Advertisements
Chapter 10 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   10 / 48

27K to 30K   out of 143.7K words

yace Daganan kowa yayi Shuru yana Sake sake Cikin Ransa.

Sakina kuwa Hajiya Fada ta Hau ta dashi Lokacin Data Tambayeta ina su Nazifin tace sun tafi nan ta Fara Fadan Rashin kunyansa tayi yawa Har ya iya zuwa bai Shigo ya gaisheta ba Sakina dai ba Mgana kai kawai ta Dukar dac kai toh me zata ce ko ita din ma Nazifi bai ma kyakyawan kallo ba Ballatana Har taga wajen cewa ya Shigo ya Gaida Hajiya Sumi Sumi tayi ta wuce Dakinta Daman Abba yana Dawowa ya Fita Zuwa Wajen Taronsu na yan Siyasa..

Duk yadda Rukky taso Sakina ta Fadamata yadda sukayi Afalon Abba kiyawa Tayi Saboda Ta tsani Rainin Hankali Rukky ba Tun yau ba ta lura tana Raina mata Nazifin ta,Tun Lokacin Auransu take Fadin ba, ajinta bane Tafi karfinshi Ballatana yanzu da suka samu mtsala sai kara Ruru wutar take tana kar Sakinar ta koma alhalin ita har yanzu bata samu wanda zai kwashetanta ba Ita tana Jiran mai kudi kuma ba wanda yazo Talakawan ma Data Raina ba wanda yazo,Kawar Sakina ne tun Suna Yara ammh ahakan ma Suna da Bambamcin Ra"ayi sai da Sakina taci Uwarta ta Damata agirman kai da kuma Takama da Isa da komai.






*Shakira...*
4/9/21, 1:53 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*



*Wattpad:JamilaUmar351*
*Janafty*💞

*Dedicated To:My Habibaty❤️Aisha Idris Abdullahi..*!


_Wannan Shafin Sadaukarwa ne gareki Babbar Yayata Wato *ANTY MARYAMA*, Alherin Allah ya kai miki adukkan inda kike Ameen..._


*010*



"Basu Shigo Zaria ba sai Bayan Sallar Mangariba Saboda sunyi Tsaye Tsaye Kan Hanya,Sun Tsaya sun Yi Sallar azahar suka dau Hanya,Lokacin Sallar La"asar ne suka Tsaya sukayi Salla suka ci Abinci nan suka Bata Lokaci kuma Duk da basu yi Gudun da sukayi ba Lokacin da zasu je.

Direct Gidansu Nazifin suka Fara isa Abdullahi shi ya korama Mallam Wada Duk Abunda ya wakana kai kawai ya girgiza kafin yace"Allah ya kyauta na gaba..Sai ka kiyaye ka dai ji da kunnanka Abunda Nima ya gayamin..Bazan so ace yau na saka Baki ka Saki matarka ba Domin lokacin da ka ganta kuka Daidaita kanku bansani ba...ammh dai nasan dai na Fita Hakkinka wajen nuna maka Kuskuranka na Auran ya'yan masu kudi ka nuna min ba matsala Babu Abunda zai Faru Toh yanzu kuwa Dole kayi Hakuri ka Zauna da ita Ayadda kake Tunda dai kai kaji kuma ka gani..."

Inna Abu Dake zaune ta Tabe baki kafin tace"Shi ko kunya bayaji.Matarsa bata Darajasa bama Ballatana ta Daraja mu iyayensa da kannensa da yan"uwansa...Me ake da mata Irin Sakina Wlh Mallam Rabonta da Gidanan Tun Lokacin da kayi Ciwon kafar nan wajen Shekara.."Mallam wada ya kada baki yace"Wannan Duk Ba Abun Damuwa Bane Abu in batazo ba kanta Tayi mawa..Yara nawa garemu wadanda kullum ke kan Hanyar Zuwa gaishemu,Surukai nawa garemu masu ganin kimar mu,akwai wadanda ma bamu Haifa ammh suna bamu Girmanmu Saboda haka bai kamata ki Damu kanki da wannan ba..Nidai Mganata ta karshe dashi Kar naji kar na sake ganin ka saka Hannu ka Daki yar mutane Ballatana har Mahaifinta ya Kirani yana gayamin mganar Banza.."

Abdullahi yace"Haba Baba kai kuma sai ka kyaleshi..? Mallam wada yayi Dariyansu na manya kafin yace"Toh Abdullahi in ban kyaleshi ba Dukkansa zanyi..? Ko nima na Biye mishi muyi ta sa"in sa,Banga Laifinsa ba Domin Duk Abunda ya Kirani ya gayamin ba kowa ya jamun ba sai Nazifi toh akan me zan damu kaina.?Yafada yana kallon Abdullahi da Nazifin Duka atare.

Inna Abu Tace"Ina fa Mallam Abun ne na Hausawa da suke Fadin dan kuka Shi ke jama Uwarsa Jifa..."Mallam wada yace'Shine ma Abu."Daga Nazifin har Abdullahi ba wanda ya kara Mgana Gwarama Abdullahi Sudan Taba Hira da Baba wadan Nazifi kuwa kala bai ce toh me zai ce..?bayan duk Abunda Baban ya Fada gaskiya ne Dama Abunda ya Gudanmai kenan shi Alokacin bai gani Idanuwansa Sun Rufe da Soyayyar Sakina da kuma Cikar Burinsa da Muradinsa.

Daga gidan su Nazifi masallaci suka wuce sukayi sallar Mangariba sai Suka Shiga Gidan mama  sai ya samu ma Su Amira Auwal ya Tafi kaisu bai ma Dawo ba Zama sukayi suka gaisa Da mama Shi da Nazifin Tana Tambayansu Daga ina Abdullahi yace Daga kano Daganan bata kara Neman jin ba"asi ba Domin ba Abunda ya Shafeta bane Mariya ce kadai agidan ita ta Zubo musu Tuwon Dawan Datayi Miyar kubewa Bushashiya sanin Abdullahi masoyin Tuwon Dawa ne ana kawowa Abdullahi ya kalli Nazifi yana Fadin"Mutumina gafa Tuwon Dawa..?

Yamutsa Fuska Nazifi yayi kafin yace"Kai kaci..kayi Sauri ina so na ijiye ka a gidane kaduna zan koma adaran nan.."Abdullahi yamike yana Fadin"Kaduna.?haba ka bari gobe da safe mana.."

Nazifi yace"Gwara na tafi yau din kawai Kaji mutumina."Abdullahi bai sake mgana ba ya Fita waje ya wanko Hannunsa ya Dawo Daki,Ya zauna Lokaci Daya ya Tankwashe kafa ya Bude kulan Tuwon Dana Miyar kamshi na Tashi na kashi da manshanu Domin Abdullahi yadda agidanshi bai Ciyar da iyalansa Cimar Banza Hakama Kannensa da Mama Suma Suna Cin Cima mai kyau Domin Duk wata yadda zai siya kayan abincin Gidansa haka zai Siya na Gidan Mama haka kuma zai Damkamata kudi a Hannunta,Daga chan bakin Titi akwai wani mai nama wanda Abdullahi yama mgana Su Mama zasu Dinga karban na miya in Wata yayi ya Biyashi da Gudu yayarda Sanin Abdullahi bazai Taba mai wasa da kudi ba.

Yana cin Tuwon suna Dan Taba Hira da Nazifi wayarsa tayi Kara Ya Dakata da cin Tuwon ya Ciro wayar nasa Dake gaban aljihu da Hannu Daya yaga Sunan *MY WIFEY..* ya fito baro baro Ajiyar Zuciya ya Sauke yana Fadin"Nayi laifi ban kira Hausina ba Tun Dazu da mukayi mgana muna Hanyar Dawowa..."

Yafada Lokaci Daya yana Daga Kiran Dagachan Bangaren Hafsah tace"Hello Abban Amira kun iso ne..? Cikin Sanyin murya yace"Mun iso yanzu ba Dadewa Hausina..Muna gidan mama da Nazifin yanzu zai maidoni inda ya Daukoni.."Yafada yana Kallon Nazifi Lokaci Daya da Dariya Hafsah tace"Shikenan sai ka Dawo..Su Amira ma Auwal ya kawosu yanzu ma ya Fita.."Kai ya kada yana Fadin"Haka Mama tace ya kyauta..Sam na manta Dasu kafin na Fita ban kirashi dama nace in yadawo kasuwa ya Maidosu gida ba.."Hafsah tace'Nima Asha"afan nayi..Gashi mama Ta saka ya maidosu aie.."Cikin gamsuwa yace"Ta kyauta..Sai na iso.."Daga haka ya yanke Kiran Hararansa Nazifi yayi yana Fadin"Mallam zakayi ka gama na kaika gida ko kuwa na kara gaba..?

Abdullahi yace"Wani ka kara gaba..?dama agidan Mama ka Daukoni..? Wlh ko lagos zaka kwana yau ba kaduna ba sai ka maidani Inda ka Daukoni kajima na Rantse maka.."Nazifi bai kara mgana ba ya maida Hankalinsa kan wayarsa Shima Abdullahin ya Cigaba da cin Tuwonsa.

Sallamar Jidda ce ta katse musu Shuru Atsakar gida Mama ta amsa wacce ke dan kai da kawo Cikin Bacin rai Mama tace"Ina kika Tsaya jidda..?Daga ki mika ma Baba ayyah Rariyanta Shine sai kije ki share kafa kiyi zamanki sai bayan mangariba..?

Jidda ta kada kai Tana Fadin"Mama gidansu Rumana fa na Shiga.."Mama tace"Au..Toh zaki Bayani ne yayanku na ciki.."Sai Lokacin ta Lura da Takalma Sawu Ciki guda Biyu bakake,ido ta zaro Tana Dafe Kirji kafin ta samu Zarafin mgana ba,Abdullahi Dake Cikin Daki yadan Daga murya yana Fadin"Shigo nan don Ubanki Jidda.."

Yafada cikin zafin rai da Wani bacin rai na yadda Jidda take neman ta Fita zakka acikinsu,Jikinta a sanyaye ta Shiga Dakin tana kallon mama wacce ta Juya ta Shiga Kitchen tana Fadin"Ni bar kallona..Jidda sam bakijin mgaa na mariya tafiki gudun Zuciya wlh."

Akofar dakin ta Coge tana wani Raba Ido Nazifi ta gaisar ya amsa yana kallonta kafin ta maida kallonta kan Abdullahi tana Fadin"Ina wuni yaya.."Ko kallonta baiyi ba sai cin Tuwonsa kawai yakeyi Ganin haka yasa Jikin Jidda ya Fara rawa Domin ta Tuna kwanaki sai da yaja mata kunni kan ana aikanta tana Biyawa Gidan kawaye musamman ma Gidansu Rumana wacce dama ya Rabata da ita saboda Rumanar yar Duniya ce gata bata da kunya Duk haka yan Gidansu suke kuma yajama Jidda kunni kan Ta rabu da ita ita kuma Taki Domin kawartace Sosai Ajinsu Daya a makarantar Boko da islamiya.

Mariya ce ta Fito Daga Uwar Dakim Mama da Hijabin Datayi Sallah zata Wuce Abdullahi ya Kirata ta waigo tazo Hannu ya nuna mata yana Fadin"Kwashe wannan kayan na koshi.."Ba musu ta Durkusa ta Tattara kololin ta Fita Zuwa waje suka Hada ido da Jidda Ta sakarmata gwalo ita kuma ta Harareta mikewa yayi ganin haka yasa Jidda ta Fita da Sauri tana Rawan Jiki ta zata zai Daketa ne sai taga kawai ya Nufi bakin Robam Ruwa ya Diba ya wanke Hannunsa Tas yana Fadin"Mama tun yaushe kika aiki yarinyar nan.?

Mama ta Fito Daga kitchen tana Fadin"Tun wajen Biyaar na yammah fa ammh sai yanzu ta Shigo Gidan.."Bai ce komai ba sai da ya gama wanke Hannunsa ya Dago da kansa yana yarfe Ruwan Hannunsa Lokoci Daya yana Fadin"Ke zo nan..' yafada yana kallon Jidda wacce ke Tsaye tana ta Raba ido.

Cikin Tsoro ta kariso Gabansa Tana wani Fiki Fiki da ido Cikin Fushi yace"Daga gidan Uban kike..?Da mama ta aike ki tace ki biya wani waje ne..?Yafada yana Kallonta Lokaci Daya yana kara mata da Harara,Kai ta Fara Sosawa Ta kasa mgana Wata Tsawa ya Dakamata wanda ba ita kadai hatta mariya sai da Tsawar ta Razanata ta makale acikin kitchen tana leken Ya Abdullahi Dake Tsaye a tsakar Gidan yana Faman Huci,cikin Fushi yake Fadin"Bada ke nake mgana ba..?

Baya Jidda taja Cikin Rawan Jiki Dana Murya take Fadin"Dama..
da..ma..Bata je Makaranta Ranar jumma"a bane  Shine na Shiga na gani ko lafiya.."karamin Tsaki yaja kafin yace"Saboda Nan ne inda Mamar ta aike ki ko..? Kin Raina maman ko..? Shiyasa duk inda ta Ijiye ki baki iya zama sai kin Chanza Directiom kinfi son Kullum adinga Bin Ra"ayin ki kuma azura miki ido ana kallonki ko..?

Yafada cikin Tsawa Muryanta ta Fara Rawa kamar tayi kuka tace"A'a..."Nuna ta yayi da yatsa yana Fadin"Saka gwiwoyinki a kasa Don Ubanki yau sai kin Raina kanki Duk wani Tashen iskancinki sai na Sauke ki mishi Gobe in Aka aike ki Daga Gidan da Mama tace ki Tsaya baza ki iya karawa gaba ba.."Yafada yana waiwaigen neman Abun Duka.

Da Sauri Jidda ta Zube har ta Fara Hawaye sanin Halin Ya Abdullahi Tsaf zai saka Sanda ko Bulala ya mata dukan Tsiya ko agefen Kwalan Rigansa Tana Kuka take fadin"Don Allah ya Abdullahi kayi Hakuri Na Rantse Har ga Allah bazan kara ba.."Wani karamin icce ya Dauko ya Nufeta Dashi yana Fadin"Nasan sai kin kara Hauwa"u...."Da sauri tace"Wlh bazam kara ba kaji ma na Rantse yaya.."

Mama na gefe tace"Rantsuwar banza ce kike yi Jidda da kukan Tsoro ammh baki da gudun magana sam.."Abdullahi yace"Kyaleta Mama ni yau zam kawo karshen Taurin kanta Don Ubanta maza ki kwaben Hijabin Jikinki Kinsan Allah yau sai Fatar Jikinki ta Daga saboda Duka kila Daga yau zaki kiyayi Tsayawa inda aka aike ki da kuma Rabuwa da wannan Yarinyar mara Tarbiya da Tuntuni na Raba Tsskaninki da ita.."Jin haka yaasa Jidda ta kara Rushewa da kuka tana Rokon Abdullahi da yayi Hakuri ammh yaki Sauraranta yace tayi maza ta Cire Hijabin Jikinta.

Hatta Mariya da suke Takun saka da Jidda sai da taji Tsausayinta Shiyasa arayuwarta tana Gudun Abunda zai saka ta Shiga Tarkon ya Abdullahi,Mama kuwa ita kanta Tsausayin Jiddan ya kamata sai dai bata isa ta Hana Abdullahi Daukan mataki kan Jidda ba Tunda batajin mgana Ba sau Daya ba ssu Biyu ba yasha mata Fada kan Shigen yawon Bin Gidajen kawaye in Mama ta aiketa da kuma Kawance da yarinyar nan Rumana ammh Jidda bata jin mgana sam.

Nazifi ne yaji magiyar tayi yawa ya Fito yana Fadin"Kai Mutumina Don Allah ka kyaleta..Tunda ta amsa laifinta kuma ta baka Hakuri karka Daketa plz."Cikin Bacin Rai Abdullahi ya Kalli Nazifi yana Fadin"Kana fa ganin Dabi"un Yarinyar nan..? Rawan kanta zai saka Wlh na kusa kasheta da Duka.."Nazifi ya karisa Kusa da Abdullahi yana karban Sandan Hannunsa Lokaci Daya yana Fadin"Cool ur mine Mutumina...Kamata afuwa Ko saboda ni don Allah.."

Yafada yana kallon Abdullahin wanda yake ta sakin Huci Shi kadai,Ajiyar zuciya ya sauke bai yi mgana ba Nazifi ya waiwaya ga Jidda yana Fadin"Maida Hijabin jikinki..."Da sauri ta maida hijabin Jikinta din wanda ta Riga ta Cire Har Farar T.shirt din Jikinta ya Bayyana wanda ya Bayyana Sirrin Kirjinta,Kau da kai Nazifi yayi da Sauri yana jin wani yanayin da bai Taba ji ba Duk da Duka Kannen Abdullahi ba wacce bata tashi agabansa ba.

Fushin Abdullahi ya sauka yasa Cikin Sanyin Murya yace"Daka bari na mata Dukan mutuwa Abokina..Bar ganin Tana wannan kukan bai Hana gobe ta kara maimaita laifinta.."Nazifi ya Juya batare daya ma Abdullahi mgana ba,Ya kalli Jidda yana Fadin"kinga tashi Tsaye.."Ba musu ta mike tana Share Hawaye Mama dake gefe tace"Da baka kwace ta ba Nazifi..Daka bari ya Mata ko kadan ne.."Nazifi yace"Haba mama...Har da ke Autan ki ce fa..'

Mama tace"Autan ne batajin mgana Nazifi yayansu ne Daidai da maganinta Tunda Daga Mariya har Auwal Ta Raina su Basu isa suyi mata mgana taji ba.."Nazifi ya sakarma Jidda ido kawai yana kallonta Lokaci Daya yana Nazarinta Ganin tana ta Share Kwallah da gefen Hijabinta yasa yace"Hauwa"u...!!!

Ya kirata Cikin wani Sauti Wanda yasa ta Dago Jajayen Idanuwanta Tana kallonsa Cikin wani yanayin da ita kanta batasan Dalili ba Taji kawai yaya Nazifin yau yana mata kwarjini Duk da Daman babu wani wasa Tsakaninsu Dalilin yana abokin Babban Yaya agaresu Cikin mutuwar Jiki ta Sadda kanta kasa Ta Kasa Jure kallonta.

Shima anashi Barayin Hakane Wani Iri yake ji acikin jikinsa game da idanuwanta,Cikin Dakiya yace"Kin dai gani yau na kwace ki hannun Yayanki...Gobe kuma Bana nan in kika Kara kinsan Abunda zai biyo baya ko..?Nida kaina bazan Hanashi Hukuntaki ba Tunda bakijin mgananr na gaba Dake.."

Jidda tace cikin Raunin murya"Bazan kara ba Ya Nazifi..
"yanayin yadda ta Fadi sunan nashi ya kara kashemai jiki ammh sai ya basar Cikin son Girma yace"Kinyi alkawari..?

Ya fada yana kafeta da idanuwansa Bata Dago ba ta Daga kanta tana Fadin"Insha Allahu nayi alkawari Ya Nazifi...!!!!Lumshe idanuwansa yayi kafin ya Bude yana Fadin"Naji Dadin haka..Plz ki zama mai jin mgana kada na sake Dawowa gidanan naji ance Jidda tayi wani laifin kuma kiyi Respect din Na gaba dake,Mariya da Auwal They elder dan u in suka gayamiki gaskiya u hv to Listem to Them yau in basu ba kina da wasu Shakikan yan"uwan da zasu Fada miki gaskiya ne..?

Jidda ta girgiza kai mirmishi Nazifi yayi kafin yace"Yauwa..Toh Maza ki Dauki Buta kiyi alwala ki Shiga Daki kiyi sallah sai kizo kici abinci ko..? Kai ta Fara Dagawa kafin tace"Nagode ya Nazifi..Allah ya saka da alheri.."Tafada tana Wucewa Bakin Fanfo inda Jerin,butoci yake ta zari Daya Lokaci Daya tana Cire Hijabin jikinta ta sagale Jikin igiya ta Fada Bayi Da kallo Dukkansu suka Bita Barin ma Nazifi Daya zama wani Mutum mutum na ganin Irin Dirin da Allah ya bama Jidda wanda bai taba lura ba sai yau.

Kallonsa ya maida kan Abdullahi kafin yace"To Babban yaya..Case din ya mutu sai kazo na ijiye ka Gida na kara gaba.."Abdullahi baiyi mgana ba ya Duka yana Saka Takalminsa Shima Nazifin ya Duka yana Saka nashi atare suka Dago suna ma Mama sallama sai Lokacin Mariya ta Fito Daga kitchen tana Fadin"Ya Abdullahi zani Gidan kawata wacce Muke karatu tar..."

Bazaki ba.."Bata karisa mgana ba ya Katse mata Hanzari batare Daya Jira Rokonta ba Kawai ya Fice Nazifi na Dariya ya Rufamai Baya Shi da kanshi yasan Halin Abdullahi kaifi Daya ne wani Lokacin ma yana Fa ganin kokarim Hafsah duk da baya ganin Hakan Abdullahi keyi wani illah ne,ammh fa Duk da Haka Abubuwan na Abdullahi sun Tarar da Halinsa na rashin son Daukan Raini da kuma Wulakanci ga kuma Fada da Fushi.


Akofar gida suka Hadu da Auwal nan ya gaishesu Cike da Ladabi nan yake Fadama Abdullahi yana Bukatar kudi zai siya Handout na makaranta Abdullahi bai yi gaddama ba ya Zaro 5k cikin Walet dinsa ya mika ma Auwal din Ya karba yana ta mai Godiya Yana wajen Har Motar Nazifi ta bacema ganinsa yana Daga masu Hannu Cikin Farinciki ya Shiga Gida yana nuna ma Mama kudin da Abdullahin ya bashi Mama itama tayi ta saka albarka.

Ganin Jidda sai wani kumbure kumbure take ne yasa Auwal din ya Tambayi Ba"asi mariya ta koramai Abunda ya Faru kallonta yayi harda Cizon yatsa yana Fadin"kash...Banso Ya Nazifi ya Karbeta ba naso yau ya Abdullahi ya Chasamin wata Hallita Naga karshen Rashin kunya da Taurin kai.."

Yafada yana Dariya Jidda Dake Zaune saman Cafet a dakin mama tana Yanke kumban kafarta ta Dago tana kallonsa kafin ta maida kallonta kan Mama wacce ke kokarin Zura Hijabi zata yi sallah tace"Mama..Mama kinga ya Auwal ko..?.
Tafada Cikin Shagwaba Mama ta kalli Auwal tana Fadin"Toh Baban Banza Baban gwabo..Ina Ruwanka da ita..? daga kai har Mariya kar wanda ya kara Tankamin Autata Tunda bata Kulaku ba ki kyaleta,kuma sai ka tashi Zuwa salla gashi chan ana Kira a wasu masallatan.."

Ta Fada Lokaci Daya tana Tada Sallah Auwal Yar dariya yayi kawai batare da yayi mgana ba ya Tura Kudinsa alijuhu ya Zura Takalminsa ya Fice Mariya kuma tatashi ta Shige Dakinsu wanda ke kusa da Na Mama Duk cikim Falo Daya,Wanda abaya Ciki da Falo ne Abdullahi yasa aka gyarashi aka Hade da wani Daki aka Fitar ma da Mama babban Falo da Uwar daka sai kuma aka Fitar da wani Daki Shima nasu Mariya,Duka Dakunan suna da Bandaki aciki sai Dakin kusa da na Mama ciki da Falo ne shima agyare yake Nan Zannira ke sauka in tazo ganin gida ko kuma in anyi baki Domin Har katifan kasa akwai acikin Dakin,Daga Wajen Kofar gida kuma Dakin Auwal ne,Gidane babba sosai katon Madafinsu ga kuma Wawaken Filin Tsakar gida ga Tailet din waje na Bahaya da kuma Fitsari.

******

Nazifi yana ijiye Abdullahi a kofar gida bai Shiga ba sukayi sallama ya koma,Yana Shiga Gidan su Amira suka Rugo suna mai oyoyo harda Hafsah wacce ta Chaba ado Daga wajen ya miika mata wayarsa da Kuma Links din Rigarsa bayan ya amsa sannu da zuwanta yace"Bani Ruwa abuta nayi alwala kafin na Shiga Ciki."

Da Sauri ta koma Daki ta Daukomai yayi alwala kana suka Dunguma Dukkansu Zuwa Ciki agida yayi sallarshi kana ta gabatar mai da abinci Tuwon Shinkafa miyar Shuwaka

10 / 48