Advertisements
Chapter 19 Reading MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar BookTok Hausa Novels
Advertisements



Follow us on social media

Facebook Telegram TikTok WhatsApp X

MASIFAFFAN NAMIJI by Jamilaumar

Author :  Jamilaumar Category :  Complete Novels

Chapter   19 / 48

54K to 57K   out of 143.7K words

wai zata kaisu gidan Mama ga abokan wasansu su Muhsina ko Mahsana ne na manta."Yafada yana Hararan Subai"atu da Zannira kafin ya Cigaba da Fadin"Ga masu ya"yan nan.Daya nada Biyu Daya kuma wajen Hudu ba dole Mama Taki samun Hutu ba in banza ne Renon ya"yan su kai ma Uwayen mazajensu mana.."Nazifi yace"Allah sarki Raine yakai fa Mutumina..Ita kanta Maman Dadi take ji in ga ya'yan naku sun Cika gida.."

Abdullahi ya karkace kai yana Fadin"Ba wani nan...Badai a son Barinmun Uwata ta Huta kawai Shine Mgana.."Yafada yana Danna wayarsa Zannira ta kalli Subai"atu kafin suka Hada baki wajen gaishesu,Nazifi ya amsa Cikin Sakin Fuska lokaci Daya yana Tambayasu ya Hidima,da Allah sanya alheri,Abdullahi kuwa ko Dago kai baiyi ba Zannira ce tace"Ya Abdullahi gamu..Kace mu Fito Nida Subai kana jiranmu awaje.."


Cikim Iko yace"Eh ai na ganku.Sai da kuka gama Raina ma kanku Hankali kana zaku zo..? Yafada yana jefa musu wani kallo Subai ta yanko Rantsuwa tana Fadin"Yi hakuri Ya Abdullahi na tsaya bama Saleem Nono ne.."Kai kawai ya kada yana Fadin"Ko ma Saleema ne..wannan ke ya Shafa Na kiraku ne dama na Tambayeku menene amfanin Girmanku.? Dama baku da wani amfani bansani ba..? In yau bani awaje baku iya zama madadina amatsayinku na manya..?

Yafada yana sakarmusu ido,Cikin mamaki Zannira tace"Ikon Allah Duk me ya kawo wannan kuma Mijin Hafsatu..."Tafada Cikin Zolaya Harara ya makamata yana Fadin"Allah zan make ki naga alaman yarinyar nan kin Rainani Sa"anki ne ni..? Yafada yana nuna Kansa kai ta girgiza Tana Fadin"Wane ni da zama Sa"an Abdullahi Mijin Hafsah uba ga Amira da Amir Babban Yaya ga Zannira da Subai,Uba ga Mariya da Auwal harda Jidda wazai ce kai sa"ansa ne sai da ya Raina kansa.."Ta karishe fada tana Dariya,Ba Nazifi da Subai ba Hatta Abdullahi sai ya Murmusa yana Dariya ya kai mata Duka ta kauce Gimtse Fuska yayi yana Fadin"Yarinya kin gama Raina ni zanyi mganinki..Ammh kafin nam ina so ku Fadamin Tun ranar da kukazo samari nawa yarinyar nan Jidda ta gayyato nan garin..?


Zannira da Subai suka kalli Juna kafin Subai tace"Samari kuma Yaya..? ai Jidda bata gayyato kowa ba.."Abdullahi yace"wanda ta gayyato fa yau...yanzu nan ma muka gansu nan kofar gidan suna Zence.'Ido suka kwalalo atare kafin Zannira tace"A nan kofar gidan..? Wlh bamu sani ba Ya Abdullahi..".

Yace" Daman ina zaku sani Tunda kun zama manyan banza kusan Halinta Shiyasa na Hanata zuwa kuka matsa sai tazo meyasa Tunda kusanta data samu waje shikenam bazaku saka mata ido,Ku kabarta tana Abunda taga Dama...?"Subai tace"Wlh kajima mun Rantse Yaya bamu sani Su damam nan suka kwana wajen Amarya ita da Mariya da sauran kawaye mu kuma Gidan dake kusa da gidan Goggo muka kwana Sai dazu ne kafin Daurin muka zo,kuma muna fa tare da ita Sai dai Lokacin da akema Amarya Hoto ne Naga banganta ba, sai kila Lokacin ne ta samu sa"a ta Fice.."


Zannira ta kada baki tace"kai jidda bansan me take so ta zama bane yarinyar nan.."Abdullahi yace"iskanci mana..Kinga Dan iskan yaron ma Data gayyato..? Ni saboda Haushi Tunda Nazifi ya hanani Dukanta na koma Gefe..."Subai tace"Allah ya kyauta..ammh Abun nata sai gaba yake.."Abdullahi yace"Ku kyaleta tayi na karshe..In kun dawo Daga bikin zamu Tattauna Aura zanma shegiya taje chan ta karata.."Nazifi ya kalli Abdullahi yana Fadin"Aure..? zannira tace"Ina Bayanka Wlh..Auran take so in ba haka ba ba zata Dinga gayyatan kananan yara maza da sunan samarinta ba.."

Subai tace"aifa mganinta kenan Batajin mgana Ita ko Duba yanayin mariya bata yi..? Abdullahi yace"Ba irinsu Daya ba...Mariya bata da rawan kai ita kuwa Jidda kanta na Rawa da Iskanci..Ku kylenni da ita zan yi mganinta dama Mama ke Saka baki ina kyaleta ammah dis time around komai yazo karshe..Ku koma Cikin gida ku saka mata ido kawai Shine aikinku.."Zannira tace"Shikenan insha Allahu..Tasan Abunda tayi ba wamda ya kara ganinta kuma Tana cikin gidan ko.?


Nazifi yace"Eh tana ciki.Ni nace ta Shiga Ciki."Kwafa Subai tayi Abdullahi ya saka wayarsa Cikin aljihu yana Fadin"Mutumina mu wuce mun bar Baba yana Jiranmu..'Nazifi yace"Ok muje..."Zannira tace"Sai anjuma Allah kai ku lafiya.."Abdullahi yace Ameen Subai tama Zannira Rada a kunni Abdullahi na gani yace"Ke Subai kin bani da munafunci.."Dariya tayi tana Rufe baki,Zannira tace"Wai cewa tayi zaka tafi baka ga Hafsah ba..? Tayi kyau sosai Allah..."


Harara ya watsa musu yana wucewa yace"kilama Na riga ku gani kuna Haukan gulamku.."Yafada yana wani mirmishi Dariya Nazifi ya saka yana Fadin"Allah mutumina kodai ta Turo maka ta waya ne..? Abdullahi yace"Bansani ba Ina Ruwan mutum..? Kai in Sakina ta turo maka wani abu ina Tambayanka ne..?

Nazifi yace"Daga tambaya..? Yafada yana Dariya karamin Tsaki Yaja ya wuce ya barshi da su Zannira suna mai Dariya,Sallama suka karayi ya wuce agaban idonsu suka Shiga Mota suka wuce suna Daga musu Hannu,Kana suka koma Cikin Gida,Basu fadama kowa Abunda ya Faru sai aka bige da Hiran Hafsah yake son gani har Subai na Zolayanta da ashe ta Turama Abdullahi gayunta tace"Me za"a fasa..? Shifa ya siya kayan Dole kafin kowa ya gani shi ya fara gani.."Dariya suka kwashe mata Dashi.

Jidda basu kara ganinta ba sai da suka koma gidan Goggo Habiba lokacin da za"a tafi da amarya Subai ce ta jawota Dakin da suke suka mata Fada sosai Zannira harda dungurinta,kuka kawai Jidda keyi kuma suka ce Mariya ta sakamata ido in sunje gidan Amarya Tunda Malumfashi Za"a kai Amaryan yanzu nan,su kuma bazasu ba sai gobe,Nan Hafsah taji Kiran da Abdullahi yayi musu Harda da ita sukama Jiddan Fada,Bata da ta cewa Gashi kuma harda Inna Abu a yan kai Amarya da,Umman sadiq Zannira tace ga Jidda nan su saka mata ido haka suka Tafi Malunfashi Jidda nata bata rai.


Da daddare Hafsah ta Turama Abdullahi Hotunanta ta Chart,Ya gani ya Turo mata Sticker mai Love,Tare da Fadin"Wow....Das is my Wife..U look so good and Adorable...😍😍,Ammh i Miss u come back soon Wifey..!Sai ya Turamata Sticker kuka😥😥Ita kuma sai ta Turamai."Tanque MIJIN HAFSATU..HAFSATU ma tayi Kewar ABDULLAHINTA...!







*Shakira...*
4/9/21, 1:55 PM - 😂😂: *MASIFAFFAN NAMIJI..!*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janafty💞*

*Dedicated To:My Habibaty💞 Aisha Idris Abdullahi..*!


_Ina Kike Y'a guda Tamkar da Dubu....Diyar kwarai irin albarka Wato *RAHMA UMMU FAREESA..* Ladingota,Taho wannan Shafin na yau gabadaya mallakin kine Dota..Ke Ta Dambance awajen Janafty Ina Rokon Allah Ya Cigaba da Dafa miki acikin Rayuwarki Har Abada..Son kauna wanda baya karewa D'iyata..._




*019*




'"Cigaba da Charting sukayi Abdullahi na gayamata yadda yayi kewarta,Ita kuma tana Biye mai Tana mai Tabara da sangarta Ganin ta kunnoshi Da yawa yasa ta kashe Datan kawai ta sauka tana Sauke Numfashi.

Subai"atu Dake gefenta ta waigo Tana Kallonta Bayan itama Tagama Waya da Mahmud dinta Dayake suna katifa Daya ne a kasa matar gidan ta Shimfida musu,Makotan su Goggo Habiba ne,Ita kuma Zannira tana Bisa gado Ita da yarinyarta sai Jamila Diyar goggo Habiba da wasu baki Suna Dakin Uwargidan Dayake gidan Uwargida da Amarya ne,sakamakon Chan gidan Goggon Baki sunyi yawa Ba wajen kwana yasa Goggo tace Jamilarta Ta kaisu gidan Alhaji Isa din su kwana makotansu ne ana zaman Mutumci da karrama Juna.

Ganin Kallon Datake mata ne yasa Hafsah tace"Kallon fa..? Nanawa ne..? Subai tace"Ke zan Tambaya naga kingama Chart da Yayanmu kina ta Sauke Numfashi kodai kodai..?Cikin Sauri Hafsah tace"Kodai me..? Subai na Dariya tace"Kodai ana Bukatar Yayan Namu ne..? Wani Duka Hafsah ta Dakama Subai tana Fadin"Kefa yar iska ce. ? Mugun saka idonki yayi yawa kina waya da naki mijin ammh hankalin na wajena ko..? Sai na Fada masa Allah."

Subai na Dariya Tana Fadin"Yo yau naga ikon Allah Ina Laifina gani nayi kuna gama Mgana kin Hau Nurfafashi Dole na maganta.."Tafada tana kashema Hafsah ido Daya,Kafin Hafsah ta Bude Baki tayi mgana Wayarta ta Shiga kara Da Sauri Subai ta Saka Hannu ta Dauki Wayar ganin An Saka *HUBBY*❤️ yasa Tagane Abdullahi ne,Mirmishi ya kwace mata da Dariya tace Tana Kallon Hafsah.."Lalle Su ya Abdullahi manja...Ahe Hubby ne kuma.."Tsaki Hafsah tayi ta Fizge wayar Tana Fadin"Bai kai a kirasa da Hubbyn bane.? Ko me kika maidashi Yar rainin Hankali.."Ta karishe fada Tana Hararanta Dariya ta kama Subai tanayi Har tana kara kwanciya kan Katifar ita kuma Hafsah sai ta Juya mata baya ta Daga Kiran Kafin tayi mgana Taji Abdullahinta ya Saki kakkarfan Ajiyan zuciya Cikin Rudewa tace"Abban Amira me ya Faru..?

Shagwabemata yayi yana Fadin"Umh.Uhm bake bace..! Itama Cikin Tabaran tace mai"Ni kuma.?me nayi..? Ta fada tana wani karya wuya Kamar wata karamar yarinya,Baki kawai Subai ta saki Tana kallonta,Dagachan Bangaran Abdullahi yace"Ina ta Kiranki baki Daga ba...Zuciyata har ta Fara Zafi Hafsatuna.."Karya wuya Hafsah ta sake yi kafin tace"Afuwan Megidana..na dan Fita ne Shiyasa.."Cikin Kaguwa Abdullahi yace"Ina kika je kuma da wannan Daran..? Da sauri Tace"Ba fita nayi ba..Tsakar gida na Fita naje nayo Fitsari Kafin mu kwanta.."Ajiyar Zuciya ya Sauke yana Fadin"Kina ina ne..? Gidan goggo..?

Hafsah tace"A"a muna makotansu inda muka kwana Jiya..Chan ba wajen kwana Don ma yau an ragu wasu sun Bi amarya.."Abdullahi yace"Eh yanzu Muka gama waya da Umma take Fadamin ita da Inna Abu sun raka Amarya Malumfashi.."Hafsah tace"ai kam mu sai gobe zamu je mu ga Daki in Allah ya kaimu.."Yace Allah ya kaimu Plz Hafsatuna ki Dawo Goben Allah gidan yayi min Girma Ina jin kewarki Sosai.."

Hafsah tace"Insha Allahu ko bamu Dawo gobe ba Jibi Tun Safe muna Tafe.."Ba haka yaso ba Dayake Goggo Habiba ne sai yace"Ok Allah ya kaimu ina Yaran nan ne..? Subai da Zannira..?

Hafsah tace"Ga Subai nan Zannira kuma Tana Ciki mu muna Falo ne.."Baki ya Tabe yana Fadin"Sai da safe...Ki kularmin da kanki kinji ko..? Hafsah tace"Insha Allah..kaima haka.."Dagahaka suka yanke Kiran Sai ji kawai Hafsah tayi Subai ta Fado mata tana Fadin"Ke daman Haka ya Abdullahi ya iya Rage murya yana Shagwaba..? Ashe dai ba Masifa kadai ya iya ba.."

Hafsah tace"Allah zan gayamai kina mishi Labe in yana Waya da Matarsa.."Da Sauri Subai tace"Rufamin Asiri Don Allah..Kada ki kara jamin wani Fadan Bayan wanda dazu nasha.."Dariya ta kama Hafsah itama Subai din Tana Tayata Kwanciya suka gyara Lokaci Daya Suna Cigaba da Hira Cikin Hiran ne Hafsah ke tambayan Subai Labarin yayar Mijinta nan take Fadamata Tunda Ummi tazo ta bata Hakuri kuma tace zata jama Uwanin kunni Shikenan Daga Lokacin ko Haduwa sukayi Sai dai Harara Daga nesa Hafsah ta gyada kai tana Fadin hakan yafi Gwara kowa ya zauna iya matsayinsa,Suna Cikin Hirar ne Barci ya kama Hafsah ganin haka yasa Itama Subai din tayi addu"ar Barci ta kwanta.

Washegari Tun  wajen 10am na Safe su Hafsah da Zannira da Subai sai Jamila da wasu Jama"ar suka Tafi malumfashi,Wajen azahar suka isa Dama anyi Danki wasu kaya ne suka Tafi dashi na kitchen sai akwatunan amarya da Sauran Kayan amfani Sun iske Su Umman Sadiq sunyi wanka suna ma Ta Shirin dawowa ne,Nan suka Hadu suka kara gyaran gidan Amarya Bayan sun gama Manyan su Umman Sadiq da Wasu Daga Cikin Dangin Babanta suka mikata gidan Surukanta Dayake ba Nisa da Gidan Da yaron ya gina chan suka Barta Daganan Tashar Mota suka kara samu zuwa Danja,sai Dare suka iso Goggo Habiba sai Hamdala take tana kuma Fatan Yadda komai ya gamu Lafiya yasa Baki su koma Gida Lafiya.

Washegari Tun 11pm na safe yan Zaria suka taso wajen 1saura na Rana suka iso Gidan Mama suka yada Zango Daman nan ne Daba,Yara suna ma iyayensu oyoyo,Sun Sauka ba Dadewa Zannira Auwal ya Rakata Tasha tayi Tashan Golf zuwa Kaduna taso ta bari sai gobe ammh Mijinta ya Hana Dole ta koma aranar,subai da Hafsah ne suka kai Dare,Inna Abu kuma Suna Sauka ta karisa Gida.

Da daddare Bayan Abdullahi ya Taso Daga wajen aiki ya Biyo,akuma Lokacin ne yace Mama ya yanke Hukunci aure zai yi ma Jidda sai Lokacin ya gayamata Abunda ya Faru Ranar da sukaje Daurin Aure,Jin Haka yasa Mama ta goyi Bayansa Umman Sadiq ne kadai tace A"a kada ayi gaggawa abari ta ida karatunta,jidda na Jin haka ta Fara kuka tana bama Abdullahi Hakuri sai da aka kai Ruwa Rana da Taimakon Umman Sadiq ya yarda zai barta ta Zana WEAC DA NECO dinta wanda sun kusa Farawa ammh da Sharadin in ya kara ganinta da wani Saurayi batare da Wa'adin Daya Dibarmata ya Cika ba wlh ko Shawaran su Mama bazai Nema ba sai dai taji Ya bada ita Sadaka ga koma waye kuwa Jin haka yasa ta Tsorata sanin Halinsa kaifi Daya ne, in yayi mgana baya Chanzata kuma in yace Eh toh eh din ne Har Abada.

Subai ta Fara Tafiya Gida Mijinta yazo ya Dauketa ita da yara Hafsah kuwa sai wajen 11pm na Dare Abdullahi ya kwasheta ita da yara zuwa Gida,Duk da Ranar ta gaji gata gajiyan tafiya gata Zirga zirga ammh Abdullahi bai Daga mata kafa ba sai da ya nuna mata yadda yayi kewarta kamar yadda yake Fadi,Washegari kuma Goggo Habiba ta kira kowa tamai Bangajiyan Biki tace kuma Tana nan zuwa Tamusu Bangajiya Dama kuma sun zo da Sakon Su Cincin dasu Dubalim wanda tace abama Mama ta Rabama wanda ya dace.

******

*After 3 Month..*


"Zuwa Lokacin Dai haka Abubuwa sukayi ta Gudana Da Dadi ba Dadi,Bangaran Hafsah da Abdullahi kuwa komai yana Tafiya Daidai Kusan dai yanayin na Abdullahi Watarana Dadi Watarana kuma Madaci Dayake Hafsah Ta Riga ta gama Saninsa Bata Biyemai ta Riga ta san Halin mijinta Baya son Raini yana son abashi Girmansa Shiyasa ta zama mai Biyayyah da Sadda kai,komai Cikin Taka TsanTsan take bata kaunar Taga tayi Abunda zai batamai Rai Ballatana Har wani Fada ko karafinsa ya Shiga Tsakaninsu.

Bangaran Sakina kuwa da Nazifi Babu Chanji sai Abunda ma yayi Gaban Nazifi ya Riga ya gama Fita Sha"anin Sakina ya ijiyeta a onesite,Ya kama Harkan gabansa ,Mganar neman Auransa kuwa Tunda sukeje Gidan Salisu Engr,bai kara komawa wani waje ba,Bawai ya hakura Da karin Auren bane a'a yana so sai zuwa gaba in yaga wacce zata iya Rikesa Ba kamar sakina Datayi ma Rayuwarsa Rikon Sakainar kashi ba,Yana son in zai kara Aure yayi Shi Don Allah da kuma yarda sunnar Manzo ta tanadar Baya son ya kara Tafka irin kuskuran Daya Tafka a Baya.

Ganin Ginin Abdullahi nata Nisa yasa Shima Nazifin ya Fara Gina Filinsa na Gaskiya tare da Taimakon Shawaran Abdullahi Data Baba wada,Sai kuma sukayi Tunanin gwara su koma Masters dinsu,kafin abubuwa su sake yi musu yawa Abdullahi dama Tun Tuni ya Turama Office dinsu Takardan yana so ya karo karatu kuma An Riga anyi approving din Requesting nashi shi bai maida kai ba,ammh mganar Nazifi yasa ya maida kai kan Karatun Dukkansu atare suka yanke Shawaran zasuyi,Tunda Dama Shi karatun Masters ba kamar Digiri bane ba koda yaushe kake Shiga makaranta ba,Wani Lokacin ma sai kayi Sati baka Shiga ba, Tunda Daman ga ayyukansu da kuma iyalansu,Abdullahi ABU Zaria ya nema Shi kuma Nazifi sai ya nemi Kasu Kaduna State University kuma Cikin ikon Allah Dukkansu suka samu kowa kuma abangaran Daya karanta kafin kace me har sun kamallah Registration sun Fara Karatu.

Cikin wannan Lokacin ne Jidda tayi Candy dinta Sai jiran Sakamako,Yanzu Zuwa gidan Mama sama sama ne Abdullahi baya samun Wani Lokacin kansa gana office ga na makaranta Shiyasa Wani Lokacin sai ya kwana Biyu bai je gidan Mama ba in ma zai je a gurguje yake zuwa ya Fito Shi kanshi Nazifin Sai yayi Sati Biyu Zuwa Hudu bai Shigo Zaria ba,wani Lokacin sai yazo Duba gininsa,ko kuma yazo gaida su Baba wada,Dukkansu yanzu basu samun Lokacin kansu Ballatana na iyalansu gwara ma Abdullahi yana Bama Hafsah da Iyalansa Kulawa daidai gwargwado,Nazifi kuwa Bai Damu ba Sakina na Abuja sai tayi Sati uku bata Lekosa ba Shima bai damu ba yana ta karatunsa ya maida kansa Busy,In Sakinar bata zo ba,baya Damuwa kamar baya Ita kanta ta sani Domin ko Masters din Daya Dora bai Gayamata ba sai da tazo Tagani tayi mamaki Sosai ganin yanzu Nazifi ya Daina Damuwa da Lamarinta kamar baya Shi kuma ya maida kansa Busy ne saboda samun Saukin wasu abubuwan kuma ya samu Yanzu bai Cika Son Damuwa da wata Sakina ba Azumi yake Litini da alhamis,in tazo ta bashi ya karbi Hakkinsa in bata bashi ba baya Matsama kansa wajen nema,Ganin haka yasa Sakinar ta Fara Shiga Taitayinta ta kan dawo Bayan Sati Biyu ta kwana uku Zuwa Hudu kafin ta koma Ammh Duk da Haka Bata Dada Nazifi da kasa Da zuwanta da Rashin Zuwanta Duk Daya yake Daukansu saboda bata da kunya Har da Complain ta Faramai da Zargin Cewa ko ya Fara neman mata ne Ranar yayi Dariya kamar zai kwanta a kasa Abun ya Bashi mamaki bai iya ce mata Komai ba kawai ya Fita batunsa aransa kuma ya Jinjina Rashin kunyar Sakina yaTabbatar ma kansa Duk Iskancin Datakeyi Shine ya sakarmata Shiyasa ammh Daya Fahimci Fita Batunta Shine Matsala sai ya nuna mata Shi yama Fi son tayi Rayuwar Yancinta Domin Cikar Burinta ba Damuwa Tun Sakina na Mamakin Nazifi har ta Daina Har Bincike ta saka akayi mata ko yana Bin mata ne..? Ko kuma Aure zai kara ammh bata sameshi da Ko Daya ba sai tayi Tunanin Kila Shima ya Fara gane Abunda Ta Dade tana nuna mai ne.

****

Ana Cikin Hakane Sai ga Mahaifiyar Jidda ta Diro Nageria wato Hajiya Sa'adatu wacce ake Kira Hajiya Sa"a,Hajiya sa"a Irin matan nan masu son Abun Duniya da Budewar ido suna Rabuwa da Mahaifinsu Abdullahi ba yadda iyayanta basu yi ba da Kartaje Saudiya neman kudi ta Zauna Tayi auranta taki,dama kuma Mahaifinsu ya Rasu Sai mahaifiyarsu ne kadai ga kanwarta Lariya dama su Biyu Ta Haifa.

Wata kawarta ta mata Hanya tatafi Chan Saudiya wajen Shekara ashirin kenan Tun Bayan Data yaye Jidda,Tunda kuma tatafi bata Dawo ba Har Mahaifiyarsu ta rasu ammh Sa"a bata Zo ba,Har Akayi bikin Lariya bata zo ba,sai da ta Shekara wajen Biyar achan kana aka Fara Jin labarinta ayadda tace Zuwanta da Shekara Uku tayi Aure ta auri wani Balaraban data Fara mai aiki agidansa Matarsa ta rasu,Daga baya kuma sai ta Rika aiko da sakon kudi da kuma kaya ga Lariya tana Saidawa Dama asalinsu yan Zaria ne a anguwar Samarun zariya,Dayake kuma Basu da wasu Dangin Duk sun kare sauran kannem Mahaifiyarsu ne kuma sun Fita batunta Tunda sukace karta je Saudiya takaranci Taje suka Fita Sha"aninta,Sai Gidan Babansu wanda Duk sun

19 / 48