Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
Doguwar Rigar Dake Jikinta.
Salisu yace"Abdullahi Rabona Dakai Tun Ranar Daurin Auran Nazifi Fa haduwa tayi wahala ango kuma an koma Kaduna ko..? Abdullahi yace"Wlh fa..Sun koma Kaduna tun Satin chan Hala kunyi waya ne..? Salisu Dake Tsaye yace"Eh Munyi mgana Dashi yace min ya koma Bakin aikinsa..'"Abdullahi yace"Haka Hutunsa ya kare.."Salisu yace"Masha Allah..Allah Basu zaman lafiya.."Abdullahi yace"Ameen yasu Hajiya..? Salisu yace"Lafiya lau...Dazu ta bar Asibitin nima yanzu na Shigo Ina Shirin Wucewa ne ma sai kaga..Ke Bahi bashi Kujera mana kina Zaune.."
Bahiya Tayi Saurin Mikewa Tana Turama Abdullahi kujeran kai ya Girgiza yana Fadin"No..Nagode Nima ba zama zanyi ba Wucewa zanyi Dare yayi...Allah kara afuwa.."Dukkansu suka amsa da Ameen,bahijjat da Bahiya kuwa a kalaman Yayansu Salisu suka Tuna inda suka san Abdullahi Suna Ta mamaki Me ya Hadashi kuma da Anty Barkat Basu da amsa wannan Tambayan Abdullahi yayi musu Sallama zai Tafi Salisu yace su Fita Tare Yace Bahijjat ta Shirya ya ijiyeta Gida Tunda Bahi kadai ke kwana da Barkat din Godiya sukayima Abdullahi yace ba Bakomai Barkat Dake zaune tana Jin Tama Warke Gabadaya ya kallah yana Fadin"Sai anjuma..Allah kara afuwa sai munyi waya.."Kai ta gyada mai Tana Fadin"Nagode Ameen ya Allah...!
Daga Haka suka Fice Harta Bahiya Datatafi Rakiya Suna Baya Suna Gulma da Bahijjat,Barkat kuwa suna Fita ta Sulale ta Fada kan gado Tana ma Allah Godiya,Farinciki kamar ya Kasheta Wayarta Dake kan Dirowan Gadon ta Rarrafa ta Dauka ta Shiga Ma"ajiyan Text ta Turama Abdullahi.
_Tanque so much...For u Care...Barkat Relli Appricent..._ lokacin Daya ji Shigowar Sakon Suna Sallama ne da Salisu Shiyasa bai Duba ba,Salisu da Bahijjat suka Shiga Motar Salisu Ita kuma Bahiya ta koma Shi kuma sai ya Tada Mashin Dinsa ya Bar asibitin kusan Tare suka Fita da Salisu.
Ganin Tara ta wuce yasa yayi Gudu Bisa Mashin din ya Isa Gida Koda ya koma Tuni Su Amira Sunyi Barci Hafsah ma ta Bingire saman Kujera Shi ya Kashe Wutar Dakunan Dana waje ya gyara ma su Amira kwanciya Ita kuma Hafsah ya Dauketa Zuwa Ciki Sai Lokacin ta Farka ya Direta Saman gado tace"Abban Amira sai yanzu ka Shigo..?
Kai Tsaye yace mata"Eh..Na Shigo Kin kwanta kinbar kofa Bude."Hamma Tayi kafin tace"Wlh ina Jiran Dawowarka ne Barci ya kwasheni."Yana CireRigan Jikinsa yace"Aifa..Naga alama ai Tunda kika samu wannan Cikin kika zama Raguwa.."Baki ta Tura tana kunkuni Sai ta bashi Dariya ya Murmusa yana Fadin"Eh karya nayi..?ki Rantse da Allah ba ki zama Raguwa ba..? Banda barci babu Abunda kike iya Tsinana ma kanki Ballatana ma ni na Saka Ran za'a ji Tsausayina.."jin haka yasa taJuya Baya Tana Fadin"Sai da Safe.."Dariya ta kamashi yayi yana Fadin"Zaki sani ne Yarinya zan kamaki.."
Kayansa Ya Cire ya Sauya Dana Barci Wutar Dakin ya Kashe kana yazo Gefen Hafsah ya kwanta ya ja musu Bargo Ya Jawota Jikinsa ya Rumgume yana Sakin Ajiyar Zuciya tana Jinsa sai ta Kara lambo Shi kuma yasan Batayi Barci ba yasa ya Zura Hannu yana Shafa Cikinta Da Sauri ta make Hannunshi Dariya yayi yana Fadin"Au baki barci ba..? Da sauri tace"Allah nayi barci bakai ka Tadani ba.."Tafada a Shagwabe tana Tura baki Hancin nata ya lakuce Lokaci Daya yana Kara Rumgumeta Cikin Jikinsa.
Washegari kuma Sai da yaje office kana ya Bude Sakon Barkat Mirmishi kawai yayi sai ya Kirata wannan karon ita ta Dauka ya Tambayeta Jiki tace taji Sauki Kilama an juma su koma Gida yaji Dadin Haka yayi mata Fatan Sanun lafiya Kafin ya yanke Kiranshi yana Shirin Tashi Office yaga Sakonta na anyi Dirsharge Dinsu bai Kirata ba sai ya Tura mata Sako da Cewa"Alhamdulillah...May Allah grant u Shifa Ameen..."
Bai Kirata ba Sai da aka kwana Biyu da Sallamanta kana ya Kirata Yana Tambayanta ya Jikinta tace mai ta samu Sauki Sosai yanzu hakama tana Shirin Komawa Cikin makaranta Saboda Suna da Test Ranar Monday Har ma yana Tambayanta ta samu Wajen zama ne tace A"a Hostel zata je Wajen Bahiya Suyi Sukwatin,Fatan alheri yayi mata Kafin Suyi Sallama da Juna Barkat Tana jin Cewa acikin Ranta Lokaci kadan Kawai ya Rage Burinta ya Cika akan Abdullahi.
Su Bahiya suka Gayama Hajiya Labarin Zuwan Abdullahi Asibiti da kuma Kiran da yake mata itama Tayi mamaki Sosai,Hakama Salisu Dayazo ta Tambayeshi ko yasan Wani Abu Dake Tsakanin Abokinsa da Barkat din yace Wlh bai sani ba Shima Yadda Ya ganshi A asibitin ya bashi mamaki matuka Tunda bai mai mganar ba Shima bai Mishi ba Hajiya Tace Allah sa muji Alheri Domin Tana Hasashen Wani Abu Allah ya Tabbatar mata,su Bahiya da Bahijjat kuwa gajiya sukayi da Tambayan,Barkat meke Tsakaninta da Abdullahi ammh Wlh ko kallo basu Isheta ba Basu Damu ba sanin Halinta na kyaluwa da Banzatar da Mutane Haka Har Ranar lahadi Tayi Ita da bahijjat suka Tattaro Suka Koma Cikin Makaranta Dama Ciwon Barkat din ya Dawo da Bahiya Din Bahijjat Kadai Suka Bari Agida Aina ma Tana Makaranta ammh Ta kusa Dawowa Domin Exams Zasu Fara ayi Hutu Su Dawo Gida.
Abdullahi bai kara Neman Barkat awaya ba itama Bata Kiranshi Sai dai kowani Safe da Yammah Da Sakonta yake cin karo,Har ya Riga ya saba da Sokonninta in bai gani ba har Damuwa yake,Domin acikin Sakon nata Dauke da kalamai na Nuna Damuwa Sosai da Mutum da kuma addu"o'in Fatan alheri da nasara da kuma Cigaban Rayuwa Uwa uba kuma da Tambayan Lafiyan iyalansa Tun Baya maida kai har ya zama Shina ya kan Tura mata na Happy Jumma"ar ko Gud Morning Duk a zuwan kulawa yabawa ne.
Ranar Friday ya Shiga Cikin Makaranta sai ya Kirata tace Tana Cafterian,Sai yace Kawai Ta Jirashi Gashi nan zuwa ba Jimawa sai gashi Barkat Tayi mamaki Sosai kan yadda Abubuwa Suketa zuwa mata da Sauki nan suka zauna Suka gaisa ta sa aka kawo mishi Drinka da Snacks,Yana ta mata Tsiyan sai yaci Tunda yar makaranta Tana da kudi,Ita kuma sai mirmishi Take Cikin Jin Dadi da jin kai,Sun Dan Jima atare awajen Suna Hira Farkon mganace kan Harkan karatun kafin sun gangara kuma Kan Harkan Rayuwa Shi ya Daukesu Wajen awa Daya suna Hira Ya Fahimci Barkat Tana da Ilimi Sosai da kuma wayon Sanin zamantakewar Rayuwa Sosai Ganin yammah tayi yaasa yayi mata Sallama da zai Tashi ya Biya Duka kudin Abunda suka ci Barkat din Ta bata rai akan ita zata Biya ya Hanata Dole ta Hakura Tare Suka Jero tare Har Zuwa Wajen Daya Faka Mashin Dinsa nan sukayi Sallama kan sai Sunyi yawa Ya Hau Mashin Dinsa ya Tafi Tun yana Hanya yaji Shigowar Sako Sai da ya isa gida ya Duba ya ga Sakon Godiya ne Masu Cike da kalaman Jan Hankalin Da Namiji Daga Barkat Abun yayi Mishi Dadi Sai da Shima yamaida mata da Sakon Godiya Shima Tare da kalaman Jinjina Gareta Daga karshe yayi mata Fatan Samun Nasara a Test din da Suke Rubutawa,Lokacin yana Falo ne Zaune kan Daya Daga Cikin Kujerun Falon Hafsah kuma na Zaune,a kasa ta Mike kafa Su Amira kuma na gefe suna Wasa Mgana ma Take mai kan Zata Fara Zuwa awo ammh Gabadaya Hankalinsa Baya Tare da ita Ganin haka yasa ta Tago Tana kallonsa Sai Taga yana Mirmishi Shi kadai mamaki ya Cikata Tayi Galala Tana Binshi Da kallon Mamaki Domin Abunda Bata sani ba Barkat din ne Tayi ma Abdullahin Tayin ko zasu koma Whatsop ne Yace mata Why not Dama yana Online sai gashi Tamai Mgana Korafi ta Faramai na Yadda Ta Girmamashi a matsayinshi na Bakonta ammh Shi kuma Sai ya Biya kudin Komai Shi kuma sai ya na mata Wasa yace Watarana Zai zo Su Fita Tare Sai ya karar da Duka Kudin Kashewarta na makaranta Tun Hafsah na kallon Abdullahi Tana mamaki Hardai ta Daina Tana Kallonsa ya Tashi ya Shige Ciki Bayan yace mata Ta kai Su Amira Ciki Da ido ta Bishi Acikin Zuciyarta Tana mamakin me ya Dauke ma Abdullahi Hankali Wanda yasa ko Mganarta bai Saurara ba..? Bata da wannan amsan Dole ta Kira Amira tace ta kama Hannun Amira Suje suyi Fitsari Tazo su kwanta Domin Tunda ta Zauna Taji Bayanta ya kage Bata iya Tashi.
*******
Bangaransu Jidda kuwa Sai da Suka kwashe Kimanin Sati Biyu Suna Cin Amarsun kana Sakina ta Diro Gidan,wanda babu Wanda yasan da Zuwanta Ko Chan Gidansu Basu sani ba Domin Hajiya da Alhaji Badamasi yace bazata koma ba sai Nazifi ya Tako ya zo da Kafarsa ya Bata Hakuri Toh ina Zata Jira Tunda Nazifi ya Shukata kamar Dussa ta kirashi Har sau Shurun Masaki ammh bai Daga Kiranta ba kuma ta Turamai Sako Shima bai Taba maida kai Ba ganin Haka yasa ta Shirya ta koma Abuja bakin aikinta Duka Duka kwana Shida tayi Ta Dauki Excuse na Bata Jin Dadi Daga Abujan Direct Kadunan ta wuce.
Ai kuwa Tun Ranar Data Diro garin Da Mugun gani taci karo,Domin Nazifi da Jidda ta iske a Tsakar Falo Yana mata yan Goye Goye Kuma Dukkansu ba wasu kayan Kirki ajikinsu Sai Wani Wasan Banza Suke Abun ya Soki Zuciyarta ganin Yadda Nazifi yayi kiba Sosai ya Murje kamar ba shi ba Ita Kanta Jidda ta Sauya Aure da Jin Dadin Rayuwa Sun Sauyata ta zama wata Babbar mace kugunta da Kirjinta sun kara Cika Sosai.
Su basu ma san da Shigowarta ba Sai Jin Katon Tsakin Dataja musu a Tsakar kansu sukaji Gabadayansu suka waigo Ganin Sakina Sai da gaban Jidda ya Fadi Tana Goye Bayan Nazifi ganin bai Sauketa ba itama sai ta kara Lafewa,Kallon Sakina yayi Yana Fadin"A"a uwargida Sarautar mata..Kece Tafe ba Sanarwa.."?Yafada Lokaci Daya yana Sauke Jidda yana Fadin"Babyna Sauka muje muma Antynki Oyoyo..."
Sauka Jidda Tayi tana Murza ido Cikin Shagwaba Take Fadin"Ni ban yarda ba yaya sau Goma fa kace zakamin Doki Dokin.."Kanta ya Shafa yana Fadin"Ehmana..Dole nayi miki Babyna,...Kinga Antynki Ta Dawo Bari mu gaisheta sai muzo in yi miki Doki Dokin ko..?jin haka yasa Tawashe baki tana makaleshi Sakina Dake kallonsu Taji Wani Bakinciki Na Taso mata Daga kasan Ranta bata Jira Sun kariso ba Taja karamin akwatinta ta Shige Dakinta Tana Kokarin maida Hawayen Idanuwanta kada su gani Taji kunya,Tana Shiga ta Banko Kofa Harda saka key Ta Sulale nam kasa Lokaci Daya tana Fashewa da wani kuka Dake Fitowa Daga Kasan Ranta.
Da kallo Suka Bita Nazifi ya Tabe baki irin mai Damu ba Jidda ce tace"Yaya naga ta Shiga Ciki bata Tsaya mun gaisa ba.."Nazifi ya rikota yana Fadin"Karki Damu Bbyna..Zaku gaisa anjuma Yanzu muje Kitchen na Tayaki Girki in mun gama Muje muyi wanka ina so zan Fita ne.."Da to ta amsa kafin Su Rankaya Tare zuwa Kitchen Domin indai yana Gidan Tare suke komai Abunsu Gwanin ban Sha"awa,in ka gansu sai sun Baka Sha"awa Sosai Jidda Take Fitoma da Nazifi Salo Salon da Yayyinta su Subai"atu suka Koyar da ita,Dawowarsu kaduna Zannira tazo Itama Taje mata Hakama Hajiya Sa"a da Hajiya lariya Sunzo mata Hakika Hajiya Sa"a tafi kowa Farincikin Ganin yadda yarta ta koma gwanin Ban Sha"awa nan suka wuni sai yammah Suka Tafi,Nazifi da Jidda sukayi ta ina suka saka Dasu Hajiya Sa"a taji Duka Hankalinta ya kwanta Tana ta Jin Dadi da alfaharin yarta ta samun Gidan Zama nagari Tare da Jajirtatten Miji mai Kokarin Sauke Nauyin Dake kanshi,Su Mama kuwa kullum sai ta Kirata sunyi mgna ita da Inna Abu Mariya ma Haka Tagama nacin Mariyan Tazo Taki Zuwa Tana Tsoron ya Abdullahi Domin Tana da Tabbacin indai yaji labari bazai Barta ba.
Tare sukayi Girkin suka Gama Doya Jidda ta Dafa da Miyar Soup na Kifin Saidin,Tare suka Jera komai Bisa Dinning,ganin ana Ta Kiran Sallar mangariba yasa Nazifi ya bar Jidda na gyara Kitchen din Shi kuma ya koma Daki ya Shiga wanka ya Shirya yazo ya iske Jidda afalo yace mata zai Fita masallaci Dagachan zai Biya wani Waje Ta Faramai Shagwaban kar yaje ya zauna ya Rumgumeta yana mata alkawarin bazai Dade ba Har Kofar Falon ta Rakashin kafin suyi Sallama tana mai Addu"an Dawowa lafiya tana Juyowa Taci karo Da Sakina Data Fito Daga Cikin Dakin Ta Tana wani Taku Daya Bayan Daya tayi wanka ta sauya kaya ammh kallo Daya zakayi mata ka Fahinci Tasha kuka Domin ga Fuskarta nan ta Kumbura da idanuwanta.
Kallon Jidda take Ido Cikin Ido Irin na Wulakancin nan,ita kuma Jidda sai ta Dauke kai Tana gaisheta Bata amsa mata ba sai ma Tsaki Data saki Ta koma ta zauna kan Daya Daga Cikin Kujeun Falon Lokaci Daya Tana Daukan Remot din Tibin Dake Falon Jidda bata Damu ba ta Wuce Cikin Bedroom dinta itama tana Juya mazaunanta, da kallon Mamaki Sakina ta Bita Tana Tunanin Dan Hakin daka Raina Daman Shi ke Tsole maka ido.
Nazifi Sai Wajen 9pm ya Dawo Gidan Lokacin Jidda tasha Wanka an kashe Dauri itama Tazo Falo ta Zauna Tana Jiran Dawowarsa yana Shigowa tatashi da Gudu ta Daneshi tana mai Sannu da zuwa Shima Rumgumetan yayi yana jin Wani Farinciki acikin Ransa sai da suka kariso Falon kana ya lura da Sakina Cikin Mamaki yace"A"a uwargida Sarautar mata..an Fito..?Kallon Tara Saura tayi musu kafin ta Dauke kai Bai Damu ba Jidda taja Hannunsa Zuwa Saman Dinning Daya ma Sakina Mganan tazo Suji Abinci Ko Kallonsu batayi ba basu Damu ba Sukaje suka cinyarda juna Sakina na Zaune ne ammh Rabin Hankalinta na kansu Duk yadda taso Ta kauda kanta Ta kasa ganin Karuwan cin yarinya karama Kiri Kiri,Shi kuma yana Zaune yana Biye mata,Taji kamar Bakinciki ya kasheta.
Bayan sun kamallah Cin Abincin suka Dawo Falon nan ne Nazifi yace yana son mgana Dasu Dukkansu Nasiha ce kawai yayi musu sai kuma mganar Raba kwana,ya Saka cewa in Sakina ta Dawo zai koma Wajenta Har tatafi Tunda dai ita bamai zama bane sai tayi Sati Uku bata zo Gida ba,In kuma Batanan sai ya koma Wajen jidda,Ya bama Sakina Daman tace wani Abu taki cewa komai sai ma Tsaki Data saki Ta Tashi Ta Shige Ciki Da kallo Dukkansu suka Bita Jidda kuwa Duk ta Damu na yadda yau zasu Raba makwanci ita da yayan nata,Ammh Daya Lura da Haka sai ya Fara Kokarin kwantar mata da Hankali Sai da ya Rakata Har daki tayi wanka ya Tayata ta saka Kayan Barci ya kwantar da ita Shima ya Bita suka kwanta Suna makale Da Juna Yana mata Hira Sama sama Har Barci ya kwasheta kana ya Zare Jikinsa ya gyara mata kwanciya ya Rage mata Wutar Dakin ya Lallaba ya Fice Zuwa Dakin Sakina.
Koda yaje Dakin Sakina ya Iske ta kwance kamar mai Barci nan kuwa ba Barci Take ji ba kuka Take yi jin Motsinsa yasa tayi Lamo kamar mai Barci Tailet ya Shiga ko Ta kanta bai bi ba,Wanka yayi Ya Fito ya Saka kayan Barci ya Koma Gefenta chan Nesa ya kwanta ya juya mata Baya Jin Haka yasa Kukanta ya karu Na Bakinciki ganin Nazifi ya Juya mata Baya Shi ko Daman Ba Tun yau ba ya Daina neman wani abun Wajen sakina sai Dai in da Son Ranta.
Gajiya tayi da kukan ta Rarrafa ta isa Gareshi Ta Rumgumeshi Tana kuka yana jinta yasan Bukatartace ta kawota sai ya Shareta ganin bazata iya Jurewa ba yasa ta Faramai Salo Salo Wanda ya kasa Jurewa ya Juyo Gareta Shima ya Fara maida mata martanin Wasanninta Awannan Daran dai Sun Mori Juna Sosai Domin yayi mamakin Hadin kan da Sakina ta bashi Wanda Shi Rabon da ta bashi Irinshi Har ya manta.
********
*Bayan Wata Daya...*
Acikin Wata Dayan Daya Gabata zaku matukar mamaki in nace muku Soyayyah mai karfi Ta Shiga Tsakanin Abdullahi Da Barkat,wanda Daman ita Barkat din ita ta Fara Jan Tsanin Da Abdullahi ya Hau kai,Batare Daya sani ba ya jishi ya Fada Tarkon Soyayyar Barkat Cikin kankanin Lokaci ba Domin komai ba sai Domin Ta iya Salon kulawa da Namiji Da kuma Salon yadda Namiji zai Fada Tarkon Sonta Batare Daya sani ba.
Da Farko Abun nasu ya Fara da Kamar wasa ne sai kuma Abun ya zama na gaskiya Suna Chart kuma Suna Waya kuma suna Sharing Din mgana ta Text massages,In Abdullahi ya Shiga Makaranta Zai Nemata Suje Cafteria ko Libary su sha Hira sai Yammah Suke Rabuwa wani Lokacin ma sai Dare zai Taho Ta bashi Su Chaculate da Minti Tace ya kawo ma su Amira,In ya kawo musu Baya Cewa Inji Wance Ita kuma Hafsah Duk a Tunaninta Shi ke Siyowa ammh kuma ta Fuskanci Wasu Chanje Chanje Daga Abdullahi kamar na yawan Rike waya a ahannunsa Duk da Baya Waya da Barkat din sai ya Fita ammh Suna Chart ko Massages in yana Gida kana Yanzu Sai ya Kule kansa acikin Daki yana ta latsan Waya wani Lokacin Abincinsa baya ci sai Chan Dare Hafsah dai Har ta kare ta tambayeshi yace Bakomai Sai kawai ta kyaleshi ammh kuma idanuwanta na kanshi Domin Tafi kowa sanin Waye Abdullahi.
Abdullahi Abun yazomai a Bazata ne a Baya bashi da Niyyar kara Aure Domin yana ganin yana da Hidomomi,Sai dai Shigowar Barkat Rayuwarshi komai ya Sauya yaji yana da Sha"awar kara Aure nan kusa Duka Burinsa na Hafsah ta Haihu a Sabon Gida ya Rushe shi ya Fara tunanin in Barkat Zata amince Dashi zai gyara Dakin Dake kusa da na Hafsah ya ijiyeta kafin Komai ya kankama Zuwa Bayan Haihuwar Hafsah din yagama Komai sai su koma Gabadaya.
Hafsah Ta Fara zuwa Awo asibitin Tudun Wada awon Cikinta wanda ke Cikin Wata na bakwai yayinda Gefe Guda kuma Soyayyah Tana kara nuna Tsakanin Abdullahi da Barkat,Babu Wanda Abdullahi ya gayamawa sai Nazifi wanda Shima ya Bashi Shawaran Shi yana ganin bai kamata yayi Aure a irin wannan yanayin ba ammh Sai ya Nuna mai ba komai Zai Tuntubi Barkat din yaji in zata amince ta Fara zama awannan Gidan da Suke Ciki,in ta amince zai Ggyara Dakin dake kusa dana Hafsah ta Fara zama kafin ya kamallah Ginin Gidansa.
In zai yi Wayar Dare da Barkat din Falo yake Dawowa Saboda Hafsah yanzu Saurin Barci Gareta nan da nan Data kwanta sai Barci ya kwasheta,Yau ma Din Haka din ne ta kasance Tun 9pm ta kwanta Su Amira ma Abdullahi ya Kaisu Dakinsu ya kwantar Dasu,ya Dade a falo Suna Charting da Barkat din sai ya Nuna mata yana son zai yi mgana da