Advertisements
Chapter 10 Reading Afiyya by Ayshatuuu BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

Afiyya by Ayshatuuu

Author :  Ayshatuuu Category :  Complete Novels

Chapter   10 / 31

27K to 30K   out of 90.3K words

saboda shi nayi ta
tolerating abubuwan da Zan iya maganin su. Ummiey da suka dawo Kaya ta kawo min
sosae sannan tazo ta ganni ta bini da nasihu, ana gobe zasu tafi Istanbul na dawo
daga islamiyyar da Mummy ta sani a marakawa, Yaya Shehu zaune yayi kyau cikin
carton brown shadda, dinkin kanshi abin kallo ne, idanun shi masu kaifi na kaina
dukda Yana sanye da farin glasses Wanda nafi tunanin medical glasses ne, Dan kusan
ko da yaushe Yana fuskar shi, kanshi yasa hula wadda ta kafu kasancewar Yana Tara
gashi, a hankali se naji yanayin nan ya fara dawowa, na dinga daga kafata a hankali
har na Isa inda yake nace


" Yaya! Ina wuni"


Ya bini kallo, inaga Yana mamakin yadda na koma ne tamkar an zuke ni yace


" Me yake damun ki? Kingan ki kuwa?"


Nayi Dan murmushi nace


" Nothing a Little stress"


Ya harareni yace


" Ban yarda ba, see Zan iya Kai karar kawun ki nan wajen human right fa"


Se ya bani dariya dukda he's serious nace


" Human right? Time ne"


Se ya gyada Kai kawai ya fara tambayata yadda nake na Dan Jima a tsaye sannan ya
Miko min Leda yace


" I'll miss you so much, tunda like zuwa Nigeria Bata taba min dadin da tayi min
irin wannan ba. I've found and uncut gem here"


Na bishi da kallo Ina jin yadda words dinsa ke sinking a hankali ya dage min gira
yace


" Take care of yourself, ki tuna Ina sonki da lokaci yayi Zan aureki Inshaaa Allah"


Na tura Baki nace


" Wanne irin aure Kuma? Kai Yaya"
Yayi dariya tareda sunkuyar da Kai yace


" I'm serious ba lallai karamin kanki ya gane ba, just know someone somewhere loves
you alot!!"


Wannan kalaman nashi were deeply buried in my heart, Yaya seda ya saka na binne su
saboda yadda ya dinga showering Dina da tashi kalar soyayyar. Dukda Bai furta ba
Amma ni Kam zuciyata dumu dumu ta kamu da son shi, lokaci lokaci takan tuna Yaya
Shehu Amma na yarda Zama wake daya is very toxic, wannan dalilin yasa Yaya Shehu
baiyi tasiri cikin zuciyata ba! Duk wannan bidirin iyayen shi Basu sani ba sun tafi
bin bokaye yadda zasu karba dukiyar hannun Uncle Babawo Amma Abu ya faskara, ko
address din guraren ba su sani ba, se takurar da ake min ta Kara yawaita, Amma idan
na fito Naga dansu se naji Babu komai watarana zai wuce. A hakan na Gama ss2 inada
shekara Sha hudu, ni kaina na kasa lissafa yadda akai a 14y har nake ss2. Bikin
Siyama ya tashi Amma bansan yadda akai ba kamar an binne maganar se ta mutu, tayi
kuka kamar zata mutu, nasha jinta cikin dare tana fadin ita guduwa zatayi, ban taba
tambayar ta abinda yake faruwa ba.




Junaidu




10years leap!




Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 Aisha Hassan kwalam First bank of
Nigeria, send evidence of payment through 09063467258
[15/12, 10:38] +227 98 36 59 34: 21


Ita kadai take ta kallon gurin da Kawu Sa'idu ya tashi tana Kuma tantamar ko tana
cikin hayyacinta da har ta kasa magana dashi, ita dai Mummy Abu daya ta sani tunda
Suka hada idanu da Kawu Sa'idu taji tamkar an Mata format ne cikin kanta, taji gaba
daya tsoron shi ya kamata Wanda tunda take Bata taba ji ba, kasancewar yayi rashin
ji Yana yaro Kuma shi kadai ne bashi da madogara a gidan yasa Suka Raina shi, Dan
ita se ta ga dama take ce Masa Yaya, lokuta da dama idan kowa ya kasa fada Masa
laifin sa to ita ke tunkarar shi ta fada Masa, dalilin da yasa basa shiri ko kadan
gasu Kuma sako da sako.


" Mom Rooks seda na fada Miki Yaya Sa'idu..."


" Me ka fada min Tijjani? How do you want me to believe ni dinnan na kasa karbar
Afiyya a hannun shi? Dan Allah Bari mana! Me Sa'idu yayi da na kasa fuskantar shi
nayi maganaI'm a failure kenan"


Uncle Babawo ya mike ya riko hannun Mummy cikin lallashi shi kanshi he's confuse
sosae da sosae, shima when it comes to him baya tsoro dama Tijjani ne me tsoro, shi
kuma Abbuna Yana da dauke kai, mutum ne me kawaici shiyasa tafiyar su tayi nisa
shida Kawu Sa'idu.


" Mom Rooks ki daina daga murya, tabbas something is fishy kizo muje mu hada Kai
muyi tunanin possible solution"


Mummy na dawowa ta wuce mu a zaune a parlor Muna game din whot, ko sannun da muke
Mata Bata amsa mu ba, se naji jikina yayi matukar sanyi naji na daina gane su star,
carpet, pick 2, general pick and stuffs. Na aje na hannuna tareda ja da baya na
jingina kaina da jikin sofa, Rooks ta dubeni tace


" Menene?"


Na girgiza Mata Kai, ta bude baki da niyyar yimin magana taji Mummy na kwala Mata
Kira, Haka ta mike ta tafi Babu jimawa ta dawo fuskarta kawai na kalla Naga Bata
cikin jin Dadi,whot din ta tattare ta aje gefe tace min


" Mu tafi daki"


Na mike nayi gaba tabi bayana, wani iri nake ji na dinga jin kamar nabi Mummy daki
na tambaye ta me ya faru? Ya sukai itada Kawu Sa'idu Amma se naki kawai na hakura,
idan nabi a hankali zanji me akace, tunda a kaina ne na tabbatar.




" Kina ganin kukan da kikeyi shi zai samo Miki mafita kenan?"


" Darling ya zanyi? Na kasa tunanin yadda zanyi fa, ko magana kwakwara na kasa Yi a
gaban shi"


Abban Rooks ya ruko hannun ta cikin sigar lallashi yace


" Allah ya kaddara zaman ta Bai Kare anan ba se kiyi hakuri kawai, Allah ya San me
yake nufi"
Bangaren Ummiey sunata Shirin tafiya maiduguri Dan suyi sati daya sannan se su dawo
Ringim su Kara sati sannan su wuce Istanbul. Gaba daya Ummiey ta hautsuna gidan Kai
ka rantse da koami na gidan zata tafi maiduguri din, Daddy na zaune shi da Shehu
suna kallo ta fito rike da wayatta a hannu,




" Wato Kai kowa Yana aiki Kai shi ne kazo ka tasa TV a gaba kenan?"


Shehu ya kalli Daddy, Daddy ya kalle shi, ya Masa alamar ya tashi, Babu musu ya
Mike yace


" Ummiey yanzun me ya rage?"


" Ko sannu ba zaka dinga leko ni kana min ba? "


Ya sauke ajiyar zuciya yace


" Kiyi hakuri Ummiey sannu da aiki, is there any thing I can help with?"


Ta girgiza Kai tace


" Yi zamanka kafin Baban ku yace bullying dinka nake"


Daddy yayi dariya yace


" Ummiey indai tafiya ta tashi ba Zaki zauna ki huta ba"


Nadia ta karaso ta zauna kana kallonta zakaga so much stress a tattare da ita, ta
kalli Daddy zatayi magana Ummiey tace


" Kin hada boxes din guri guda, bana son mantuwa fa"


Shehu dake tsaye ya saki dariya, Nadia ta tura Baki tace


" Na hada komai fa Ummiey"


Shehu ya zauna Yana kallon iyayenshi yace
" Ummiey can I share my opinion here?"


Ta gyara zaman ta tace


" Why not? Me ya faru?"


Yace


" Ummiey tunda zamu tafi gobe, me zai hana mu tafi da Afeey Kinga it's an
opportunity tayi reconciling da Yan can."


Tayi shiru tana kamar tunani yayinda Daddy dasu Nadia Suma suke kallonta suna
sauraron amsar ta, ta Dan kalli Daddy sannan ta maida kallon ta Kan Shehu tace


" Tunanin hakan Bai ma zo min ba, Nads jeki kawo min wayata a bedroom na Kira
Maryam"


Daddy ya girgiza Kai yace


" Not Maryam, Afiyya hannun Sa'idu take so shi ya kamata kije ki tambaya"


Ta gyada Kai ta dubi Harith da shigowar shi kenan tace ya fita da mota zasu je
gidan Kawu, Daddy ya dubi Shehu yace


" Kaji Ummin ku fa tafiyar da zata iyayi a kafa shi ne har se taje a mota"


Ta harari Daddy, Shehu ya daga hannun shi yace


" Daddy ni dai ba ruwana!"


Sukai dariya daga haka ta fita, cikin saa Suka same shi a gida, tunda yaji zancen
zuwanta yasan Yana da nasaba Dani Dan hakan ya Zama cikin shiri, a tsakar gida aka
shimfida Mata tabarma ta zauan, dama Harith Bai shigo ba a mota ya zauna. Suka
gaisa sama sama ita da Ummaan su, sannan Kawu Sa'idu ya zauna Suka gaisa cikin
mutunci, ta dago tana kallon shi kawai suna hada idanu se taji ta kasa magana ganin
yadda ta Dan rikice yasa ya Kara rike idanun ta cikin nashi,


" Hajiya Mariya akwai wani abunne? Ai yarinyar na gidan Maryam se zasu koma zata
dawo nan"


Ta mike tana fadin
" Ai bansani ba, Bari naje gidan kawai"


Tayi sauri ta juya har ta kusa zaure yace


" Kada ki dauki yarinyar nan kije da ita wani guri"


Ummiey ta juyo a hankali bakinta na San fadin abubuwa Amma suna hada idanu tace


" Ina zan kaita kawai ganinta nazo Yi!"


Ya gyada Kai Ummiey ta tafi tana jin jiri kamar zai kwashe ta, Ummaan su ta fara
dariya tana fadin


" Wannan Abu yayi , da bakai Haka ba da tuni komai ya rushe!"


Shima dariya yayi yace


" Gashi Ina juya su yadda nake so, da farko banyi tunanin aikin zai ci har haka ba,
saboda malamin Yana tantanmar yiwuwar aikin akan Maryam da Mariya da Babawo, se
gashi Kuma yayi"


Ummaan su cikeda farin ciki tace


" Yanzun tunda ka samu wannan se zancen karbar dukiyar ya kamata ka maida hankalin
ka akai"


Ya shafa Kai yace


" Da kyar na karbi wasu filaye anan hannun Tijjani, Amma na gurin Babawo se anyi da
gaske. Amma akwai wani malami a Niger an fada min naje gurin shi"


" Ya kamata dai ! Da zafi zafi ake bugun karfe"




Ummiey na shiga mota ta dafe kanta dan ji take kamar zai fado, Harith ya dubeta a
tsorace yace


" Ummiey what's wrong? Me ya sameki?"


Cikin rawar murya tace
" Kaini gidan kawun ka Bashir"


Haka ya juya motar Suka nufa gidan su Rooks, dukkan mu Muna zaune mun samu bakuncin
Shehu da Kuma Uncle Babawo, kamar ranar Suka fara haduwa se Hira suke duk yawanci
akan diaspora ne. Shigowar Ummiey yasa Shehu mikewa da sauri ya nufe ta, ya riko
hannun ta Yana tambayar Harith abinda ya faru, Muna kitchen muka fito, Mummy ta
karasa ta zaunar da Ummiey ta fara tambayar ta abinda ya faru. Ta dubeni ta saki
hannunta daga kanta tace muje daki zasuyi magana , Haka muka juya jiki a sanyaye,
Ummiey tace


" Maryam kin tabbatar Sa'idu baya bin bokaye?"


Mummy ta kalleta da mamaki tace


" Wanne magana ne wannan?"


Ta gyara Zama ta kwashe komai ta fada musu, Uncle Babawo yace


" That's it! Addua zamuyi nace Miki something smells fishy"


Sunata maganan not minding yadda Yaya Shehu yayi shiru deep in thought, se can yace


" Inada shawara! Me zai hana ayi Mata aure kunga bashi da wani right over her
kenan"


Ummiey ta Kai Masa hannu tace


" Baka da Kai nawa Afiyya take zakace aure"


Mummy ta rike hannun Ummiey yace


" A nice idea! Amma waye zai aure ta?"


Yaya Shehu ya kaudar da Kai yace


" Ni! Ina son ta Zan aureta!!!"
Afiyya is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of
Nigeria, send evidence of payment 23




Shekaru goma sun wuce a bangaren shi, Yana ganin hakan tamkar satittika goma be
Suka wuce. Yakan tuna kamar Wasa yaje yayiwa Fatima asiri Dan ta fita harkar shi ko
kuma ya amfani da hakan ya firgita ta saboda Shiga hancin shi da takeyi. Asirin shi
ya tonu Malam ya Kama shi dumu dumu da wannan laifin ya Kuma koreshi daga gidan
Baki daya. Ya fito daga gidan Babu bacin Rai ko firgici saboda a ganin shi su sukai
asara bashi yayi ba, Yana Kuma fatan watarana zasu zo su durkusa har kasa su
rokeshi afuwa, su Kuma nemi taimakon shi, Yana tuna fuskar mahaifin shi Malam
lokacin da yake fada amsa ya fitar Masa daga gida ya Kuma manta cewar Yana da uba
da uwa, wannan abin idan ya tuna Yana Kara saka shi jin kaimin daukar fansa, Yana
jin ta kowanne Hali Dole ma se ya dauki fansa, Dole ko sama da kasa zata hadu to
tabbas se yayi kudi.


Shekarar farko ya dukufa wajen ganin ya tara kudi Dan yayi sustaining living, gang
din su Yana nan sede Jarma baban shi ya fahimci halin da ake ciki na korar shi daga
makaranta, ranar ya daku a gida ya Kuma saka Yan sanda Suka zo sukai raiding inda
suke zaune, huzaifa ya samu ya gudu aka Kama Malam da Junaidu sannan aka bi huzaifa
aka Kama shi. Kowa iyayen shi seda suka zo Amma Banda na Junaidu, Baban Jarma na
tuhumar su da Bata Musu Dan shi, sun daku akai bailing Malam da huzaifa aka bar
Junaidu shi kadai, seda ya kwana biyar sannan huzaifa yazo yayi bailing shi, a
ranar sukai gagari min fada a tsakanin su. Tunda sukai bailing shi Bai musu magana
ba har sukaje shagon shi, ya Shiga yayi wanka sannan ya fito ya same su duka sunyi
daidai, huzaifa ya kunna weed din shi se zukawa yake Yana fesarwa, yayinda Malam ke
zaune Yana harhada syrups cikin kwalabe, Jarma wayace hannun shi Yana daddanawa,
Bai musu magana ba ya ketare ya saka Kaya sannan ya dawo ya fita Yana jin huzaifa
na Masa magana ya Masa banza, Babu jimawa se gashi ya dawo da wuka a hannun shi,
gadan gadan ya nufi Jarma da wukar Yana kokarin Burma Masa, cikin hanzari ya Mike
tare da cillar da wayar gefe, ya tankwabe hannun Malam syrup din ya malale a kasa,
Malam ya dago zaiyi masifa yaga abinda ke hannun Junaidu, ya kwala ihu hakan yasa
Jarma ma ya yarda abin da yake hannun shi, Suka fara tsere a Dan karamin shagon,
Jarma na fadin


" Junaidu me kake Yi hakane, Dan Allah ka aje wukar"




Malam ne yayi ta maza ya tsaya Yana fadin


" Me mukai maka? Ka yanka ni idan ka Isa Kai Dan iska ne"


Wukar hannun shi yasa ya yanke shi damtsen hannunshi, wani ihu ya saki a take jini
ya fara zuba, ya dubwsu idanun shi yayi jawur yace


" Wannan shi ne magana ta karshe, Rana ta karshe da dayan ki zai Kara zuwa inda
nake! Babu ni Babu ku idan ba Haka ba Kuma yadda na yanke shi to kashe mutum zanyi"


Jarma ya matso yace
" Junaidu me kake fada Wai? Ka fita hankalin ka ne?"


Ya Kara matsowa da wukar zai yanke shi yayi baya da sauri, da kyar Jarma ya daure
hannun Malam Suka give kowanne mamakin dalilin da yasa Junaidu yin Haka yake, shi
Kuma a nashi ganin Babu wani amfani yin kawance dasu. Daga wannan ranar ya koma
rayiwar shi daya, baya yiwa kowa magana, ko zaiga dandazon mutane dari to bazai
musu sallama ba, massalaci baya zuwa sallar ma bayayi. Ya koma garejin da yake aiki
ya cigaba da aiki Yana Tara kudi, sede a wañnan lokacin kudin Babu albarka da kyar
yake samu yayi saving na kudin haya, wannan yasa ya fara tunanin zuwa neman saa.
Bashi da wani aboki, Bai Kara Neman gida ba, mutanen dake zaune dashi Banda alkabai
Babu abinda suke ja Masa da bakunan su, kowa ka tambaya to bazai fada maka abin
alkhairi a tattare dashi ba. A hakan shekara ta wuce ya samu da kyar ya biya kudin
haya, ya Shiga ta biyu inda ya Kama wata sanaar kuma, wannan hannu bibbiyu da yake
se yaga ya fara samun abinda yake nema. A hakan shekaru Suka Kara wucewa, iya aikin
makanikanci ya iya wannan dalilin yasa duk yadda ake cewa me gurin ya koreshi
saboda munana dabiun shi ya gagara, mutane da yawa idan sun kawo gyaran mota ko
abin hawansu zasu ce su Junaidu suke son ya gauara musu Amma ba hakan ke nufi zai
musu magana ba ko zai kula su ba.


A shekara ta biyar ya hadu da wani Gaye Dan Niger, sunan shi Safiyyu ya hauro daga
Niger ya shigo Nigeria, inda ya samu mazauni anan Niger din. Halayen su iri daya ne
da Junaidu har gwara Junaidu ma ansan asalin shi Amma shi kuwa kana kallon shi ko a
accent dinsa zaka San cewar Dan Niger he's a foreigner. Shagon Dake gefen na
Junaidu nan ya kama haya, Babu Wanda kewa wani magana seda akafi wata biyu se yaga
kawai Safiyyu ya saya wannan shagunan gaba daya, shi ba aiki ma yakeyi ba hakan ba
karamin mamaki da Kuma daga Masa hanakli yayi ba, Amma saboda shi ba ma halin shi
bane yiwa mutane magana ba se Bai kula shi ba. Watarana ana zafi Safiyyu ya fito
Yana Shan iska shima Junaidu ya fito, suna zaune Babu me magana cikin su, se can
Safiyyu yaga Abu ya gilma, ya Mike tsaye ya dubi Junaidu dake faman danne danne a
waya yace


" Maciji na yawo anan gurin!"


Ai tuni ya Mike ya nade sallayya yayi baya Yana kokarin komawa shagon shi Amma ya
dakata, jin Safiyyu na fito Babu jimawa Sega macijin a gaban shi, ya tsugguna ya
dauka macijin sannan ya murde Masa Kai ya wullar Yana wata irin hatsabibiyar
dariya! Junaidu yayi shiru yana jin akwai Wanda ya fishi kenan? Safiyyu ya matso
cikin hausar shi ta Yan can yace


" Kana bukatar taimako ne?"


Junaidu yayi shiru deep in thought with so much hesitation Amma Kuma Yana bukatar
yayi kudi ya cika burin shi,


" Idan kana bukatar abu, kwankwasa min kawai zakayi!"


Ya fada sannan ya wuce ya bar Junaidu tsaye Yana tantanmar abinyi....
AFIYYA is not free, pay 300 to 3091721807 A'isha Hassan kwalam First bank of
Nigeria, send evidence of payment through 09063467258to 0906346725824




Ya Jima a tsaye Yana kokwanton abinda zaiyi, shi duk abin shi yasan maciji is a no
place for him, Amma ta Yaya gayen ya dauki wannan macijin ya murde Masa Kai, ya
haska fitilar wayar shi yaga tabbas ga ga macijin a yashe a kasa Kai daban Haka
gangar jikin daban, ya juya da sauri ya nufi daki ya rufe, yeah shi yasan he's bad
idan ana zancen bad guys yasan a kaf kazaure Yana sahun farko to Amma akwai
abubuwan da shi yasan bazai iya tunkarar su ba. Hakan yasa ya daina shiga sabgar
shi, duk inda yasan zasu hadu ya daina. Kwatsam Yana aiki wani yammaci fada ya hada
su shida wani abokin aikin shi, Kuma a gaskiya wancan ne bashi da gaskiya tunda
Junaidu idan ka dauke oga zai iya kwana uku ko kanzil Bai cewa wani ba, abinda ya
kawo shi kawai yakeyi, kawai Dan ana hirar yanmata da Kuma aure se gayen yace ai
wallahi ko kanwar shi zatayi kwantai bazai bawa me Hali irin na Junaidu ba, shi
Kuma Junaidu fitowar shi kenan daga kasan wata mota, karaf maganar ta shiga kunnen
shi, Yana zuwa kawai Bai ma musu magana ba ya cakumo wuyan rigar shi ya Kai Masa
naushi a Baki, Wanda yayi sanadin fashewar bakin jini ya fara zuba. Duka suka taru
suna kokarin raba su Wanda da kyar suka samu Suka babanbare rigar Musa daga hannun
Junaidu, ya maka Masa harara sannan ya koma ya cigaba da aikin shi, kowa ya Kama
abinyi ai Musa se ya fara zage zage Yana fadin ai duk sunsan komai, shi Wanda
iyayen shi suka tsine Masa Suka Kore shi, baya sallah baya zuwa massalaci,

10 / 31