Cikin irin jin haushin nan tace
"Da baka rama marin datayi makaba...mazan hausawa da akwai hakuri wallahi da mazan
yarenmune da yarinyan nan bata kara marin mace yaruwanta balle namiji" Salem Dan
murmushi yayi yana tunanin
"Bakisan abinda ke faruwa don ina tabbatar maki when am done with her ko dabba
bazata iya tabawaba balle mutum" dan murmushi yayi
"To ya zanyi tunda ni talaka ne...wai ke wace yaraece?" Ya tambayeta, Ahankali tace
"Yoruba" ido Salem ya kwalo don sam bata kama da yare
"Kambu " yace cikin ranshi sannan yace
"Yoruba? Amman meyasa kike Hausa kaman bahaushiya?"
"Nan aka haifeni"
"Wow..ya ake cewa kina da kyau da yarenku?" Dan daria tayi shima Abdul yayi
"Ni ban iyaba Amman inaji"
"Baki iyaba kwata2? " Dan girgiza kanta tayi sannan tace
"Naiya few words" Dan daria yayi sanda Abdul ya nuna mashi hanyan dazasu bi, saida
yabi hanyan sannan yacigaba dacewa
"To ya ake cewa my friend da yarenku?" Ahankali tace
"Ore mi" dan daria yayi kafin yace.
" zaki zama oro mi?" Cikin daria tace
"Ba oro mi naceba...I said ore mi" dukkansu daria sukayi kaman sun wani dade na
sanin nuna
"To naji..zaki zama ore mi?" Shuru tayi kaman bada ita yakeba.
Saida ya kara cewa
"Baki bani amsaba?" Kallon shi tayi ta mirror suka hada ido tayi murmushi tare da
kauda kanta
"Cewa nayi will you be my ore mi" ahankali tace
"You are funny.. Ka taba ganin inda mace da namiji sukayi abota?"
"Eh mana in kuma babu sai mu zama na farko" tawa shuru tayi bAtace komaiba ba salem
ya sake cewa
"So zaki zama ore mi?" Batace komaiba har suka zo gidansu,
"Nan zan sauka" tace mashi, tsayawa yayi ta bude ta sauka sannan tace
"Sakallahu akhaairan..." Murmushi yayi
"Ameen nagode" juyawa tayi ta fara tafiya, Salem yabi bayan ta da kall, cikin
ranshi yana
"See hips" Salem da akwai san hips, binta yayi da kallo har saida ta kusa shiga
gida sannan yace
"Ore mi..baki gayamin sunan kina?" Ahankali tawa tace
"Tawakaltu"
"Lovely name for a beautiful owner" tawa daria tayi tare da dan girgiza kanta
sannan ta shiga gida.
Tun waje Salem kejinmuryan yara suna anty tawa oyoyo. Salem kallon yanayin unguwan
yayi sannan yace
"Alhamdulillah" kallon Abdul yayi sanda yake juyawa da motan yace
"Alh yau nasamu mace ta farko da tayi min daria" shima Abdul cewa
"Gaskiya kam..ko mun samu amarya?" Hararan Abdul yayi
"Kanason first love taci ubana kenan" Abdul murmushi yayi
"Sir ai bakasan ikon Allah ba" Dan daga kai Salem yayi kafin yace
"Gaskiya kam Amman kada Allah yabamu abinda yafi karfinmu"
"Ameen" Abdul ya amsa mashi, wuri ya samu yayi parking
"Alh kadawo nan ni nagaji da wannan driving din" ba musu Abdul yafita ya barwa
Salem wurin bude Salem ya koma driver seat suka bar wajen, dan yawo suka danyi duk
wacce ta tsaida su sai Salem yace kar su tsaya yana cewa
"Alh mu wuce kawai banason shan zagi da yamman nan.

Bayan kwana uku Salem ya stinci kanshi da tunanin tawa ,duk yanda yake kokarin
kaudata daga cikin ranshi ya kasa , kwance yake tunanin duniya ya isheshi
" ya Allah koda nafito Neman mata ban fito da niyyan Neman wata kabila ba...why do
I want to see her again... Why is my heart always remembering her?...ya rabbi
choose the right path for all Muslims " aduan dayake kenan cikin ranshi
"Tawakaltu... Trust in Allah.." Juya kwaciyanshi yayi tare da daukan wayanshi,
Khalid yakira, bayan sun gaisa Salem yafara cewa
"Guy wallahi am falling... " da sauri Khalid yace
"From were" daria Salem yayi sannan yace
"In love.. And I think it's love at first sights" ihu Khalid yafara yi yana cewa
"Yeyyy..mission accomplish.. Sai kadawo gida musha shagali..." Dariya Salem yayi,
Khalid yakara cewa
"Friend gayamin ya take" ahankali Salem yafara cewa
"Guy bakace, tana da dan tsawo Amman ba sosai ba, sannan tana manyan idanuwa kaman
na mage..." Khalid yayi saurin cewa
"Kaman naka kenan" daria Salem yayi sannan yacigaba dacewa
"Tana da dimple sannan ga round face.. In short guy kaman kanwar rihanna" daria
Khalid yayi sosai, Salem bai saurareshiba yacigaba dacewa
"Wallahi guy she has the perfect ass..." Wani irin ihu Khalid yayi
"Slim ayya ita kake so...hope ba ass din kawai ya burgeka ba?" Da sauri Salem yace
"Wallahi dukkansu nakeso..dukda hijjab dinta bai bani daman ganin boobs daita ba
Amman nasan da akwaisu..wallahi guy the lady is endoured.." Cikin daria Khalid yace
"Wannan kwatancen daka bada bansan yarinyan kake so ko jikinta kakesoba..." Da
sauri Salem yace
"wallahi guy I have never wanted something so bad...inason yarinyan nan... I just
meet her three days back but am missing her badly"
"Naji...gayamin..yar wacece a garin..." Ahankali Salem yace
"Gaskiya inaji ba yar kowa bace..asalima she's not an Hausa..." Da sauri Khalid
yace
"Wace yarece"
"Yoruba" wani irin mugun ashar Khalid ya saki sannan yace
"Shike nan ansamaka wani abu aruwa kasha"
[10/8, 12:06 AM] Fadila S. Takko: ❤
ZAKISAN KONI WAYE

®zuwairat(ummu maryam)

1⃣6⃣

Salem lumshe idanuwa yayi, daman yasan hakan zai faru, Khalid yacigaba dacewa
"Friend am disappointed in you...ace duk Matan duniya ka rasa wacce kakeso sai wata
Yoruba?...daman muggan masu asirine, kilan sun baka wani abukaci..."
"Please stop screaming... Kar ka kashe min kunne dalla...don na gaya maka damuwata
sai ka tsaya yimin maganan banza?...get off my phone!!!" Salem ya fada cikin fada.
Da saurin Khalid yace
"It's not like that... Amman Salem ina kai Fulani ina Yoruba?..."
"Please...ka bar magana kaman jahili mana...Yoruba ba mutum bace..ko matanmu finsu
sukayi....wallahi tunda nafito she's the first person da bata yimin rashin
mutunciba..."
"Haba slim saboda yarinyan kake kirana jahili?...gaskiya sun kamaka" afusace Salem
yace
"Wallahi Khalid ka kara cemin sun kamani zamu bata da kai..wallahi ko maganan ban
gaya mataba...kawai nagaya maka don Neman shawaran ka Amman you getting me upset"
Khalid kwantar da murya yayi
"Slim am sorry... Amman ka duba wannan lamarin..kana ganin Umma zata
yarda?..gaskiya ni ashawarata kar ka gaya mata..." Shima Salem ahankali yace
"Am trying not to say anything.. Amman cikin kwana uku nan Kaman shekara uku..."
Ahankali Khalid yace
"Yanzu Salem yanda ka tsani tara mata shine kake shirin yin mata biyu..."
"Kaman ya mata biyu?" Salem ya tambayeshi, cikin zolaya Khalid yace
"Ga wata chan zaka aura kuma gashi har yanzu baka daina neman Matan aureba.." Dan
daria Salem yayi
"Ai ita wancan ba aurenta zanyi dan muyi zaman aureba..kaima kasan dalilin dayasa
zan aureta...dana gama daita zan maidata wurin ubanta..."
"Karfa daga karshe muji chanjin labari..."
"Kaima kasan ba haka nakeba..I always keep my word...yanzu please best meye
abinyi.. Wallahi I think I love that gal" Dan daria Khalid yayi
"Hmmm..ni dai yanzu ban abun cewaba sai ince Allah ya zaba mana abinda ya fi
alkhairi" haka suka Dan taba hira kafin suyi sallama.

Salem gyara kwanciyanshi yayi yacigaba da tunani, shi kanshi yasan da kyar ummanshi
zata amince da abinda ke faruwa.



Abangaren su ameera kam babanta yayi mata order kaya na gani na fada, kuma yar uwan
dad mai suna anty safiya ta dauko nauyin gyara ameera don mom kam ko kallo basu
ishetaba, da sai gayawa mutane yake zai aurar da yarshi da ance gawa sai yace ga
dan tsohon shugaban kasa, da an tambayeshi yaucene bikin sai sai yace jira yake su
bashi rana, ko tunanin rashin aikinshi baya yi.


Tawa kam tun ranar da Salem ya ajiye ta bata kara tunashi ba sai yau da take kwance
gaman maminta tanayi mata ta tanayi mata tausa kasancewan kullum mami sai tayi mata
tausa in dare yayi saboda yawan gajiya, zumbur ta mike zaune kaman wacce ta tuna
abu ta jiya wajen mami tafara cewa
"Mami kin san wannan mutumin da nake baki labarin shi kwana kin baya?" Cikin magana
irin ta wayanda basu jin dadi sosai mami tace
"Wane mutum kenan" da sauri tawa tace
"Wannan mutum da wata yarinya ta Mara..."
"Eh na tunashi..me ya sameshi kuma?" "Ba komai..jekaranjiya na ganshi har ya bani
lift..."
"Meye lift?" Mami ta tambayeta
"Ya maido gida kyauta..." Baki mami ta bude tana
"Ah..ah..ah..toyin... Kina hawan motan Wanda baki Sani bako?..." Da sauri tawa tace
"Mami ban taba hawan motan kowaba...shima rokona yayi..." Cikin fada mami yacigaba
dacewa
"Rokonki din banza...salan a yanke maki kai?...in badan yaran yanzu Baku da tsoro
ba ina ke ina hawan motan Wanda baki saniba..."
"Mami..yi hakuri...bazan karaba.."
"Ke kullum cikin bada hakuri kike..." Tafada cikin fada sannan ta sassauta murya
tafara cewa
"Omomi...bawai ina hanaki samun sauki bane..Amman irin abubuwan dake faruwa yanzu
ya kamata ko wacce yarinya ta guji mutanen da bata saniba.."
"Mami sorry..."/
" naji..kar ki

6 / 44