Author : Jamilaumar Category : Complete Novels
Duka Bikin Wata Biyu aka saka Dayake Nazifin yana da Gida Akaduna sai Abun yazomai da Sauki.
Farkon Auransu Nazifi ya zama Dan Gata kuma Abun kwatance Domin Sha Tara na arziki Mahaifin Sakina yayi mai ya Bashi Motar Hawa,da kuma Gida Lafiyayye anan garin kadunan ganin Haka yasa Nazifi ya kulle Gidansa Ya koma Gidan da Uban matarsa ya bashi Wanda Sai dai Abdullahi ya nunamai Rashin Dacewar haka ammh yaki ji Ransa na wajen Burinsa wanda baida Amfani.
Kayan abinci kuwa na kusan Shekara aka Cika musu Store kayan Aure kuwa Gida sai wanda yagani Saboda kyau da kawatuwa,Da Farko zamamsu ya Fara Cikin Soyayyah da kauna sai Daga Baya komai ya Chanza Zani,Domin Sakina dai Tafi karfin Nazifi ta Fara Nunamai Tana Bukatar Rayuwar yanci ne da kuma Sakewa,Domin Tana Takama Tana da komai Ubanta Nada kudi Ita kuma tana da Ilimi Farkon Samun mtsalansu Aikin Da Mahaifinta ya sama mata agidan Tibi na NTA Abuja bama Tare da an Tuntubi Nazifin ba,Wanda dama kafin Auransu da Sakinar sai da Alhaji Wada ya Kira sa yajamai kunni da kuma Fadan kan Gidan Dayaje ya Nemi Aure kamar sunfi karfinsa ammh ya Nuna Babu Abunda zai Faru Sakina na Sonshi akwai yaga karshen so Daya nuna Bazatayi aiki ba Babanta da kanshi ya Kirashi yamai wankan Tsarki ya kuma ce Dole Sakina tayi aiki Dama ai ya sani amfanin karatun nata tayi aiki Dashi ko kuwa in ta Zauna zai kare mata Lalurorinta ne Shima yana nema yadai Ci Zarafin sa Sosai Shida iyayensa Irin dai basu da komai Ranar Nazifi bai iya barci ba Saboda Bacin Rai ita kanta Sakinar bata Saurareshi ba Kano ta Tafi sai ta kwana uku ta Dawo bayan Tagama Duka Shiryen Shiryenta Har Gidan da zata Zauna achan Abujan ya kamallah Domin bazata Dinga Zuwa tana Dawowa ba Nazifi yana ji yana gani Sakina ta Fara aiki bada izininsa ba kuma in Tatafi sai tayi Sati Biyu bata zo kaduna ba in kuma tazo Bata wuce kwana uku ta koma Nazifi ya Shiga Damuwa Sosai ya Fara lalacewa,kuma ya kasa Iya Fadama kowa sai Abokinsa Abdullahi wanda kuma yace Allah ya kara Dama kowa ya Siyi Rariya yasan zata Zubda Ruwa.
Da Farko Sakina ta nuna ma Nazifi ya Dinga zuwa mata Abuja Weeked in ya samu Lokaci Domin Har ga Allah tana son Mijinta sai dai Rayuwarta da Goal dinta na Rayuwa na gaba da komai,Sai yaki ya Fara Fadan Ta Raina mai yawo,ita kuma sai ta kyaleshi Daga Baya ganin zai iya Fadawa Halaka yasa yake Kokarin Zuwa mata Weekend Duk Sati,Ganin haka sai Taji Dadi ta kara Sangarcewa in bashi yazo ba sai tayi wata bata Shigo Kaduna ba Tun Nazifi na Boyewa ma iyayensa Har Labari ya kai musu Inna Abu tace Allah kara Alhaji wada ne kadai yace Allah ya kyauta Domin koma miye ya Faru Nazifi shi ya Deboma kansa Ruwan Dafa kansa da kansa.
Wannan Dalilin ne yasa Ba Abdullahi kadai Nazifi kebama Shawaran ba"a Sakarma ma Mace ba Abokansu Dadama yana Fadama Haka masu karamin Tunanin Irin na Abdullahi sai su yarda da Batunsa Duba da ganin Irin yadda Rayuwar Nazifin ta Dawo Yana da mata kamar bashi dashi Shiyasa yanzu yama Daina Kwana akadunan kusan kullum yana Hanyar Zaria zuwa kaduna Bambamcin Shine kawai Auren ammh bawani Ci gaba,Abdullahi Nadaga Cikin abokan Nazifi makusantansa wadanda suke da Labarin Irin Abubuwan da suka Faru Dashi Shiyasa Daya bashi Wannam Shawaran bai yi wani Dogon Tunani ba ya yarda da Mganarsa Domin baya kaunar yayi Sakem da Mace zata maidashi wani Salallamame Ita da iyayenta ba gwara ya kame kawai Shima ya zama namiji Domin ya Tabbata bazai Taba yarda Hafsah tamai Irin Abunda Sakina Take ma Nazifi ba Shiyasa ya Sauya alaqan zaman nasu Kuma yake ganin Riba da Daidai kan Abunda yake mata Shine zai sa Ya zama Namiji acikin Gidansa mai iko kan komai.
*******
Acikin wannan Halin ne Hafsah ta samu Cikin Hajara wato Amira Ammh samuwar Cikinta sai ya Rage wani abun Tunda Abdullahi na son Hafsah Sosai kuma yana Tsausayinta Lokacin kuma Cikin yazo mata da laulayi Sosai Don har Asibiti ta kwanta,Tasha Lodojin Ruwa Lokacin har Umman Sadiq tazo Dubata itace Dataga Halin da Hafsah ke Ciki tama Abdullahi mgana kan Ya maida Hafsah gaban mahaifiyarta ta kula da Ita Bai so ba Domin ya nuna Rashin Amincewarsa ammh sai Umman Sadiq tafi karfinsa Dole ya amince Ammi ta Dauki Hafsah Zuwa Gida,Tana kula da Ita Nazifi bai sani ba sai Daga Baya ya Dinga Zuga Abdullahi da Cewa yayi kuskure Shikenan kuma Komai iyayentavzasu Juyashi Shi kuma Bashi da yadda zai yi Umarnin Umman Saddiq ne kuma Yana jin kunyar Ammi gaskiya bazai iya mgana ba Dole Nazifi ya sakamai ido Sai da Hafsah Tayi wajen Wata Biyu a Gida kana ta Dawo Gidanta Lokacin Taji Sauki Sosai tayi Kiba Cikin ya karbeta Tayi Bul Bul Ganin haka yasa Abdullahi ya lallaba yana ta amfana Da Ni"imarta Ba Fada sai dai Abunda Ba"a rasa ba.
Abdullahi yaso Hafsah baza ta Haihu a gidan Hayan da suke ba sai kuma Allah bai yarda ba anan ta Haifi Santaleliyar yarta mace mai kama da Ubanta da Uwarta sak,Asibitin Chika ta Haifeta ta kwana Washegari suka Dawo Gida Mamace ta kwana Dama da Ita,Tun Kafin Hafsah ta Haihu Dama ya gayamata bazata Wanka Gida ba,bayaso Shiyasa da Ammi ta Fara mganar Komawarta Gida Jego ta Cemata Abdullahi ya hana da Farko Ammi taso tamai mgana sai Alhaji Hamza ya Hanata yace ta Barshi ai Mijinta ne Shike da Hakki akanta Abunda ya yanke Shine Daidai Hajiya Hadiza ma Datazo Tana Fadan meyasa Hafsah bata Dawo Gida ba,Ammi ta Fadamata Dalili,jin haka yasa tace Ammi ta samo Wata ko Cikin yan'uwanta Taje ta zauna da Hafsah Din Tunda Mama ce ke ta Zirga Zirga Zuwa Safe da yammh Tana ma Hafsah wanka ita da Jinjiran Jin Haka yasa Ammi tama wata Matar Yayanta mgana wanda Dama yayan nata ya Dade da Rasuwa Asibi Ita ta je ta Zauna da Hafsah,ammh sai da Ammi ta Kira Abdullahi ta gayamai Shi kuma ya amince.
Anyi Shagalin Suna Cikin Farinciki da Annushuwa Raguna Biyu Abdullahi ya yanka yarinya yaci Sunan Umman Saddiq Hajara kenan,su Subai"atu ne kan Gaba kan komai Zanniratu ma tazo Daga kaduna da Kayan Barkanta,Umman Sadiq kuma Kishiyarta Da suke Kira Iyami ce tazo ita dasu Sadiq dasu Zahra,Hafsah tayi Goshi Domin Harta Sakinar Nazifi Tazo Sunan da yammah da Leda Cike da kaya Dayake Sakinar bata da laifi akwai da Sakin Fuska ba Ruwanta Bayan Aurensu da Abdullahi Sunje kaduna Sau Daya Lokacin sun sameta Tana Gida Itama tazo Sau Daya sai wannan Shine Zuwa na Biyu.
Duk nan suka kwana wasu kuma Gidan Mama suka koma suka kwana wasu kuma Wajen Ammi musamman ma yan"uwanta,Maijego tayi Goshi ita da yarta Hajarah wacce ake ma alkunya da Amira,Hafsah tacigaba da wankan Jegonta Cikin kulawa Da kuma Taimakon Asibi wacce ku kula dasu Ita da Amira a zaman Asibi Awajen Hafsah Bata koma ba sai da yabon Abdullahi da kyakyawan Hallayarsa acikin Bakinta,Domin ko Korafinsa ne yatashi baya yadda yayi shi Gaban wani ahalin Hafsh sai dai kaji kowa na Yabonshi Sosai ta koma da Kayan arziki da Abdullahi ya Hada mata Wanda Abun yayi ma Ammi Dadi Sosai Ta kuma Kara Godema Allah Data samu Suruki Irin Abdullahi.
Bayan Haihuwar Amira Haka zamansu ya Cigaba da zama Dai Kadahan kadahan Zuwa Lokacin Tuni Hafsah ta saba da Sabbin Halin Abdullahi tayi Tambayan Duniyan in Wani Laifi tayi mai ya gayamata yace bata mai komai ba Dole ta kawo Ido ta sakamai iyaka in ya Fara Fadansa ta Bashi Hakuri Taja Bakinta tayi Shuru wani Lokacin ko Suna Cikin Dadi Dashi sai ya samo Abunda zai Mata Fada akanshi Wanda ma bai kai yayi mgana ba Tun yana Damunta Har ya Daina ma Damunta Tunda ta lura Abdullahi ya Chanza ba kuma zai Daina Wannan Fadan nashi da Korafinsa ba.
Amira na da Wata Shidda Abdullahi ya kamallah Ginin Sabon Gidansa Dake Tukur Tukur Zaria suka koma akuma Lokacin ne ya siya Sabon mashinsa,wayyo kudina Sunyi Walima Sosai da Saukar al"qurani na Tarewa,Komawarsu Sabuwar anguwa tazo musu da Ssuye Sauyen Rayuwa Sosai Ciki harda Da karin Bunkasan Abdullahi ya samu karin Girma awajen aiki har ya Bude Shagon Provisio a kasuwar Tudun Wada Dake Zaria Auwal ke zama mai ashagon Shi da wani yaro Sani Auwal sai in ya Tashi Daga makaranta yake zama nan poli Shima yake Karatunsa kuma Abdullahi ne ke Dauke da Nauyinsu Shida Jidda da mariya.
Sai da Amira ta samu Shekara uku da Haihuwa kana Hafsah ta Haifi Usman wanda suke ma alkunya da Amir,Zuwa Lokacin kuma Babu Abunda ya Sauya zani,Sai ma ya karu Domin abaya Abdullahi baya Hanata Fita in Bukatar Hakan tataso ammh yanzu kai Tsaye zai ce bazata ba ko Ina ne kuwa,Gidan Mama kuwa in bashi yayi Ra"ayi ya Dauketa ba Ya kaita ba Bazai barta Taje ba Hakama Tudun Wada ammh Shifa yana zuwa akai akai Shi dasu Amira,Bangaren Nazifi da Sakina ma ba wani Chanji Gashi Har yanzu Haihu Shuru,Nazifin ya Fara Damuwa Domin yana Bala"in Son yaga kwansa a Duniya ammh Daya ma Sakina Mganar sai tace bata Shirya Haihuwa ba yanzu Sai nan Gaba Gabadaya Duk ya Rame ya Lalace wani Lokacin dama Burikanmu Suna iya Jefamu ga Halaka bamu sani ba.
Mariya da Jidda sun zama yanmata,Mariya Sch of Heatlh Takeyi nan Jama"atu Sch Of Health Kofar Kibo,Sai Jidda Dake Shekaran karshe a matakin Sendondry,Suma Dukkansu Suna Karkashin kulawar Abdullahi Domin Baya musu da wasa Musamman ma Jidda da Batajin Mganar kamar Sauran Abdullahi kadai Take Shakka.
Amira aka Fara sakawa a makaranta Kafin Amir ya Shekara Biyu a sakashi Suna Zuwa Tare,Da Farko Abdullahi ke Daukosu in sun Tashi Daga Baya kuma sai ya samar musu mai mashin nan kusa Dasu yana zuwa yana Daukosu Bayan Haihuwar Amir Sunje zamfara Shida Hafsah sukayi kwana uku Suka Dawo Lokacin kuma da Saddiq yayi Sauka ma Taje ta kwana Daya ta Dawo Tana zuwa in wani Abu ya Faru Hafsah Bata Da matsalan kowa game da Dangin Mijinta,Kowa na Girmamata baga Umman Saddiq ba,baga Mama ba,kowacce Tana ji da Ita haka kannen Mijinta baga Masu Auran ba baga yanmatan ba Kowa Anty Hafsah in Tana da matsala Guda Daya baya Wuce masifar Abdullahi da Korafinsa na Fama.
*****
Ganin yau sun Tashi Cikin Farinciki babu Yan masifan da Fadan a kusa yasa yana goge mashinsa dinsa Ta Rako su Amira da sukayi Shirin Makaranta ta kallesa Tana Fadin"Abban Amira Don Allah yau ka bar ni naje Gidan Subai"a na mata barka,Ta Kirani Jiya Tana ta Nuna Rashin Jin Dadinta kan Rashin Ganinmu Dagani har kai."
Dagowa yayi yana kallonta Lokaci Daya yana Ggyara zaman Tek tile din Gaban Rigansa kafin yace"Wato Nine bansan inda kaina ke min Ciwo ba ko..? Ita Don Ubanta Subai"an yaushe Rabonta Dana ga kafarta acikin Gidan nan Shine Domin bata da kunya Har Tana da Bakin mgana..! ?
Kan Hafsah na Kasa tace"Kai ma kasan Mahmud kulle fa garesa Abban Amira.."Taran Numfashinta yayi da Fadin"Oh Wato Shine ya san Ciwon kansa Bandani ya Hana Matarsa yawo acikin Gari sai ni gani Sakarai na barki kije ko..? Dariya ta kusa kama Hafsah ta Danne ta kafin tace"Kadai yi Hakuri naje din Abban Amira Tunda Harta Haihu Banje barka ba banje Suna ba..",Ido kawai ya sakar mata Ganin Haka yasa ta Lamgwabe kai Tana Fadin"Don Allah...Don Allah plz kar kace A"a.."Tafada Tana Sakarmai kyakyawan Idanuwanta wanda suka Taimaka wajen kashemai Jiki Karamin Tsaki ya saki kafin yace"Ki Shirya ki Tafi..ammh ban amince ki Kai mata yammah ba..Kowa ta zauna Gidan Mijinta.."
Dariya Ta kama Hafsah,Sai da Ta Murmusa kamata yayi Tana Dariya Da Sauri yace"Zan Sauya Ra"ayina yanzu matukar kina min wannan Dariyar taki.."Jin haka yaasa ta kame Bakinta kawai Tana kauda kai Kwandon abincin Amir ne a hannunta Amira na Rike da nata ta Rakasu Har Kofar Gida,Ya Dorasu kan Mashin Din Ita kuma ta mikama Amira kwandon Amir tana Fadin Allah ya Kiyaye Abdullahi ya kalleta yace"Basai kin Tsaya yin Girki ba..zan gayama mai mashin Dinsu in ya Daukosu ya kaisu Wajen mama..Ke kuma ki Dawo Da Wuri kibiya ki gaida mama in na Tashi aiki zan Biya na Daukoku mu Dawo Gida.."
Da Sauri Hafsah tace"Angama Ranka ya Dade...."Tafada tana mai Mirmishi Duk yadda yaso kar ya Nuna sai da ya Nuna Jin Dadinsa Kafin ya Kada kai kawai Yaja mashinsa Ita kuma Tana Binsu da Daga Hannu.
Gidan Ta maida ta kulle Cikin Farinciki yau dai Allah ya Dorata kam Abdullahi,Sama sama Ta karya da Tea da Bread da Soyayyan kwai,Tayi Sharan Daki Ta gyara ko"ina Sai ga Almajirinta yunusa yazo tace ya Zubamata Ruwa in yagama sai ya karya kana ya wanke mata kwanukan ita kuma ta Shiga wanka Koda ta Fito Har ma Yunusan ya gama yana Sharan Tsakar Gidan,agurguje ta Shirya Saboda Zumudi ta saka wani Sabon Less Dinta wanda Abdullahi ya Dinga mata Riga da Sikat,Babu Abunda zata ce ma Abdullahi sai Godiya Domin ko matar Wani Hamshakin mai kudi bata ta taba Nuna mata saka kaya ba Baya da Korin Iyalansa ta wannan Bangaren ita dasu Amira Duk wata sai ya Siya musu Sabbin kaya.
Leshin yada da kalan Marun ne ajikinsa Shiyaasa ta saka marun Din Hijabinta ta Dauki Jakarta mai kalan marun sai Takalminta wani mai Tudu sanin Halin mijinta yasa batayi kwalliya ba Hoda kadai tashafa sai kwalli,Sai Liptick,Wardrope Dinta ta Bude ta Dauki Daya Daga Cikin Atamfofin da Anty Hadiza ta kawo mata ta saka Cikin Leda wanda zata kaima Subai Tunda wannan karan Shi bai Siyama Subai"an komai ba,Batamai mgana ba gudun karya ce ma Tafasa Zuwan.
Kashe Wutar Duka Dakunan Tayi Kana Ta Rufe Kofar Bedroom dinta da Dakinsu Amira ta Fito,Yunusa Tagani yana Jiranta nan ta gayamai yatafi kawai anguwa zata tafi sai Dare zata Dawo Naira 100 ta bashi Tace ya Siya wani Abu da Rana yaci ya karba yamata Godiya ya Tafi Ita kuma Ta saka key ta kulle kitchen din,Ta Fito Ta kulle Gidan da makulli ta taka Zuwa Bakin titi nan ta samu Abun Hawan da zai kaita Har Bambamli inda Gidan Mijin Subai"a yake,Tana so ta bata mamaki ne Shiyasa bata ma Kirata ba Sai dai Ta Kira mama Tun Tana Gida ta Fadamata yau gidan Subai"a zata Wuni za"a kawo mata su Amira in an tasosu Daga makaranta Mama tace bakomai Dama suna da kaya nan gidan Maman Shiyasa ma Hafsah bata Daukan musu kaya ba.
Mai napep bai Direta ko"ina ba sai kofar Get din Gidan Subai"a,ta Sauko ta Biyashi Kudinsa ta isa ga get din ta Kwankwasa maigadin yana lekowa ya ganta ya Bude mata Kofa yana mata Maraba ta amsa Cikin Fara"a ta Shiga Haraban Gidan kenan suka Ci karo da Mijin Subai"a ya Fito zai Fita nan ta Tsaya Suna gaisawa Cikin mamaki yake Fadin"Anty Hafsah idanuwanki kenan ko..? Har Sweetheart ta gaji da korafin Rashin Zuwanki ta Hakura.."
Hafsah tace"Na wanke wannan Korafin gani yau Wuni zan muku.."Cikin fara"a yace"Masha Allah aikuwa mun gode yaya Abdullahi ya Mana kara Karisa Ciki zan Fita zuwa Gidanmu ammh bazan Jima ba zan Dawo.."Hafsah tamai addu"an Dawowa lafiya ya wuce ya Shiga Motarsa ita kuma ta Karisa Kofar da Zata Sadata da Cikin Falon Gidan.
*Anitha...*
4/9/21, 1:52 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*
*Wattpad:JamilaUmar351*
*Dedicated To:My Habibaty💞Aisha idris Abdullahi..!*
*005*
"Da sallama abakin Hafsah ta Shiga Babban Falon Gidan na Subai"a Dayake mijinta Dan Babban Gida ne kuma yana da aiki mai kyau Medical lap ya karanta Babban Ma"aikaci ne a asibitin Chika Dake samarun Zaria.
Babu Kowa afalon sai Jaririnta mai Suna Salim Dake kwance Bisa Kujera Cikin Towel yana ta Barcinsa Kusa Dashi Hafsah ta karisa Tana Fadin"Tsiyata da Qawata wauta yaushe zaki bar Karamin yaro Shi kadai Cikin Falo ke ki tafi naki Sabgar..? Ga Iska ko ta ko"ina nata Kadawa Cikin Falon.."
Tafada Lokaci Daya Tana karisawa ta kashe Fankar Falon ta kuma Dauki Rimot din A.C ta kashe kana ta Sauke Jakar Hannunta da Ledan ta zauna ta Sunkuci yaron Bisa Hannunta Tana kallonsa sai Sharan Barcinsa yake Hankali kwance yaci wasu kayan Sanyi masu kyau sai Tashin kamshi yake yi Yaron sak Babanshi ne Hasken Fatan Subai kadai ya Debo.
Bata Jima Zaune ba sai ga Subai Ta Fito Daga Cikin Bedroom Dinta Tana wani Taku Daidai da Waya a Hannunta mamaki ya sandarar da ita ganin Hafsah zaune Dauke da Salim Baki ta saki Tana kallonta tama kasa karisowa Dariya ta kama Hafsah ta Bude baki Tana Fadin"Rufe baki Kuna ki Karaso sakarya Uwa kawai.."Da Sauri Subai ta karisa Gareta ta Fada gefenta Ta Rumgumeta tana Fadin"Innalillahi kai Qawas kin Bani Mamaki ne sai na ganki kamar Daga sama Wlh.."...
Tafada Cikin Wani Farinciki Daya kasa Boyuwa acikin Ranta Hafsah Ta Saki Mirmishi kafin Tace"Mamakin dama nake so na Baki Shiyasa ban Hidi miki gani Tafe ba..Sai nazo na iske kin bar yaro shi kadai Cikin Falo kuma kin kure Fanka da A.C ko..? Jego kike yi ne Subai ko kuwa Danyan Iskancin Jego ko..?
Wata Dariya Subai ta saki kafin tace"Kaji yar rainin wayau..Wai ke Hafsah kemin Fadan Yara..?Don Kaniyarki Koda kika yi Aure na Haihu so banga me zaki Fadamin ba.."Tafada tana Dariyarta Harara Hafsah ta sakarmata kafin tace"Waya gayamiki bata Daganan Wlh..banga alaman kin san komai ba Tunda kika bar Jariri Dayan Haihuwa Shi kadai kuma kika sakarmai sanyi ba zaki sani ne in sanyi ya kamashi ke zaki Dinga jelan zuwa Asibiti Allah na Tuba bama Fata.."Subai tace"Naji Zan gyara Mu bar mganar..Allah laifin Honey ne shi fa na barmawa na Shiga wanka Kinga sai ya ijiyeshi nan ya Fice abunshi.."Hafsah tace"Mun hadu dashi da zan Shigo Har muka gaisa Shima yana tamin Tsiya ke Subai kiji Tsoron Allah kin gama Barbadini a Duniya ko..?
Wata Dariyan Iskanci Subai ta kara Saki kafin tace"Yo Uban wa yaja ma kansa..? In da kinzo ai bazakiji korafi na ba ballatana Honey yaji Wlh ya san baki zo ba Daga ke har shi Uban gayyar wanda baki san laifinsa Yaya Abdullahi.."Hafsah tace"Kya dai ji Dashi Malama Na dai wanke Duka laifin gani nazo yau nan zan Wuni