Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
Dayake Cimarsane sai yaci kadan yace ta bari da safe ta Zafafa mai ya Riga yaci Tuwon Dawa wajen Mama Daga haka yaja ya"yansa Zuwa Ciki yana Biyema Shirmensu.
Da sukayi barci da kansa ya Daukesu Zuwa Wajem kwanciyarsu ya kwantar,Yayi musu addu"a,Ya koma Bedroom dinsu ya kwanta ita kanta Hafsah bata Damu kanta ba ganin yanayinsa kar tayi mgana Allura ta Tono garma,Sai dai tayi mai uzuri da gajiyan tafiya da kuma Zuwa Office washegari nan kuwa batasan bacin Ran da suka kwasa agidansu sakina ne bane,da kuma na Jidda bai gama sakinsa ba.
*Anitha...*
4/9/21, 1:54 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Janafty*❤️
*Dedicated To:My Habibaty💞Aisha Idris Abdullahi..*
_*Na Sadaukar da wannan Shafin kachokan zuwa gareki FAUZIYA S MADAKI..❤️,Janafty na Matukar Godiya da karamcinki gareni..Nagode kwarai Allah ya bar zumunci*_
*011*
"Washegari ma Haka ya tashi Ba Fara"a sosai Tunda Hafsah Taga haka sai ta kama kanta sanin in ya tashi da irin wannan yanayin Ita yake saukemawa aikuwa Duk Kafa kafanta sai da ta samu nata Rabon.
Jakar yaran na makaranta ya Duba yaga an basu Homework kuma ba"ayi musu ba nan fa ya fara ma Hafsah Fadan Tana da Careless kan ya"yanta Tunda har za"a basu aikin gida Tun Ranar jumma"a ammh tana gayamai bata san am basu yi ba Shuru kawai tayi mai saboda tasan ko tayi mgana bazai saurareta ba ammh laifin na Amira ne domin ita tace an basu Homework Ranar jumma"a Da suka Dawo Daga makaranta sai tace taja Amir ta koya mai suyi Homework Din tare,Tunda Gobe zasu tafi gidan Mama ba Lokaci ashe Amira bata Kama ma Amir din sunyi ba,gashi yanzu Fada ya koma kanta.
Haka ya fice Ranshi bace ko Cikakken kari bai yi ba,Kuma ranar bai Dawo Gidan da Wuri ba sai Dare Nan ne ma yake Fadamata Daga Tudun wada yake Ammi da Daddy na gaisheta sai Lokacin Taga sakin Fuskarsa.
Ranar sati ta zagayo Ranar asabar da kanshi ya kaisu Amira Chan Makarantarsu Ta hadda Daganan kuma ya Biya Gidan mama bai Dawo ba sai pass 12 bai jima da Shigowa ba sai ga Nazifi yazo Daukansa,Dama ko da yazo yana wanka ne,Yana Fitowa ya Shirya a gurguje,ya saka Kaya yace Hafsah ta bashi wasu Takardu Daya bata ajiya ta Dauko ta bashi suka Fice bashi ya Dawo Gidan ba sai wajen karfe Goman Dare agajiye ya Dawo wanka kawai yayi yaci abinci Hafsah tamai Tausa barci ya kwasheshi bai mata bayani ba sai da Safe Lokacin suna karyawa.
Ashe Fitar da sukayi Jiya Filinsa na Gaskiya ya saida wanda suka Siya Tare da Nazifi Kusa da kusa sai shi ya saida nashi Ya cika da kudin Hannunshi ya Siya wani Babban Fili a GRA,shine basu Dawo ba sai Dare sai da akayi Cike ciken Takardu da kuma sallaman Dilallai.
Hafsah ta kallesa tana Fadin"Meyaasa ka saida wanda kuka siya da abokinka Abban Amira..? Yana kurban Tea din Dake Hannunsa yace"Saboda na Gra din yafi Girma Sosai zai isheni na gina 3Flat harda Wadatar Filin Ijiye mota ina so in Allah ya yarda bayan na gama Ginin Gidan mun koma sai na Siya mota ko..? Wanchan kuma bai da Girma Sosai da kadan yafi wanda muke Cikin nan fa.."Kai Hafsah ta gyada kafin tace"Da wannan dan wannan kuma..Allah ya sa albarka Allah kuma yabada ikon Ginawa.."Ya amsa mata da Ameen nan suka cigaba da karyawan Jefi jefi suna Taba Hira.
Bayan yayi wanka Taga bai da Shirin Fita ta kallesa yana Zaune gefen gado yana latsa wayarsa tace"Yau Nazifin ba zai biyo maka ku fitan bane..? Bai Dago ba yace"Ai tun jiya ya koma Kaduna...Sakina ta je mai weekend.."Yar Dariya Hafsah tayi kafin tace"a"a lalle Dole kuwa bazaka ganshi ba kila sai Wani Weekend din."Tabe baki Abdullahi yayi kafin yace"Allah sa tayi mai zuwan ko na marmarina ne,Jiya muna Wajen Siyan Filin nan na Gra ta Kirashi tace ta tadawo bata ganshi ba,Shine bama mu gama Dashi ba nace ya tafi kawai ma karisa awaya kawai.."Hafsah tace"Ka kyauta.."Daga haka ta Dinke bakinta Shima gogan bai ce mata komai ba sanin Halinsa yasa ta Tura Kofar Tailet ta Shige Tana so ta wankeshi kafin ta Fara aikin waje.
Ranar litina kuma Yana office Mijin Zanniratu ya kirashi yana Shaidamai Haihuwan zannira ammh aiki aka mata Tana asibiti an ciro mata yarta mace,Barka Abdulllahi yayi da kuma Sakon sannu ga ita Zannira suna gama waya ya Kira Mama yana Fadamata tace itama yanzu Suka gama waya da mijin Zannira din nan Mama tace yakamata ko Mariya atura taje ta zauna da ita kafin adawo da ita gida Tunda Jidda na makaranta,tana Shekarar Karshe a sakandiri ita kuma Mariya Karatu suke basu da Test shiyasa.
Nan Abdullahi ya amince yace Mariyan ta Shirya tatafi in da akwai kudi hannun mama ta bata tatafi kafin yazo Mama tace Shikenan suka yanke Kiran nan da nan Mama ta Umarci mariya ta Shirya tatafi kaduna ta zauna da yaran Tunda ita Zanniratun tana asibiti,Murna ta kamata Dama ta takura zaman Gida baka zuwa ko"ina nan da nan ta Shirya kanta ta Shirya kayanta,Mama Ta bata 2k tace ta Rike Ahannunta in kuma ta isa takira waya Dayake Abdullahi ya siya mata Wayar hannu Vivo tana Karawa da ita.
Wajen la"asar ta Kira Mama tace ta isa,yanzu ma Mijin Anty Zanniran zai kaita asibitin nan Mama tace in sun isa ta kirata ta hadata da Zannira din ta mata Barka Bangaren Hafsah kuwa Subai"atu ta kirata tana shaida mata Haihuwar ta kuma Tambayeta yaushe ya Dace suje Barka su Duba Zannira din Hafsah tace"Duk lokacin da kika ga ya kamata.."Sai subai tace Jibi in Allah ya yarda ta Shirya zata Biyo da Direbanta ta Dauketa sai suje suyi mata Barka su Dawo kafin Suna kuma yazo Da haka suka Rabu da Subai suna gama waya ta Kira Ammi ta shaidamata ita kuma tace bari ta Kira Mama ta mata barka.
Bayan Abdullahi ya Dawo da Daddare Taji bai mata mgnar ba yana cin Abinci ta kallesa Tana Fadin"Ashe kuma Zannira an sauka Abban Amira..? Ya Dade bai bata amsa ba tama Zata bai jita bane tana Shirin maimaita Tambayar tajisa yana Fadin"Eh dazu da safe megidanta ya Kirani yana gayamin anyi mata C.s ne.."Hafsah tace"Wh haka Subai take Fadamin dazu..Allah sarki Allah Bata lafiya Subai tace zamu barka Jibi kafin suna ya zagayo.."
Yana jinta kamar bazai Tanka ba sai kawai taji yace"Ok.."Daga haka bai kara mgana ba yacigaba da cin Abinsa Gefe daya kuma yana Kallonsu Amir da Amira Dake yin Homework dinsu Hafsah kuwa murna ta kamata ganin Abdullahi ya amince batare Daya yi wata mgana ba Sai da kuma wani Shashe na Zuciyarta na gayamata ai Zannira kanwarsa ce zai so taje ta gaisheta.
Ganin Haka yasa bata kara mai mganar ba sai Ranar tafiyar,Tun safe tatashi da Shirinta sai dai me Bai Fita da Wuri ba su Amira ma mai mashin dinsu ya kira yazo ya Daukesu yace bada Wuri zai Fita office ba yau mamaki ya kama Hafsah sai kuma ta Shanye mamakin Tunanin kila suna da Taro ne,Domin wani lokacin in suna da Taro yakan kai 10 da wani Abu agida kafin ya Fita,Tuna haka yasa bata damu ba Cikin Lokaci tagama Komai na Gidan ta yi wanka ta Shirya Cikin Wata Atamfarta mai kyau da Garari mai kalan green,Sai ta saka Hijabinta gree da Takalminta baki jakarta ma Haka,Gaban madubi ta tsaya tana kallon kanta ta madubi Abdullahi na Gefe kan gado yana ta Danne danne kan Laptop dinsa Jifa Jifa yana Maida kallonsa kan Hafsah wacce ke ta Shiri acikin Ransa kuwa mamakinta ya kamashi tana nufin wai wannan gayamai datayi Shine azuwan neman izini..? Saboda ta Rainashi bata Daukeshi da Daraja ba kenan toh sai yagani in zata iya zuwa batare da Cewarsa ba.
Bai gama wannan Tunanin Zuccin ba yaji wayarta ta Shiga neman Dauki da Ido Daya ya maida kallonsa kanta yaga ta Daga wayar Lokaci Daya tana Rataya Jakar hannunta Cikin Fara"a take fadin""Uwar muhsin har kin iso ne..?
Dagachan Bangaren Subai"a tace"Eh gani kofar gida...ko sai na Shigo ne..? Hafsah tace"Toh da dai kin Shigo kun gaisa da yayan naki.."Subai Ta rike baki kafin tace"Wai kina Nufin wai yana nan bai Fita office ba..?Hafsah tace'Eh inaga sai anjuma zai Fita.."Tafada tana kallon Abdullahin wanda yayi Saurin Dauke kai kamar bai san kan me suke mganar ba nan kuwa Hankalinsa kacokan yana kan Hafsah.
Subai tace"Nifa bawai na Shigo bane kinsan Halin yaya sai ke Wlh Qawata.."Dariya Hafsah tayi Tana Fadin"Ki fada.Yana jinki Wlh.."Jin haka yasa da Sauri Subai ta katse wayar Lokaci Daya tana Saba Saleem akafadarta ta Fito Daga Motar kirat Jeep tana Fadama Direban bari ta Shiga su Fito tare da Hafsah din yace bakomai Hajiya.
Ko Minti Biyar ba"ayi ba sai ga Subai"atu tayi sallama a tsakar gidan,Hafsah Dake Ciki tayi Wuf ta Fito tana amsa sallamar nata Lokaci Daya tana mata Maraba Falon Subai ta Shigo Tana Fadin"Mu shigo ko mu koma.."Hararanta Hafsah tayi kafin tace"Ku koma mana yar rainin Hankali.."Tafada tana Karban Saleem Dake hannun Subai din kan Daya Daga Cikin kujerun Falon suka yada zango suna gaisawa kafin Subai ta Fara waige waige tana Fadin"Ina ya Abdullahin..? Ko iskanci ne Saboda dai na Shigo..?
Hafsah tace"A'a wlh..Yana Ciki bari na Shiga namai mgana.."Tafada tana Tashi sabe da Saleem ta Shiga Dakin inda ta barshi nan ta iskeshi Cikin kulawa tace"Abban Amira bakaji Shigowar Subai bane..?
Hankalinsa na Bisa Syestem dinsa yace"Naji....!! tazo lafiya..? Yanayin yadda ya amsa mata yasa kawai tasha Jinin jikinta Jiki a sanyaye ta Juya Tana Fadin"Ta Shigo ne ku gaisa wucewa Zamu yi.."Bai ko Dago ya kalleta ba Har ta Fice,Ba Dadewa Shima yabi bayanta Suna cikin Mgana da Subai ya Fito Cikin Jallabiyarsa mai Ruwan kasa,Da Sauri Subai ta gyara tana Fadin"Ina kwana yaya..?
Yana Tsaye yace"Lafiya lau ya yaran..? Yafada yana mikama Hafsah hannu ita kuma ta sai ta mikamai Saleem Dake hannunta Karbansa yayi yana Fadin"Yayi yawo sosai.."Subai tace"yaya yayi fa 3month.."Tafada tana kallonsa da Mirmishi yana Tsayen ya sake Fadin"Duk da haka dai Subai"atu...yau kin zo mana Wuni ne..?
Daga ita har Hafsah Da kallo Suka Bi Juna kafin Subai ta maida kallonta kan ya Abdullahi Tana Fadin"Wuni kuma yaya..? A"a ba wuni nazo ba..Hafsah bata gayamaka ba,? Abban Muhsin ne ya bamu Direba zai kaimu Kaduna muje mu Dubo Anty Zannira kafin Ranar suna.."Kai Tsaye yace mata"Eh ta Fadamin mana.."
Cike da mamaki Subai ta kalli Hafsah kafin tace"To yaya ai yau ne zamu je din...Shiyasa na Fito da Wuri saboda mu Dawo da wuri kaga Hanya bakyau.."Mirmishi yayi kafin yace"Ok Nidai cikin Zencenta naji tana Gayamin Zaku Tafi Barka kaduna...."
Jin Haka yasa Hafsah tace"Ammh Abban Amira na gayamaka."Tafada Cikin Raunin murya kai Tsaye yace"Wa kika gayamawa..?ni...?Kika dai yi Zencenki ina jinki,na dauka kinaa mganarki ne kawai Domin wannann Zence ne na mata ban Daukesa aneman izinin ba.."Yafada yana Mikama Subai Saleem wacce tayi Jugum Tana kallon Ikon Allah.
Idanuwan Hafsah ya kawo kwallah Cikin wani Rauni tace"Na dauka danaji kace Ok ka amince naje din ne.."Karamin Tsaki yaja kafin yace"Saboda kin Rainani ko..? Haka kurum Saboda Subai"atu ke Auranki sai ta Shiryamiki tafiya ke kuma ki Hau ki zauna Batare dani mijinki kin Tuntubeni ba kuma da kike mganar kin gayamin Daga Ranar kin karamin mgana..?Kin sameni kin ce Abban Amira muna so zamuje Mu gaishe da Zanniratu kafin suna..? Kin sameni..?
Yafada yana Tsare ta da ido Jikin Hafsah yayi sanyi kawai sai ta Dukar dakai Hawayen idanuwanta suna kawowa Subai kuwa addu"a take aranta Allah sa kada Fadan ya Dawo kanta Tabe Baki yayi ya juya yana Fadin"Kinga kenan baki da Tafiya sai ki bari Ranar suna sai ki Tafi..Shima in kikamin irin wannan Tafiyar kinsan Allah bazaki ba.."Yafada kai Tsaye yana Shirin Shigewa Bedroom
Da Sauri Subai tace"Don Allah yaya kayi Hakuri munji munyi kuskure bazamu kara ba..Ammh Don Allah yanzu kabari muje mu Dubata bazamu yi Dare ba da yardan Allah...."Waigowa yayi Lokaci Daya yana Hararan Subai din Wacce ta sadda kai kasa gabanta na Faduwa cikin Gadara yajuyo yana kallon Subai"atu Lokaci Daya yana Fadin"Kinsan Allah.? Bafa zataje ba ayau..Sai dai in ku Rushe tafiyar yau wlh...In kuma bazaku Rusheta ba ki kama Hanya ki Tafi Tunda ke kin gayama Mijinki kuma ya barki har ma yabaki Direba kinga ke sai ki kama Hanya ita kuma Ranar data Shirya tafiyan in ta nemi izinina na barta sai tatafi taje ta gaisheta ta mata barka ta Dawo.."Daga haka bai kara komai ba ya Shige Ciki.
Hafsah Data ke Rike Hawayenta sai gasu sun Zubo Sharr,Subai ta kalleta Tana Fadin"Wai ke baki Fadamai bane..? Hafsah ta Dago idanuwanta cike da kwallah tace"Wani irin ban gayamai ba.? Ina Ranar da mukayi waya da Daddare bayan ya Dawo muke tadin Haihuwan dani Dashi anan ne toh nake gayamai mun yi waya Yau zaki Biyomun mu tafi muyi mata barka yace min Toh kinji Dalilin Daya saka ban karamai mgana ba.."Ta fada Lokaci Daya tana Share kwallar Idonta.
Subai ta saki ajiyar Zuciya Tana Fadin"Toh yanzu ki Tashi ki Bishi ki gani ko zai yarda mu tafi gaskiya in bamu je ba bamu kyauta ba Duk da Mariya na chan Jiya Mama da Inna Abu fa sukaje suka Dubata suka komo.."Hafsah tace"Karma na batamiki Lokaci Subai ki tafi kawai kice ina mata barka Duk da daman na Kirata awaya na mata sannu..Ranar suna in yabarni sai na taho..
Subai tace"Kina ganin in kika lallasheshi bazai yarda ba.."Hafsah tayi yaken Dole lokaci Daya tana Fadin"Hmm Kema Subai da wata mgana kike ina ce kin Rigani sanin Halin yayanku kaifi Daya ne in yace Abu toh hakan take ba Chanzawa Tunda yace bazani ba Toh fa din bazani ba Sai dai wani Lokacin kawai..'Subai tace"Kai kai..Ya Abdullahi Danja ko Daru ne ma Zance.."Sai da ta Fada kana ta koma tana Rufe baki Lokaci Daya Tana kallon Hanyar Bedroom din Hafsah idanuwanta Duk suna waje
Mikewa tayi tana Saba Saleem Lokaci Daya Tana Fadin"Zan tafi Hafsah in naje zan gayamata kin so Zuwa yayanmu yayi Tsiya.."Tafada tana yar dariya Hafsah ma yaken tayi ta mike tana Fadin"Allah kaiku lafiya ya Dawo daku lafiya..ki gaishemin da ita Don Allah."Subai tace"Zataji insha Allahu sai ki lallabasa ya barki zuwa suna mu Tafi Tun ana gobe mu dawo Washegarin suna.."
Kai kawai Hafsah ta Kada kafin tace"Wa..? Lalle nema ina ma laifin Ranar suna mu kwana Daya bazai barni ba zai ce Ko Biki ne iyakarta kenan.."Subai tace"Gaskiya Qawata ina jinjina miki wajen Fama da yayanmu Wlh bazan iya ba.."Tafada tana Bata rai Hafsah batayi Mgana ba illah kada kai kawai datayi.
Tsakar gida suka Fito Subai na kara Saba Saleem Bisa kafadarta Tana Fadin"Lokacin muna gida munci Ubanmu ammh Mariya tace Har gwara kila lokacinmu yanzu basu da wani Motsi ko Fita Zakayi sai da izininsa Auwal ya Fadamin Jidda ce kecin kwal ubanta a wajensa.."Ta karishe tana yar Dariya Kada kai Hafsah Kawai Hafsah tayi tana Fadin"Ai fa..Sai ta rika kiyayewa kamar kowa.."
Har Kofar gida Hafsah ta Raka Subai Tana Dagamata Hannu,Har Motarsu ta bace ma ganinta kana ta koma Cikin Gida,Tana Shiga Suka ci karo da Abdullahi ya yo Shirinsa na zuwa Office sabe da Jakar Breifcase dinsa,Ko kallonsa batayi ba kawai ta saka kai ta Shige Dakin su Amira ta Shige ta Haye yar katifarsu kawai ta fashe da kukan Data ke ta Rikewa tun dazu Labulan Dakin ya Daga yana kallonta Cikin mamaki,sai da yadan Jima kafin ya kada kai yana Fadin"In kin gama kukan Jin Dadin ni na Fita.."Daga haka kawai ya sauke Labulen ya Fice Tana daga kwance ko Dagowa batayi ba Ballatana ta amsa mai.
Tana jinsa ya bude Dakin da Mashin Dinsa yake ya Fito Dashi ya Goggoge ta kafin ya Fice Tana Jin Tashin Mashin din nashi da kuma Tafiyarsa ammh bata Daga ba,Sai da tayi kukanta ya Isheta kana ta Share Hawayenta Tana Nan kwance Taji wayarta na Ringing Daga Falo ta Fito ta Dauki Wayar ganin Umman Sadiq yasa ta gyara muryanta ta Daga Kiran suka gaisa nan take tambayanta su Amira tace suna makaranta,ita Hafsah ke gayamata Haihuwan Zannira Umman Sadiq din tace ai mama ta Kirata ta gayamata in ta samu Dama Zatazo tayi barka Zahra ce batajin Dadi nan Hafsah ta mata ya Jiki basu Dade suna mgana ba sukayi sallama.
Agaskiya Hafsah tayi Dacen Surukan kwarai baga Mama ba baga Ummin sadiq ba wanda Duk kwannan Duniya sai ta Kirata taji ya suke..? Matar bata da matsala ne sosai,Abdullahi ma Suna yawan mgana Sosai,Duk da in ba ya Fada ba ba wanda zai ce Ba Mama bace ta Haifesa ba Saboda bai Taba nuna wani bambamci tsskanin Mama da Umman Sadiq ba,Gidan kakaninsa kuwa yana Zuwa Sosai yaje ya Wuni ya Dawo,koda bazai kwana ba Harda Nazifi sun sha Zuwa in sukaje yaBiya yaga Umman Sadiq sai dai in sun Daawo Hafsah taga sako inji mama kana zata san sun je gusai aranar.
Har yammah Hafsah bata saki ba ko Girki batayi ba,Complex ta jikama su Amira suka Sha Bayan sun Dawo Daga makaranta Subai"atu kuwa ta isa kaduna Lafiya ta samu ma an sallami Zanniratun ta koma Gida,Da taga Subai ita kadai sai da ta tambayi Hafsah Wanda daman Ita Subai din ta mata waya kan tare zasu zo nan Subai take basu labarin Abunda ya Faru baki Zanniratu ta Rike kafin tace"Na Shiga goma ni Zanniratu dama wai Har yanzu Ya Abdullahi bai chanza Halinsa ba..?
Mariya na gefe tace"Sai ma Abunda ya karu Anty...Kinsan Allah da bai amunce ba da ko ke bazan zo na zauna miki ba.."Zanniratu tace"Lalle ya Abdullahi isar nan da ikonsa Na nan Tare dashi Haka Aliyu na ke Fadin Yayan naku ya cika Fadin rai da isa ni kuma nayi ta karesa Duk da dai nasan gaskiya ya fada,nima Jiya Daya Kirani yayi min Barka Kunsan me yace min..?
Gabadayansu suka Girgiza kai Cikin Takaichi tace"Wai ina Dauka sai cemin yayi mai cikin Haihuwa..Nace kamar ya Ya Abdullahi..? Bude bakinsa sai cewa yayi Wai na cika haihuwa duka duka yaushe nayi Auran har nayi ya"ya har Biyar..?Subai da mariya suka saka Dariya kamar Cikinsu ya kulle Mariya tace"Kadan Daga aikin Ya Abdullahi kenan Anty Zanniratu..
"
Subai tace"Yau ai naga lukutar masifa..Kiri kiri yace Hausi baza je ba....Sai dai in mu sauya Ranar Tafiya.."Zanniratu tace"Allah sa